Showing 204001 words to 207000 words out of 209154 words
love you so much.. Kuma nayi zaton zaki tub’a... But then... Yau d’in nan na yarda cewa Ke baki cancanci a kiraki uwa ba..!”
Mommy da duniyar ya soma juya mata, hawaye Ta soma tana rok’on Musaddiq “Musaddiq don’t please.. You are my son Musaddiq..Don’t do this to your Mom.. Musaddiq Kurku fah za’a jefa mahaifiyarka..!”
Cikin tsananin daka tsawa hawaye na tsartsafowa daga idanunsa yake fad’in “No..! I’m not your son Mommy.. Kin kashe D’an Safeenah da kanki Mommy.. Wace irin uwa ce zatai ma d’iyarta haka.. Idan zaki iya kashe D’an Safeenah wanda yake jininki ne Mommy Tabbas zaki iya kashe kowa sabida bak’in zuciya irin naki..!” Hawaye yaci gaba da gangaro masa ana ci gaba da fad’in “You don’t deserve to be a mother.. Baki canci zama uwa ba Mommy.. Babu uwan da zatai abinda kika aikata yau, son zuciyarki yakai mak’ura..!” Ya k’arashe yana mai kuma girgiza kai hawaye basu daina ambaliya a fuskarsa ba.. Lokaci guda yasa kai ya fice cikin sassarfa.
Mommy ta biyo bayansa a guje tana kuka tana k’walla masa kira amma inaa tuni ya fice.
Zubewa Mommy tai a wajen ta d’aura hannayenta biyu aka tana k’walla wani irin ihu had’ida kiran sunan Musaddiq da tuni ya fice.
A d’ari Mommy Ta mik’e Ta nufi d’aki ko takan Safeenah dake murk’usoso a d’aki batabi ba Ta suri mayafinta da jaka ta fice daga gidan hankali tashe.
**
Mu’azzam kaw tinda ya fice daga gidan da k’afafunsa kurum yake tafiyar yanaji kaman ba’a saman k’afafun nasa yake tafiyar ba, maganganun Mommy sai Yawo suke a kwanyarsa, hannayensa sakale cikin aljihunsa. Mommy ta kashe masa d’ah a gaban idanunsa. Matar da ya d’auketa uwa Itace tai masa hakan.. Shi duk tunanin duniyar nan ma ya rasa wane dalili ne zaisa Mommy ta aikata abinda ta aikata Wai kawai dan Ta rama abubuwan da yai mata.. Toh ma Wai shi mai yai mata da tsanani da zata d’auki wann d’anyen hukuncin.? Ya k’arashe tunanin nasa yana zama saman wasu kujerun shak’atawa dake d’an k’asa da layin masu kad’an.
Mu’azzam yai zaune yana tunanin lamarin nan ya hango Musaddiq na tahowa.
D’an kauda fuskarsa gefe yai kad’an har lokacin yana jin zuciyarsa na masa zogi.
Musaddiq ya k’araso jikina sanyaye ya zauna a gefensa ba tareda yace komai ba.
Sun b’ata lokaci a haka babu mai cewa komai kafin Musaddiq ya soma fad’in “I’m sorry.. I’m sorry Mu’azzam.. Please forgive me..!” Kansa a k’asa yake maganar.
Da mamaki Mu’azzam ya d’ago yana dubansa, Maiyasa yake basa hak’uri bayan bashi yai masa laifi ba.
Hannun Musaddiq dake aje gefen Mu’azzam d’in saman kujeran da suke zaune bisa Mu’azzam ya dafa, Musaddiq ya d’ago idanunsa masu zuban ruwa yana duban Mu’azzam d’in.
D’an girgiza kai Mu’azzam yai yace “Maiyasa kake bani hak’uri Musaddiq.. Baka aikata mun komai ba.. Mommy ita ta aikata laifin ba kai ba..”
Kuka sosai yazo wa Musaddiq ya rungume Mu’azzam yana kuka yake ci gaba da fad’in “Nayi shiru ne sabida ita d’in Mahaifiyata ce.. Mu’azzam ka yafe mun.. Ka yafe mun it I kept this from you..”
B’anb’aresa daga rik’on da yai masa Mu’azzam yai yana binsa da kallon mamaki yake girgiza kai “What do you mean Musaddiq..? What are you trying to say..?” Ya tambaya cikin rud’ani.
Cikin zuban hawaye Musaddiq ke fad’in “Mommy ‘yar damfara ta d’aukawa mahaifiyarka a matsayin mai magani Mu’azzam.. Ba don komai ba Sai dan ya fice mata daga gida da kuma rayuwar mijinta gaba d’aya..”
Bibbiyu Mu’azzam ke ganin Musaddiq zuciyarsa na wani irin harbawa.
SameenaAleeyou📚
[9/3, 8:39 AM] My mom: *GIDAN ARO*
*64*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Kauda kansa gefe yai yana d’an shafa sumarsa kad’an cikin rashin yarda da abinda Musaddiq d’in ke fad’i “Kamin magana da yaren da zan fahimta Musaddiq..” Ya fad’i cikin rarrabewar kalamai.
Musaddiq da har lokacin bai daina zuban hawaye ba, yaci gaba da jinjina kai “I’m sorry Mu’azzam.. I really I’m sorry brother.. Dan Allah ka yafe mun.. Ban zaci Mommy zata kawo wann lokacin bata hankalta ba.. Had I known abubuwa zasu kasance haka da nayi magana tuntuni koda ta kasance mahaifiyata.. Inajin laifina ne daka rasa D’anka, Watak’ila da nayi magana tuntuni da an d’auki mataki kan Mommy.. Watak’ila da baka rasa D’anka ba..!” Kuka ya hanasa ci gaba da magana yayinda Mu’azzam yai zaune yana ganin duniyar na jujjuya masa.
Ya k’ura ma waje guda idanu, cikin wane irin yanayi da zai iya cewa bai tab’a kasancewa ciki ba, a hankali cikin kwantacciyar murya yake fad’in “Tell me everything Musaddiq.. Ka sanar dani duk abinda ka sani..”
Musaddiq dake duk’e wajen tafukan hannayensa yasa ya shafe fuskarsa dasu, kafin ya shiga jinjina nasa kan shima.. Lokaci guda ya shiga karanto wa Mu’azzam duk abinda suka faru harda yanda suka juya maganin Kyallu shida Ajidde da k’udirin Kyallu na turo Ajidde gidan dan tai mata sata.. Musaddiq na labarta masa abubuwan da suka faru Mu’azzam d’in na tuna komai daki daki harda lokacin da Ajidde taso masa sata farkon zuwansa gidan.. Allah sarki ashe ba b’arauniya bace kaman yanda ya zata.. Ashe tilasta mata yin satan akayi.. Shin wace irin duniya muke rayuwa ciki..? Haka Musaddiq ya dinga karanto wa Mu’azzam duk abubuwan da suka faru gameda jinyar Aunty Nuratu da rawar da Ajidde ta taka wajen watsi da maganin Kyallu tana kuma karb’o mata ayoyin Allah daga wajen Malama Hafsah.. Yarinyar da yake ma kallon shashasha mahaukaciya, yarinyar da yake ma kallon bata cancanci kasancewa kusan mahaifiyarsa ba balle tai mata jinya.. Yarinyar da yai mata lak’abi da Mahaukaciya.. Ya kuma lumshe idanunsa a hankali yana jin zuciyarsa na wani irin harbawa..
Muryar Musaddiq ya sinkayo yana ci gaba da fad’in “Shisa a lokacin da ka dage sai Ajidde ta bar gidan nima na dage cewa bazata tafi ba.. Shisa nima nai duk yanda zanyi nabi duk hanyar da zanbi domin na tabbatar Ajidde bata bar gidan ba..Nida Ajidde tuni mun had’a Team wajen ganin munyi watsi da maganin dasu Mommy suka so d’aura Aunty Nuratu akai..” Muryar Musaddiq yaci gaba da rawa “This is the least I can do bayan cutar da Aunty Nuratu da mahaifiyata taso yi..”
Musaddiq ya had’a hannayensa biyu alamun rok’o ya duk’a saman gwiwoyinsa yana fuskantar Mu’azzam still hawaye ne saman fuskarsa “Mu’azzam dan Allah kai rangwame wa Mahaifiyata.. Dan Allah ka mata rangwame..!”
Cikin sauri Mu’azzam ya kamo Musaddiq ya rungumesa yana jin wasu k’walla masu zafi suna ciko idanunsa yayinda kukan Musaddiq ya k’aru.
Cikin wane irin yanayi Mu’azzam ke furta “Mommy ta tafi da nisa Musaddiq.. Ka sani, banyi niyyan d’aukan mataki akan Mommy ba sabida kisan d’ah na da tai akan idona..” Ya d’anyi fasali yana duban Musaddiq d’in kafin yaci gaba da fad’in “Kasan Maiyasa..? Sabida Sadaukarwa mai girma da tayi na jinyar mahaifiyata tsawon shekaru.. Amma bayan labarin da ka bani yau Ina shakkun idan Mommy tsakani da Allah ta shafe shekarun nan tana jinyar mahaifiyata.. Musaddiq kai hak’uri, bazan tab’a sassauta ma duk wanda ya cutar da mahaifiyata ba.. Ina buk’atar ganin Mommy.. Akwai tambayoyi da dole zata amsa mun.. Idan ta aikata wani abu domin ta cutar da mahaifiyata, I’m sorry Musaddiq.. But I won’t spare her..!” Ya k’arashe hawaye mai zafi na gangarowa daga idanunsa guda zuwa k’uncinsa. Daga haka Sa kai yai ya nufi hanyar da zai kaisa gidan.
Musaddiq yai saurin take masa baya suka nufi gidan a tare.
Saidai suna shiga gidan suka tadda wani tashin hankalin Safeenah suka hango saman k’arafan dake balcony d’inta Ta kama ginin Ta d’ale zata fad’o k’asa ga ma’aikatan gidan sunyi cincirindo Sai rok’onta suke tai hak’uri Ta sauk’o.
Shigowarsu Mu’azzam yai daidai da shigowar Kiki itama ta dawo daga makaranta kenan ta tadda wann badak’ala dake tashi cikin gidansu.
Musaddiq fad’i yake “Feenah don’t.. Don’t jump please..”
Safeenah na kuka take fad’in “Mutuwa zanyi Musaddiq.. Meye amfanin rayuwar.. Bata da sauran amfani.. Ka barni na mutu nima..!” Tana maganar tana kuka tana kuma yunk’urowa kaman zata duro k’asa.
Ko kulawa da Mu’azzam da tuni ya haye sama basuyi ba.. Dukan k’ofan d’akin Safeenah dake kulle ya dinga ti da k’arfasa har saida ya bud’e d’akin.. Yai azaman shigowa balcony d’in yanda Safeenah ke tsaye tana fad’in zata fad’o k’asa Musaddiq na bata hak’uri, Kiki kam ma school bag d’inta Ta d’ora aka cikin tsananin daburcewa tana kuka.
A daidai sanda Mu’azzam ya shigo Safeenah har ta saki k’arafan ta nufo k’asa, ya daka firgitaccen tsalle daga yanda yake ya tallafo Safeenah had’ida janyosa ta dawo cikin jikinsa.
Ganinsa da tai sai ta kuma fashewa da wani sabon kukan ta fad’a cikin jikinsa tana fad’in “Our Baby.. Our baby Mu’azzam.. Mommy killed our child.. Ta kashe mana D’a.. Mommy ce ta kashe mana D’a Mu’azzam.. Bazan tab’a yafe mata ba..”
Sosai ya rik’eta cikin tsananin tausayi yana furta “Ya isa Safeenah.. Kiyi shiru haka nan.. Ya isa..”
Safeenah ta kuma fashewa da wani kuka daidai sanda Musaddiq da Kiki suka k’araso wajen. ‘Yanuwan suka k’arasa a guje suka rungume Safeenah babu kaman Kiki wacce Ta mak’alk’aleta sosai tana fad’in “Addah Feenah don’t please.. Don’t ever try that again.. Wllhi muna sonki..”
Fincika Safeenah tai daga rik’on da Kiki tai mata, tana kuma jada baya bata daina hawaye ba take fad’in “Baku nake so ku soni ba.. The only person da nake so shine wann..!” Tai nuni da Mu’azzam dake tsaye gefe yana dubanta.
Safeenah taci gaba da jada baya tana kame cikinta tana fad’in “Daga shi sai D’anmu.. Su kad’ai nake so su soni a Duniyar nan.. Ban damu wani ya soni ko ya k’ini ba idan har zasu soni, idan har zan kasance tare dasu.. Kuma d’ah na yana nan I’m sure Mommy batai nasaran ciresa ba kaman yanda tai niyya.. Zo ki tab’a kiji Kiki.. Ina iya jin motsinsa..” Tana maganar hawaye saman fuskarta amma murmushi take tana kuma shafa cikinta.. “Ga D’ah na nan.. D’ah na yana nan.” Tai Saurin K’arasowa wajen Mu’azzam tana fad’in “Kaji D’anmu na motsi.. Gashi nan yana motsi.. He’s a fighter.. Bai yarda Mommy ta datse masa rayuwarsa ba..”
Ana haka d’aya daga cikin ma’aikatan gidan ta shigo da package ta mik’awa Kiki tana fad’in delivery man ne ya kawo Wai a shigo ma Safeenah dashi.
Kiki ta amsa ta nufo d’akin, Safeenah tana hangota da package d’in ta mik’e tana fad’in “Look my Halal.. Ga kayan Babynmu da nai order jiya online ya iso.. First gift d’insa daga wajen Mamansa.” Tana maganar tana warware package d’in ta shiga fito da kayyayakin wanda duka kayan yara ne.. Kama daga kayan sakawa na early born baby zuwa takalmi harda toys.. Sai fito da kayan take tana sunbatu Tamkar dai mai tab’in hankali.
Kiki tai lamo tana duban ‘yaruwarta cikin tsananin tausayawa yayinda Mu’azzam ya shafi fuskarsa kad’an ya janyo Musaddiq suka fice.
“Ina Mommy..? Na tabbata bata gidan nan..” Mu’azzam yace yana duban Musaddiq.
Girgiza kai Musaddiq yai “I have no idea.. Bansan yanda taje ba..”
Mu’azzam ya kafesa da idanunsa da suka gama kad’awa zuwa ja “Musaddiq zan sake tambayarka a karo na biyu, Ina Mommy take..?”
Girgiza kai Musaddiq yai yace “Wllhi ban Sani ba.. Tare da kai muka shigo..”
“I know, nasan tare muka shigo.. But maybe zaka iya sanin yanda taje.. Gidan ‘yar uwa, Abokiya ko wata Confidante haka..?” Ya k’arashe yana tsare Musaddiq d’in da idanu kaman dai yana interrogating nasa.
Musaddiq ya kuma girgiza kai “Ban sani ba Mu’azzam.. Kuma idan na sani zan fad’a maka..”
Jinjina kai Mu’azzam yake yana duban Musaddiq d’in “Zan nemo Mommy.. Zan nemota duk yanda ta shiga.” Yana ida fad’in haka yasa kai ya fice cikin sassarfa.
Musaddiq yana komawa cikin gidan ya tadda Safeenah sai tsalle take tsakiyar d’akin tana juyi tana rungume kayan baby cikin jikinta.. Sai sunbatu take Kiki na gefenta tana kuka.
Kuka ne yaji yazo masa, cikin sauri ya fice daga d’akin yana kame kansa dake tsananin sara masa..
Kiki ma cikin kuka ta kulle Safeenah a d’aki kafin ta shiga dialing Daddy.
Daddy dake zaune gefen Aunty Nuratu sai ganin kiran Kiki yai na shigo masa, koda Daddy ya d’aga wayar Kiki kuka ta fashe masa dashi tana fad’in “Daddy... Daddy dan Allah kazo.. Daddy komai ba lafiya a nan.. Daddy Mommy Ta gudu.. And Safeenah is gone crazy..” Ta k’arashe cikin tsananin kuka tana mai duk’awa k’asa.
Alhaji Marwan ya soma karanto Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un a hankali kafin yace “Karimatu lafiya.. Ki nastu ki sanar dani meke faruwa..”
Cikin kuka Kiki ke fad’in “Daddy kawai ka dawo kafin Adda Feenah ta rasa ranta.. Daddy bazamu iya ba dan Allah ka dawo..” Ta k’arashe cikin kuka sosai.
Daddy ya lumshe idanunsa a hankali kafin yace “Ina Hajara..? Wai me yake faruwa a gidan ne..?”
Cikin kuka take fad’in “Daddy kawai ka dawo dan Allah Daddy..!” Kuka ya hanata ci gaba da magana.
K’ok’arin natsa kansa Daddy yai kafin yace “Shikenan, ki natsu kinji.. Ina nan tafe.. Ki kwantar da hankalinki kinji.. Ina Yayanki Musaddiq..?”
Kiki ta d’an waigo saidai bataga Musaddiq ba “I don’t know Daddy.. Maybe sun fice da Ya Mu’azzam..”
Daddy ya jinjina kai yace “Take care of your sister kinji koh.. Don’t leave her alone.. Zan kira yayun naki..” Daga haka katse kiran Daddy yai yana neman layin Musaddiq, saidai wayar Musaddiq bata shiga.. Ya kira na Mu’azzam ma bai samu ba.. Tanata rantse ringing ba’a d’agawa.
Juyowa Daddy yai yana duban Aunty Nuratu. A hankali ya d’aura hannunsa guda saman nata dake aje gefensa. Ya k’ura mata idanu kafin ya d’ago hannun nata ya sumbata. Lokaci guda yake furta “Kin tuna.. Kin tuna lokacin da ni d’in na tsinceki.. Kina cikin yanayi ne irin wann.. Ko ince yanayi mai kama da wanda kike ciki yanzu.. Baki san kanki ba a lokacin.. Kinyi losing memory... Bakisan komai ba, baki kuma san daga wata duniyar kika Zo ba.. A lokacin ina makaranta ne a can jihar Lagos birnin Ikko, dani da Yayana Abubakar.. Ranar sa ce ta k’arshe a makaranta..” Daddy yai shiru a daidai lokacin da ya soma tuno wani b’angare na rayuwarsu a baya.
_WAIWAYE_
Samaruka ne guda biyu suke zaune a k’ofar University of Lagos. K’aramin wanda duka duka babban bazai tsere masa da shekaru biyu zuwa uku ba ya dubi D’anuwan nasa wanda kallo guda zaka masu ka fahimci akwai shak’uwa da k’aunar juna irinta ‘yanuwantaka mai k’arfi tsakaninsu “Hamma zanyi kewarka sosai a makarantar nan.”
Wana aka kira da Hamma ya dubi D’anuwan nasa murmushi saman fuskarsa, Ya d’an shafi sumarsa kaman yanda yake masa a ak’asarin lokuta. Sai yace “Nima zanyi kewarka Marwan.. Amma kar ka damu zan dinga kawo maka ziyara.. Lagos ai ya zama mana gida.. Sann ga Salman kwanan nan shima zai taho ya soma nasa karatun.. Bazakai kad’aici ba..”
Marwan ya d’an b’ata fuska yace “Jami’a ba kaman sakandare ba balle kace zaka ke kawo mun ziyara.. Nasan Salman zai taho kwanan nan amma da kai nafi sabawa D’anuwana.. Zanso nima na koma kusa da Baffah da Inne na k’arasa karatu na a can.. Gaskiya na gaji da zaman kudu.. Balle yanzu da baka nan banjin zan iya..”
Abubakar wanda shine Hamman Marwan ya kuma murmusawa yace “Zaka iya Marwan... Wayasani ko matarka a nan Kudu take. Kaga sai ka samo mana sirka a nan.” Yai maganar Cikeda barkwanci.
Marwan ya zaro ido waje kad’an ya girgiza kai yace “Aure a kudu.. Kaima kasan Baffa da Inne bazasu tab’a amincewa da hakan ba.. Musamman Inne..”
Abubakar ya murmusa kad’an yace “Kasan menene..? Tashi muje..” Ya k’arashe yana mik’ar dashi tsaye.
“Ina zamuje..?”
“Gari zamu zaga kafin na tafi..”
Marwan ya murmusa kafin yace “Toh ina zamuje..?”
“To the Port.. Muje muga jiragen ruwa muyi nishad’i bakin Teku..” Abubakar ya basa amsa kai tsaye.
Marwan ya murmusa yace “Zanji dad’in hakan kuwa.” Suka murmusa a tare yayinda Abubakar ya janyo D’anuwansa suka soma tafiya.
Sanda sukazo tashan jirgin Ruwa sun tadda tashan wayam babu kowa kaman anyi yak’i an cinye.. Sukaita Yawo tsakankanun jiragen ruwa suna kallon wasu jirage da suka k’one.
Marwan ya tsaya jikin wata babbar jirgi da ta lalace yana kallon cikin jigin, nan ya hango kaman k’afar mutum daga kwance.
Baiyi wata wata ba ya haye ya shige cikin jirgin yayinda Abubakar ya soma kiransa yana fad’in yazo su tafi kafin wani abun ya samesu.
Marwan ya girgiza kai yace “Ka jirani a nan Brother ina zuwa..” Bai tsaya sauraron D’anuwan nasa ba ya shige cikin jirgin yana kuma mamakin abinda ya hango.
Saida ya k’araso sosai ya kuma tabbatarwa k’afar mutum ne ke reto.. Cikin sauri ya soma k’ok’arin janye katakon da ya rufe fuskarta zuwa gangar jikinta. Gabansa ya yanke ya Fad’i sakamakon bayyanar kyakkyawan fuskarta.
A hankali Marwan ya furta”Nooor..” Yai fasali yana kuma dubanta kafin ya duk’a a hankali “Mai kikeyi a nan baiwar Allah.. Wacece ke...?”
Yanayin suturan dake jikinta da wani irin kitso dake kanta wanda akai kaman gammo da sumarta ya tabbatar masa watak’ila daga wata nahiyar ta taho nan.. Ya duk’a a hankali yana kuma k’are mata kallo.. Kyakkyawar budurwa ce wacce bazata gaza shekaru 15 ba a wancan lokacin. Marwan yai zaune ya tasata gaba yana kallonta yama mance tareda D’anuwansa yake. Har saida Abubakar d’in yaji shiru ya shigo cikin jirgin yana neman D’anuwansa, can ya hangosa zaune gaban mutum. Ya k’araso a hankali yana dubansa.
“Marwan wacece wann..?” Abubakar ya tambaya.
Marwan ya girgiza kai alamun bai sani ba, Abubakar yai saurin k’arasowa ya kamo hannunsa “Tashi mu tafi.. Tashi mu bar wajen nan..”
Marwan ya girgiza kai “No.. Bazamu tafi mu barta a nan ba.. She needs our help..”
“But we don’t know her Marwan.. Ina zamuje da ita... Kaga Zo mu tafi kafin wani ya ganmu.. Ban yarda da wajen nan ba..” Abubakar ya k’arashe yana k’ok’arin janyo D’a uwansa Marwan.
Tarjewa Marwan yai yana fad’in “No bazan tafi na barta ba.. I’m staying right here with her.. Dan Allah ka taimaka min mu d’auketa mu kaita asibiti..”
Abubakar yai shiru yana duban D’anuwan nasa yana kuma duban budurwar dake kwance idanunta a lumshe “Marwan bamu santa ba, bamu San daga wace duniya take ba.. Bamu San wacece ita ba.. Maybe ‘yanuwanta suzo nemanta.. Kaga kazo mu tafi bana so ka saka kanka a matsala..”
“Hamma bazan tafiba ba tareda ita ba.. Idan kuma kai zaka tafi fine kaje..”
Ya k’arashe yana mai k’ok’arin d’agota.
Abubakar yai tsaye yana dubansa sai kuma