Showing 66001 words to 69000 words out of 153980 words
tunanin dak'yal ya samu bacci ya kwashesa washegari da misalin 4pm yana zaune a kujerar palourn su suna Hira da Ammy Chuchu ta shigo gidan "da fara'arta ta ce " Lah yaya Kaine two days bana ganinka karkaga yanda nayi missing dinka "murmushi ya sakar mata ya ce " Daga ina Haka Auta na ganki da jaka"gefenshi ta zauna ta ce "Daga gidan Aunty Zey nake kwana na biyu a Chan " Kice ziyara aka kai mata "Murmushi tayi ta ce" Eh Yaya "Ammy ce ta ce " Tofa keda kikace zakiyi sati me ya maidoki"Dariya tayi ta ce "kewarki ta dawo dani ammy Gani nayi bazan iya ba ina gari bana ganinki sainayi ta tunanin kewa zatayi miki yawa gasu y'an rainin wayan yaran nan na Aunty Zey nayi da su taho mu taho suyi maki kwana biyu sukaki wai Saidai in gidan Uncle zankaisu shiyasa na tahowata watau ni sun rainani"ta fad'a tana turo baki" murmushi Ammy tayi ta ce "Ai yaran nan sarkafar iyaye garesu shiyasa nama hakura da a kawomun su Dan ba zama ba zasuyi sun fiso su jisu kusa da iyayensu sai suje Chan su karata Tunda ga Auta ai nasan ke kin bani Yaranki ko" Dariya Chuchu tayi tare da rufe fuska ta ce "Kai Ammy Saidai yaran Yaya dai" Ohhh bazakiban ba kenan kun nunamun Yayan shine kawai nawa ko to shikenan Shima Allah ya kawo nasan kuga yanda nima zan gwada muku banbanci Dan Ko halawa na sayawa yaranshi bazan bawa naku Ba "Dariya Chuchu tayi ta ce " Kai Ammy Bafa haka nace ba "MD najin hirarsu bai tanka ba saida Ammy takawo zancen yaransa Yaji zuciyarsa wani iri a ranshi ya ce " Allah yasa nima ina da rabon ganin nawa yaran"ganin hirar zata sanya MD tunani ya sanya su sakin hirar suka kama wata MD ne ya kalli Chuchu ya ce "Tunda kika dawo Hutu bakije gida na ba why" Sorry yaya Aunty Amera na gidan shiyasa bana son zuwa "Bata fuska yayi ya ce " Ita ga dodonki ko?girgiza kai tayi ta ce "Yi hakuri Yaya ba haka bane" Saura kwana nawa hutun naku ya k'are "3weeks" Okay shirya mu tafi ki k'arasa hutun a gida na "Kamar zatayi kuka ta ce " Yaya Za abar Ammy ita kadai fa "Sanin Halin Chuchu sarai ba jituwa Suke da Amera ba ya sanya ta cewa" Kayi hakuri Babban yaya tayi maka kwana biyu nima banajin dad'in gidan ni kad'ai sai masu aiki "To shikenan Ammy" ya fad'a Ajiyar zuciya Chuchu ta sauke Kala biyu Chuchu ta d'auko suka tafi gidan MD dukda ranta bayaso a palour suka tarar da Amira ta harde kafa daya kan d'aya tana latsa waya y'ar aiki durkushe gabanta tana mata tausa a kafa "Tsaki Chuchu taja a ranta ta ce " kamar wata yar shugaban kasa mtwsss fuska murtuke ta zauna palour Bayan MD ya zauna Dagowa tayi tare da Fara Murmushi ta ce "Honey yaushe ka dawo" Yanzu "ya bata amsa yana lumshe ido " Tsawa ta dakawa me aikin ta ce "Bazaki tashi ki tafi ba kina ganin mijina ya dawo Dan kutumar ubanki zaki zauna a nan ban muku dokar cewar ko a bisa sabani idonku ya had'u da na mijina a bakin aikinka ba to kema yau aikinki ya k'are Dan haka kije na koreki daga yau na kuma ganinki a hanyar layin nan ma sai nasa an kama Duka ilahirin danginki " Cikin kid'imewa y'ar aikin ta fara kuka tana magiya ta ce "Dan girman Allah Hajiya kiyi hakuri wannan Aikin shine madogarata idan na rasashi bansan ya zanyi ba kiyi hakuri ki yafemun ina tsoron tashi ne karkice kuma nayi laifi shiyasa kimun rai Hajiya" D'auketa da wani irin Mari Amera tayi Wanda Marin saida ya tsoratar da Chuchu ta ce "Ni zan fad'a magana ki musa mun Dan Ubanki y'ar matsiyata dake zanyi musayar baki tana shirin Kara d'auketa da wani marin Chuchu tayi Sauri ta shige gabanta " Wani banzan kallo ta watsawa Chuchu ta ce "Ke kuma ina ruwanki matsa kiban waje" bazan matsa ba idan ke bakisan darajar d'an Adam ba ni na sani me yarinya tayi miki Dan zalinci zakiyi mata irin wannan Marin Dan kina tutiya da arziki kifa sani arzikin nan da kike tak'ama dashi Allah ne yake rabawa ga duk Wanda yaso suma talakkawan basu sukayi kansu ba Allah ne yayosu haka haka masu arzikinma Duka yin Allah ne akanme zaki dinga wulakantar da na kasa dake dandai kawai suna karkashinki"wani banzan kallo Amera ta watsa mata kafin ta ce "Allahu Akhbar ke kuma yaushe kika fara wa azi bamu da masaniya" banza Chuchu tayi mata tare da kama hannun yar aikin sukayi waje kudinta 20k dake hand bag d'inta ta bata tare da bata hakuri "kafin ta dawo Inda ta samu MD haka ta barsa kamar komai bai faru ba a ranta ta ce Wlh hada laifin yaya da ya bari Matar nan take iskanci yanda taso" Bata kuma waiwayar Amera ba tayi wucewarta D'akin da take sauka tana Jan tsakin Haushi da tsanar halin Amera "MD ko sai Bayan barin Chuchu wajen ya rufe Amera da fad'a akan Abunda take bata kyautawa " Nanfa ta tubure tace wlh kome zaice Saidai yace Amma indai akan wannan ne yanzu ta fara ganin bata bakinshine ma zaiyi rabuwa yayi da ita kwanan Chuchu biyu a gidan Wanda kamar a k'aya tayishi ta koma gida Koda ta koma ta bawa Ammy labarin abunda ya faru girgiza kai tayi ta ce "Rabu da ita duniya ce " MD ko yananan yana lissafin kwanakin da ya ragewa su Chuchu su koma makaranta.
Kowa idan zai koma makaranta bak'inciki yake na rabuwa da gida banda Zarah dake d'okin komawarta sch Dan wannan Karin ba k'aramar takura Tasha ba wajen Mama Rabi ba Bugu amma akwai zagi da bakaken maganganu ga aiyuka dukda wannan baya damunta saboda ta saba yaune komawarsu sch Wanda tunda safe ta shirya Bayan Baba ya sallameta da abunda ke aljihunshi dukda dak'yal ta Amsa nan yayi mata nasihohi kamar yanda ya saba yi mata Bayan fitarshi ba jimawa itama ta shirya sosai taji dad'in Rashin ganin Mama Rabi a gidan Dan yanzu ta tarki yawo gidan su Asmy suka wuce Inda daga Chan suka wuce Tasha suka hau motar Zaria minti hamsin me kyau ya kaisu har hostel Bayan sun huta wayarta Zarah ta janyo tare da dannawa Chuchu kira ta ce "Ya dai daughter munfa shigo bamu ganki ba " Daga bangaren Chuchu ta ce "Haba daman nafison saikunzo nazo nima gani nan tahowa gobe daman nagama parking d'in komai na " Okay to muna Kallon Hanya ki gaishe da Ammy"zataji Zan fad'a mata insha Allah "washegari Chuchu ta shirya ta taho makaranta Wanda driver ne ya Kaita MD Bayan ya shigo gidansu ganin baiga Chuchu ba ya sanyashi tambayar Ammy ya ce " Ina Chuchu wai Ammy"Ai ta koma makaranta tun d'azu kenan batayi maka bankwana ba auta kenan Wani abun sai ita nafa zata tayi maka bankwana"Girgiza kai yayi ya ce "may be ta kira waya ta tana kulle" Koda ya koma gida tun a hanya yake jinshi cikin farincikin da ya rasa dalilinshi.........โ๐ฟ
*Masu fitarmun da Littafi ina sane daku kuma ku sani ku da Allah tunda na fad'a basau d'aya ba sau biyu ba akan a daina fitarmun da Littafi duk mai buk'atar son karantawa Yana da damar saya ya karanta cikin nutsuwa da kwanciyar hankali*
*ina bawa wadanda sukayi mun magana sukaji shiru hakuri nayi loosing chat Dina gabak'i d'aya babu d'aya Dana d'aga na sakonku please Wanda sukayi mun magana ko suka turo kati sukaji shiru su sakemun magana Please banyi hakan da gangan ba inbanda matsala da na samu ngd masoyan Asali ga masu buk'atar Karin bayani su tuntub'eni akan number wayata kamar haka 07026166536*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. ๐ฏโโ๏ธ๐๐๐*
1, *MU GANI A ฦASA...*๐ฅ
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ฦWAI..*๐ฅ
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*๐ฅ
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*๐
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*๐ฉโโค๏ธโ๐จ
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huษu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ษaya N300
*DOMIN TURA KUฦIN KAI TSAYE*๐
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya๐
0810 433 5144
Masu tura katin MTN๐
0814 179 9224
ฦณan ฦasar Niger zasu tura nasu anan.๐
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huษu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ษaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐๐ฉโโค๏ธโ๐จ
_*Miss Hajo ce*_๐ค๐ฟ
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: ๐
ฟ๏ธ.........*51 & 52*
"Kinsan na Fad'a maki akwai kanwar mamanmu anan to shine takoma gidanta da zama ta na d'an rage Mata ayyuka saboda mijinta baya nan" ayya kice yanzu munzama mu biyu Gaskiya zamuyi missing nata sosai wlh"cewar chuchu"wlhko ai bama kadanba danma ai ba koda yaushe take Chan ba zata dinga dawowa nan" dukda haka dai Chuchu ta fad'a...washegari Bayan dawowarta daga lectures around 5pm tana kwance Kan sopa ta na Karatun exams din dake tunkaro musu shikuma yana operating a system "Kallonta yayi yaga ta maida hankalinta ga karatun da take Bayan ya gama aikin da yake a laptop ya linke ya Aje tunani ne yake karfa yayi gudun gara ya fad'a gidan zago taya za ayi Ace wata biyar yanzu da Auren amma bata samu ciki ba gashi har saura wata hudu yarjejeniyar su ta kare a ranshi ya ce " kodai matsalar daga gareni take?Amma ai Duk asibitocin da naje sun gwadani lafiya ta qalau to me hakan yake nufi "wani tunani yazo masa ya ce " Karfa aikin banza nake Yarinyar nan da abunda takesha tunda wayayyace zaiyi wahala ta yarda ta dauki ciki "wata dabara ce ga fado masa yace bari nayi mata low nagani idan hakane " Mamy"ya kira sunanta a hankali "Aje littafin dake hannunta tayi ta ce " Na'am"Karatun nan tund'azu kike yaci ki bari inba so kike ki hardace littafin ba "murmushi tayi ta ce " Ai da zan samu dama ma na hardace book din da zanji dadi sosai "Uhm kaji dictionary" y'ar Dariya tayi Kad'an ta ce "Uhm"Na tambayeki zaki bani amsa"? Gyada mashi kai tayi ta ce " idan har na sani zan baka ,insha Allah"kina son yara kuwa?Murmushi tayi ta ce "Ina so mana sosaima kuwa " kice mijinki yaji dadi zaki Haifa mai yara da yawa"Gabanta ne ya bada daram tunowa da Hafiz "murmushin da ya lotsar da dimple dinta ta ce " insha Allah"tana rufe fuska "murmushi yayi ya ce " Kenan ni bazaki Haifa mun ba "Wara idanu tayi saikuma ta turo baki ta ce " Matarka kaima ta Haifa maka mana nima mijina zan haifawa "yana jinjina Yarinta irin ta Zarah ya ce " Ayya ni ai matata bata haihuwa shekararmu Tara da Aure amma ko b'atan wata bata tabayi ba "cikin muryar tausayawa ta marairaice ta ce " Ayya wlh harkun bani tausayi Allah ya baku mai amfani Amma kuma kai kana son yara ne"ina sonsu sosaima kuwa tun kafin nayi Aure nake da burin Son yara ina sonsu sosai Wanda har nake tunanin sonsune da yayimun yawa yasa Allah ya jarabceni har yanzu bai bani ba"girgiza masa kai tayi ta ce "kadaina wannan tunanin kasa a ranka lokacin samun sune kawai baiyi Aure,Da Haihuwa Abu ne da Allah ya sanya musu lokaci dole sai lokacin Su yayi tukwana sukan zowa bawa ina maka fatan Allah ya baka masu amfani" Murmushin da baiyi niyya ba ya sakar mata ya ce "Hakane To Allah ya kawo lokacin" a ranshi ya ce "Ga dukkan alamu ba abunda take sha amma Indai hakane Tabbas ina cikin jarabawa ya zanyi da Hajiya kaka?Tabbas dole ne duk yanda za ayi Amera ta koma America kafin na samu mafita " Tunanin me kake ?ya tsinkayi Muryar Zarah "murmushi ya sakar mata ya ce " bakomai Please zaki iya girkamun tuwo irin na rannan"Shiru tayi kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce "akwai kayan Had'in ne?Eh akwai komai a ciki" Okay Badamuwa ta fad'a tana Mikewa da Kallo ya bita harta shiga kitchen din kafin ya sauke ajiyar zuciya a ranshi yana mamakin yanda yake sauya wasu dabi'un game da halayyarshi idan yana tare da ita har yake tsayawa yayi doguwar Hira da ita ko Dariya da murmushi Wanda ko a gida bakowani lokaci ba yake yinsu a ranshi ya ce "Saboda Yarinyar simple ce bata da hayaniya?wata zuciyar kuma ta ce " saboda ka chutar da ita a farkon mu'amularka da ita Wanda idan bangyara mu'amula ta da ita ba ko Bayan rabuwarmu zata rikeni mugu a cikin ranta "da wannan tunanin har aka kira Sallar magriba sai Bayan isha'i Zarah ta gama Tuwon da miya ta juye a warmer a dining ta jera Kafin taje tayi Sallar isha'i Bayan tayi wanka ta sanya doguwar Hijab d'inta ta fito Zaune ta tarar dashi a palour yana cin tuwon cikin nutsuwa sosai MD yaji dadin Tuwon fiye da na rannan sai lumshe ido yake da hannu yayi mata nuni da good kafin ya furta " Thnks"a hankali"murmushi kawai Zarah tayi batace komai ba "Bazakici ba ?Sai anjima ta fad'a " a hankali"Zoki zauna muci tare"girgiza masa kai tayi ta ce "A a a " Sanin kanki ne banason musu ko?a sanyaye ta k'arasa ta samu guri gefen k'asar da yake ta zauna "ko kefa mumu girl" Wata irin harara ta banka masa kafin ta maida kanta kasa tana turo baki"murmushi kawai yayi "Cike da jin kunya Zarah takecin abinci bata wani ci da yawa ba ta ce ta k'oshi ba yanda baiyi da ita ba akan tadawo amma takiya ganin zata sanya masa kuka ya sanyasa cewa" Shikenan rigimammiya"tana turo baki ta koma Daki wayarta ta janyo ganin missed call ya Hafiz ya sanya tabi kiran saida ta katse kafin ya kira Hira suka fara Sosai cikin Sauk'i da k'aunar juna sosai suke waya Zarah na kwance saman bed tayi rubda ciki batasan har lokacin da MD ya shigo dakinba ba saida ta tsinkayi muryarsa da cewa "bani wayar " Cikin kid'imewa Zarah ta kashe wayar tana addu'ar Kar Hafiz yaji muryar MD "Dan Alla meye haka wai dan Allah idanfa yaji muryarka me kake tunanin zai faru" tsaki yaja ya ce "so what Dan yaji muryata baki da Gaskiya kenan" Shine fa Wanda zan aura"ta fad'a kamar mai shirin yin kuka"Ni kuma Wanda kike Aura a yanzu ba ?saiki bambance ni dashi wayafi matsayi "Tana turo baki ta ce " Kai ai mijin wucin gadi ne shikuma shine mijina na har abada "kwabe mata bakin yayi ya ce " Ki dinga sanin maganar da zakiyimun hope kin fahimta ko nayi maki kama da sa an wasanki sannan ya fusge wayarta dake ringing yabar dakin"takaici ya ishi Zarah rasa me zatayi tayi kawai sai ta fashe da kuka ta ce "Allah ya isa mugu azzalumi saikace shine ya sayamun wayar da zai amshe wlh nidai an cuceni da aka lakabamun wannan alkakaidin ya zamemun k'arfen kafa ke Asmy kina Chan kina rayuwarki hankali kwance ni kin barni da kunci tana wannan sabbatunta a haka har bacci ya kwasheta MD ko Shima kwanciya yayi yana buk'atar Ta amma wannan Karin bazai jeba Dan karyaja raini a wajen yarinya k'arama harta gane larurarshi ta kawo mashi raini Irin yanda Amera tayi masa Dukda Amera intayi masa babbace ita ko wannan karamar yarinyar da auren wuri ya haifi kamarta bazai yarda ta samu damar raina sa ba...washegari koda ya tashi a daddaure ya tashi ya koma MD dinshi na ainahi Zarah na ganin haka ta kasa masa Rashin kunyar da taso masa akan wayarta saboda muddin tana ganinshi a haka tofa bazata iya gaya masa maganaba ta rasa ya akayi mutumin yake mata kwarjini duk maganar da taso fad'a masa wani lokacin saita kasa a haka ta tafi lecture d'inta batare da ko magana ta had'asu ba inbanda gaisheshinda tayi ya amsa ciki_ciki a sch Asmy ta ce " wai ya akayi nayi ta Kiran numberki kashe sannan ina wayarki"tsaki Zarah taja Dan daman haushin asmy din takeji Dan duk ita taja mata wannan Abun ta ce "Bansaniba" Dariya Asmy tayi ta ce "Allah baki hakuri bani na kar zoman ba rataya aka bani" Tsaki Zarah taja tare da shiga motar driver da yazo daukarta batare da tayiwa ma asmy bankwana ba da dare around 10 tana karatu ya kira sunanta amsa masa tayi ba yabo ba fallasa "Zoki amshi wayarki''ya fad'a yana fito da wayar daga aljihunshi Dan yasan fushin nan da take Na wayar ne " Cikin Sauri ya Mike tare da zuwa "ta mik'a hannunta kenan zata amsa wayar ta subce mata ji kake tasssssss " Hannu aka Zarah ta d'ora ta ce wayyo Allah na ta fashe "Ya Allah MD ya fad:'a kafin ya yunkura ya d'auko wayar da tayi kwatsa_kwatsa kasancewar tilles duba wayar yayi yaga ai tagama amfani Zarah ko tuni harta fara hawaye ta ce Ta lalace ko"Baice mata uffan ba sai zaro sim din da yayi ya ce " ta gama nawa wayar take na biyaki"Dukda taji zafi a ranta amma hakan bazaisa ta ce zata sanyashi ramuwa ba Girgiza kai tayi ta ce " a a a ba saika biya ni ba tsautsayine ko a hannuna ai zata iya fashewa "yayi mamakin jin furucin ta dan A tunaninshi tuburewa zatayi ta ce saiya biyata baice uffan ba sai rike sim d'inta da yayi washegari Zarah harta hakura da waya Bayan ta dawo daga lectures Sannu yayi mata ta zauna tana maida numfashi " Amshi "ya fad'a " Kallon abunda yake nuna mata tayi taga kwalin waya ne "Ta wacece" ta fad'a a hankali"taki "ya bata amsa kai tsaye " wara idanu tayi tace Ni kuma ai bance ka rama munba baxan ansa ba "ba ramuwa bace kyauta ce Na baki" make kafada tayi ta ce "a a bazan amsa ba " saboda me?saboda dalilin ka yardamun yasa ka sayamun"Girgiza mata kai yayi ya ce "Daman nayi niyya ne ki amsa karki