Showing 60001 words to 63000 words out of 153980 words
Cikin glass din da aka Zage yake kallonta saurin barin Kallonshi tayi saboda gabanta dake fad'uwa gashi ta kasa gaba ta kasa baya Asmy ma kallonsu ta tsayayi tana son ta tuno Inda tasan fuskar cikin Sauri ta tuno Tabbas shine Mustapha mijin Zarah na *AUREN WATA TARA* "jaber ne ya fito da fara arsa ya ce " manya ne a gari yau kenan Me kukazoyi Asmy "ba tare da kallesaba Dan tun sanda Sukayi cheche kuce din wannan a waya tayi block dinsa ta ce"wani gida ne muka je nan Ciki "ina zaku yanzu?Zaria " ta fad'a "Okay ku shigo " mu tafi naga magriba ta wuce sannan samun hawa a unguwar nan Abu ne mai wahala "cikin Sauri Zarah ta ce " a a zamu koma da Kanmu" ranki ya dad'e kiyi hakuri ku shigo mu mikaku ko garrage ne"ya fad'a da sigar zolaya "Tana kauda kai Zarah ta ce " mungode amma zamu koma da kanmu" "zungurarta Asmy tayi tare da Hararar ta kasa kasa ta ce " ke wai baki da hankali ne duk wuyar da muka sha Munsamu sauki zaki wani ce a a to wlh Saidai na tafi na barki anan amma na gaji"harararta Zarah tayi "MD ne da ya gaji da tsayuwa ya ce " wai tsayuwar me keke Malam ka tsaidamu in basusan a taimakesu ka rabu da su man ha a ka tsaida mutane a titi"Dagowa Zarah tayi ta Kalleshi daidai Shima ita d'in yake kallo cike da takaicin da jin haushi ta hararesa tare da murguda baki taja tsaki tare da Yin gaba abunta ta ce "Ke kuma da baki da zuciya saiki shiga a wulakantaki"Sosai Asmy tayi mamakin Zarah Bayan wuyar da suka sha sannan ma ina ta sani a Kaduna ga duhu ys fara za a taimakesu ta tsaya shine zata k'iya jaber ne ya ce " Rabu da ita ki shigo muje "girgiza kai tayi ta ce " kawai kuje bazan tafi na barta ba "MD ne daga mota ya sauko ya ce " Ki shiga kuje "da mamaki jaber ya ce Kaikuma fa " Hararar da yayi masa ne ya kusa sanyashi Dariya Itama Asmyn saida ta kusa dariyar shiga tayi Ita da jaber Inda suka Tada mota Suka bar wajen shi kuma ya bita da harta fara nisa ya ce "Mamy" Banza tayi masa tanajin haushin disgin da yayi musu "Mamy " ya k'ara maimaitawa "bata waiwayoba haka baisa ran amsa ba " Cikin Sauri yabi bayanta Taku baiyi biyar ba ya cimmata Tare da shan gabanta wani irin Kallo tayi masa sai kuma ta kauda kai tana turo baki "Ta ce " ka bani hanya zan wuce "tsaki yaja tare da cewa " Ke wace iri ce Wai ina zaki da magribar nan angaya maki kd Zaria ce da zaki tafi ke d'aya da dare a kasa Ke uwar y'an Zuciya "turo baki tayi tare da cewa " to ina ruwanka Inma.me zai sameni...bata k'arasa fad'a ba sakamakon murde mata baki da yayi cike da mugunta saida ta saki Kara kafin ya saki ya ce "Ni sa'anki ne da kika rainani ko wace magana kike fad'amun ko Dan Kinga ina d'an sake miki fuska an gaya maki ko wace magana ake fad'amun stupid kawai" durkushewa a wajen Zarah tayi batasan lokacin da wani kuka Yazo mata ba Dan sosai taji zafin murde mata bakin da yayi "sosai kukan nata ya bawa MD Haushi ya rasa wace irin yarinya ce wannan Ganin tana shirin Mikewa tabar wajen ya sanyashi saurin ruko hannunta kokarin fusgewa ta fara ya rik'e gam ganin tana wasting time nasa ya sanyashi rungumota gam a k'irjinshi a tare suka sauke nauyayyar Ajiyar zuciya Zarah ko shiru tayi sai Lafewa da tayi tana shak'ar daddad'an k'amshin turarenshi mai sanyaya zuciya Wayarshi ya lalubo tare da dannawa wata number kira ringing biyu aka daga wayar yayiwa Wanda ya kira bayanin Inda yake Ba ayi minti biyar ba saiga lafceciyar mota fake a wajen An fito an bud'e masa back seat tare ya shiga da ita dukda turjewar da ta fara suna shiga Driver yayiwa motar key suka bar wajen Hade kanta da guiwa tayi ta fara kuka na babu gaira babu dalili tsaki yaja a ranshi ya ce " sudai mata matsala ce wlh ita wannan matsalar tata ma tafi ta kowa mtwss"jin kukan ya fara damunshi ya sanyashi saurin janyota Jikinshi tare matseta tsam kamar zai maida ita ciki gidanshi dake nan g r a ya umarta driver da ya kaisu Bayan sun isa har lokacin shashekar Zarah take jin an tsaida motar ya sanyata saurin Dagowa Kallon wajen tayi daga mota kafin ta kalli MD da a ka bud'e masa yake shirin fita saurin ruko hannunshi tayi ta ce "Ina ne ka kawoni nan kuma" ba tare da ya Kalleta ba ya ce sayar dake nazoyi dukda Zarah tasan wasa yake mata bai hanata tsorata ba marairaicewa tayi ta ce "Dan Allah kayi hakuri ka maidani Makaranta Dare nayi " Banza yayi mata ganin ya fita Ya sanyata saurin fita itama ta bishi baya tana karewa katafaran gidan Kallo Aljannar duniya kenan"ta fad'a cikin ranta binshi ta dingayi cikin Sauri duk Inda ya nufa Dan taji akwai karnika a gidan kuma ita daman ba abunda ta tsana sama da k'are ganin yayi mata nisa ga haushin Karen dake tunkarowa ya sanyata saurin Rugawa a guje Aiko nan Karen ya biyota Dan tayi gudu daukarsa bata Gaskiya ihu Zarah ta fasa tare da rugawa taje ta kankame MD tsam ta fashe da kuka tana yarfe hannu ta gama rikicewa daidai lokacin da Karen ya Iso Inda suke yana haushi murmushi MD yayi ya ce "matsoraciya a ransa common kare ya firgita ta Cikin kuka ta ce " Dan Allah ya Musty ka taimakamun kar Karen nan ya cijeni wlh tsoronsa nake please mubar gidan nan Dan Allah "ta fad'a ta na k'ara kankamesa " Shafa bayanta yayi yana Daddab'a cikin sigar lallashi batare da yace mata uffan ba shafa kan Karen yayi Tare da ce masa yabar wajen Lokaci guda Karen yabar wajen Ajiyar zuciya Zarah ta sauke Dan Allah kadai yasan irin yanda zuciyarta ke Bugawa saboda tsoro "matsoraciya saiki sakeni tunda na kori Karen kuma daga yau Kika karayimun musu ko na fad'a magana kika maida ga da abunda zan hadaki ina da ire_irensu sunfi goma" cike da kunya ta zame jikinta daga nashi turo baki tayi Jin Abunda ya ce "wara idanu yayi tare da nuna kanshi da yatsa ya ce " ni kikewa"cikin shagwabar da ta zame mata jiki duk sanda tazo mata ta ce "Nifa ba da kai nake ba " ta k'arasa fad'a hawaye na sauka daga idanunta "Had'iye kukan ya fad'a yana kama hannunta " kamar an d'auke nefa haka ta Had'iye kukan shi kanshi har Dariya taso ta bashi ya fusge "harsuka isa katafaran palourn gaban Zarah na fad'uwa saida ta kusa kauyanci cin karo da hadaddun turkey furnitures d'in da suke shake a palourn komai na palourn y'an waje ne bazaka tab'a cewa a Nigeria kake ba "a rakube ta zauna d'aya daga cikin kujerun palourn tana ta kalle_kalle a wayance Wanda bazaka tab'a cewa tanayi ba a ranta ta ce " Wasu na cikin wahala wasu bama susan anayi ba jifa Dan Allah wannan lafcecen gida da kayan cikinsa kamar baza a mutu ba "zaki iya tashi kije kiyi salla kafin na dawo ga bedroom Chan" ta tsinkayi muryarshi data dawo da ita daga duniyar tunanin da ta Lula Firgit ta Kalleshi kamar mai shirin fashewa da kuka ta ce "Amma kuma ni kad'ai zaka bari a gidan nan ni tsoro nakeji wlh karnikan nan karsu shigo Su cinyeni ni kadai" murmushin da baikai fuska ba yayi ya ce "bazan jima ba zandawo babu abunda zasu maki bazasu shigo nan ba " Badan taso ba ta ce "To Amma karka jima Dan Allah " Ba tare da ya amsa ta ba yayi Hanyar waje tanajin fitarshi ta turo baki tare bin kofar da harara ta ce "Mugu Allah saiya sakamun ta fad'a tana nufar d'akin da ya nuna mata Dan tayi salla Nanma saida tayi kauyanci cin karo da kayan alatun dake dakin ga gaban mirror din dake shake da kayan shafa irir_iri tab'e baki tayi cikin Sauri ta shiga toilet tayi alwala ta fito Bayan ta tada salla cikin Sauri ta bar d'akin Dan ji take a tsorace take palourn ta dawo ta zauna Kan kujera tare da Yin tagumi sai Bayan isha i Taji tsayuwar mota lek'awa tayi ta window taga shine cikin Sauri ta koma ta zauna harya shigo Mikewa tayi ta ce " yawwa nazo mu tafi ya Musty?Batare da ya Kalleta ba ya ce "Sai gobe " yana gama fad'ar haka ya Aje take away din da ya shigo dashi tare da Yin hanyar dayan bedroom d'in da Kallo ta bishi har ya wuce Tana turo baki ta daga wayata da Asmy ke kira daga bangaren Asmy ta ce "Wai kina ina harna dawo tun d'azu " Ina kd "ta fad'a kasa kasa" Kd kuma to me ya zaunar dake "Ya ce sai gobe " ta fad'a tana shirin fashewa da kuka "Daga bangaren Asmy tayi Dariya " Au cewa zakiyi Amarci za a sha keda Angon naki"Dogon tsaki Zarah taja cike da jin Haushi ta ce "Banza y'ar iska Allah kiyaye wannan ya zama mijina " kit ta kashe wayar tana Jan tsuka Daren ranar dai taga MD baida shirin maida ita gashi tunda ya shiga bai fito ba Bayan tayi Sallar isha I a palourn bacci ya kwasheta cike da gajiya gararanbar da suka sha A waje MD ko daman tuni yayi bacci Dan yau akwai gajiya a tare dashi Dan dawowarshi metting kenan daga Abuja suka had'u dasu Zarah washegari Around 10 Zarah ta shirya tana palour Tana jiran fitowarshi ya fito ya maida ita Cikin tsadaddan shaddarsa ya fito yasha shiga ta alfarma ta manyan mutane kallo d'aya Zarah tayi masa tayi saurin k'asa da kanta saboda gabanta dake fad'uwa sosai taga yayi wani irin masifar kyau a sanyaye ta ce "Ina kwana" muntashi lafiya ya fad'a yana karasowa palourn "Tare da cewa " Kinyi break fast ko?gyada mishi kai tayi "eh " Okay to muje a saukeki "Cikin farinciki Zarah ta d'ago ta ce " Thnks "Dan tayi mamaki dazai maida ita cikin Sauri saikuma ta ce " Naga bakayi break ba fa"Eh bana ra'ayi ya fad'a "Dan azumi yake tab'e baki Zarah tayi tare da mik'ewa ta ce " kai ka sani miskili kawai" a tare suka jera suka fito gwanin sha'awa kamar wasu masoya Dan sosai naga matching d'insu Shigowar Mota ya sanyasu tsayawa bin motar MD yayi da Kallo harta karaso parking space d'in yana kallon motar Kafin yaga fitowar Amera cikin shigar da ta saba ta K'ananan kaya driver yana rik'e da Akwatinta shock a wajen Amera tayi ganin mijinta sun fito tare da wata daga cikin gidan lokaci guda idonta ya rufe wani azababben kishi ya taso mata dak'yal ta iya daidaita numfashinta dake sartse mata cikin bala'i da masifa ta tunkaro Inda suke Wanda har lokacin suma kallonta suke musamman MD da yayi mamakin zuwanta Zarah ko tuni cikinta ya Dori ruwa Ganin yanda take tunkarosu " Tsaye Amera tayi tare da daure k'aramun beil din da ta yafa a kugu ta ce "Yau akwai kutumar bura uba a garin nan kace yau akwai tashin bomb a kaduna wanda zai tashi da uban kowa Wace karuwar y'ar Iskar ce wannan Mustapha ?......✍🏿
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️.........*49 & 50*
"Kishiyarki ta ce a gaishe da ke " wara idanu Zarah tayi saikuma tayi Dariya tunowa Da Amera rufe bakinta tayi tana gumtse dariyar da tazo mata Kallonta ya tsayayi yanda take dariyar cikin nutsuwa jin ta gimtse ya sanyashi murmusawa ya ce "Ko na kira maki ita kiji da kunnanki"Tana Dariya ta girgiza kai" Murmushi yayi ya ce "Kina tsoranta ne?" Uhm saboda Kaura ce karta kasheni"wara idanu yayi cike da mamakin jin Abunda ta ce ya ce "Matar tawa ce Kaura" Dagowa tayi ta Kalleshi sai kuma ta turo baki tayi kasa da kai "d'an murmushi yayi ya ce " ni kike turowa baki Ko Duk kishi ne ya sanyaki haka?da mamakin jin Abunda ya fito daga bakinshi ta ce "Allah kiyaye " meye kikewa Allah kiyaye kishin nawa ne bakyayi "Gyada mashi kai tayi" wara idanu yayi ya ce "to meyasa nasan dai duk mace na kishin mijinta? Ai kai ba mijina ba ne " To me d'inki ne?Mijin wucin gadi ne ko kuma mijin *Auren wata Tara* kaga ko akanme zanyi kishinka "Dariyar da bai shirya ba MD yayi wara idanu tayi ganin yanda yake dariyar sosai yayi kyau da Dariya saida ya tsagaita kafin ya ce "mumu girl kin iya fadar magana daman har haka"harara ta maka masa kamar zatayi kuka cikin shagwaba ta ce " Ni ba mumu ba ce "Murmushi yayi ya ce " To Beauty ce?I don't know "ta fad'a tana shan magani" yanda tayin ne ya k'ara basa Dariya ya ce "Kin iya shagwaba daman kenan ?Batace uffan ba " shiru sukayi na Dan mintuna kafin ta d'ago ta Kallesa ta ce "Wai daman kana Dariya" Murmushi ya sakar mata yana lakutar kumatunta ya ce "Saita kama " marairaicewa tayi ta ce "tafiyi maka kyau akan had'e fuskar nan da kake ka dingayi " murmushin ya sake mayar mata ya ce "kina son ganin ina Dariya kenan "Samun kanta yayi Da daga mashi kai "to zan dingayi daga yau mumu girl ya fad'a yana Mikewa " kamar zatayi kuka ta ce "Ni Allah ka daina Cemun mumu bana so" To Mamy "ya fad'a yana shiga bedroom da kallo ta bisa har ya bacewa ganinsa kafin ta sauke ajiyar zuciya lumshe ido tayi a ranta cike da mamaki ta ce " Daman yana magana haka harda Dariya "samun kanta tayi da sakin murmushi sai wajen 6 ta ga ya fito da wasu K'ananan kayan da ya saba zama da su a gida a lokacin waya na K'are a kunnen ta tana saya da Hafiz da ya kira kallo d'aya tayi masa ta kauda kai tana cigaba da wayarta da Hafiz ta bangarenshi Shima kallo d'aya yayi mata ya zauna yana kallon Kwallo a makekiyar plasma din dake manne a d'akin cikin shagwaba ta ce " A a a Ya Hafiz Gaskiya ni bazanyi kamu ba banason bidi'a a bikin kawai walima zanyi "daga bangaren Hafiz ya na Dariya Ya ce " na manta fa ashe Amaryar tawa Malama ce Amma Dan Allah ki bari ko event d'aya ne ayi please abun zaifi kayatarwa"Girgiza kai tayi ta ce "a a a ya Hafiz kawai ka barshi ni Allah bazan iya kamu ba gwara ma kayi lunch kaida abokananka yafi" Eh kuma kin kawo shawara me kyau zanyi lunch din kawai yanzu me kike?bakomai?ina Asmy?gabantane ya fad'i ta rasa k'aryar da zatayi"ta ce "Uhm gata nan " Okay kwana biyu bamu gaisa ba b'ata mu gaisa "Gabanta ya k'ara bada daram Dagowar da zatayi ta sauke akan MD da ya kura mata ido ba ko k'iftawa in ina ta fara ta rasa abun cewa Chan kuma ga ce" Uhm tadan shiga toilet "okay to shikenan next time magaisa ki kulamun da kanki bye I love you" love you too"ta fad'a kasa kasa tana rufe fuska "Bani wayarki?ta tsinkayi Muryarshi daga sama" Da mamaki ta dinga Kallonshi kafin ta ce "wayata kuma ?Eh ko kurma ce Ke ?To saboda me zanbaka wayata " Saboda kin karya Dokar gidana ba ayimun waya a cikin gida dama ko waye sai anfita "Mamaki duk ya cika Zarah " a ranta tace waishi wannan wani irin mutum.ne mai siffa biyu dazu mutumin kirki yanzu ya koma wani Kamar mai tsaron wutar jahannama "Samun kanta tayi da cewa " Ai baka fad'amun ba da wannan dokan "yanzu ai kin sani" Danne fushinta tayi Dan batason rigima ta mik'a masa wayar ta na shan kunu"Amsa yayi yana cigaba da Kallo ba ayi minti biyar ba Kuma saitaga ya maido mata cikin Sauri ta amshi wayarta tana Sanyawa a jaka Mikewa tayi ta shiga bedroom ta na turo baki da dare Take away yayi musu sukaci Around 10 Zarah harta kwanta Amma bacci bai d'auke taba taji shigowarshi tana jinshi ya shiga wanka a ranta ta ce "shidai baya gajiya da wanka kamar kwado Saikuma ta ce " ai naga alama tsaftace tayi masa yawa "tana jinshi ya fito ya shafa lotion da turarruka masu sanyin k'amshi Gado ya zauna tare da janyo laptop dinsa ya fara operating cikin nutsuwa Zarah tana jinshi har bacci ya d'auketa jin saukar numfashinta Alamun bacci ya d'auketa ya sanyashi linke Laptop din ya maida ita gefe Dan tun dazu dauriya kawai yake amma a matse yake janyota yayi jikinshi tare da Fara Aika mata sakwanni Zarah cikin bacci taji abun kamar a mafarki tana farkawa taga gaske ne Zatayi magana yayi saurin hade bakinsu waje Daya....... MD shine Baidamu gamsuwa ba sai wajen Asuba Dan yarinyar jinta yake kullum kamar Kara mata dadi ake tamkar Zuma haka yakejinta gashi kuma mamakinshi na hakurinta duk yanda ta gaji da abun Bata nuna masa ta gaji cike da gajiya Zarah taje tayi wanka Dan sosai tayi likis