Showing 1 words to 3000 words out of 113985 words
Assalamu Alaikum, Thank you so much for choosing to read this document...
NO COPYING OF THIS STORY IN ANY FORM.
NO TRANSLATION IN ANY LANGUAGE.
THE UPLOADING, SCANNING AND DISTRIBUTION OF THIS BOOK IN ANY FORM WITHOUT THE OF THE AUTHOR IS ILLEGAL AND PUNISHABLE BY THE LAW.
KU SANI CEWA LAIFI BAYA BUYA!
Labarin WAYE SHI zai tafi ne akan soyayya tsakanin mutum da wata halittar.
Kuna ganin hakan abu ne mai yiwuwa?
Biyo ni ciki mu tarar da gwagwarmaya da kuma k'addarar rayuwar Sa'adha, duk akan rashin sanin WAYE SHI.
Ina fata labarin zaiyi muku dad'i da kuma ma'ana!
AYSHA MAHMOUD SHAFI'EE.
?????????
??????????????
??
?¡î?¡î?
"Nanne! nanne! nanne!!...ki tashi nace koh?"
Yarinyar da aka kira da nanne ta motsa sannan ta cigaba da baccinta.
"Zaki bude ido ko sai na tashe ki da ruwa..."
Inna ta fada tana dad'a girgizata, jin haka yasa ta zumb'ura baki sannan ta mike tana murza ido ta cikin dogon gashin kanta daya hargitse ya rufe fuskarta.
"Ki tashi ki wanke ido ki fita tun kan salisun ya tafi, kin san tun jiya muka yi haka dake."
Nanne ta dago ta kalli agogon dake kafe a dakin, k'arfe takwas da kwata na safe, gabadaya baccin da tayi bayan sallar asuba ma bai kai fi na awa biyu ba. Kwata-kwata ta manta sunyi da inna cewar yau zata je da safe ta gayawa salisu irin audugar da zai d'ebo mata a gonar baffansu wajen daza'a fitar da auduga yau kafin masu siyen kamfani su d'ebe masu kyan ciki, wai da ita zata yi sak'ar mayafan da amare zasu yafa ranar wankan amarya (Hakan wata al'adarsu ce ta wata kabila daga nijer)
"Allah inna da kin san gajiyar da na kwanta da ita da kin hakura wani daga cikin su yaya umar kawai ya fad'a masa.
"Kema kin san ba ganinsu zanyi kafin su fita ba don haka ki tashi ki d'auraye ido kije tun kan salisun ya tafi na san zasu fara yin gaba, don tun dazu nake jin dirin motoci zasu fara tafiya."
Nanne tasa hannu ta tattara gashinta baya sannan ta tufke shi, ta shiga band'akin dake jikin d'akin ta zuba ruwa a buta ta wanke bakinta da fuska sannan ta fito, inna ta miko mata hijabi daga inda take zaune.
"Haba dai, wannan ya cukurkude, bari in duba wani."
Ta bud'e wardrobe ta janyo wani mai d'an tsaho ta zura sannan ta karbi k'atuwar ledar da innan ke nuno ta dashi.
"ki masa bayani kamar yadda na fad'a miki jiya dan Allah."
Yadda ta marairaice murya yaso ya bata dariya sanda ta fita daga dakin, da yake a hawan farko suke tana iya hango k'aton tsakar gidan da ba mutane sosai saboda safiya sai daidaikun 'yan aikin dake wucewa akai akai.
Ginin gidan nasu dake cikin wata unguwa a katsina, dad'ad'd'e ne da akayi shi da dakakken gini da ko k'usa ba kasafai take huda shi ba, sannan gabadayansa hawa uku ne, daga bakin gingimemen gate din dake jikin zungereriya katangar data zagaye gidan, faffad'ar haraba ce da tsaf zata d'auke bikin masu dangi, akwai manyan rumfuna na ajiyar motoci da kuma shukar fulawowi data zagaye filin gabadaya.
Daga can jikin ginin gidan kuma doguwar baranda ce data bi tsawon fad'in wajen inda d'akunna ne a jere guda shida na yayyansu maza, a tsakiyar su kuma k'atuwar kofa ce data shigo ciki zuwa bangaren baffansu dake daga dama, inda ya had'a da k'aton falo na saukar bak'insa da kuma d'akuna biyu a ciki da bandaki, daya gefen hagu kuma k'aton kicin din gidan ne wanda shi kansa waje biyu ne dashi, da b'angaren da aka kafe da durowoyin ajiya, sai madafi inda ake jibge tarin itace da kuma manya-manyan tukwanen girki.
Bayan shi babu komai a k'asan sai manyan sito guda biyu, da ake ajiyar kayan gona, matattakalar hawa sama mai fadi ce data d'auka daga tsakiyar katon tsakar gidan kuma ta rabu hagu da dama saboda kowanne b'angare a zagaye yake da d'akunan matan baffansu su hudu ras!, inda kowacce take da falo da kuma manyan dakuna guda biyu kowanne da band'aki a ciki, sai wajen inna wato mahaifiyar baffansu inda itama take da katon falo sai dai daki daya ne da kuma band'aki.
Hawa na biyu kuma na karshe faffadar baranda ce inda wajen yafi ko'ina a gidan girma, a d'an zagayeta da gini daidai misali yadda in ba d'age mutum yayi ba ba zai iya gano k'asa ba, a nan suke shanyar kaya, kayan miya da kuma zaman shan iska kasancewar akwai kujeru kala-kala harda 'yan furanni na tukwane. Kuma daga nan kana iya hango gabad'aya kewayen unguwar da tsilli-tsillin gidaje ne kawai wanda da yawansu ba mutane a ciki, wasu ma ba'a gama ba.
A kaftanin 'ya'yan baffansu Nanne ce ta goma sha bakwai, sannan akwai mutum biyu mata 'ya'yan aunty amarya data girma a k'asanta.
Uwargidan baffa ta farko, hajiya Nasiba da ake kira da hajiya babba, 'yar maigidansa ce dake can cikin garin katsina, kasancewar baffansu d'an asalin nijer ne ya shigo katsina. tana da 'ya'ya shida, Ahmad, Nasir, Muhammad, ishaq, farida da kuma Aisha. Maza hudu mata biyu, kuma 'ya'yanta sune manya a gidan, don Ahmad da farida sunyi aure saura maza uku da mace daya Aisha.
Sai Mama Rabi wadda ita kuma 'yar uwarsa ce ya auro daga nijar, ita 'ya'yanta hudu, Ibrahim, sulaiman, umar da macenta daya jamila. itama ta aurar da babban d'anta ibrahim. Sai Mama halime wadda itama 'yar nijar d'ince amma ba 'yar uwarsa ba, 'ya'yanta hudu duka mata, khadija, maryam, nafisa, da kuma zainab. Khadija ce kawai tayi aure a cikinsu.
Sai aunty Amarya mai 'ya'ya biyar kasancewar haihuwarta ta farko tagwaye ne maza, salim da suraj, sai mai bi musu sadiq, safiya da kuma surrayya.
A duk cikin 'ya'yan baffan, nanne ce kawai bata da uwa a gidan, mahaifiyarta bafulatanar adamawa ce kuma tana can tare da 'yan uwanta, baffansu ya aureta ne lokacin da wani sab'ani ya shiga tsakaninsu da mama Rabi har ya sake ta, toh a wannan lokacin ne yaje adamawa halartar wani taro na manoman nijeriya da akayi kusan sati ana gudanarwa, anan yaga mahaifiyarta a d'aya daga cikin masu goge-gogen wajen da suka kwana.
Farko abokananshi ne suka fara tsokanarshi da cewar ya kamata ya koma gida da bafulatanar adamawa tun lokacin da suka ganshi yana tambayarta wani abu, shikenan kuwa zance ya koma gaske inda a satin basu baro adamawa ba sai da suka je har gidansu nuratu aka tabbatar musu kuma an bashi ita, anan suke ji ma ashe bazawara ce ta taba aure harda yara biyu.
Ko da ya dawo, ya sanar da inna mahaifiyarsa, bata hana shi ba sai dai matansa da suka nuna rashin son abin, hankalin mama rabi yafi na kowa tashi tunda a lokacin tana ta yawon bin 'yan uwa kan a bashi hakuri ta koma darajar 'ya'yanta.
Sai dai ubangiji ya riga ya tsara al'amarinsa don ba'a fi wata daya ba aure ya tabbata tsakanin baffansu da nuratu, ta kuma tare a b'arin mama rabin, duk da kasancewar nuratu bazawara, amma baffa ya nuna mata so wanda har hakan ya dinga b'atawa matansa rai, kasancewar baya b'oyewa koda kuwa a gaban 'ya'yansa ne.
Shekarar nuratu daya da rabi a gidan, ta haifi diyarta mai kama da ita, sai dai ta d'auko hasken fatar baffan tunda ita nuratu ba fara bace, baffa ya sanya mata SA'ADHA nuratu kuma ta lak'aba mata NANNE wanda shine ya bita.
Tun daga haihuwarta ne kuma nuratun ta sauya hali, ta fara rashin mutunci kala-kala a gidan, rashin kunya tun daga kan baffan har inna ba wanda ta kyale. Nasiha da kyaliya ba wadda baffa baiyi ba amma a kullum abin gaba yake. Ganin haka, ya sawwak'e mata saki d'aya ba da son ransa ba, don har a lokacin yana k'aunarta, tayi niyyar tafiya da nanne amma ya hana. Saboda haka ta dire ta ta koma adamawa, daga baya ne suka samu labarin cewa ashe gidan tsohon mijinta take son komawa kuma ta koma d'in bayan ta gama idda.
A lokacin da hakan ta faru, mama halime tana shayar da autarta zainab, baffa ya roki da ta hada da nanne amma kiri-kiri ta rantse ba zata shayar da 'yar kishiya ba sai dai in itama ya saketa.
Aunty amarya ma da bata dad'e da yaye d'anta na biyu sadiq ba tace bata san zancen ba. Hajiya kuwa ba mai tunkararta da irin haka, kasancewar ba shirgin kowa take shiga a gidan ba har dashi baffan kuwa, kuma ma 'ya'yanta duk sun riga sun girma a lokacin. Daga karshe dai inna ce ta dauki nanne, duk da cewa da farko itama bata shiga zancen ba don tana cike da d'acin abinda nuratun tayi musu.
Da taimakon tatacciyar madarar shanun da a kullum ake tatsowa daga gonar baffa nanne ta girma a hannun kakarta, inda kuma innar ta dauki son duniya ta dora akan nannen, ya zama tamkar bata da jika ko d'aya a duniya sai ita, har ta kai ma in kana son farin cikinta to ka yiwa nannen wani alkhairi.
Sannan tun tashinta sau uku baffa yasa aka kaita adamawa wajen mahaifiyarta, sai dai ita nuratun tana yawan yi mata aike ta hanyar turo 'yan uwanta.
Gabadaya ilahirin jama'ar gidan baffa, har kuwa da tulin ma'aikatan dake cikin gida da gonaki, nanne zata iya kirga masu nuna mata kulawa a cikin 'yan yatsunta kawai, don daga wad'anda suka tsane ta sai masu nuna cewa Allah baiyi halittar ta a cikinsu ba, saboda kuwa dalilai biyu, na farko ta tashi a cikin bakin fentin mahaifiyarta daya shafeta, don da yawansu tsanar da suke mata ta samo asali ne daga irin abinda nuratu tayi a gidan bayan haihuwarta, sai kuma saboda tsananin rashin kunyarta da ba ta kan wanda bata bi in abinta ya tashi, harda manyan mazan gidan kuwa da take d'an shakkarsu.
Hakan kuwa ya samo asali ne daga rashin kwab'ar data samu daga inna, don duk gidan har baffa ba wanda ya isa yayi mata tsawa akan wani abu in tayi ba daidai ba sai anga b'acin ran inna, wani lokacin ma ta yini tana sababin cewa don anga yarinya bata da uwa a gidan ne.
Shi yasa ta tashi kusan a sangarce, saboda kowa a gidan na shakkar bacin ran inna, don in bata yi da kai shi kansa baffan baza ka samu fada a gunsa ba. Mutane da yawa in suka kalli fuskar nanne baza su ce tana da magana bama balle rashin kunya, tafi kama da irin miskilan nan dake takama da wani abu nasu, amma yini d'aya tare da ita zai rusar da wannan ma'anar.
Duk cikin jama'ar gidan, babu wanda nanne take ganin tsana b'aro-b'aro a wajensa irin mama rabi da 'ya'yanta, kasancewar baffa bai dawo da ita gidan ba sai bayan an yaye ta. Amma hajiya babba babu ruwanta da ita in ba aiken inna ne ya kaita wajenta ba, haka ma 'ya'yanta, shi yasa su take ganin mutuncinsu.
Mama halime kuwa nunawa take yi Allah bai halicci inuwarta a gidan ba, bata ko ambatar sunanta balle tabi ta kanta a duk harkokinta, tafi karkata ga yadda baffa zaifi fifita ta a cikin matansa, hakan yasa suma 'ya'yanta basu damu da ita ba, sunfi damuwa da samun harkar kyale-kyale kamar yadda ta d'ora su akai, sai dai kuma duk randa wani abu ya had'o su da nannen, kowa sai ya san ana tashin hankali a gidan kasancewar da sauran 'yan uwansu ma ba mutunci suke ba.
Aunty amarya ce mai kyararta da kuma hantara in bata ga idon inna ba, wanda ita kuma nannen in dai babu 'yan biyunta da take shakka a wajen zata rama ne da irin maganar data fito bakinta kafin ta bar wajen, ita kuma ta bita da zagi.
Ma'aikatan gidan ma basa shiga harkarta, don data had'a ka da inna hanyar samunka a wajen baffa ta fara rawa kenan.
¡ñ©n¡ñ
WAYE SHI?
AYSHA SHAFI'EE
02
(¡î_¡î)
Nanne na sauka k'asa taci karo da Mama Azumi shugaban ma'aikatan dake kula da girke girke. Mace daya a cikin kalilan d'in 'yan aikin gidan dake nuna mata kauna.
"A'ah uwata ce da sassafen nan?"
Ta sake turo bakin daya zame mata jiki.
"Wallahi ba yadda na iya ne inna ce ta taso ni, ya akayi Kema kika fito da sassafen, wani abun za'ayi yau?"
"Yo, mu ai fitar safe yanzu ta ganmu, kin san masu kawo lefen jamila da safe suka taso, kuma kila wajen azahar zasu iso tunda a gobe zasu koma, ga aikin tarbar tasu da yawa."
Nanne ta d'an zare idonta tace.
"kice yanzu gabad'aya gidan zai tashi."
Don lefen jamila shine na karshe da za'a kawo kuma wanda kowa yafi d'okin gani a cikin na yayyen nata hud'u da za'a aurar, kasancewar wanda zata aura din a can nijar yake, d'an wata yayar baffan nasu ne da suke kamar cousins ita da baffan, kuma k'anin mahaifin baffan ne ma ya had'a auren, a cewarsa sunyi nisa da danginsu hakan zai dad'a kusanci tsakaninsu ya kuma sa zumunci ya d'ore.
Shine da akace baffan ya bada 'yarsa ya had'a da jamila 'yar gidan mama rabi, wanda zuwan yaron d'aya wajenta, aka tsaida maganar auren tare da nasu Aisha d'iyar hajiya babba da zata auri cousin d'inta, da Nafisa da maryam 'ya'yan mama halime.
Dama kusan duk sa'anni ne su hud'un, har ana zasu tafi su bar ita jamilan kasancewar ta dorawa kanta akidar sai mai kudi zata aura, don kowa shaida ne a gidan bata saurayi sai d'an wani babba ko mai nauyin aljihu, to sai abin yazo a daidai, don wanda zata aura d'in mai suna Al'ameen, mahaifinsa shahararren mai kudi ne a nijar d'in, shi kansa baffan ma bai sanshi sosai ba saboda gabadaya karatunsa a k'asashen waje yayi, shi yasa ma da akayi had'in babu wanda yaji bakin jamilan ko ita mama rabi akan basa so.
Wanda da ace bashi da kudi, kowa a dangi sai yaji masifar da zasu yi wadda zata sa a fasa auren. Amma yanzu mama rabin bata da magana sai habaicin cewa ana yiwa 'yarta kishi.
Kuma kusan hakane, don hajiya babba ce kawai bata sa ido akan auren ba, saboda ita irin k'ananan abubuwan nan wani bata ma sanin anyi, danginta na uwa da uba kaf! masu arziki ne, shi d'an wan nata ma da Aisha zata aura in bai fi su Al'ameen d'in kudi ba zasu iya karawa.
Amma mama halime ba wanda ya kaita kishi, ganin ita har 'ya'ya biyu zata aurar, amma duk cikin mazajensu ba wani mai shahararren arziki sai dai rufin asiri, duk da cewar kuwa 'ya'yanta sunfi kowa gayu a gidan.
Don a lokacin da taji zancen ma cewa tayi kamata yayi tunda itace mai 'ya'ya mata baffa yayi had'in da zainab, wai ai jamilan tana da tarin samarin dake sonta. Sai dai sanin kanta ne baffa ba zai taba yin hakan ba, tunda jamilan itace gaba da zainab.
Ita kuwa Aunty amarya bak'in cikinta bai wuce na cewa 'ya'yanta sune k'anana a gidan ba basu kai minzalin da za'a fara damawa dasu ba, tunda 'yan biyunta manya sai yanzu suke jarabawar fita daga sakandire, Kuma ko a cikin mazan sune k'anana, don muhammad da nasir ma 'ya'yan hajiya babba aiki suke yi banda Ahmad ma da yayi aure, ishaq ne kawai ya koma k'aro karatun masters, suma 'ya'yan mama rabi bayan ibrahim da yayi aure, sulaiman da umar duk aikin suke yi.
****
"ke don uw**ki ina zaki da sassafen nan?"
Muryar sulaiman ta katseta a daidai barandar waje, d'a na biyu a wajen mama rabi, yana tsaye daga jikin 'yar karamar katangar data raba k'ofofin d'akunansu da hanyar shiga gidan yana danne-danne a wayarsa, har tayi tunanin me yasa bai tafi aiki ba ta tuna cewa duk ranar da za'a fitar da kaya a gonar baffa tare da mazan gabadaya yake zuwa, har da masu auren ma kuwa, ita ko kadan bata kula ta wuce shi bama, a ranta tace.
Ba dai uwata ba sai dai taka.
"Nace ina zaki?"
"Inna ce take son auduga, shine zanje in yiwa salisu bayanin irin wadda za'a kawo mata."
Ya d'ago ya kalleta.
"Duk mutanen da zasu je ba wanda zai iya fad'a masa sai ke?"
"Ni ta yiwa bayani ne don zai fi saurarata."
Ya kalleta da mamaki.
"Saboda ke k'anwar babbarsa ce?"
Tayi kamar tace wani abu amma sanin hakan zai iya zama kamar ta zage shi ne yasa ta had'e rai ta juyar da kanta gefe.
"Koma ciki kafin in take ki."
Dama abinda take jira kenan, saboda haka tun kafin ya rufe baki ta taho fuuu! ta wuce shi.
"Yo, daya dawo min dake shi ya san irin wadda nake so ne koko ma zai fad'awa salisun ne?"
Inna ta tambaya tana kallon nanne dake cin d'umamen da mama Azumi ta kawo bayan fitarta.
Hankali a kwance ta daga kafad'unta.
"Nima ban sani ba...tunda har ya iya zaginki ina ruwansa da wata audugar da kike so."
"Wai ni ya zaga b'aro-b'aro?"
Ta saki lomar data d'auko cikin hannunta.
"Toh inna uwata fa yace, a duniyar nan ina da wata uwar ne bayan ke..."
Inna ta sake kwafa tana kokarin tashi.
"Rabu dashi dani yake zancen, Allah zai kawo shi har nan wajen ina zaune, daga shi har tasa uwar kuwa da yake tak'ama da ita."
Awanni hud'u bayan haka, Sadiq d'an wajen Aunty amarya dake sa'an Nannen ya shigo rik'e da wata k'atuwar leda cike taf! da farar audugar. Ya dire ta a gaban inna wadda ta hau dubawa tana sababinta, sannan ya matsa kusa da nanne dake yankan farcenta ya d'an sunkuyo yace.
"'Yan mata..!"
Taja wani dogon tsaki ba tare da ta d'ago ba, tun lokacin da ya samu labarin cewa in tana yarinya aka tambayeta ita mace ce ko namiji sai ta fara kuka tana cewa ita 'yanmata ce shikenan ya addabe ta, dama k'iris yake jira ya samu wani abin da ya san bata so, tunda a duniya burinsa kawai yaga ya tsokane ta.
"ke kika d'aukewa ya suraj kayansa da aka shanya a baranda? tun jiya yake nemansu."
Jin haka yasa ta d'ago da dara-daran idanunta ta kalle shi.
"Shi yace maka ni na d'auka, a ina zanga wasu kayansa ma balle in d'auka."
"Na san zaki iya daukar ne shi yasa na tambaya, in ma kece gwara tun wuri ki mayar masa, don wallahi ransa ya b'aci kuma yanzu zasu dawo, nima don yaya sulaiman yace in biyo su Aminu ne da tare zaki ganmu."
Caraf! kuwa inna ta karbe zancen.
"Kaga ni bana son neman tashi hankali da safiyar nan, daga aiko