Showing 93001 words to 96000 words out of 153980 words
musu ta shiga horn yayi mai gadi ya bud'e masa get tsit kakejin motar shiru bamai magana har suka isa cikin Makarantar daidai sanda yayi parking Dagowa yayi ya Kalleta daidai Shima ita d'in yake kallo Saurin kasa da kanta tayi "saida sukayi kusan 10 minute bame magana cikinsu kafin MD ya damko hannunta ya sanya mata takardar A hannunta Dagowa tayi tare da kallonsa ta kalli takardar hannunta da bai saki hannun ta ba har lokaci Bayan few minutes ta tsinkayi muryarsa da cew" Murna kike zamu rabu ko"Shiru Zarah tayi gabanta na fad'uwa "Murmushin da batasan ma anar sa ba taga ya sakar mata tare da sakin hannunta ya ce " Ina ne garinku?Shiru tayi saikuma ta ce"basaikaji ba"wani murmushin ya kuma saki ya ce "Bakison na halarci bikin naki kenan?Gyada masa kai tayi alamar eh"muga wayarki ya fad'a tare da amsa kwafar numberta yayi ya sanya a wayarsa Wanda duk bata lura da hakan ba kafin ya mik'a mata ya ce " Gashi Amarya sai wataran"Amsa tayi sosai tayi sanyi" Bud'e gaban motar tafi tare da fita a hankali harta fita MD baibar kallonta ba Itamadin so take ta Kallesa amma nauyi ya hanata Tanajin tashin motarsa ta juya ta dinga Kallon motar har ya bar wajen a sanyaye tayi hanyar hostel Asmy kadai ta samu a ciki tana ganinta ta taso tare da cewa "Ya sakeki dai ko?A sanyaye Zarah ta gyad'a mata kai" Alhmdllh "Asmy ta fad'a Tana shirin amsar takardar Zarah ta rik'e cikin rawar murya tace "bari na fara karantawa " Gabanta na fad'uwa ta warware takardar abunda ta gani ne a ciki ya kusan tarwatsa kwalwarta saida ta gama karantawa tsaf hannunta har karkarwa yake batasan sanda takardar ta zame kasa ba durk'ushewa a wajen Zarah tayi tare da fashewa da wani irin kuka mai cin rai kamar wacce aka aikowa sak'on mutuwa d'ora hannu aka tayi ta ce...✍
07026166536
*JUMA'AT KAREEM*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Miss Hajo ce*_: 🤙🏿
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️.........*67 & 68*
"Sati Ukku fa baba"ta fada idonta na cikowa da k'walla " eh sati Ukku muka tsaida saboda shekara hud'u ba wasa ba munriga munshirya komai na biki da kayan daki tuni na tanada komai Saidai jiran rana Kina da matsala ne da hakan"Goge hawayen tayi ta ce"a a a Baba naga yayi kusa ne"Murmushin dattaku Baba yayi ya ce "baiyi kusa ba Zarah Iyayen yaron sun nuna yana son ne ayi abun wurwuri shiyasanya muka barshi a haka din " kasa tayi da kanta saida Baba ya k'ara mata nasihohi sosai kafin ya bata umarnin fita Zarah kamar jira take yace ta fita tana zuwa d'akinta tayi rubda ciki ta fashe da kuka Cikin kuka take cewa "Na shiga ukku ya zanyi da rayuwata taya ina musulmai zan yarda A daura mun Aure Bayan akwai Auren wani a kaina sannan ba idda ba komai ka cuceni Musty tsakanina dakai Sai Allah ya isa mugu azzalumi" Sosai take kuka Daren ranar bacci sai barawo ne ya d'auke ta washegari koda ta tashi da ciwon kai ta tashi saboda kukan da tasha Bayan tayi wanka d'akinta ta koma Dan yanzu kwata kwata zaman gidansu baya mata dadi Khairat ce Daman Suke Dan Hira da ita gashi itama Bata gidan bare Safiya yunwa takeji Amma tashin hankalin da take ciki tasa ta manta da abinci sosai ta Lula duniyar tunani "tana cikin wannan tunanin Asmy ta shigo saida ta daddabata tasan da zuwanta Firgit tayi ta mik'e tare da kallonta da Itamadin ita take kallo a sanyaye Asmy ta ce " Kinji Sati ukku aka sanya Aurenki da Hafiz yanzu nakeji wajen Mama"Naji"zarah ta fad'a kamar zata fashe da kuka "Tagumi Asmy tayi tare da lulawa duniyar tunani Wanda itama Zarah tagumin tayi Sunkai minti goma ba Wanda yayi magana kafin Asmy ta ce " nayi Danasanin *Auren wata taran* wannan da Akayi Zarah Bacci da idona jiya ya gagareni nasan duk ni na ja maki wannan tashin hankalin ji nake inama akaina wannan Abun ya faru bake ba Zarah akwai babbar matsala Bazaiyu ayi Auren nan ba muddin bai sakeki ba sannan koya sakeki dole saikinyi idda "murmushin da yafi kuka ciwo Zarah tayi Dan yanzu idanunta sun fara k'afewa da kukan ta ce " Hmmmm"Hawaye na sauka daga idon Asmy ta kamo hannunta ta ce "Dan Allah Zarah ki yafemun da nazama silar shigarki wannan hatsarin wlh tallahi da nasan haka zata faru da ko makamanciyar haka bazaiyu ba A lokacin sonki da tsoron rasaki ya sanya harna amince da Auren nan bansan abun nan zai zama Haka ba Zarah na cuceki naci Amanar.....rufe mata baki Zarah itama hawayen take ta ce " Kidaina cewa haka Asmy wlh ban rik'e ki da komai a zuciya ba na d'auki hakan a matsayin kaddarata kidaina cewa haka Wannan din ya zama sirri a tsakanin nidake karmu sake wani yaji labarin nan Asmy mun tafka Babban kuskure duk laifi na ne "Ba laifinki bane Zarah laifi nane yanzu menene mafita kwana nayi ina tunanin mafitar da zamu samu Amma kaina ya kulle" Bamuda mafitar da ta wuce Addua Komai ya Riga ya lalace Mafitarmu d'aya Allah shi kadai zamuyi ta roka Dan ba abunda yafi karfinsa shine kawai zai kawo mana mafita"cewar Zarah "wayarta ce tayi ringing kamar bazata dauka ba saita d'auka tana ganin Hafiz ne saida gabanta ya fad'i saida ta kusa gama ringing tukwana ta d'auka tana daidaita muryarta karya gane tana kuka " A sanyaye ta gaishesa ya amsa cikin so kauda tare da shaida mata yana k'ofar gidansu"ina zuwa"ta basa amsa tare da katse kiran kallon Asmy tayi ta ce "Hafiz ne yazo" Okay gyara fuskarki mu fita tare daman Mama tace mutaho tare saina wuce gida idan kin sallamesa kije gida Mama na nemanki"To"Zarah ta fad'a tare da mik'ewa saida ta wanko fuskarta kafin ta dawo ta sanya k'atuwar hijab d'inta Tare suka fita da Asmy Bayan Asmy ta gaishe da Hafiz tana shirin barin wajen ya ce "a a dawo babbar kawar Amarya ai wannan zuwan Naku ne ku biyu Naga Amaryar tawa bata shirya ba har yanzu gwara mu mu fara shirin karmu biya tata" murmushi Asmy tayi ta ce "Hakane kam" Zarah ko bata tanka ba saboda wani iri da take ji"Mota Hafiz ya shiga Ya d'auko invitation masu yawa mik'awa Asmy yayi ya ce "gashi Dan ku fara rabo da wuri" Saida Asmy ta wara idanu kafin tayi Dariya ta Ce"lallai ango wannan zumudi haka invitation da wuri to shikenan"murmushi yayi ya ce "Ai dole nayi zumudi kam Abun shekara hud'u ya rage sati Ukku ina zama ya ganni" hakane kam to Allah ga kaimu "Ameeen Sai Maganar event ko walima da kukeso Kuyi duk abunda kuke buk'ata ki rubuta gobe idan nazo saina amsa" To shikenan ranka ya dad'e"Asmy ta fad'a"Bayan barinta wajen sai sannan ya maida Kallonshi ga Zarah da tayi kasa da kanta cike da kulawa ya ce "Yadai my wife lfy?lafiya qlau ya Hafiz Ina kwana" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Alhamdulilla an kammala sch lafiya ko to Allah ya taimaka jiya din naso zuwa wlh Wani kiran gaggawa ne akamun katsina shi ya hanani zuwa am sorry Kyautarki tana gida na mance da ita " murmushi ta kirkira ta ce "Ba komai Ai " Duk yanda Hafiz yake yiwa Zarah Hira kin sakin jiki tayi dashi Ganin hakan yasa ya tafi saita d'auka ko kunyarsa ce takeji Dan ya Santa akwai kunya Koda ta shiga gidansu Asmy Bayan ta gaishe da mamansu nan ta zaunar da ita ta fara bata magunguna Wanda tunda ta bata Zarah ta fahimci na meye ba ason ranta ba ta fara sha sai Dan batason yi mata musu Bayan nan ta d'ora tayi mata dilka ta amare sosai ita kanta tayi mamakin karuwar sanyin na Zarah Saita lak'anta hakan da Bikinta dake karasowa tundaga ranar kullum Zarah tana gidan su Asmy mamansu tana yi mata Dilka da magungunan gyara bangaren Mama Rabi ko Sosai Zarah tayi mamakin yanzu wani mutunci da take mata ba zagi ba komai har tana mata maganar shirye shiryen biki itama ta bata invitation tayi tata gayyatar ranar Zarah sossai mamaki ya cika ta Nan ta d'auko invitation din da chungum din da ya kawo mata daga baya ta bata tana mamakin wannan saukowar mutuncin na Mama Rabi na lokaci guda bangaren Baba ma sosai yayi mamakin yanda take nan nan da bikin kamar za ayi bikin diyarta a tunaninshi Zatayi bakin cikin kayan d'akin da akayiwa Zarah saiyaga itace mai cewa ma a k'ara wani abun ayi Abu na fita kunya sosai a ransa yaji dadin sauyawar tata har yana murnar kila yanxu ta sauya hali.
Kallo d'aya zakayi masa ka lura yana cikin tsananin damuwa har wata rama yayi idonshi lumshe kamar mai bacci nanko tunani ne chunkushe a ransa Ya Lula duniyar tunani yaji wayarsa tayi ringing saida tagama ringing bai daga ba wani kiran ya k'ara shigowa kamar bazai duba ba saikuma ya janyo wayar a hankali tare da Kallon screen din wayar Ganin number Ammy ce ya sanyashi saurin picking a sanyaye ya gaishe ta ta amsa masa ba yabo ba fallasa tare da cewa "kana ina?Ina Abuja " Okay to kazo Hajiya na nemanka "yana kwance baisan lokacin ya Mike zaune ba a matuk'ar makance ya ce " Hajiya kuma Ammy tazo garin ne?Eh tazo tun jiya kuma tace kome kake karka wuce gobe bakazoba"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un "ya shiga maimaitawa a cikin zuciyarsa Ammy bata jira amsarsaba ta kashe wayarsa dafe kansa dake tsananin sara masa yayi ya ce " Oh my god"Ya Hajiya takeso nayi da rayuwata ne Wai,dalilinta na shiga halin da nake ciki yanzu kuma ta k'ara zuwa ta k'ara jagula lissafi cikin Sauri ya lalubo number Amera ringing biyu ta d'auka "bai saurari abunda take cewa ba ya ce " kome kike kiyi gaggawar dawowa gida kafin nan kafin 12:na ranar gobe "Daga bangaren Amera ta ce " Subhanalla honey lafiya"Lafiya nadai fad'a maki ki baro k'asar nan "Saboda me honey wlh gobe ake fara bikin Chichilayo" MD ji yayi kamar ya shak'eta da wayar baisan lokacin da yace "uwar bikin chichilayo Dan Iskanci ina Miki maganar Serious zaki sakomun maganar wata tsinanniyar arniya ki zauna karkizo ki saurari abunda zai faru kishiyar da bakiso ita zaki tarar"Daga bangaren Amera wani irin bugawar zuciya taji batasan lokacin da ta fashe da kuka ba Ta ce " nashiga Ukku ni Sadiya me kake nufi honey bangane yaren naka ba "Tsaki yaja ya ce " ki sameni a Abuja gidana Dake life camp buzu quarters Hajiya tazo kuma kinfi kowa sanin zuwanta"yana gama fad'ar haka ya katse kiran yana jan tsaki Sosai yakejin haushin kansa da na kowama yanzu ta ina zan nemo yarinyar nan?ya tambayi kansa "lumshe ido yana tuno da Dadin yarinyar lokaci guda mood dinsa ya sauya dak'yal ya iya hada ruwan tea tare da matsa lemon tsami kusan goma Dan tun Bayan rabuwarsa da ita kullum saiya sha sa yake iya samun bacci ga tunaninta da yaki barin kwalwarsa daidai da second guda washegari tun karfe shida na safe MD yaji bugawar part din da yake tundaga bedroom dinsa yajiyo saboda wani irin knoking da ake da karfi jallabiyarsa ya zura tare da fitowa palourn yana bud'ewa yaci karo da Amera kallo d'aya yayi mata yasan a matuk'ar firgice take ga idanunta da sukayi ja jawur Fadowa jikinshi tayi tare da fashewa da wani irin kuka mai tsananin gaske sosai take kuka kamar ranta zai fita Wanda MD Jin kuka nata yake har cikin ransa sosai ya tausaya mata wannan nadaga cikin abunda yasa ake ganin kamar Amera ta gama dashi Bayason ganinta cikin wannan halin hakan yasa ko maganar Karin Aure bayaso Daddab'a bayanta yafara cikin sigar lallashi Dak'yal ya samu har suka k'arasa palourn Inda ya zaunar da ita Cikin kuka ta ce " Honey karkaga tashin hankalin Dana shiga ban iya bacci ba Jiya da Daren da ka kirani na tafi Airport Sai 1am jirginmu ya tashi dak'yal na iya kawo kaina nan honey mutuwa zanyi a kanka "Numfashi mai zafi MD ya fesar kafin ya d'ago ya Kalleta ya ce " kibar kukan nan bashi da amfani kalleni muyi magana ta fahimta "Cikin Sauri ta Goge hawayen tace ina sauraranka honey" Hajiya ce tazo kuma take nema na kinsan zancenta bai wuce na Rashin haihuwar da banayi akan na k'ara Aure to shine nake son mu samawa Kanmu mafita tun kafin Abu yazo yafi karfinmu kinsan halin Hajiya sarai"ya nemu ya biye mata maganar ta ta baya Dan karta k'ara shiga tashin hankali "Dukda haka saida hankalinta ya tashi cikin kuka ta ce " to yaya zamuyi Honey ina mafita Bansan yanda zamuyi da ita ba ni kaina na k'agara naga jini na Ina son haihuwar nan fiye da yanda baka zato honey Allah ne bai bani ba "ta k'arasa fad'a cikin kuka " cikin sigar lallashi ya ce "Akwai mafita" Firgit ta d'ago ta Kallesa ta ce "Wace mafita ce Honey" Zamu cewa Hajiya kina da ciki zamuje tare yanzu kiyi pretending din ciwo akwai maganin da zakisha Zai sanyaki amai Dan duk su tabbatar da abun kafin mu nemu mafita"cikin tsananin mamaki ta ce "Idanfa suka gane honey nan gaba Bayan munsan ba cikin garan ba" Ajiyar zuciyaya ya sauke yace kibarmun sauran abunda nakeson kiyi yanzu kenan kawai"Nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Shikenan honey zanyi hakan Allah yasama na samu cikin gasken kafin Su gane" Murmushi ya sakar mata ya ce "Ameeen My Merah" k'arfe 11am tayi musu a Palourn Ammy a lokacin kowa na palourn har Hajiya Har Aunty Zey da tazo Bayan an gaggaisa Amera ma wannan Karin cikin ladabi ta gaishe da su Hartana tambayar Zey ina su Mema Zey Ta ce "suna gidan kakarsu sunje mata yini" masha Allah na kwana biyu bangansu ba ai da sun yarda da sunyi mana Hutu muma"Murmushi zey tayi ta ce "Aikam dai" Chuchu ta k'asar ido take Hararar Amera a ranta ta ce "munafuka batayi mamakin yanda ta gaisa da zey ba saboda daman Chan ita Zey kamewa gareta har mutane suna cewa duk gidansu itace mai girman kai hakan yasa Amera ke shakkarta Dan tasan halinta ba shiga harkar mutane take ba Amma aka shiga tata akwai masifa " Ammy ce ta ce "Chuchu ki kawowa Amera abun Tabawa mana ga Alamun sunshawo hanya" Badan Chuchu ta so ba ta tashi tare da dauko mata juice ta koma Inda take tana Danna waya A cup Amera ta zuba ta fara sha tana cikin sha taji maganin da MD ya bata a mota ya taso mata cikin Sauri ta Aje cup din tare da yamutsa fuska "Ammy ce dake lura da ita ta ce " Lafiya dai ko?Tana yamutsa fuska tace "Naji Inajin amai....bata k'arasa fad'a ba Taji ya tunkaro mata da gudu ta Riga toilet din palourn nan ta fara kakarin amai harta samu ta danyi Kad'an Duka mutanen dake cikin palourn da Kallon mamaki suka bita Hajiya ta ce " Ikon Allah itafa wannan aman me take"Shiru MD yayi ya kyale ta "Har Amera ta fito daga toilet din tana Murmurdewa irin anji jikin nan cike da kulawa Ammy ta ce " Sannu yaushe kika fara irin haka?nafi sati biyu ina yi amma kwanannan yafi matsamun?kuma kunje Asibiti "?girgiza kai tayi ta ce " a a a Ammy bamuje ba"Hajiya ce ta ce "Kinji sakarkaru abunda ake nema shekara da shekaru ya samu shine zaku watsar kunjimun Sakarkarun yara kai kasan da haka shine baka sanar mana tun wuri ba " MD yasan sarai da shi Hajiya take ya kauda kai yana maida Kallonshi ga television "kaji da mugun halinka dai Hajiya ta fad'a tare da Kallon Amera ta ce " Sannu ko bari a kira likita ya duba ki "Murmushin jin dadi Amera tayi ta kwanta kan doguwar sopa tana maida numfashin karya Kallon Ammy Hajiya tayi ta ce " Fatima kirayo likita yazo ya duba yarinyar nan Allah sa abun alkhairi da muka jima muna jira ne ya samu"Murmushi Ammy tayi ta ce "To Hajiya " Nan Ammy ta kira Family Dr d'insu Akan tanason ganinshi zai duba patient "Har lokacin MD hankalinsa gabak'i baya ga y'an d'akin Har Dr yazo Wanda gaisawa kawai sukayi da MD ya shigo Inda Hajiya tayi masa bayanin gwajin da zaiwa Amera nan ya shiga gwadata Inda ya dauki jininta da awon fitsari yaje baima bar gidan ba ya tsaya a mota Bayan few minutes ya dawo rik'e da paper da murmushi a fuskarsa Hajiya na ganin haka ta washe baki ta ce " Kardai kace mun ciki ne Dr "Da fara a a fuskar Dr ya ce"Tana dauke da cikin Wata Biyu " Ai gudar da sukaji Hajiya ta rangadane ya kawo kowa ya maida hankalinta Wajenta "Alhmdll Alhmdllh Allah nagode maka ranar da nadade ina jira gashi tazo da raina da rayuwa kai amma yau rana ce da bazan tab'a mancewa da ita ba a rayuwa ashe da rabon zanga jinin Mustapha a rayuwa kai Allah na gode Maka " sosai Hajiya ta shiga sabbatunta na murna Ammy ma ita kadai tasan farincikin da ta shiga haka su Chuchu da Zey MD ta ido yayiwa Dr d'in jinjina Irin aikinsa yayi kyau murmushi dr yayi masa "Hajiya ce ta kalli MD da babu Alamun yayi farinciki da