Showing 108001 words to 111000 words out of 153980 words
ce ta sartse ganin fitowar zahra daga ita sai rigar bacci cikin kayayyakin da ya sayo mata Wanda Hakanan take sanyawa d'an bata da wasu Cikinta ya fito yayi das a jikinta Cikin b'acin rai da hawaye ta ce " Waikai d'aukar me kayimun marar galihu ko.kuma me mi.kake nufi da ajeni a gidan nan da kayi kamar wace y'ar iska ....saurin katse.kiran md yayi gabansa na fad'uwa tsoransa Allah kada Ammy taji abunda zahra ta fad'a kallonta yayi fuska ba wasa ya ce "Zaman Aure kike?Tana binsa da wani banzan kallo ta ce " lallai kai baka da kunya ma.wlh har kana da bakin da zaka iya furta wannan Kalmar Wacece zatayi zaman Aure da mugu azzalumi Wanda baisan damuwar wani ba damuwar kansa kawai ya sani mayaudar....bata k'arasa fad'a abunda takeson Fad'a ba MD yayi sama da ita bai direta ko ina ba sai kan Bed yana shirin danneta ta k'walla Kara ta ce "Wlh tallahi ka sake kayimun wani Abu zanyi maka abunda ba a tab'a yi maka shi a rayuwa ba " banza MD yayi mata ya rungumota jikinta sosai tare da Fara Aika mata K'ananan sakwanni ganin zai birkitawa kansa lissafi gashi yayi alk'awarin bazan k'ara wani Abu da ita ba saboda cikin dake jikinta daidai kunnanta ya rada mata a hankali "ki kwanta kiyi bacci yanzu indai bakyaso wani Abu ya faru" Zahra najin haka ta Had'iye kukanta Batasan lokacin da wahalallen bacci yayi awon gaba da ita ba saida yaji saukar numfashinta tukwana ya sauke ajiyar zuciya ya zame a hankali saida ya sha ruwan liptop da lemon tsami tukwana ya samu bacci ya daukesa washegari zahra ta tashi bayan asuba dan ta makara salla shiko md koda yayi salla ya fita daga dakin ya koma nasa Bayan tayi alwala ta gabatar da salla Sosai ta rokawa mahaifinta samun lafiya dukda MD ya fad'a mata ansallamesa yaji sauk'i amma bata yarda ba Tana gama salla yunwa ta ciyota tsaki taja Dan yanzu wata irin jin yunwa takeji da taci kamar bataci ba hakan yasa yanzu ta daina masa zuciya da abinci Dan ita ke illatuwa kofa ta nufa tana turawa taji a rufe tsaki taja Dan sosai takejin haushin kulleta din da yake ko yaushe kamar a gidan yari tsaki taja tare da komawa ta zauna tana lazumi tana addu'ar Allah zubar da cikin nan dake jikinta ba ayi 30 minutes ba MD ya shigo d'auke da plate din wainar kwai kusan guda biyar sai cup din tea da bread a hannunsa kai tsaye gabanta ya nufa dasu a hankali ya ce "Good morning mummyn baby" Tsaki taja tare da kauda kai Dan murmushi yayi Dan ya saba da abun nata ya Aje kafinma ya ce ta ci tuni ta fara ci Dan yunwar data ciwo ta saida abun yaso basa Dariya ganin yanda ta murtuke takeci kamar an mata dole cewa yayi "ki gama ki shirya muje Asibiti ayi miki scanning sannan ya kamata mu fara zuwa awo" wani banzan kallo tayi masa cike da takaici ta ce "Allah kiyaye Allah tsari gatari da saran shuka a tunaninka ni zanje Asibiti saboda lafiyar cikin nan Dana tsana Aiko Inma kana wannan tunanin tun wuri ka bari Dan wlh ba haihuwar....saurin kwabe mata baki yayi cikin bacin rai ya ce" Da Allah yiwa mutane shiru "Dogon tsaki Taja Wanda MD Inda sabo harya saba da tsakin nata wanda duk duniya bayan ammy babu wanda ya isa ya masa su wanje lafiya ta ce" Satoni dinma da kayi Allah saiya sakamun wlh Dan laifinka d'aya da y'an kidnapping"tsaki MD yaja tare da mik'ewa ya ce "Idan kina buk'atar wani Abu ina palour" Da harara ta bisa har yaban palourn wajen Azahar zahra ta karajin wata yunwar koda ta fita palour zaune ta samesa yana aiki a laptop Wuri ta samu ta zauna tana shashan magani so take tace masa yunwa takeji ta kasa ganin baiyi mata magana ba ya sanyata cewa "yunwa nakeji fa Malam" Kamar bazai tanka mata ba ya ce "Me kike son ci a kawo miki" Bana son Cin abincin restaurant Dan ban yarda da tsabtarsu ba bazan sake ci ba"Yana mata kallon mamaki ya ce "To shiga ki girka?Harara ta banka masa ta ce " Wlh kaji na rantse ko hanyar kitchen bazanyi ba"Aje laptop d'in MD yayi yana kallonta ya ce "To wa kike tunanin zai girka maki" Kai da kayi cikin da ke sakani jin yunwar kai zaka dinga girkamun harya zube.........🤙🏿
*Ohni wai yaushe zahra ta zama y'ar Rashin kunya haka*🙆🙆😆
*Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536*
*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*
1, *MU GANI A ƘASA..🔥*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5_ *AUREN WATA TARA👩❤️👨*
_Miss Hajo_
Guda ɗaya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huɗu N700
Guda biyar 1k
*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*
Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.
Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
...........🥚👩❤️👨💥🌎....
*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number 08141799224
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*
*_Miss Hajo ce_*✍🏽
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️.........*71 & 72*
"Daman ita ce momcy din taki?Gyada masa kai tayi ta ce " Eh ita ce Yaya"ita ce mai muryar nan kenan?Nanma sake gyada masa kai tayi"Maida Kallonshi yayi ga hoton yana mamakin kenan k'awar Chuchu ce da takeji dinnan da ita yayiwa haka sosai Abun yazo mai a bazata yanda bai tab'a kawowa a ranshi ba "Kallon Chuchu ya kumayi ya ce " sunan ta na Gaskiya"Zarah Yusuf yaya ko ka Santa ne Wai"Zarah Yusuf ya maimaita a ransa Tabbas ita d'ince "Kafin ya kalli Chuchu ya ce " ta ina zan Santa Bayan ba tab'a ganinta nayi ba "Eh yaya Amma kagani ko ta had'u sosai ko?Ba Laifi ya fad'a yana Mikewa " binshi tayi ta ce "Yaya ina zaka kuma Bayan baka bani shawarar abunda zanyi mata ba bakace hoton yayi asashi ba "duk yanda yayi miki kiyi amma karkiyi mai hoto ?,binshi tayi ganin ya nufin hanyar stairs ta ce " Yaya Saboda me nafison nayi mata me hoto"Saboda bazaiyi kyau ba da hoto please ki barni na huta "ya fad'a yana hayewa sama Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta koma palour gefen Ammy ta zauna tana d'ora kanta kafadarta ta ce " Ammy wai kinji yaya kar ayi me hoto ko ayi me sunan kawai"Amsar hoton Ammy tayi ta ce "Masha Allah hoton yayi kyau amma kiyi mata mai sunan kawai zaifi watak'ila batason saka hotontane kinsan y'ar tawa ustaziya ce " Murmushi Chuchu tayi sosai takejin dad'in yanda Ammy ke son kawar tata ta ce "To shikenan Ammy wai Kinga da yaya yaga hotonta wlh saida yayi ta Kalla Kinga yanda lokaci guda ya sauya kamar daman ya santa" Murmushi Ammy tayi ta ce "Yanzu ba wannan ba kiyi Sauri ki kira mai jakar kar lokaci ya k'ure " Mikewa tayi ta ce "Barima kawai na tafi da kaina na masa bayani Dan gobe nakeson su iso guda D'ari biyar ai sunyi ko Ammy,?" Ta fad'a tana yafa beil"Eh sunyi please ki dawo da wuri banda gudu da mota a titi"......MD tunda ya shiga d'akin ya rumtiya duniyar tunanin Zarah Bai tab'a tunanin Zarah zata kasance itace kawar Chuchu kuma ita ce mai Qiri'ar wannan data ki barin kwalwarsa "sosai yaji zuciyarsa ta k'ara chunkushewa a halin yanzu baya da buri da yake dashi fiye da na ganin yarinyar tunda suka rabu Baccin kirki baya iyayi batare da tunaninta a ransa Wanda shi kanshi har mamakin hakan yake amma sai ya lakanta hakan da tausayinta ne da yake A ransa ya ce Tabbas wannan babbar dama ce ta sameni da zanyi amfani da ita wajen Gano Address d'inta Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " wannan Karin da Chuchu zanyi amfani"Wayarsa ce tayi ringing Ganin Amera ce Ke kiran ya sanyashi picking baiyi mamakin kin masa maganar kin kulata da yayi kwana biyu Dan yasan indai tana gidansu bata da matsala bataki ya barta tayi wata a gida ba Bayan sun gama waya baice yaushe zata dawo ba haka batace masa zata dawo ba dukda tana son ganinshi.
Yau Tuesday Zarah ta tashi da zazzabi kin fad'awa kowa tayi ciki harda Asmy ranar mai lalle tazo dak'yal ta daure akayi mata danma a gidan su Asmy akayi mata ba Mutane sosai sai wasu cousin sisters d'inta na wajen Baba da sukazo Akayi musu tare sosai K'unshin Zarah yayi masifar kyau sai sannan ta fito a Amaryar Washegari Laraba tunda Safe sukaje saloon dukda tana Kokarin nuna ba komai a fuskarta ana cikin yiwa Asmy Bayan Angama yiwa Zarah tana gefe wayarta ce tayi ringing dubawa tayi taga Chuchu ce "Bayan tayi picking daga bangaren Chuchu ta ce " yanzu zantaho sis ki turomun Address d'in gidan idan nazo Funtua wace unguwa zance"Sosai Zarah tayi kokari wajen daidaita Nutsuwarta ta ce "Jabiri Gidan Malam Yusuf Zakice " okay to gani nan insha Allah "Murmushin k'arfin hali Zarah tayi ta ce " Allah ya kawoku lafiya"Bayan sungama wayar angamawa Asmy gida suka wuce tare.
K'aramar akwati chuchu ta zuba kayanta sai murna take yau zata hadu da su Zarah 50k Ammy Ta bata ta kai gudummawarta Dan tace bazata samu halarta ba Bayan ta fito Harabar parking space d'in gidan Driver ya saka mata akwatinta a boot MD ya fito fuska ba walwala "Karasawa Inda yataho tayi tana kamo hannunshi ta ce " yaya yanzu zan tafi daman kai nake nema "yana Kallon motar da zata tafi ya ce" Wani gari ne zaki?Funtua ne Yaya ka manta bikin momcy da na fad'a maka"yaushe ne d'aurin Auran Asabar ne " shine zaki tafi tun yau Dan azarbabi "kamar zatayi kuka ta ce " Dan Allah yaya karkace zaka hana wlh mune manyan kawaye idan banjeba tun yanzu sai yaushe"Dan tasan halinshi sarai sai yace zai hanata "Jim yayi kafin ya kalli driver ya ce " fito da kayanta Daga motar nan zankira Wanda zai kaita "Jaber ya dannawa kira Bayan ya d'auka ya ce " Bloody Dan Allah ba abunda kake yanzu"Daga bangaren jaber yace "bakomai ya akayi" Inba damuwa kazo gidanmu ina son ganinka"Okay gani nan zuwa kana gidan "Eh" Kallon Chuchu yayi ya ce "Koma ciki kafin yazo ya kaiki" To yaya "ta fad'a tare da Juyawa Dan ta lallab'ashi karyace bazata ba ba ayi 30 minutse ba Jaber ya Iso gidan a palourn sa na part dinsa dake gidan suka yada zango..shiru jaber yayi Bayan ya gama sauraren MD Dagowa yayi ya Kallesa ya ce " Allah ne ya kawo mana mafita cikin Sauk'i amma nayi mamakin yarinyar da iliminta da komai zata yarda a d'aura mata Aure kan Aure "Numfashi MD ya fesar ya ce " Ni kaina nayi mamakin ta dalilin sanin ilimin nata bazata yarda a d'aura auren ba Alhalin da igiyar Aure na akanta ya sanya harna rabu da ita kafin Allah ya kawo mana mafita amma kana gani komai na shirin jagulewa"Ai bazaiyu a daura Auren nan ba Tunda muka samu address d'inta ai mungama samun dama Dole ne za a fasa Auren nan "Cewar Jabir "nasan da hakan bazan tab'a yarda A tabka wannan Babban kuskuren ba Amma tayaya kake ganin zamu magance matsalar" Ka barmun komai a hannu na bloody yanzu ba zankai Chuchu garin ba Kuma zangano gidansu ai magana ta k'are"Numfashi mai zafi MD ya fesar ya ce "Allah fitar damu" Ameen bari naje na sauketa kawai kome kenan saina dawo "Gyada masa kai MD yayi yana lumshe ido kan Kujera Bayan tafiyar su Chuchu ya jima yana sake_sake a ransa gabak'i d'aya kanshi ma ya kulle akan Lamarin yarinyar nan lumshe ido yayi kafin ya bud'e ya ce " Allah yasa ta tabbata ciki ne da ita Ya rabbissamawati"ya fad'a yana daga hannu yana rokon Allah ji yayi duk duniya yanzu kuma ba abunda ayake da buk'ata irin yara sosai yaji soyayyar cikin dukda bai tabbarba shi kanshi da akwaishi ko babu Amma zuciyarsa tafi rinjaya masa Akan akwai cikin wayarsa ya lalubo daidai numberta da yayi save da "Mamy" ya dinga kallo kamar kullum sai yayi kamar zai Danna mata kira wata zuciyar ta hanesa Dan yasan har yanzu fushi take dashi lumshe ido yayi a hankali ya furta "Simple babe baki da hayaniya " Kara lumshe ido yayi tunowa da zazzak'ar qiri'arta Da har yanzu idan ya tuno yakanjita a tsakiyar kansa ya ce "Ashe kece mai zazzak'ar muryar nan" Juyar da kansa yayi gefe saikuma ya saki murmushi ya ce "Koya taji.lokacin da ta ga takardar nan" Samun kanshi yayi da tsananin Bukatarta a kusa dashi koba komai irin zaman da sukayi dukda na d'an lokaci ne yana yi masa dadi sosai dabi'un yarinyar da hallayarta yake burgeshi Kara juyi yayi kan kujerar ya bud'e idonsa ya ce "Ashe kece kika k'ara inganta rayuwar kanwata Tabbas baki chanchanci Rashin Kyautatawa daga gareni ba ,dole ne na gyara kuskuren da nayi a baya wata zuciyar tace masa " To idan fa Chuchu suka gane kayi mata haka ya zasuji"tsaki yaja ya ce "Ai ba Laifi na bane Laifin Jaber ne tun Farko daya kawo wannan muguwar shawarar " To me yasa ban Sake ta ba "Wata zuciyar ta basa amsa da " saboda kana tausayinta" "tausayi kamar ya " ya k'ara tambayar kansa "Tausayi irin na musulunci " idan kana tausayinta me yasa da yarjejeniyar auren ku ta kare kak'i sakinta ta auri wanda take sonsa yake sonta "Saboda ina son inganta rayuwarta" Shi wancen sani kayi da har bazai inganta rayuwarta ba "Suk shi daya yake maganganun nan da zuciyarsa "tsaki yaja tare da buga kansa da hannu da karfi ya ce "OH MY GOD" na zauna ina ta tunanin k'aramar yarinya zata chazamun kai ".
Jaber yana sauke chuhu ya karema gidan kallo daga mata boot yayi ta fito da kayanta da kuma gudummawar jakunkunan da suke a wata k'atuwar leda zagayowa tayi Inda yake gaban mota bai fito ba ta ce " yaya Jaber Please ka fito ka taimakamun d'aukar akwatin nan wlh tayi nauyi "Harararta yayi ya ce " wannan Dan Abun ne bazaki iya d'auka ba Kice zasu kwana anan"Turo baki gaba tayi ta ce "Shiyasa banso Yaya yace kai zaka kaini ba wlh dan nasan kaima duk kusan halinku d'aya" Dariya yayi ya ce "Kome zakice kice " Tana shirin sake magana ta Hango Asmy ta fito daga gidansu ta nufo Inda take jaber na ganin asmy gabansa ya tsananta fad'uwa karta zo ta ganesa asirinsu ya tonu wajen Chuchu Dan yasan Sarai Asmy ba control gareta ba cikin Sauri bai saurari Chuchu ba yaja motar da karfi tare da saurin barin arear da Kallo Chuchu tabi motar Kafin ta tab'e baki Rungume juna sukayi da Asmy suna murnar ganin juna kafin Su wuce gidansu Inda Zarah take da gudu Suka Rungume juna suna Daukin ganin Juna Sosai Zarah ta d'an wartsake Dan tayi murnar ganin kawar tata sosai aka karrama Chuchu a gidansu Asmy fiye da tunanin mai karatu da dare yayi ma anan suka kwana Dan Zarah batason zuwa gidan su taro ya fara yawa washegari gidansu Zarah suka wuce sakamakon yawan nemanta da dangin babanta suke d'akin Zarah suka yada zango sosai Zarah ta nunawa Chuchu taji dad'in gudummawar jakunkunan da akayi gudummawar Ammy kuwa kin amsa tayi ba yanda Chuchu batayi da itaba amma taki amsa tace hidimar tayi yawa ganin jayayyar tasu tayi yawa ya sanya Chuchu Maida kudin jaka da niyyar ranar da za akaita ta had'a mata dasu ....Mama Rabi ce Gaban malamin ta (nikam nace boka dai)Cikin tashin hankali ta ce "Malam baki na da naka kace Auren nan Babu shi bazaiyu ba akwai Babban al'amarin dazai ruguza Auren Kace basainasa anyi komai ba Amma har yanzu banga Alamun lalacewar Auren nan ba har ana jibi d'aurin Aure hankalina fa a matuk'ar tashe yake Malam" buga kasa bokan yayi ya ce "Kina da gaggawa a kowani al'amari rabi na buga na buga amma amsar d'aya ce Auren nan babu shi Leko ki gani da idanunki " Lek'awa cikin kwaryar Rabi tayi ta ce "Malam ban fahimta ba " Da yatsa ya nuna mata ya ce "Kinga wancen na nesa da Hasken nan guda biyu Wanda ya fad'i d'innan" tace Eh "To shine mijin da ake shirin daura Auren ta Riga tayi masa nisa nesa ba kusa ba Babu Aure tsakaninsu" Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "To Malam hasken nan fa guda biyu Dana gani hannayensu rik'e Dana juna" Itace tare da Abokin rayuwarta tun sanda kikaban aikin nan Dana buga haka nake ganinsu Saidai naga Haske amma fuskokinsu sunki bayyanuwa "Cikin tsananin tashin hankali ta ce" Malam abokin rayuwarta kuma to meyasa Sukaki bayyanuwa sai Haske"Saboda suna da tsananin ibada da addu'a ko tsafi mutum yake tofa ina tabbatar maki bazasu tab'a Tab'uwa ba biyun nan ba kinsan ba irin aikin da ban maki ba kinsan yanda aiki na yake kamar yankan wuk'a to wannan Biyun bani da k'arfin ikon da zan iya musu asiri saboda babu Aljanin dazai iya tunkarar su yin kokarin hakan ma zai iya jawo mana asara babba Saidai a iya binciken da nayi su biyun suna da tsananin Kusanci da junansu sannan dukansu Haskene a cikin rayuwar kowannensu musamman ita Yarinyar da haskenta yafi nashi "uwar zufa ce ta ketowa Mama Rabi Cikin tashin hankali ta ce " Malam kace Haske ne su Duka biyun"Wannan maganar haka take kuma duk Inda kikaje haka za a fad'a maki"To Malam bazaiyu a raba su ba dan tun yanzu hankalina ya fara tashi aiduk Inda Haske yake alkhairi ne Taya za ayi Ace Zarah Haske ce kuma Shidinma ya zama Haske"Dariya yayi ya ce "Kina da tsananin hassada Rabi yanzu ki fad'a abunda ya kawoki " Goge uwar zufar data keto mata tayi ta ce "Malam Auren