Showing 129001 words to 132000 words out of 182697 words

Chapter 44 - KANWAR-MAZA-1_2-COMPLETE BY AYSHACOOL

12 Jul 2024

22420

yazo kan da kansa, kawai sai kuma ganin message ?in sa na gani, wai za shi katsina, uban me zai je yi a katsina?"

"To amma yanzu ina zaka je?".

"Zan je na yi aikina da kaina ne" ya bashi amsa yana kallon agogon hannunsa.

Jabir ya gyara tsayuwarsa ya ce "Kayi aikinka ko ka ?atawa kan ka lokaci, wata ?ila akwai dalilin da ya sanya yake yi maka yawo da hankali, ka yi ha?uri ka bi komai a hankali, ka bashi yau zuwa gobe in Allah ya kaimu mana".

Adam ya girgiza masa kai ya ce "No, ba zan iya ba" ya juya zai nufi mota. Jabir ya ri?o shi ya dube shi ya ce "Bashir amintaccen ka ne, bana tunanin zai yi wani abu da zai yi maka yawo da hankali, ko ya cutar da kai, Please ka bashi ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ne" da ?yar jabir ya lalla?a takawa dan ba laifi Adam akwai ba?in taurin kai".

***
A hankali take motsawa, ta fara ?o?arin juyawa, dan gaba ?aya a tunaninta bacci take yi, sai dai ta ji wani irin azabar ra?a?i a ?eyarta, zuwa kanta da wuyanta, a hankali ta tashi zaune tana waige-waige.
Jaririn yana nan in da ya fa?i, yana ta motsawa a hankali yana zura hannunsa a bakinsa, yana ta numfashi sama-sama. Rumaisa ta zuba masa ido hawaye na zuba daga idonta, haryanzu jikinsa da ?azantar haihuwa, duk ya fita a hayyacinsa. Wani irin jiri take ji, ta kalli in da ta fa?i ta ga jini, na in da ta fasa ?eya ta fa?i.
Ta kalli ?ugunta haryanzu tana ?aure da ?ankwalin Anty Aisha da ta bata, ta ja jikinta zuwa kusa da jaririn, ta ri?e hannunsa tana kuka "Ka yi ha?uri yarona, na kasa baka kulawar da yakamata, kaga nima yarinya ce ban san me kake bu?ata a matsayin ka na jariri na, na rasa yadda zan yi mu bar wurin nan, dan Allah kar ka mutu kamar yadda mamanka ta tafi ta barni" tayi maganar kamar tana yi da sa'anta.

A haka cike da tsananin muradin cigaba da rayuwa, ta sake ?aukarsa ta mi?e cikin ?arfin hali, ta cigaba da tafiya, sai dai ba ta je ko ina ba ta kasa, ta silale ta zauna a jikin wani dutse ta zubawa sarautar Allah ido.

Kamar a mafarki rumaisa ta ga wasu irin dandazon shanu sun cika wurin, ita dai ba ta san ta in da suka ?ullo ba, ta hangi mai kiwonsu, yana ta ratsawa ta cikinsu. A gefenta ta din ga ganin wata inuwa, ta ?aga kai sai ta ga wata bafulatana, doguwa do jerin ?orrai a kanta, ta kalli rumaisa ta ce "'yar nan dan Allah taimaka mini na sauke ?orran nan".

Ruma ta harari matar ta kawar da kai, kamar ba ta ga a halin da take ciki ba, take cewa ta sauke mata wannan uban ?waryoyin, can matar ta kuma cewa "Rumaisa da ke fa nake" ruma ta kalli matar cikin mamaki za ta yi magana ta fasa, ta kwantar da yaron, ta mi?e ta kamawa matar suka sauke ?orran.
Ta koma ta zauna ta na cigaba da kallon jaririnta, matar ta din ga auna nono, ba tare da kuma tankawa rumaisa ba, can rumaisa ta ce "Dan Allah baiwar Allah ki taimaka mini da ruwa da nono na bawa yaron nan, ni ko ba zaki bani ba, shi ki bashi dan Allah".

Matar ta yi murmushi ta ce "Ai na zata ba zaki kulani ba, na tashi na yi tafiyata".

Ta mi?awa rumaisa battar ruwa, ta kar?a ta ?ago jaririn za ta bashi, matar ta kar?e shi ta bashi ruwan, sannan ta bu?e wata ?warya ta tsiyayo madara fresh ba a da?e da tasota ba, ta fara bashi, aikuwa duk da bashi da lafiya, haka ya din ga kar?a yana sha, kamar zai cinye da mazubin.

Rumaisa sai murmushi take, ganin ya samu ruwa da abun da zai ci.

Matar ta kalli ruma ta ce "Ba dan halinki ba bari na san miki ruwa ki sha, ruma manyan gari, ruma kaya da yani, gwagwarmaya na gaba ba ta zo ba kuma ba ta wuce ba".

"Wai ke a ina ki sanni?" Ruma ta tambayi matar.

Matar ta yi murmushi ta ce "Ke waye bai sanki ba, kar?i ruwan ki sha, kar kuma ki manta ki kula da amanar da aka baki, Allah ya taimake ki baki mini rashin kunya ba, Kodayake jikin ta ?aura yayi la'asar, wallahi da a dajin nan zan barki, amma ki ka taimaka mini, sha ruwan na rage miki hanya " rumaisa ba ta gama gane me matar ke cewa ba, ta kar?i abun ruwa ta kafa kai, sai dai ma?warwa biyu ruwan ya ?are ba ta ?oshi ba.
Lumshe ido rumaisa ta fara yi, tana jin yadda kanta yake ?ara nauyi, ta kar?i yaronta daga hannun matar ta rungume, sai sunkuyar da kai take, kamar ta yi shaye-shaye saboda ji take kamar zata fita daga hayyacinta.

"Ke!ke! Baiwar Allah me ki ke yi a gefen titi haka?" Rumaisa ji ta yi kamar ta farka daga bacci, ta bu?e idonta sosai, irin zaman da tayi ta rungume yaron a haka take, sai dai a wani wurin ta ganta daban, jeji ne wurin sai dai tana zaune a gefen titi, kwalta ?o?ar.

"Me ki ke yi a nan, ina zaki je?"

Ta ?aga kai ta kalleshi amma ta ba ta kula shi ba.

"Ko dai mahaukaciya ce ne? Wannan yaron na waye, ni da na zaci tsohuwa ce ashe yarinya ce, daga ina ki ke ?an waye a hannunki?"

"?ana ne" ta bashi amsa.

Mutumin ya ce "A'a ba dai ?anki ba, ina hijjabinki, ina ne gidanku?".

"Kai dan Allah ka ?yaleni haba" tayi maganar tana neman wurin kwanciya.

"Karki kwanta da jaririn nan a wurin nan, ki gaya mini in da zaki in kai ki".

Ta kalleshi ta ce "Ka san ?orayi?".

"A'a wanne gari ne?"

"Tun da baka sani ba Shikenan, na gode sosai" gani yayi kamar maganar da rumaisa take yi, haukacewa ta yi ba a hayyacinta take ba. Wata dan?areriyar mota ce ta yi parking a wurin da mutumin yake tsaye a kan rumaisa, da tuni mutane suka fara taruwa a wurin.

"Bawan Allah lafiya, meyake faruwa ne?".

Ya kalli na cikin motar ya ce "Wallahi kaga yanzu nake dawowa, na biyo hanya ns ga wannan yarinyar da jariri, ta ma dai ?i bari na ga yaron, amma kamar dai mahaukaciya ce".

"A'a dawanau ce ni ba mahaukaciya ba, kai haka ake tainako ?ishirwa nake ji, amma ko ruwa bai bani ba yake ce mini mahaukaciya".

Na cikin motar ya ?auko ruwan roba, ya fito ya bawa rumaisa, ta kar?a ta ta?ar?are ta shanye shi a ma?warwa uku tayi jifa da jarkar.

Ya kalli rumaisa a tsanake ya ce "Na ji kin ambaci dawanau, ke 'yar kano ce?"

"Eh, dawanau asibitin mahaukata ne, dan Allah idan ka san kano ka kaini, kar jaririna ya mutu, bashi da lafiya" tayi maganar cikin magiya.

Ya ce "Ok babu damuwa, amma Meyasa na ganki a haka? Ina hijjabinki kalleki futu-futu fa, ga raunuka a jikinki, kalli kanki yana zubar da jini, jikinki babu hijjabi, ?afarki babu takalmi, dole ayi zaton ko baki da hankali".

"Kwana kusan sittin fa a dajin nan, saceni aka yi, dan Allah ka tashi ka mayar da ni gida" salallami mutanen wurin suka ?auka.

A take ya ciro id card ?in sa, ya nunawa mutanen, shi jami'in tsaro ne, dan haka ya ce zai tafi da rumaisa babban asibiti na cikin garin katsina.

Rumaisa ta ce ita fa ba ta so a kaita ko ina sai gida, ya fuskanci yarinyar kafaffiya ce, dan haka ya ?yaleta ya ce ta taso sai ya ?auki wakilcin mutum ?aya su tafi, su tsaya su yi reporting wa police, su wuce da ita asibiti.

Sai dai duk yadda rumaisa ta so ta tashi ta kasa, saboda ji ta yi ?affuwanta kamar ba nata ba, ?arshe sai ?aukarta aka yi aka saka a motar suka tafi.

Sai dai fa fafur ta hana kowa jaririn nan, yana ?an?ame a jikinta, jin abubuwan take kamar a mafarki, Allah ya ku?utar da su, ta din ga jera hamdala ga Ubangiji.

Sai dai rumaisa na sanya ran an kama hanyar kano ne, ta gansu a asibiti, aka zo da wheel chair, aka ?orata a kai, nurses zasu kar?i jariri ta ce ba ta san zance ba.
Emergency aka shiga da su, aka yi ta lalla?a rumaisa ta bayar da jariri ta ?i, ta ce idan aka matsa mata, ko da rarrafe sai ta gudu daga asibitin.

Kasancewar mutumin da ya tsinceta shi ma ba ?an gari bane ba, idanya barta babu wanda zai kula da ita, ya sanya a ka bawa rumaisa ?an taimakon gaggawa, ya ?au rumaisa tare da rakitar 'yan sanda biyu, suka taho kano.
Suna tafe a hanya rumaisa tana ta surutai, masu kama da na fita a hayyaci, ta ce wanna ta ce wancan, ita dai gata nan kamar mai barci kuma kamar zautacciya.

Ba su suka iso kano ba sai bayan tara na dare, suka biya suka kuma report ga police na kano, aka yi rubuce-rubuce, sannan suka wuce da rumaisa asibiti.

Suna zuwa aka kar?i su rumaisa, da tuni hankalinta baya jikinta, tun a hanya aka sai abin ci aka bata, amma ta?i ci, ba ta ma da nutsuwar da zata ci Abincin.

Aka zare jaririn hannunta, da a yanzu numfashi ma yake neman ya gagare shi, da yawa sai da wasu suka yi hawaye, ganin halin da jaririn ?anyen haihuwa yake ciki, cibiyarsa ta ya?une tayi ba?i, jikinsa duk ?azanta, aka samo kaya aka saka masa aka wice da shi nursery domin bashi taimakon gaggawa.

Ita kanta rumaisan sai ka kai zuciyarka nesa zaka iya ta?ata, saboda yanayin da take ciki na ?azanta da dau?a, ba yadda ba su yi ba su kwance ?an kwalin ?ugunta, amma aka kasa, ?arshe suka ?yaleta suka fara kokawar ceto rayuwarta, ita kanta sai da aka saka mata oxygen, saboda sama-sama take numfashi, aka ?ebi jininta aka tafi yi mata gwaje-gwaje.

***
Kusan mintuna uku tana zaune a dining tana ta juya cokali a cikin kofin shayin, amma ta kasa ?agawa ta sha ko da sau ?aya, sai zancen zuci take. Jin an dafa ta ne ya sanya ta ?ago a hankali ta kalli ammi, a take ta fara ?a?aro murmushin da bai wuce iya le?enta ba.
Ammi ta ja kujerar kusa da ta iman, ta zauna ta ce "Autana, ko ban tambayeki ba na san abun da ki ke ji, kuma na san ke mai juriya ce, dan haka kar ki saka maganganun da wambai yayi a ranki, ki manta da komai, ki mayar da hankali a kan karatunki, da kin kamma sakandare, zan turaki Mexico wurin laila, ki nutsu ki yi karatunki a wurinta, kuma in sha Allah zan sama miki miji na gari, mai tsoron Allah wanda zai ri?e mini ke tsakani da Allah"

Iman ta rungume Ammi ta ce "Ni dai a'a ammi, zan zauna a tare da ke, bana son mu rabu, zan cigaba jure komai in rayu a kusa da ke".

Ammi ta yi murmushi ta ce "Duk abun mutum dai dole sai aure ya rabamu, watarana sai mutum ya tafi gidan miji"

Iman ta ce "Sai mu tafi tare, duk wanda zai aureni, sai ya yi wa ammina nata ?akin".

Yana sanye da farar jallabiya, ya ?ora rigar sa?i ta sarauta, da farar hula, yana tsaye yana kallonsu, ya ?an yi gyaran murya, hakan ya sa suka ?ago suna kallonsa.

Ammi ta ce "Ina zuwa haka?"

Ya gyara agogon hannunsa ya ce "Zan je gidan turaki ne in gaishe shi".

"Amma ina fatan ba wani abun zaka je ka gaya masa ba, ka tayar masa da hankali?"

Takawa ya girgiza kai alamar a'a, iman ta ce "Yaya a dawo lafiya".

"Allah ya sa, ki kula ki sha magungunan ki a kan lokaci".

Ta jinjina kai ta ce "In sha Allah" daga haka ya fice daga falon.

"Ammina, bari na je na sha magani na ?an kwanta".

Ammi ta ce "To babu laifi, amma dan Allah kar a je a zauna ana tunani, idan na gani ba zan ji da?i ba".

Iman ta yi murmushi ta ce "Ba zan yi ba in sha Allah, in dai kina nan Ammi wane tunani zan yi?" Tayi maganar tana mi?ewa tsaye tana yi wa Ammi murmushi.

Ko da ta je ?akinta, ta tarar da baba uwani tana ta yi mata bincike bincike.

"Baba uwani" ta kira sunanta a razane ta waiwayo ta kalli iman ta ce "A'a uwar ?akina kin shigo?"

Iman ta ce "Eh, amma me ki ke nema ne?".

"A'a babu abun da nake nema, baki gani ba, gyara ?akin nake yi, ke da ba lafiya ba, kaye-kaye nake yi miki ai".

"Amma baba uwani na sha gaya miki, gyaran ?aki ba aikinki bane ba, ya zaki din ga wahalar da kanki da yawa haka, kiyi wancan aiki kuma ki zo ki yi wannan".

"To imanuwa idan ban yi miki ba wa zan yi wa, kuma gashi ba cikakkiyar lafiya ce da ke ba, na san sai ki ce zaki yi da kanki ma".

Iman ta girgiza kai ta ce "Kar ki damu baba uwani, ki yi tafiyarki kawai, za a gyara ?akin ma ai babu datti, ina son in ?an kwanta ne".

"To Shikenan babu laifi, ki huta lafiya"

Iman ta bi bayanta da kallo, daga bisani kuma ta je ta nemi wuri ta kwanta.

***
Cikin ?osawa take wayar, cikin yanayi mai kama da fa?a-fa?a "gaskiya Khalifa na gaji da gafara sa ban ga ?aho ba, ai yakamata ace zuwa yanzu result ya fito".

"Ke duk result ?in da ki ka gani bai yi miki ba, wanne ki ke jira? Meyasa kin fiye wutar ciki ne?"

Samha ta ce "Au haka ma zaka ce, ni na kasa gane wannan yawon da hankali, ni fa na fara jin tsoro".

Dariya Khalifa ya yi ya ce "Haba jaruma, wane irin tsoro kuma? Ai mun yi kaso mafi yawa na aikin, sauran ke zaki yi wa kanki fighting, ki bi komai a hankali, idan ki ka yi gaggawa aiki zai iya kwa?e miki, dan ni babu ruwana. Nan ba da da?ewa ba, zaki ji labari mai ?an karen da?i".

Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, Allah ya sa". Ta ajiye wayar ta yi shiru tana tunanin maganganunsa.

"Anty Samha, Anty Samha!"

Waiwayowa Samha ta yi ta kalli yarinyar a ?an hasale ta ce "Lafiya ki ke yi mini wannan kiran haka?"

"Anty Samha kin gan mu, zuwa muka yi baki yi murna ba?".

"Na ji, jeki wasanki, idan na fito ma gaisa"

Yarinyar ta ?an ?ata fuska ta ce "Shikenan, naga uncle takawa ya zo, bari na je na gishe shi".

Da sauri Samha ta ce "Jannah, bana son shirme da gaske ki ke yi ko kuwa?".

"Wallahi da gaske, ga motarsa can da hadimansa, yana wurin Baba suna gaisawa"

"Shikenan, na ji jeki maza" janna na fita samha ta tashi ta canza kaya, ta hau feshe-feshen turare.


Takawa yana jin da?in mu'amala da turaki, dattijon akwai nutsuwa da kuma dattaku, ba shi da hayaniya sam balle fa?a.
Sun da?e suna hira, sai da takawa ya fara shirin tafiya sannan turaki ya ce "Amm..wato akwai maganganu da muka ji suna ta yawo a kanka, a cikin masarautar nan, sai dai bamu yanke maka hukunci ba. Maganganu ne marasa da?i da maimaita su ma bashi da wata fa'ida, amma duk da haka zamu jadadda, a din ga kula a ?ara kiyaye martabar addini da kuma al'ada, ba zamu so zancen nan ya je kunnen mai martaba ba, mussaman yadda ake ji da kai, yake sonka, muna ta ?o?arin da?ile jita-jitar, mun sani shaye-shaye ba halinka bane ba, dan da kana yi, zamu gane, amma a cigaba da kiyayewa tare da ri?e addu'a".

Adam yayi wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya ?an risuna ya ce "Za'a kiyaye in Allah ya yarda, Allah ya ?ara maka lafiya, zamu wuce".

"To madalla, Allah ya tsare ka isar da gaisuwata ga mahaifiyarka, ka ce kwana biyu bamu ga aiken mutan daji ba ma'abota nagge" yayi maganar a nutse cikin sigar barkwanci.

Takawa ya ?an murmusa, tare da du?awa daga nan ya tashi ya fita.

A falo ya tarar ana ta shirya abinci, Janna ta ?araso gabansa ta risuna ta ce "Barka da wannan lokaci uncle".

"Barkanki dai janna, kwana biyu bana ganinki, ya makaranta?"

"Lafiya ?alau"

Ya ce "Masha Allah". Yana ?aga kai ya yi tozali da matar da ya tsana a duniya, mahaifiyar su Jamil, wato mama, bai san ya aka yi suka san ya zo ba, dan ta ?ofar baya ya shiga sashen turaki, ya nemi ayi masa iso.

Ta washe baki ta ce "Takawarka lafiya toron giwa, gaba salamun baya salamun, galadima magajin galadima, da haka za a wuce ban san an zo ba? Ai yakamata mu gaisa ko".

"Ai ban zaci idonki biyu ba, barka da wannan lokaci" yayi maganar yana ?an risunar da kansa ?asa.

Kan ta amsa samha ta fito tana murmushi "Takawa, yau kai ne a gidan namu? Zaka tafi babu ko sallama da mun yi fa?a da kai kuwa" wasu irin matsatsun kaya ne a jikinta riga da skirt, ilahirin surar jikinta ko ina a matse.

"Ku yi mini afuwa, dama ina da niyyar shigowa".

Mama ta ce 'Amma na ga kamar kana shirin tafiya, da ka yi ?an waken zagayen, ga abinci nan na saka a kawo maka ai".

"Ayi mini afuwa sauri nake ne, ana jirana, zan sake yin zuwa na musamman na barku lafiya" bai ma tsaya ba balle ya ji mai za su sake cewa ba ya fice.

***
?an ?ura mata ido yayi, bacci take kamar babu rai a jikinta, yanzu babban fatansa ya san daga in da take a nemo 'yan uwanta, su zo su san abun yi a wanke mata wannan dattin na jikinta, ko ita ma ta samu ta ji da?in jikin nata.

A hankali ta bu?e idonta, ta ?an motsa jikinta da yake ta yi mata azabar ciwo.

Ya ce "Alhamdilillah, kin farka?"

Ta yi masa ?uri da ido tana kallonsa.

Ya dur?usa a gaban gadon ya ce "Ki bani lambar wayar wani a gidanku, a sanar musu kin dawo".

A hankali ta bu?e baki ta ce "Haka muka yi da kai?"

Ya ce "Me fa?".

"Ina ?ana?" Ta tambaye shi.

"Yana sashin jarirai ana kulawa da shi, kin san ya galabaita".

Rumaisa ta ce "Lallai baka sanni ba, ni fa a kan yaron nan, sai na tayarwa da kowa hankali, a bani ?ana"
Zai yi magana wayarsa ta fara ringing, ya ciro wayar daga aljihunsa, ya kalli screen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login