Showing 129001 words to 132000 words out of 153980 words
feeding d'insu dukda taji zafi da kunyar ammy haka dai ta daure saboda k'aunar yaran da takeji ta musamman washegari zahra ta dawo normal ta dawo hayyacinta har tana iya zaunawa a danyi Hira da ita dukda nauyin Ammy da maman su Asmy da takeji MD ko ko kallo bai isheta ba Koda yayi mata ya jiki a takaice ta amsa masa da yawwa Wanda baijin dadin hakan ba Ganin yawan matan a d'akin yasanya suka fita shida Jabir shi kanshi Jabir ya girgiza da jin zahra tripplet ta Haifa Sai sannan MD hankalinshi yadan kwanta ganin jikin zahra da sauki sai sannan ya fara tashi sayayyarsa Wanda ba iya yaran yakeyiwa ba hada Momynsu Hajiya ma ranar tazo zo kuga murna da doki Da farinciki Saidai tayi mamakin da ba Amera ta gani ba Koda ta tambayi Ammy ya haka ce Mata tayi kiyi hakuri Hajiya idan muka koma gida za ayi miki bayani su Asmy da mamansu kullum sai sunzo sai yamma suke tafiya Funtua sosai aikin na zahra yayi kyau a kwana na hud'u aka sallamesu suka koma gida Inda Ammy ta ninka kulawar da take mata kafin kace me labarin haihuwar Tripple. D'in MD ya baza gari har internet sosai abokan arziki suke kiransa abokanan kasuwansa dama manya suna kiransa suna masa Barka har gajiya yake da d'aukar wayar wasu daga cikin y'an uwan Ammy ma.dake.india duk sunzo banda y'an uwan Abban su MD na Maiduguri suma sosai suka taho kwansu da kwalkwatarsu ranar daga Ammy sai Hajiya ta labartawa mata abunda MD yayi Dan shaida har videon d'aurin Auren ta nuna mata "Maimakon Ammy taga Hajiya ta daga hankalinta saitaga ta sauke ajiyar zuciya ta ce " na godewa Allah da ba a hanyar banza akayi cikin ba daura Aure sukayi dukda ba Abi shara'a ba Amma Naji dad'in ma da Ba wacce y'ar iskar ya haihu da ita ba yarinyar mutunci mai tarbiya da nutsuwa ta haifa masa kuma insha Allahu zahra saita zama tauraruwar mustapha saita kwacesa daga hannun waccen yar iskar yar marassa tarbiya da izinin ubangiji saiya so zahra ya kaunaceta tamkar ransa"Girgiza kai kawai Ammy tayi a ranta ta ce " hakan ta faru da nafi kowa farimciki "kafin ta ce " Ni yanzu damuwata Hajiya bansan me zancewa mutane ba"Barni dasu ni nasan me zance musu zance matarsa ce Zuwan da nayi na aura masa jikar Aminiya ta akwai ubanda ya isa ya ce Ba haka ba "Ajiyar zuciya Ammy ta sauke ta ce Hakane " Haka ko suka fad'awa mutane wanda ba Wanda bai yarda da hakan ba Saidai suce ba a gayyacesu bikin ba Nanfa aka fara shirin yin suna Wanda sosai MD yake rawar kafa ganin mutane sun fara yawa gashi baya samun damar ganin Zahra saboda d'akinta Ammy ta sauketa take kula da ita saboda d'inkin ta Saida ya kira Chuchu ta d'auko masa yaran idan ya gama liliyarsu ya bata ta koma dasu sosai yakeson ganin ,Zahra amma ba dama dinkuna masu kyau Chuchu da Zey suka kaiwa zahra kala"_kala tamkar Lefe kowa dai sai yaba amayar ta MD yake a yanda Ammy tayi musu bayani Asmy ko nan ta dawo take kwana Saboda kula da aminiyarta mamansu ma kullum sai sunzo Dukda sanyin da zahra tayi ana jibi suna Bayan MD yazo part dinsa na gidan yake sauka daman saboda mutane Chuchu Ya kira lokacin tana gefen Ammy dake bawa Babyn ruwa Ya ce "Ki kawo mun triple yanzu " To yaya gani nan"Ammy dake jinsu ta ce "Kice masa Bazaiyi musu hud'u ba " Daga bangaren MD yanajinta ya ce "Kice Hudubar ce zanyi musu" Kallon Ammy tayi ta ce "Yace hud'ubar ce zaiyi musu" Mika mata shi Ammy tayi ta ce "Saiki kai masa su" Zahra ko tanaji tasan da Wanda ake waya daga kwanciyar da tayi ta rumtse ido Tanajin wani iri a ranta rukayya ta dauki d'aya Chuchu ta rik'e biyu koda suka isa part dinsa Gaisheshi sukayi Tare da mik'a masa su "Kamar ko yaushe saida yayi musu addua Sannan yadanyi musu wasa kamar wasu manya Kallon su Chuchu dake shirin fita yayi ya ce " Ku jira ku koma dasu "Dawowa sukayi suka zaune sunzaci y'an mintuna ne amma saida suka kusan shafar awa suna jiransa ga ba damar su tafi saida ya gama liliyar yaranshi ji yake kamar kar atafi dasu Bayan yayi musu Huduba sai sannan ya ce " Zoku tafi da su "Cikin Sauri Chuchu taje ta amshe Su tana Dariya ta ce " Yaya me ka sanya Musu "Namijin d'aya fara mik'a mata ya ce " Yusuf"Sannan ya mik'a mata dayan ya ce "Shi kuma sunan Abba" Macen ya mik'awa Ruqayya ya ce "ita kuma Ammy" Wow Chuchu ta fad'a ta ce "Aiko yaya Harnayi musu nickname " Akhbar,Amar,Ammy kuma little zahra"Murmushi yayi mata ya ce "sunan yayi chuchun yaya Amma takwarar Ammy a sauya bazanso a dinga kiranta da sunan haka ba " hakane yaya Amma ai kaga Ammy ba zahra ake ce mata ba Fatima ake Ce mata"baice komai ba sai lalubo wayarsa da yayi ya ce "Zan miki transfer 10 millions "Kafin jibi ki shirya kayan da za a bawa bak'i jakunkuna, calendar, Turamen atamfofi super Holland da duk abunda kikaga za a raba karki sake ayi harkar karanta kafin gobe komai yazo sannan Jabir yayi wasu jakunkunan anjima zai kawo miki tare da wayoyin da nayi order daga compony duka a sanya a jakar rabon ki tabbatar komai ya tafi successful idan kudinma basu isaba kiyimun waya zanmuku transfer wasu " insha Allah yaya komai zaitafi yanda ake.so"Ajiyar zuciya ya sauke tare da Danna mata transfer Take suka shigo wayar Chuchu koda suka koma Ammy ta tambayesu ta ce "Me.Ya sanya musu" Cikin doki Chuchu ta ce "Ammy baby girl din takwararki ce kuma takwarar momcy Baby boys din kuma wannan Yusuf (Akhbar) wannan kuma Takwaran Abba (Amar)Murmushi Ammy tayi ta ce " masha Allah Ubangiji ya raya "Zahra tana daga kwance kamar tana bacci sosai tayi mamakin karar da yayi mata na sanya sunan mahaifinta tunowa da Baba da tayi ko yana wani hali yanzu ya sanyata Goge hawaye Wurinta Chuchu tayi ta ce " Tashi momcy kinji sunan yaran yayi ko "Bud'e ido tayi a hankali tare da sakar mata murmushi Dan bazata iya magana akan yaran gaban Ammy ba Sai gyada mata kai tayi alamar sunan yayi Ranar suna tunda safe aka yanka gardama gardaman shanaye Guda goma.reras raguna shidda Wanda naman shanayen.duk sadaka aka babbada gidajen marayu da gajiyayyu Sosai MD.ya taka rawar gani a wannan sunan y'an uwan Shima haka uwa uba Ammy data k'asa zaune ta kasa tsaye zahra ko duk yanda bataso tayi kwalliya ba saida Chuchu ta sanyata tun safe take sauyin.latsa latsan kaya hoto ne dai dak'yal ta yarda akayi mata tare da Yaran sannan akayi mata da Ammy da kuma Chuchu da Asmy dukda a sanyaye take saboda sosai taron mutanen ya bata mamaki Sosaifa aka shiga shagali da fidda abinci da baza Naira a bikin triplet gidan Ammy duk Inda ka hanga cike yake da mutane Wasu ma basu sansu ba haka suke zuwa Dan aci banza" Kaji ko yanda kasan Tuwo haka aka maidashi a gidan duk Wanda yaje sunan nanfa tofa ya shaida Sunzo gidan kudi sunzo Inda ba a tausayin naira Duba ga irin Abubuwan da aka rarrabama kansu ya isa mutum girgiza K'atuwar jika mai d'auke da hotunan yaran da sunansu cikinta galleliya Atamfa Holland banda Callender sai Tab d'in yara a ciki Kirar Iphone wacce kudinta ma saiya girgiza mai karatu mutane ganin amfara basu wannan Abun duniyar nanfa aka rude Wasu Dasun fito suke kiran y'an uwansu akan suzo kar ayi basu Babu alamar karewar kayan rabo saboda daman masu uban yawa akayi Chuchu itace gaba gaba kan rabo ita da Asmy duk anshiga busy ga ba ruwansu da wai sai Wanda suka sani Kowa bashi ake saboda ranar farinciki ce acewarsu duk Wanda yazo murna yazo tayasu hakan yasama suka sanya security barin kowa ya shiga amma fa sai anyiwa mutane bincike kafin Su shiga saboda karsu shiga da mugun Abu Chan na Hango *Auren wata tara*Fans Gungunsu guda Ni kaina nayi mamakin Ganin irin yawan sunfi a kirga Wanda ba ma zan iya kiran sunan su ba chan na hango khadyn sp ana yagar cinyar kaza Rachel ko ina kallonta tana zuba wasu kajin a ledar da tataho da ita su ummu suhaif sai washe baki ake banza ta samu,su halimatu ko an sha goggoro yanda kasan itace chuchu su fatima sai zazzakewa ake tana sune kirjin biki sunan ammy da amarya zahra gareta yan uwansu ne ai,chan na hango quen faridat suna fada da wata tana cewa zata sa security su fitar da ita batasan yanda suke da md ba to cousine brother dinta ne nikam hajjo ina rike da takarda da alkalami nace zuķ'i,su tsohuwa maman Siddiqa sai shafce zufa ake,su aisha,zainab oum ibisam ,jikalle ruky ,rahama ,maman nana,su nafisa kai sauran bazasu fadu ba wollah anyi kara Maman Khairat ita ce gaba Wajen yi musu jagora Akan suma suje su Amso nasu kason raba su gida hud'u tayi ta ce"Kunga ku bari mu kasu hud'u karsu ganmu gayya guda suce daman kayan suka kawomun kashi d'aya mu fara shiga kafin Sauran tunda Kunga munyi yawa "Ummu shugaba ce tayi k'araf ta ce " Wlh bazaiyu ba maman khairat kawai mu shiga gaba d'aya sanadin wanda suka fara shiga su su samu kawai mu mu rasa wlh bazaiyu ba "Ganin suna shirin yin sama ya sanya maman khairat cewa to shikenan muje mu Duka din Tunda bakusan ayi Harkar da baza a raina mu ba dukansu suka runkuta suka shiga kowa ya fito zaka kalli fuskarsa cike da farinciki sai wage baki suke kowa sai murna yake banda Sherston ghayu da ta fito hawaye jabe jabe da fuskarta wai bata samu rabo ba sosai na tausaya mata ganin yanda take kuka cikin bila'adadin mutane ita kadai ta rasa Allah sarki maman ummy da tausayi cewa tayi Dan Allah mu hada mata ko wani Dan abun ne a bata ,mutanen namu najin haka aka fara sassanfewa chan na hango lolos ta maida nata cikin hijab ta dukunkuneta ,mom shukurama cewa tayi tofa mu ma'assalam dadyn shukura yayi kira ,ummu suhaif da ummu rafi a sukace jiramu muma sun kira bansan yanda yan auren wata tara fans suka wansheba saboda barin wajen da nayi na kutsa ciki chan na hango zahra tasha tsadadden lace da yayi mata mugun kyau yanda kasan matar president Tripple dinta ko sunsha kyau cikin tsatsadan kayansu zey ta kasa ta tsare akan yaran ba a daukarsu kar a jagular su ganin Zahra a matukar gajiye take ga cs dinta da bata warke ba ga kaya masu nauyi da ta sanya ya sanya Ammy da itama tasha kyau kama hannunta ta kaita wani part din ac ta kunnawa dakin bayan ta sanyata tayi wanka ta sauya kaya kan gado ta kwanta daman gajiye take saida ammy taga bacci ya dauketa tukwana ta fita bayan ta rufe mata dakin taro ya tashi lafiya cikin girma da dattako anyi Abu na bajinta da nuna sa a md ma lunch suka shirya hatta abokanan kasuwancin shi na kasashe saida sukazo wajen lunch dinma haduwar da yayi bata baki ne iya maza kadae akayi anci ansha kafin dare ma labarin sunan triplet din,md sun baza duniya sakamakon yan jarida da suka ziyarci wajen event din da wajen sunan kuma md ba boyayya mutum bane da dare abban amira yaga bikin sunan a news cikin tsananin mamaki yacewa matarsa me nake gani haka hajiya itama tana mamaki ta ce "nima abunda na gani md yana da wata matar ne daman bayan amira"cikin tsananin tashin hankali ya dannawa amira kira a layin ta na chan kasar lokacin amira na bacci ringing din wayar ya tasheta cikin muryar bacci ta ce"hello dad cikin tashin hankali ya ce "Kina ina daughter labarin Me nake gani wai an haifawa mijinki triple yaushe kika haihu mu bamu sani ba"a rude amera ta mike ta ce "what daddy daman jita-jitar nan gaskiya ce tun last week friends dina ke kirana sunamun barka daga karshe har kashe wayata nayi nama dauki abun a rainin wayau Innalillahi wa inna ilaihiraji'un wai meke faruwa shima honey din nayi ta kiransa baya dagawa"kome kike ki maza ki dawo kasar nan akwai gagarumar matsala "cikin tashin hankali ta ce "To dad ganinam"a take ta ,Mike ko bag dinta bata tsaya dauka na passpord da wayarta kawai ta dauka ta fito kai tsaye Airport ta nufa hankali tashe zuciyarta chunkushe da tunani kala^kala ba bata lokaci tayi clearing din komai a daren jirginsu ya d'aga daga London zuwa Nigeria......... ✍
*domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Misa Hajo ce*_🤙
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️...........*91 & 92*
&
🅿️..........*93 & 94*
"Ki kwantar da hankalinki Hajiya insha Allah zai huce idanma bai huce ba ni da kaina zankoma na basa hakuri"Baba tsoho ya fada kafin yayiwa Ammy bankwana ya koma masaukinsa Da aka saukesa a gidan"Sosai Md ya burkuce ya shiga tsananin tashin hankali na rashin Zahra da yaransa gaba daya baya cikin nutsuwa cikin kwana biyu harya zabge ya rame saboda tashin hankali da rashin bacci Ga ko abinci baya iyaci saidai ruwan Lipton idan ya zauna ba Wanda yake tunanin irin Zahra Shi kanshi baisan Yana mata so har irin haka ba sai yanzu da tayi nesa dashi Gaba daya yashiga tashin hankali rasa Wanda zaiyi shawara dashi yayi sai jabir ya bude wayarsa ya Kira Dan tun Kiran da iyayen amira suke mashi ya dameshi ya sanyashi kashe wayarsa .....bangaren Zahra Itama Bata da wata walwala Sosai dukda kannen babanta na kokari a kanta Sosai baba ma Yana nuna mata ya hakura Dan har yaran saiya daukesu su yini wajenshi Amma Kuma har yanzu batajin Tana da walwala Sosai takejin kewar su Ammy ga Kuma tunanin Md da tarasa dalilin da Indai ta zauna ba Wanda take tunawa da irin rayuwar da sukayi a baya irinshi yauma Tana kwance Tana tunani batasan lokacin da wasu hawaye masu dumi suka zubo mata ba Haka kawai data zauna saita dinga tunaninsa ta rasa fahimtar abundanda ke damunta game dashi lura da rashin walwalar na Zahra ya sanya Mama habi tafiya da ita gidanta katsina Dan taci gaba da Kula da ita Komawarta katsina Zahra ta danji sassauci saboda koba komai akwai yaran mama habi Sa'anninta da Wanda suka fita sun zauna su danyi hira ta rage kawaici triple ko Daman idan ba yunwa sukaji ba tofa ba a kawosu wajenta suna hannun mama habi da yaranta haka dai rayuwa taci gaba mama habi naci gaba da yiwa Zahra gyara Sosai dukda damuwar da tasa a ranta ta rame yaranta ko sunyi b'ul b'ul abunsu gwanin sha'awa kamanninsu da mahaifinsu na Kara fitowa....a halin yanzu md kullum cikin zazzabi da ciwon Kai yake ya rame Sosai gashi yaki yaje asibiti Ammy ko itama duk hankalinta ya tashi ganin yanda beloved son din nata ya koma ita kanta batasan md Yana yiwa Zahra har irin wannan son ba sai yanzu lallashi ba irin Wanda batayi Masa ba Amma yakiji Baba tsoho ko Yana daya daga cikin gidajen Baki na md inda Ammy ta saukesa kafin Shima su waiwayi jigawa wajen ahalinsa sun Bari dai a gama da matsalar Zahra Ranar da Zahra ta cika sati ukku da tafiya idan ka kallesa saikayi Masa kuka saboda yanda ya firgice kamar ba mr MD billonia ba matashi da kudi Ranar ji yayi bazai iya jure rashin Zahra ba saboda yanda yakejin zuciyarsa kamar zata tarwatse a daddafe ya Kira chuchu a waya Koda tazo saida tayi hawaye ganin yanda Yayan nata ya zabge Address din garin da suka Kai Zahra ta basa tare da fada mashi drivern da ya kaisu baiyi wata wata ba ya Kira drivern a tare da jabir suka tafi garinsu batsari Wanda tafiyar sirri sukayi Allah yasa Drivern ya gane Gidan Koda sukayi sallama da bappa ya fito ganin Baki ne ya sanyashi masu iso har cikin gida Md kanshi Kasa ya gaishesu Har baba da yake zaune baba ya Gane jabir cikin girmamawa suka gaisa Yana tambayar jabir ya mutanen gidan sannan yayi mashi godiya akan Abunda yayi mashi Lura da shine baban Zahra ya sanya mD Kasa had'a ido biyu dashi dakyal jabir ya iya bude Baki ya ce "Baba Daman magane ce tafe damu akan Zahra"Inajinku wace magana kenan"Baba ya fad'a"saida jabir yayi Jim kafin ya. Dago ya ce "Daman hakuri ne muka zo mu Kara Baku akan Abunda ya faru Dan Allah Baba kuyi Hakuri wannan abokina ne Kuma shine mijin Zahra baban yaran shine mukazo mu Kara Baku hakuri "Kallon md baba da bappa sukayi kafin Bappa ya ce "Allahsrk shine yaron kenan To Ai komai ya wuce Hakuri an Riga anyi d'an Adam ai baya wuce rubutun Allah duka abunda ya faru ya faru ne a bisa kaddara da Kuma rabon yaran Nan dan haka daga bangarenmu ya wuce yaro tunda dai ba Zina sukayi ba Aure sukayi har aka haifi yaran ta hanyar sunna kaga ai komai yazo da sauki "saida ya md ya sauke boyayyar ajiyar zuciya "Baba Shima cewa