Showing 78001 words to 81000 words out of 153980 words
kuka na?Gyada masa kai tayi kamar tana gabansa" magana zakiyi"Eh"saboda me '"Dan naga zaiyi maka kyau ko muni zaiyi maka"yar Dariya yayi ya ce "Aiko har abada bazaki ga kukan nawa ba" Uhm idan kuma nagani fa kace me"Kasaitaccen murmushi ya saki ya ce "bama zaki gani ba Ai har abada " Banda dai cika baki idan kuma na gani fa saikaji kunya ko "Murmushi ya k'ara saki ya ce " Daga ranar da kikaga kuka na zan mallaka maki katafaran gida na dake Abuja Wanda nafiji dashi a Duka gidajena"Dariya da bata shirya ba Zarah ta fashe dashi Dukda Chuchu hankalinta bai kansu saida ta d'ago ta Kalleta bare Asmy dake gefenta "Cikin murmushi ta ce " Nikuma nayi maka alk'awarin insha Allahu sai naga kukanka"Okay haka kika ce kenan"uhm"murmushi ya saki ya ce "Ki rubuta ki Aje " Kaima ka rubuta ka aje"ta mayar masa "Naji yanzu dai ki biyo driver please" Wai me zanyi maka idan nazo"har zai mata Tsawa saikuma ya tuna Lallashinta yakeson yayi tazo cikin k'asa da murya ya ce "Ina son ganin ki ne" Uhm haka dai kace"Hakane ma ai "ki biyosa please" Zan duba ta fad'a "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " saikinzo Mamy "Murmushin da bata shirya saki ba ta saki jin ya kirata da sunan da idan ya kira ta ta rasa dalili takejin dad'in sunan Bayan ya katse wayar kallonta Chuchu tayi ta ce " dawa kike waya haka nasan dai ba hafiz bane "Murmushi Zarah tayi mata ta ce " idan fa shine"nasan ma ba shi bane saboda baki sakin jiki kina Hira dashi harda Dariya haka karfa wani ne yake kokarin kwacewa Hafiz da yayana da ba ama sashi a file ba fada "Dariya Zarah tayi ta ce " Baki da dama Daughter bari na shirya zan wuce gidan Aunty "Kallonta Chuchu tayi ta ce " Aunty kuma Kina nufin wannan Karin ma Chan zaki koma nidai wlh banaso "ta fad'a tana turo baki gaba" Dan murmushin dake lotsar da dimple dinta Zarah tayi ta ce "Zan dawo ai daughter Asmy dai tagumi tayi ta Lula duniyar tuni tasan wannan wayar da Zarah take yanda ta sakar masa jiki ko Hafiz bata waya dashi haka Dan tagane mai kiran kallo d'aya Zarah tayi mata taga yanda ta dirmiya a duniyar tunani saida ta sake wanka Kafin ta shirya ta sanya atamfarta mai blue da fari Riga da sicket sannan ta zunbula hijab d'inta blue har kasa batayi make up ba taji wayar ta sake ringing tsaki taja a ranta kafin ta daga tana turo baki ta ce " gani nan fa"tana gama fad'ar hakan ta katse Kallon Chuchu tayi ta ce "Sai nadawo" Okay to momcy a dawo lfy"Tashi Asmy tayi ta ce "Muje na rakaki" tare suka fita Kallon Zarah Asmy tayi ta ce "Naga yanzu kin saki jiki da mutumin nan please kar haka ya baki damar da zaki fad'a masa garinmu saboda ina gudun matsala wlh gabana sai fad'uwa yake ga Hafiz da ya kusa dawowa ga bikinki na k'aratowa Zarah banason Asamu matsala banason na zama silar bullowar wata matsalar" ganin yanda tayi sanyi ya sanya Zarah yin murmushi ta ce "Karki damu sis ba wata matsala da zata faru insha Allahu karki damu ai komai ya kusa zowa karshe" hakane har bakin motar Asmy ta rakata suna isa gidan a bude ta iske kofar palourn tana turo baki ta shiga da Sallama a bakinta cikin miskilanci ya amsa sallamar kasa_kasa k'arasa shiga palourn Zarah tayi cikin sanyi tare da samun guri ta zauna Dagowa yayi ya Kalleta yaga ta wani had'e rai kamar ba itace ta gama Dariya a waya ba kamar ba zai magana ba saikuma ya ce "Ba gaisuwa ko Mamy" Sai sannan ta d'ago ta Kallesa kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce "Ina yini" kasa_kasa "banaso tunda saida na roka " Turo baki gaba tayi tare da kauda kai "Ganin miskilanci takeji ya sanyashi kyaleta take away ya sanya aka yo musu kallo d'aya tayiwa abincin tace " na koshi"saboda me?ya tambayeta fuska ba wasa"banason cin abincin waje"Saina ina"Nafison na girka?ta bashi amsa kai tsaye "Okay kiyi hakuri ki daure kici yanzu kafin anjima za a kawo kayan amfani a kitchen din shiru tayi saikuma ta ce " na k'oshi banjin yunwa"Saikinci kinsan banason gardama "shiru tayi saida tayi minti kusan biyar kafin ta dauki take away din tana turo baki" a zuciyarshi ya ce "na lura yau wani miskilanci takeji Aiko gidan kikazo," Yinin ranar Zarah kin sake masa tayi tun Baidamu ba harya dawo kuma yana tunanin ko wani abun yayi mata Bayan magriba ya aika driver ya cika kitchen din da duk wani abun girki da za a buk'ata sannan ya cika fridge din kitchen din da kaji da su kayan miya Da sauran abubuwan da bazazu lalace ba a fridge Bayan isha suna zaune a palour Zarah na karanta alqur'ani cikin zuciyarta kallonta MD yayi yaga yanda ta maida hankalinta ga wayar har bata San yayi mata magana ba saida yaje ya amsa wayar kafin firrgit ta dawo hankalinta duba abunda take a wayar yayi yaga qur'ani ne take ciki mayar mata da wayar yayi tare da cewa Ki hadamun cope ki kaimun daki "Yana gama fad'ar haka yayi Hanyar d'akin saida ta gama surar da take kafin ta Aje wayar ta sata airplane cikin k'ank'anin lokaci ta hadamai had'adden tea Wanda yasha ganyayyaki Dan taga ganyayyakin hada tea a abubuwan da aka kawo Bayan ta gama a k'aramun cup ta zuba masa tare da nufa hanyar d'akin da yake saida tayi knoking ya bata umarnin shiga Zaune ta samesa laptop gabansa Dagashi sai kayan bacci a ranta ta ce " bashi da Aikin da ya wuce danna system "A sanyaye ta k'arasa d'akin tsaye tayi kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce " gashi"shiru yayi na d'an second kafin ya d'ago ya Kalleta yanda ta wani had'e rai ya ce "A garinku haka ake kawowa miji abinci" Turo baki gaba tayi tare da kauda kai"a ranta ta ce "wani sabon duniyancin kuma da kazo dashi" tsinkayar muryarsa tayi da cewa "Zoki Aje" Ya nuna mata center Table d'in dake gefenshi"Yunkurawa tayi ta Aje zata Mike da hannu d'aya ya Fard'o ta jikinsa wara idanu tayi saikuma ta fara kokarin tashi daga kanshi"a kunne ya rada mata "wannan shashan maganin da kike na meye" Bakomai fa"ta fad'a kamar zatayi kuka Kara janyota yayi jikinsa yace "Ko duk kewa ta ce da kikayi" turo baki tayi gaba ta ce "Allah kiyaye ni nayi kewar...bata k'arasa fad'ar abunda takeson fad'a ba ya had'e bakinsu waje daya.....washegari da shirin sch ta tashi a lokacin yana kwance idonshi lumshe yanajin wata irin nutsuwa da rabonshi da ita tun rabuwarsu ta k'arshe da Zarah itako tana gaban mirror tana shafa ta Cikin mirror din yake kallon yanda take shafa hoda cikin nutsuwa dimple dinta two side ya karema kallo yanda suka lotsa sai sannan ya k'ara karewa fuskarta kallo ba fara bace Chan ba haka ba baka ba irin skin d'inta ne ake kira da choculate colour saboda yanda fatar tata take luf_luf babu kurji ko kwarzano a fuskar kamar bata shiga rana hips d'inta ya dinga kallo da hijab din data sanya ta d'an lafe mata a jiki " zan tafi?muryarta ce ta dawo dashi daga duniyar tunanin d'aya Lula "Nawa zaku fito lectures" 4pm"ta basa amsa"Okay 4:30 driver zaizo "shiru tayi " Bata basa amsa ba dan harga Allah basan kwana gidannan take ba "10k ya kirgo ya mik'o mata " Kin amsa tayi "hade fuska yayi yace " kinsan dai bansan musu"a sanyaye tace "akwai kudi a hannu na shiyasa " To wannan din nake son ki amsa "ya fad'a fuskarsa ba wasa" badan taso ba tasa hannu ta amsa ta ce "Nagode" tana gama fad'ar haka ta fita tana turo baki...tun daga ranar nan kullum Zarah anan gidan take kwana Saboda driver ke kaita sch ya maido ta MD ko koda yaushe yana gida Ba Inda yake zuwa daka Kallesa zakasan yana samun kulawa saboda har wani kib'a yayi fatar nan tasa ta k'ara fresh saboda yana samun abunda yakeson tako wani bangare ga wani time d'in idan ya sanya Zarah tayi masa girki tanayi saboda yanzu ya rage mata rainin wayau da yake da yanzu har sukan zauna su danyi Hira bangare guda kuma yanayin waya da Matar sa kullum dukda taga number nigeria bata fahimta ba saboda tasan wani lokacin idan yaje kasashe akwai abunda yake kashe kudi yayi number sa ta Nigeria tayi aiki Bayan two weeks Zarah ta tafi sch saboda saurin da take ta mance wayarta a d'akin MD na kwance yaji ringing d'in waya a jaka sai sannan ya lura da jakar wacece kyalewa yayi nan wayar tayi ta ringing ganin ringing d'in ya damesa ya sanyasa janyo jakar Dan ya d'auki wayar ya kashe gaba d'aya yana zage jakar yana fiddo wayar yaga an rubuta ya Hafiz a jiki tsaki yaja tare da kashe wayar gaba d'aya yazo zai maida kenan ya Hango magunguna a ciki kamar bazai d'auka ba saikuma ya d'auko guda ansha Rabi saura Rabi kenan duba maganin ya shigayi Inda ya shiga karantawa sosai yayi mamakin Ganin maganin hana d'aukar cikine d'auko sauran biyu yayi yaga duk irinsune "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un" ya fad'a a ransa a fili ya ce "watau aikin banza muke yarinyar nan ta fimu wayau duk plane d'in da muke wata da watanni ashe da abunda take sha no wonder ace har wata Bakwai saura wata biyu karewar yarjejeniyarmu ace bata samu ciki ba ," sosai yashiga jujjuya magungunan yanajin ba dadi a ransa ya ce "Yanzu ya zanyi lokaci na kurewa" Wani shiri ne ya fad'o masa a rai Tabbas dole yayi mata plane d'in da zata daina shan maganin nan saboda ko ba Dan sabodashi ba nan gaba zai iya yi mata illa ya lalata mata mahaifa tunda ba tab'a haihuwa tayi ba "Bayan Zara ta dawo daga lectures lokacin md baya gidan ya d'an lek'a gidan gonarsa dake garin Kai tsaye Zarah wayarta data manta ta nufa tayi mamakin ganinta kashe Dan bazata manta ba bata kashe ta barta ba saikuma tayi tunanin kukan ta tafi ta kashe din tana dubawa taga missed call d'in ya hafiz kiransa tayi Bayan ya kira suka sha y'ar Hira kafin ya k'ara jaddada mata da dawowarsa saura wata guda dukda gaban Zarah Saida ya fad'i amma hakan bai hanata nuna masa tana farinciki da hakan ba " Bayan sun katse duba wani missed call d'in tayi taga na Aunty Halima ce "Itama kiranta tayi Bayan sun gaisa tace " Amarya k'in bace ba ajinki kin yada auntyn naki"Murmushi d'auke da fuskar Zarah ta ce "ba haka bane Aunty kinsan koda yaushe kina raina" Murmushi tayi ta ce "Haba dai ai ni da kike raina aina nemiki turomun address din gidanki gobe insha Aah zankawo maki ziyara tunda ke baki zumunci" Gaban zarah saida ya fad'i Hakanan ta fusge ta ce "Kai amma Aunty Dana ji dadi zanturo maki ta message yanzu" Bayan sunyi bankwana gaban Zarah ya shiga fad'uwa ta ce "Ya zanyi da Matar nan Innalillahi" gashi bama tasan address din gidan ba fita Tai Inda ta tambayi mai gadi ya fad'a mata address din da lambar gidan nan taturawa Dr Halima text d'in address din gidan gabanta ta na fad'uwa sai Bayan magriba MD ya dawo "Kallonta yayi yaga kamar akwai abunda ke damunta cewa yayi lafiya dai ko?a sanyaye tace " Lafiya qalau Sannu"ywwa ko duk gajiyar sch din ce "murmushi ta kirkira ta ce " Wlh ko sai a slow level 4 d'innan ba sauki"Yana zauniya ya ce "Hakane daman kinsan aski idan yazo gaban goshi yafi zafi Allah sa dai a gama lafiya" Ameeeen ya Allah ngd "Wani course kike" Mass com "Wow " ya fad'a tare da Jinjina mata hannu ya ce "na Sara maki" dan murmushi tayi ta ce "Ko" Eh,mana"Tunowa yayi ba course d'insu d'aya da Chuchu ba a ranshi ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Nasanma bata Santa ba Tunda ba course d'insu d'aya ba " Wayarsa da yasa alarm kafin ya shigo tayi ringing dubawa yayi ya katse k'aran tare da karawa a kunnansa kamar mai yin waya ya ce "Hello Ya mai jikin" shiru yayi kafin ya ce "Subhanallahi kenan abun hartayi worse haka Gaskiya Aisha bata da hankali haukan me take taje tayi da shan maganin hana d'aukar ciki ai yanxu gashinan ya juyar mata da mahaifa tayiwa Allah shishigi ya gwada mata ikonsa yanxu gashinan ta rasa haihuwar ma gabak'i d'aya garin shirme a Gaskiya banjiye maka dadi ba aboki Allah ya kiyaye gaba" shiru yayi na d'an dakiku Alamun kamar yana sauraran bayani daga wayar sai kuma ya ce "Ah to da gaskiyarka kam gwara kayi Aurenka tunda ita ta sayawa kanta Allah ya kyauta ita kuma ya bata lafiya" Tunda ya fara wayar hankalin Zarah ke kan abunda yake cewa kasancewar da karfi karfi yake maganar sosai gabanta ya fad'i fahimtar abunda suke cewa da tayi a ranta ta ce "Na shiga ukku karfa na illata kaina" tanajin saida ya gama wayar kamar bazatayi magana ba Dan Duk ta rude saikuma tayi k'arfin hali ta ce "Dan Allah na tambayeka" Inajinki"Wannan Wanda kuke waya dashi kamar na lura matarsa ce keshan maganin planning ne yayi mata illa ko"a ranshi ya ce "Alhamdulilla anzo wajen a fili kuma cewa yayi"eh ya akayi " shiru tayi saikuma ta ce "Bakomai amma ta jima tana sha har yayi mata illa haka?Girgiza kai yayi ya ce " a a a ko shekara ba ayi ba tana shan gashi sabon Aure ne sukayi Yanzu yayi mata illa har an cire mata mahaifa"Sosai ta firgita ta kasa control d'in kanta cikin firgici ta ce "Innalillahi yanzu kenan shikenan bazata sake haihuwa ba Amma ba kowanne maganin yake illa ba ko?...........βπΏ
*Yau dai nasan ba korafin readmore yayi Kad'an*πππ
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. π―ββοΈπππ*
1, *MU GANI A ΖASA...*π₯
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ΖWAI..*π₯
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*π₯
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*π
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*π©ββ€οΈβπ¨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huΙu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda Ιaya N300
*DOMIN TURA KUΖIN KAI TSAYE*π
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biyaπ
0810 433 5144
Masu tura katin MTNπ
0814 179 9224
Ζ³an Ζasar Niger zasu tura nasu anan.π
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huΙu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda Ιaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* π₯π₯π₯ππ©ββ€οΈβπ¨
_*Miss Hajo Ce*_π€πΏ
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: π
ΏοΈ.........*59 & 60*
"Mafi yawaicin su suna yiwa mata illa wajen lalata mahaifarsu musamman idan ba ta kan ka'ida akayi amfani da su ba dukda ni ba likita bane amma nasan da hakan suna da illa sosai musamman ga Wanda basu tab'a haihuwa ba Suka fara da shansu yana juyar musu da mahaifa sosai" wata uwar zufa ce ta karyowa Zarah "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un " kawai take maimaitawa a cikin zuciyarta "Lura da hakan ya sanya MD cewa " Yadai naga kin firgice lafiya"Daidaita nutsuwarta ta so yi amma ta kasa Mikewa tayi ta ce "Lafiya" Tana barin palourn ya saki kasaitaccen murmushi na alamar cin nasara kenan "Zarah ko na shiga wata zufar ta k'ara karyo mata ta ce " na shiga ukku kar naje na lalata mahaifata da kaina Bayan babu burin da nake dashi a rayuwa sama da ganin jini na nima na zama Uwa"sosai ta fara zirga zirga duk ta rude janyo wayarta tayi tare da kiran Dr Halima koda ta kira kashe taji magungunan ta fiddo tare da sanya su a a toilet tayi floshing da ruwa washegari da Yamma MD na bedroom dinsa yana ayyuka a laptop yayinda Zarah na palour har lokacin a firgicin tsoron abunda ya faru da Matar nan da Md ya fad'a mata take wayarta ce tayi ringing dubawa tayi taga Aunty Halima Ajiyar zuciya ta sauke Bayan ta d'auka Nan take shaida mata suna kofar gida mai gadi ya hanata shigowa yace saida izinin masu gidan "ina zuwa" Zarah ta bata amsa tare da yafa beil ta fito bayani tayiwa mai gadin akan bakuwarta ce kafin ya bari su shigo sosai Zarah ta nunawa dr Halima.jin dad'in zuwanta Inda tayi welcoming d'inta sosai a basaja nan tagabatar mata da lafiyayyen abincin da ta girka na musamman Dak'yal ta samu ta d'an tsakura Kad'an lura da Zarah kamar bata cikin nutsuwa ya sanya Dr Halima daddabarta ta ce "Yadai kanwata lafiyarki qlau kuwa?saurin kirkirar murmushi Zarah tayi ta ce " lfyqlau Aunty "hmm kawai dr Halima tace Bayan few minutes Zarah ta kasa shiru Dagowa tayi ta kalli Dr Halima ta ce " Aunty wai Dan Allah da gaske maganin hana d'aukar cikin nan yana lalata mahaifa kuwa?saboda me kikamun wannan tambayar"shiru tayi saikuma ta dago ta ce "Naji labarin wata da yayi mata illa shiyasa" shiru Dr Halima tayi tasan dai Wanda ta rubuta mata bashi da wani side effects amma tasan yanda zatayi ta tsoratata Dan itama Bason shan da take take ba Dagowa tayi ta ce "bazanyi miki karya ba kanwata yawaicinsu suna da illa kuma suna lalata mahaifa sosai da zan baki shawara ko wannan din Dana rubuta maki ki daina amfani dashi zai iya baki matsala dukda bama fatan haka"sosai Zarah ta k'ara shiga tashin hankali a ranta ta ce " na bani Ni Fatima Wannan mutumin duk shi yake neman zakamun masifa da bamuyi *Auren wata Tara"nan ba da komai bai faru ba "Dak'yal ta iya daidaita nutsuwarta a sanyaye suka yi Hira da Dr Halima hartayi mata bankwana ta fita Inda ta Zarah tayi ta wurga ido ta rasa abunda zata bata gashi ta mik'e tana shirin fita" Mamy"ta tsinkayi muryarsa daga daki"Kallon Dr Halima tayi ta ce "yi hakuri Dan Allah Aunty naji yana kirana" Ohh waida duk zaman nan da nayi mijinki na nan ikon Allah