Showing 63001 words to 66000 words out of 153980 words
ga Rashin bacci Shima Bayan yayi nashi wankan yayi alwala ya wuce masallaci Zarah na gama salla a sallayar baccin gajiya ya kwasheta yana dawowa ya isketa yanda ta takure take bacci saita basa Tausayi Daukarta yayi ya maida ita kan gadon a hankali Kafin Shima ya rungumota Bayan yaja musu blanket sune basu tashi ba sai 12Pm sosai Zarah tayi mamakin lokacin da suka kwashe suna bacci sai sannan ta tuno da tana da CA sosai hankalinta ya tashi gashi tasan Angama MD shigowarshi kenan d'akin Bayan ya shirya da dayan d'akin kallonta yayi ganin yanda ta firgice ya ce "Lafiya?Kamar zata fashe da kuka ta ce " text gareni yau tun 8 kuma yanzu har 12:30 "tunda C A ce ba saiku hade a Exams ba " Tana shirin fashewa da kuka ta ce "Yana da tsauri malamin Text din ita ke taimakawa " ya sunan Malamin "Umar" Umar Habibu"Cikin Sauri ta ce "Eh eh shi" Okay gobe zamuje saiya yi miki Tunda yanzu ta wuce "Ya yarda yayimun kuwa baya yarda fa ko assignment ya bayar kakai daga baya baya amsa bare text" Zaiyi maki karki sake musu "Shiru Zarah batare da tace uffan ba " yana gyara kwalar rigarsa ya ce "Akwai komai a kitchen ki girka Abunda yayi miki sai zuwa dare zandawo " Dan Allah na tafi hostel to "Ban bada umarni ba " ya fad'a yana barin d'akin "Dogon tsuka taja tare da kwaiwayar sa " ban bada umarni ba"ta fad'a tana yamutsa fuska tare da Jan tsaki ta ce saikace wani uba na "Koda ta fito palourn harya bar gidan Kitchen ta shiga ta girka lafiyayyan indomie da tasha vegetables da kwai sosai ta kimtsa cikinta kafin ta gyara gidan Dan Zarah Daman Chan ma'abuciyar tsafta ce ita aiki baya gunduranta Dan tayi training aiki a wajen Mama Rabi idanma batayi ba wani iri takejin jikinta Bayan ta gama tayi wanka tayi sallar Azahar what's app tahau ta d'an duba sakwanni kafin ta kwanta ta koma bacci Dan har yanzu Rashin baccin jiya bai gama Sakarta ba.
Yanda ta lafe a jikinshi yana yi mata magana kasa kasa zai tabbatar maka da Lallashinta ne ya ke " Cikin muryar mai shirin fashewa da kuka ta ce "Amma Honey Jiya ma fa Cemun kayi bazaka kwana ba yanzu kuma kazo mun da wata magana Wai zakayi tafiya maiduri yaushe rabonka da garin sanadin Hajiya kaka ta k'ara takura maka Akan maganar Aure wanda kasan bazan taba juran hakan ba zan iya mutuwa akanka md dana zauna da kishiya sanin kankane bana kaunar hakan kasan ganinka yake tuno mata da abun please honey karkaje" murza hannunta yake ya ce "My Merah kenan Baki da zance saina kishi me ya kawo zuwana kuma da maganar kishiya kinsan na jima banjeba shine zanje mu gaisa da y'an uwa " Dak'yal da lallashi MD ya shawo kanta ta amince masa Akan zaiyi one week amma tace zata zauna ne a gidansu saida yaga tafiyarta kafin ya d'auki hanyar komawa Zaria kamar ko yaushe a motarshi da ba a Santa ba Kuma mai tinted koda ya isa ya iske gidan tsaf_tsaf Sannu yayi mata ganin harda lafiyayyan girki tayi...washegari Zaune suke a office d'in Mlm Umar ita dashi sosai Zarah tayi mamakin yanda Mlm Umar ya amince cikin Sauk'i hada fara'arshi akan zaiyi mata text D'in amma question d'inta Da ban ya rubuta mata nan ya mik'a mata MD na kallonta yanda take rubutu da kanta saida ta cika paper hada bayanta shi kanshi yayi mamakin kokarin yarinyar da kanta tayi abun nan in banda yana wajen da saiyace kwafa tayi Bayan tagama tayi submitted Kallonshi tayi ta ce "Zanwuce hostel ?karkije jirani jikin mota " Zarah na turo baki ta fita Tana fita ta kira Asmy ta fad'a mata Inda suke Bayan fitarta Kallon Mlm Umar MD yayi ya ce "Tana maida hankali yarinyar?Tana da kokari ai sosai aboki School d'innan ai babu mai matsala da Zarah ga girmama malamai yarinyar akwai Ilimi wlh ga nutsuwa ai inbanda mata na hud'u ai da na k'ara da ita wlh idan kunbani ma sai na saki guda" Tashi MD yayi tare dayi mashi musabaha ya ce "mun wuce sai anjima" Binshi da Kallo Mlm Umar yayi ya ce "Tofa ko meye alakarshi da yarinya naga mood dinsa ya chanza Dan nafada Dana yi ta hud'u da ita saiya tuna last time daya kirasa akan ya kira masa ita yace masa cousin sister dinsa ce " a bakin mota ya tarar da Zarah tare da Asmy suna ta hira suna Dariya Gaisheshi Asmy tayi ya amsa ba yabo ba fallasa horn yayiwa Zarah Bayan ya shiga Sakin hannunta Asmy tayi ta ce " Sai gobe kawai karki tsaidashi "Harararta Zarah tayi tana turo baki ta shiga gaba " Har suka isa ba mai cewa uffan suna isa ta iske dogayen riguna a palourn jibge kuma duk masu manyan kudi sai hijabai "ki kwashe ki kai bedroom d'inki " yana gama fad'ar haka ya wuce ciki..washegari Bayan tayi shirin tafiyarta makaranta 5k ya mik'a mata har zataki amsa tunowa da maganar da yayi mata rannan ya sanyata amsa tare da cewa "Thnks" Karfe nawa zaku gama lecture din?Karfe biyu?Okay "tana fita ta samu driver na jiranta cikin girmamawa ya ce " Hajiya barka da fitowa nine sabon driver d'in naki da zai dinga kaiki"Da mamaki take binshi da Kallo tana tunanin me.MD yake nufi koda suka gama lecture tana fitowa taga driver d'in tana Jan tsaki ta ce "Gaskiya nidai nema ake a takura rayuwata wlh" Cemashi tayi bari ta fito tana zuwa hostel ta samu Chuchu da Asmy cikin Sauri ta Ruga ta rungumesu ta ce "Daugher yaushe kikazo" dazu na shigo wlh duk nayi kewarki momcy sosai suka dinga hira Zarah harta ma manta da driver sai wajen 3 ta tuno Firgit ta mik'e ta ce "Subhanallahi na manta nabar driver waje sai Allah ya kaimu tayi saurin fad'a tare da barin dakin tana zuwa ta samu driver d'in bai tafi ba yana can Inda ta barsa tana shiga ya ja suka nufi gidan Bayan fitar Zarah d'akin da mamaki Chuchu ta ce " ina zata wai naga ta fita "Karyar da zatayiwa Chuchu Asmy ta nema ta rasa Chan kuma kome ta tuno tayi firgit ta ce.........โ๐ฟ
*07026166536*
_Masu fitarmun da Littafi bazanyi Allah ya isa ba saboda littafi amma ku sani hakkina kuke fitarwa batare da izini na ba duk Wanda ya saya kudin karantawa kadai ya biya ba na mallaka ba kusani dai sarai akwai hakki kowa yana da damar karantawa indai ya biya 300 kachal cikin nutsuwa da kwanciyar yafi ka tsintseshi a gantali ka karanta a gantalewa cikin Rashin nutsuwa _
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. ๐ฏโโ๏ธ๐๐๐*
1, *MU GANI A ฦASA...*๐ฅ
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ฦWAI..*๐ฅ
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*๐ฅ
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*๐
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*๐ฉโโค๏ธโ๐จ
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huษu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ษaya N300
*DOMIN TURA KUฦIN KAI TSAYE*๐
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya๐
0810 433 5144
Masu tura katin MTN๐
0814 179 9224
ฦณan ฦasar Niger zasu tura nasu anan.๐
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huษu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ษaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐๐ฉโโค๏ธโ๐จ
*_Miss Hajo ce_*๐ค๐ฟ
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: ๐จโโค๏ธโ๐จ *AUREN WATA TARA* ๐จโโค๏ธโ๐จ
```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*
*BONUS PAGE*๐๐ฟ๐
๐
ฟ๏ธ........*55 & 56*
Washegari MD yana zaune yana hutawa a palour Amera na gefenshi suna zuba love Wayarshi tayi ringing dubawa yayi yaga Baba audu ne mai kula da tsohon nan na gombe cikin Sauri ya d'auka banji komai akace daga bangarenba saigani nayi ya Mike a matuk'ar firgice ya ce "Alhamdulilla Alhmdullillah Allah mungode maka gani nan zuwa yanzu " yana gama fad'ar haka ya katse kiran daka Kallesa kasan yana cikin farinciki Kallonshi Amera tayi ta ce "Honey ya naga ana kiranka duk kabi ka wani rude " Murmushi ya sakar mata ya ce "wani abun farinciki ne ya sameni " Da Fara a fuskarta ta ce"daga ina "Murmushi kawai ya sakar mata yace " zakiji idan na dawo "yana gama fad'ar haka ya fita da Kallo ta bishi kafin ta tab'e baki MD na fita jaber ya kira Inda Yayi mishi albishir kamar yanda Baba audu yayi masa a Airport suka had'u Ba bata lokaci jirginsu ya d'aga gombe kamar ko yaushe gidan suka isa sosai MD yayi farincikin samun lafiyar Baba a palour suka sameshi shida Baba audu da Matar shi tunda ya shigo Baba tsoho ya kafeshi da idanu sai Murmushi yake sakar masa Shima MD murmushin ya sakar masa Bayan sun zauna cike da girmamawa yace " ina yinin ku Baba"Lafiya qalau Yaron kirki anzo lafiya"Alhmdllh ya jikin Baba "ya fad'a yana kallon shi " Da murmushi a fuskarsa ya ce "Alhamdulilla yaron arziki hakika bani da bakin da zan gode muku a bisa ceton rayuwata da kukayi kunyimun abunda babu abunda zan iya cewa daku saidai fatan samun aljanna kuka ne yaci karfinsa cikin Sauri MD ya tashi ya koma kusa dashi tare da dafoshi ya ce " Dan Allah Baba kayi hakuri yau ranar da ya kamata kayi farinciki ne fiye da kowace rana tsawon shekaru Ashirin da wani abu kana kwance yau Allah ya tasheka ai farinciki ya kamata kayi Baba karka damu da abunda nayi maka ka daukeni tamkar jikanka Dan Allah kayi shiru bazanji dad'in ganinka kana kuka ba "Goge hawayen shi yayi ya ce " dole nayi kuka yaron nan tsawon shekara ashirin da wani Abu ina kwance kai kake kula dani sha na magani na da komai ai dole nayi kukan farinciki kafin ya damki hannunshi ya ce "Allah yayi maka albarka yaron nan yasa ka gama da duniya lafiya ya kareka daga sharrin makiya da mahassada ,Allah kareka daga sharrin makiya na jikinka da Wanda bana jikinka ba ,Allah raba ka da sharrin mahassada ,Allah ya biyaka da gidan Allah Nama rasa wace irin addua zanyi maka kayimun abunda Bazan tab'a mantawaba dashi ba a rayuwa kayimun abunda babu Wanda ya tab'amun a rayuwa Allah sa ka gama da duniya lafiya" Ameen kowa ya amsa nan yayita Jerawa MD adduo'i Bayan komai ya lafa an gaggaisa Jaber ya kalli tsohon ya ce "Baba ka tuna shekara ashirin da biyu da suka wuce abunda ya faru mun tsineka ne yashe a gefen titin a hanyar jigawa dajin Allah mukuma a lokacin ni da Amini na ya fad'a yana nuna MD da yayi k'asa da kansa ya ce mundawo daga garin kenan Wani bikin dangin mahaifi na da Abokina yayimun rakiya kasancewar tare muka taso tun yarinta a lokacin bamu da wasu shekarun kirki lokacin da muka tsinceka da farko mun tsorata Da ganinka Dan dajin nan babu alamar mutum a ciki Sai kukan tsintsayi da namun daji dak'yal dai mukayi shahada muka tsinceka kai tsaye wani local government da muke kusa da garin muka nufa dakai mai suna kazaure Inda muka kaika Asibiti da farko d'aukar mu baka da rai saida likitoci suka fara aiki akanka kafin Su fara ceto rayuwarka Satinmu guda a asibitin kazaure ganin ba wani cigaba sosai ya sanya muka wuce Asibitin kano dakai kasancewar munsanar da iyayenmu kuma suka kara mana karfin gwuiwa akan taimakon da mukayi yasa bamu samu wata matsala ba dukda kasancewar mu ba wasu manya ba watanka guda bakasan Inda kanka yake ba saboda saida akayi maka aikin Harbin da aka maka kafin Allah ya taimaka ka farfado koda ka farfado Kalmar farko daka furta shine a " Karku kasheni me nayi maka kake son hallaka rayuwata da ta iyalina"Dak'yal muka samu kabar sabbatun dak'yal ka yarda damu a lokacin Dan mun fad'a maka taimakonka zamuyi ka tambayemu a ina kake "Muka fad'a maka kano" Cikin tsananin rud'u ka ce "Ku fiddani daga garin nan indai taimakona kukeso Kuyi zai iya zowa har nan dinma ya kashe ni ina ina " Mamy Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Allah kasa bai kashe mun Mamy ba "Abunda kake maimaitawa kenan duk ka firgice akan Sai an fitar dakai daga kano saboda zasu iya biyoka nan yayi kusa da garinku " Ganin hakan duk hankalinmu ya tashi kuma muka lura kamar akwai wadanda ke harin rayuwarka rasa Inda zamu kaika mukayi gashi dukka firgice gombe shine garin da ya fadowa MD a rai a haka muka nufo gombe dakai Inda ya saya wannan gidan sannan ya samu wasu miskinai dashi da matarsa suna buk'atar wajen zama ya d'aukesu akan zasu kula dakai saboda tun sanda muka shigo garin kayi loosing memory a fahimtar mu ka manta komai sannan kuma ka daina magana wadannan mutanen su Suka dinga kula dakai da taimakon MD da adduo sa sadakokin da saukar qurr ani da aka dage Dan saidaga baya muka lura abun kamar akwai sihiri "Tofa kaji Baba a yanda muka sameka fatan kaima zakayi mana bayanin musan asalin waye kai" Tunda aka fara maganar yake Hawaye Kallonshi kawai su MD suke saida yakai karshe kafin ya d'ago ya ce"Na tuna lokacin nan yaron nan Wanda daga lokacin ban Kara sanin Inda kaina yake ba sai shekarun baya hud'u zuwa biyar Saidai bana iya komai sannan Ko nayi kokarin magana bana iyawa Bazan iya fada maku Tarihin rayuwata ba saboda tuno abun tamkar fama tsohon raunin da ke cikin zuciya ta Wanda bazai tab'a gogewa ba har abada Zadai ku iya sanin suna na "Abdussalam"Kuma haifaffan garin jigawa Wanda a halin yanzu babu garin da na tsana bana fatan ko wuce hanyarshi sama da garin nagode da taimakon da kukamun Saidai bazan iya fada muku takaicin labari na ba " Duk numfashi sukaja Inda MD ya ce "Karka damu Baba basaimunji komai ba yanzu ina kake son zama mu koma garinmu tare da Kai watau kaduna" girgiza masa kai yayi ya ce "A a yaro ka barni a nan hankali na yafi kwanciya a nan din " Ajiyar zuciya MD ya sauke yace shikenan Baba ba matsala saika zauna tare da su Baba audu koko a saya maka sabon gida idan kafison zaman kai d'aya "hawaye a fuskar sa ya ce " A a a nan dinma yayi indai ba takura su ba"Cikin Sauri Baba audu yace"ai muma bazamuso ka tafi ka barmu ba munriga ansaba "matarsama dattijuwa tace " Gaskiya kam an saba "MD bai bar garin ba saida ya bar musu mak'udan kudin da zasu buk'ata nan gaba sannan ya sanya aka sayowa Baba waya da sim Dan sun dinga gaisawa a hanya sai Farinciki yake yana mamakin wani irin Abu ne akayiwa tsohon nan da har yake gudun garinsu na haihuwa shi kanshi saboda tsaron tsohon ya sanya yake tahowa a sirrance koda suka isa kd har dare ya fara gidansu ya fara zuwa yayima Ammy albishir da samun lafiyar Baba Inda ya bata labarin abunda ya basu a takaice sosai Ammy tayi farinciki kuma tayi adduar Allah ya k'ara masa lafiya ta ce Insha Allahu Zata samu lokaci taje ta ga jikin nasa daga gidan ammy gidansa ya wuce lokacin Amera hartayi bacci saida ya shiga d'akin ta gane yadawo cikin hammar bacci ta mik'e ta ce " yaushe ka dawo honey"yanzu harkinyi bacci kenan"wlhko na gaji da jiranka na kwanta wai ina kaje haka "Wani waje ina tsohon nan da nake baki labarin mun tsinceshi da dad'ewa tun kafinma muyi Aure " Eh nagane"Shine ya warke ya samu lafiya"Tab'e baki Amera tayi ta ce "Kaidai honey baka gajiya da kwashekwashe wlh a tunanina tuni ka wurgar da talakan tsohon nan saikaje ka kwaso mana alkakai daga tsintar mutum a titi kawai ka daukeshi ka dinga hidima dashi Haba wannan Abu Dame yayi kama sai wahalshe da kanka da kayi ba dangin iya bana baba Nifa banason harka da talakkawa wlh Haba su goga maka karnin talauci " ta fad'a tana yamutsa fuska"girgiza kai kawai MD yayi Dan baiyi mamakin abunda ya fito daga bakin Amera ba Tun fil azal ita daman ta tsani talakka Wanda hakan d'abi'ar da ta taso da ita daga gidansu ne duk yanda yaso ya sauya ta amma hakan ya gagara "Baice mata uffan ba sai rage kayan jikinshi da yayi yanajinta tana gunguni a haka har yaji ta koma bacci girgiza kai kawai yayi yana mamakin yanda Amera ta tsani talaka take wulakanta mutane da batasan darajarsu ba " Bayan ya watsa ruwa gefenta ya kwanta baccin gajiya ya daukesa..washegari around 11 dare MD na kwance Amera na gefenshi tana chat da kawayenta Sai dariya take shiko ya lumshe ido babu wacce ke fad'o masa a rai sai Zarah a Gaskiya yana da buk'atar ta koba komai tana bashi abunda baya tab'a samunshi a wajen Amera koda kuwa zai shekara suna Abu d'aya "Lumshe ido yayi ya bud'e sai yaji Yana son jin muryarta tsaki yaja a ranshi , "Tunani yayi yanzu ai ko yaje zaria suna Hutu tunda ba sanin garin da take yayi ba Yasan dai tunda take zaman hostel to ba yar garin bace Kallon Amera yayi dake gefenshi tana chat ya ce " My Merah chat d'in ya isa kizo mu kwanta"Sorry honey ka kwanta wani labari ne luzy take bani ba yanzu zan kwanta ba "Shiru yayi bai kuma ce mata komai ba " Duk yanda yaso bacci ya d'auke sa kasa daukarsa yayi saboda a matuk'ar bukace yake sai wajen 12:00 yaji kwanciyar Amera janyota yayi jikinshi koya rage zafi Amera najin haka ta ce "Haba honey Dan Allah ka barni na gaji Wlh bacci nakeji" Kyaleta MD yayi badan komai ba saidan bayason takurata a ranshi yana mamakin saita dinga cewa ta gaji saikace wace ke wani aikin wahala na farko dai ita ba ma'aikaciya ba,ba y'ar kasuwa ba,ba wani aikin gida take ba macen da ko shara bazata ce ta tabayi ba ,Amma duk dare saita gama chat d'inta da kawaye tace ta gaji"Da wannan