Showing 33001 words to 36000 words out of 209154 words
itace ya kamata yace ashe mutum ce amma shine take masa zaton ba mutum bane.. Ya kafe yarinyar da idanu cike da mamaki yana mai kuma turb’une fuska..
Ajidde ta d’ago idanu daga duk’en da take tana duban Fuskarsa da dust ya b’ata masa yayi fusufusu.. Lokaci guda ta tintsire da dariya tana nuna fuskarsa take fad’in “Wllhi saikace Kuran tashe..” Tana maganar tana nunasa tana dariya..
Yanda ta wage hak’waranta tana dariya ga janbaki har kumatunta ya mugun bawa Musaddiq dariya, Ai take shima ya b’ige da dariya yana nunata yana dariyar.. Itama bata fasa nunasa tana ci gaba da dariya ba..
Cak ta tsaya da dariyar da take sakamon jiyo motsi da tai daga waje kaman wani na zuwa, tasan bazai wuce mutumin da taso b’alla jakarsa bane.. Fit ta had’iye dariyar tai saurin yin alama wa Musaddiq da hannu kan yayi Shiru..
Musaddiq ya daina dariyar da yake, yai shiru yana dubanta, lokaci guda take masa alama a hannu kan ya duk’a ya b’oye shima..
Babu musu ya duk’a ya d’an b’oye shima.. Sunajin motsin na kuma matsowa yanda suke.. Sukai likimau suna sauraron tafiyan.. Har kaman an tab’a k’ofar sai kuma sukaji an koma ba’a shigo ba.. Saida suka tabbata sun bar jin tafiyar kafin Ajidde ta sauk’e ajiyan zuciya tana furta “Allah ya ceceki Jidde yau da kin sha harsashi..”
Musaddiq yace a fili “Ke Wai gudun me kike ne..? Wacece ke ma Wai..?”
Ajidde ta mik’e tana fad’in “B’arawo ne ya biyoni.. Da k’yar nasha harda bindiga hannunsa..”
Musaddiq yace “B’arawo kuma a nan.. Bayan duka masu gadin dake tsaron babban k’ofa..?”
“Auho baka yarda ba amma ka biye mun ka b’uya.. Na fad’a maka har bindiga nadashi Allah ne ya kare bai ganmu ba da ya had’a da kai..”
Musaddiq ya d’anyi tsaki a hankali sanda Ajidde taci gaba da nuna fuskarsa tana dariya tana fad’in “Yauwa ashe dariya nake ya kaste min..”
Girgiza kai Musaddiq yai yace “Ke are you crazy.? Wait waima mai kike a nan ne..?”
Sai sannan Ajidde ta tina bada magani tazoyi..
“Jaka na..!” Ta furta tana shafa bayanta.. Lokaci guda taci gaba da furta “Na shiga uku.. Na zubar da maganin.. Shikenan yau Inna Kyallu halak’ani zatayi.. Wayyo Na shiga uku na mutu na lalace..!” Tana maganar tana kuka tana kuma lalumen maganin.. Dariyar da Ajidde take ya koma kuka..
Harga Allah yanda dariyarta ya bawa Musaddiq dariya kukanta ma dariyar ya basa.. Hannayenta biyu ta saka aka tana kukanta.
Tin yana dariyar kukan nata har kuma ta fara basa tausayi. Yai k’ok’arin saita kansa yace “Ki nastu ki fad’a mun meke faruwa..”
Ajidde ta kuma fashewa da kuka tana fad’in ta zubar da maganin.
Musaddiq yace “Wani magani.?”
“Maganin masu Gidan da Innata ta aikoni na kawo.”
Sai sannan Musaddiq ya fahimci d’iyar mai maganin Aunty Nuratu ce.
“Toh yanzu ya kike so ayi..?” Musaddiq ya tambaya.
Ajidde naci gaba da kukanta take fad’in “Ni wllhi ban Sani ba.. Abu d’aya na sani shine yau zan yabawa Aya zak’i hannun Inna Kyallu..?”
“Wacece Inna Kyallu..?”
“Inna ta ce.” Ta bashi amsa kai tsaye
“Toh yanzu mai zakice wa mutanen gidan da kika zubar masu da maganin.?”
“Nima ban Sani ba.. Kai zaka ce masu..” Ta fad’i hakan abinta.
“Ni kuma.. Ta ina na sansu da zan shiga na sanar dasu kin zubar masu da magani..” Cewar Musaddiq yana dubanta
“Toh ba Kai kana masu aiki ba Ai ka sansu..”
“A’a ni aiki kawai nake masu.. Kuma masu gidan basuda kirki balle na shiga na miki cover.. Nima aikin da ya shafe ni kawai nake ko shiga gidan banayi..”
Ajidde tai zururu da ido tace “Toh yanzu ya zanyi..? Dan Allah ka taimakeni ka shiga ka tsara masu zance ni naje naji da Inna Kyallu.. Dan Allah Kuran Tashe ka taimakeni..”
Sunan data kirasa dashi ya sanyasa dubanta kad’an yace “Ke mai kikace..?”
Tai saurin kama bakinta tace “Toh bansan sunanka ba..”
“Ba Lallai ki sani ba.. Makeup abuser..”
“Sunanka kenan..?” Ta tambaya tana dubansa..
“A’a naki dai..” Ya bata amsa kai tsaye..
“Ni sunana Ajidde Jidde Jiddodo d’iyar Kyallu mai Warka warka.. Ka fahimta..”
Musaddiq ya zuba mata idanu ya da take jero sunaye.
“Toh ai sunayen naki da yawa wanne zan d’auka.?”
“Duk wanda ka d’auka ma yayi.” Ta basa amsa kai tsaye.
Musaddiq ya murmusa kad’an sai kuma yace “Toh yanzu ya za’ayi ki fice B’arawon nan na nemanki..”
Ajidde ta zaro idanu tace “Bazan fice ba sai ka min alk’awari zaka shiga gidan nan ka kareni kafin gobe Inna ta nik’o gari tazo da kanta..”
Ya girgiza kai yace “Bana alk’awari.”
“Toh ka taimakeni kaman yanda Allah ya taimakeka..” Tai maganan tana mai k’ok’arin duk’awa..
“Ke tashi basai kin durk’usa ba.. Naji zanyi magana ma abokin aikina shi yana shiga gidan.. Toh amma mai zance masu..? Nace masu b’arawo ya biyo mai maganin..”
Baikai aya ba tai saurin dakatar dashi da fad’in “A’a kar kace haka..”
Musaddiq ya tsareta da idanu yace “Toh k’arya kika mun kenan..”
Ajidde ta shiga raba idanu tana twisting ‘yanyatsunta.. Murmushin yak’e tai yellow teeth d’inta da basu ganin brush suka bayyana kafin tace “Dama ai k’arya na maka.. Barin fad’a maka gaskiyar.. Kanaji tsinkar mangoro zanyi shine ya biyo ni a guje harda bindiga..”
Musaddiq yace “Toh kece b’arauniyar kenan..”
Ajidde ta fito da harshenta ta dangwala da yatsarta manuniya tace “Aradun Allah ban d’auki mangoron ba.. Ai kai shaida ne da ka ganni da ita..”
Sosai ta basa dariya musamman rantsuwar tata..
Ya jinjina kai yace “Shikenan yanzu kije ni nasan mai zance ma abokin nawa Sai ya fad’a masu..”
Ajidde ta jinjina kai tana masa godiya.
Har zata fice yace tsaya..
Ta dawo da baya tana dubansa.
“Idan kika fita haka mutumin da yake chasing d’inki zai ganeki.. Bari na miki dabara yanda bazai ganeki ba..” Ya k’arashe yana mai cire malfar kansa.. Lokaci guda ya d’aura mata akai yace “Yauwa he won’t be able to recognize you now.. Kina iya tafiya..” Ya k’arashe yana mai sakar mata murmushi..
Murmushin itama ta sakar masa tana mai furta ta gode..
Yanda take murmushi tana sanne ido ya mugun bawa Musaddiq dariya, Aiko nan ya tintsire da dariya.. Take Ajidde ma ta tintsire da dariya tana kuma duban fuskarsa mai lullub’e da hazon k’ura.. A haka ta fice tana dariyarsa yana dariyarta..
A b’angaren Mu’azzam kuwa tinda yabi bayan yarinyar bai cimmata ba Sai ya yanke shawarin tambayan securities na gidan gonan Ko sunga yarinyar da yake nema.. Saidai kafin ya isa wajen securities ya hango Daddy da Uncle Salman sun fito daga wani babban Office suna tattaunawa Uncle Salman d’in na nuna ma Daddy wasu documents.. Ko ba’a ce ba Business suke tattaunawa..
Suna hangosa fari’ar Daddy ya k’aru, yama daina sauraren Uncle Salman wanda shima tuni ya tsaya da bud’e takardun yana duban D’an d’anuwan nasa wanda sam inuwansu Bai jituwa..
Mu’azzam na K’arasowa Daddy ya tafi ya d’an basa light hug yana fad’in “A’a Inspector sauk’an Yaushe..?”
Mu’azzam na murmushi ya d’an sadda kai yana gaida Daddy.. Su duka biyun annuri ne saman fuskokinsu..
Uncle Salman ya d’anyi gyaran murya yace “Sirki na rungumar Sirki nan dai ba Abuja bane..”
Murmushi bai bar saman fuskar Daddy ba yake fad’in “Mu’azzam D’ah na ne ba Sirki na ba..”
Mu’azzam ya d’an kaikaito yana duban Uncle Salman, irin duban da yake masa tin yana yaro shine dai saman fuskar tasa.. Ya gaishesa cikeda girmamawa yana tambayan ya samesu lafiya..
Uncle Salman yace “Lafiya lou Mr Officer.. Saima bautan dukiyar ka da nake Kanyi wanda Yayana ya hana a cire maku Shares d’inku tun kafin rashin ‘yaruwarka..”
Take annurin fuskar Daddy ya d’auke cak.. Ya dubi Uncle Salman yace “Salman ya isa haka..”
Uncle Salman ya d’an tab’e baki kad’an yana maida hannayensa baya..
“Ni zan shige Meat Factory aiki na jirana..” Uncle Salman ya fad’i yana mai k’ok’arin shigewa.. Lokaci guda kuma ya kaikaito ya dubi Mu’azzam yace “Ina maka Barka da zuwa D’ah na Mu’azzam..!” Yai maganar murmushi saman fuskarsa.
Murmushin Mu’azzam ma ya sakar masa yana mai jinjina kai ba tareda yace komai ba..
Uncle Salman na shigewa Daddy ya kamo kafad’an Mu’azzam guda yana fad’in “Mu k’arasa ciki Inspector..”
SameenaAleeyou 📚
[9/3, 8:35 AM] My mom: *GIDAN ARO*
*13*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Inne tana ganinsa Ta soma masa lale kaman ta goyasa dan murna, Aunty Shemau ma na zaune wajen tai masa Barka da zuwa cikeda kulawa. Take ta tina wayan da sukaida Mommy, bazata tab’a bari Mu’azzam d’in ya fahimci wani abu ba.
Kakarsa sai nan nan dashi take dan Farin ciki, tuni ta soma masa tayin abinci daban daban harma tambayarsa take ko akwai abinda yake so a girka masa a gurguje. Mu’azzam yace “A’a Inne zanci duk abinda ya samu, amma zanyi wanka na duba Mamy first idan yaso sai muci dinner gaba d’aya..”
“Har dare bakaci komai ba, yammacin da saura fah..”
“No Inne babu komai ai ba wani yunwa nakeji ba ma.. Zan duba Mamy sai na d’an huta..”
Mik’ewa tai tana fad’in “Mutum yayi tafiya bai saka komai cikinsa ba inyi.. Badai a gidan nan ba..” Ta k’arashe tana mai kiran ma’aikatan.
Mu’azzam yabita da kallo murmushi saman fuskarsa zuciyarsa Cikeda k’aunar ahalinsa.
“You must be jet lagged.” Musaddiq ya fad’i murmushi saman fuskarsa yana mai k’ok’arin k’arasowa cikin parlorn.
Juyowa Mu’azzam yai sanda Musaddiq d’in ya k’araso fuska fal fari’a sukai handshake suna d’an hugging juna.
“Wai dama kana tafe.. Kuma shine baka fad’a mun ba.. I would’ve arranged something for you. You know this place is boring and annoying..”
Da mamaki Mu’azzam ke duban Musaddiq dake sanye da uniform na ma’aikatan gidan gona“I can see you’re better off here.. And to be honest, naji dad’in ganinka haka da uniform kana aiki..”
Musaddiq ya fuzar da fuci kad’an yana ‘yan waige waige dan ya tabbatar Inne bata wajen “Ai ni kawai matar nan ta gama dani.. Wllhi wnn jarabbebbiyar tsohuwa Ta gama dani.. Musaddiq Marwan Gamji no longer exists.. I guess fate has decided for me.. Ni kuma kalan nawa K’addaran kenan..” Yai maganar sanda suka jera suna tafe hanyar d’akin Aunty Nuratu..
Mu’azzam yaci gaba da fad’in “Haka shine da kyau Musaddiq, kaga one day you’ll takeover the family business. After all, Wannan shine mafarkin da a Kullum Daddy yake.. Wani daga cikinmu ya kula da kasuwancin Ahalin.. Saidai ni tuni Allah ya k’addari ba d’an kasuwa bane kaman yanda Daddy yaci min buri ni D’ansanda ne.. Naji dadi sosai da naga kai d’in zaka cika burin Daddy.. I’m so proud of you Musaddiq..”
“Kawai ka fito fili kaima kace kana Farin ciki da k’untata rayuwata da akai..” Musaddiq yace yana kuma b’ata fuska
Murmusawa wann karon Mu’azzam yai ya kaikaito yana duban Musadddiq sosai “Watarana zaka fahimci Inne gata ta maka Musaddiq.. We all love you, and we want what’s best for you..” Yai maganar kyakkyawan murmushi saman fuskarsa.
Gajeren murmushi Musaddiq d’in ma yai yace “Sai ka shafe watanni Abuja kaji bana nan sannan ne zakace a dawo maka dani and your Grandma bata kyauta ba data d’auke ni..”
Mu’azzam ya d’an daga fuskarsa suna ci gaba da takawa a hankali, ba tareda ya dubi Musaddiq d’in ba yace “At least zan d’an huta da rashin jinka..”
“Au haka kace. Zamu gani ai.. I know rashina a gareka tamkar rashin police force ne..” Cewar Musaddiq daidai sanda yake tura k’ofan d’akin Aunty Nuratu sallama saman bakunansu.
Aunty Shemau suka tadda ta gama kintsa Mamy ta d’aurata saman wheelchair.. Ta fad’ad’a murmushinta tana duban Mu’azzam d’in “A a Mu’azzam ka shigo, Aiko har na gama shiryata zan kawota wajenka.. Sai gashi ka shigo ma..”
Cikeda jin dad’in yanda Aunty Shemau ke kulada mahaifiyarsa yace “A’a dama zan shigo Aunty.. Sannu da d’awainiya fah..”
Aunty Shamau tai saurin katsesa da fad’in “A’a Haba dai Mu’azzam wani d’awainiya kuma.. Kawai na d’aura daga yanda ‘yar uwata Aunty Hajara ta tsaya ne. Aunty Nuratu ai ‘yaruwa ce a garemu.. Ka daina mana godiya kaman wani hidiman muke.. Ciwo ai na kan kowa, fatan mu dai Allah ya bata lafiya ya tashi kafad’unta..”
Gaba d’aya suka amsa da Ameen daidai sanda Mu’azzam ya k’araso gaban wheelchair d’in ya duk’a Aunty Shemau na kuma gyara mata kanta da ya tank’washe a karkace.
Mu’azzam ya zuba mata idanu zuciyarsa fal k’aunarta gauraye da tsananin tausayinta, Allah sarki inama wani na iya yaye ma wani cuta da ya bada duk abinda ya mallaka koda rayuwarsa ce dan mahaifiyarsa Ta sami lafiya.. Saidai ba haka abin yake ba. Allah shine yake jarabtan bayinsa da cuta ba Don ya k’isu ba saidai dan ya jarabci imaninsu da wannan cutan sannan ta kuma zame ma bayinsa na k’warai kankarewar zunubi..
Inne ce ta shigo tana tambayar ko mai maganin ta iso.?
K’irjin Musaddiq ya buga dan sai yanzu ya tina da Ajidde da yanda sukai..
Inne taci gaba da fad’in “Shemau ki kirata muji ko lafiya bata iso ba har yanzu.. Ni bana son ana sako shiririta cikin lamarin jinyar nan..”
Aunty Shemau ta d’an daburce tana fad’in “Ai Inne tace tana tafe.. Inaga abin hawa ne bata samu ba..”
Musaddiq yayi caraf yace “Wait. Wai mai maganin Mamy.. Ai kuwa tazo amma saidai akwai maganin data mance bata taho dashi ba wanda za’a bata yau d’in.. So sai ta koma, and I don’t think zata iya dawowa yau dan wajen da take zuwa akwai nisa daga nan.. And kaman hadari ne a garin..”
Duk suka juyo suna dubansa kafin Inne tace “Wannan ai shirita kenan..” Inne ta fad’i tana duban Musaddiq. Taci gaba da fad’in “Kuma sai ta rasa nawa zatai bayani sai kai..”
“Toh ai ni ta samu Inne shisa ta fad’a mun..” Baikai aya ba tace “Kai rufe min baki..” Ta dubi Aunty Shamau tace “Shemau ki kira matar nan kiji bayani daga bakinta dan ban yarda da zancen Gidado ba.”
Aunty Shemau ta jinijina kai tana fad’in “Toh Inne zan kirata..”
Shidai Mu’azzam bai bi tankasu ba hannun mahaifiyarsa rik’e cikin nasa har lokacin..
A haka har d’akin ya rage saura shi da mahaifiyarsa.. Addu’o’i ya dinga mata har Shemau ta shigo ta taddasa. Nan take sanar dashi mai magani tace ko zuwa gobe za’a iya bata idan Allah yakai rai dan lokacin ma ruwa ake tsulawa..
Ta kuma k’arasowa tana fad’in “Kaje ka huta kaci abinci Mu’azzam gani nan ga Hindu zamu kula da ita...”
Gajeren murmushi ya d’anyi had’ida mik’ewa yana ma Aunty Shemau godiya..
Yana ficewa Shemau ta Sauk’e ajiyan zuciya had’ida fuzar da fuci a hankali.
Ta maidoda dubanta ga Aunty Nuratu tana aika mata mugun kallo
“Nakasasshiyar banza.!” Ta fad’i tana mai hankad’a wheelchair d’in da Aunty Nuratu ke kai..
**
A b’angaren Ajidde kuwa koda ta koma gida ma Kyallu ba taro ba Sisi jibaganta tai Ta jefata d’akin Tumakai tace ta Kwana dasu, D’akin da Kyallu ke aje dabobbinta harda turke tayi ma Ajidde Wanda idan tai mata laifi take d’aureta a nan itama Ta Kwana tareda dabbobin.. Haka tayi lamo jikin turken da Kyallu ta d’aure mata k’afafu tana rungume da hular da ma’aikacin Gidan Gonar ya bata wanda bata San koda sunansa ba. Saidai tuni Ta masa lak’abi da Kuran Tashe..
Dikda azaban da take ciki hakan Bai hanata sakin murmushi ba sanda ta tina had’uwarta da mutumin wanda ko sunansa bata sani ba.. Tanaji can k’asar zuciyarta tana son ta sake ganin wannan fuskar tasa mai lullub’e da hazon k’ura wanda ya sanyata dariya da nishad’i har ya mantar da Ita ukuban da Inna Kyallu ke mata..
Washe gari bata aiki Ajidde ba da kanta tai shiri Ta nufi gidan dan bama Majinyaciyar maganinta..
Kyallu tana fita Ajidde ta samu ta k’ok’arta ta tsinke Turken data d’aureta. Gefe da Gidansu akwai wata mata wacce malama ce kuma har matan aure tana koyarwa, wasu lokutan idan Kyallu Ta fice tsiddabarunta da bokancinta gidan Malama Hafsatu take zuwa domin ta taimaka mata da abinci..
Yau d’inma hakance ta kasance da Ajidde..
Malama Hafsah na aji tana ma matan aure karatu Ajidde ta shigo da k’yar da k’yar kaman zata kifa k’asa..
‘Yan aji suna ganin Ajidde suka soma k’ok’arin mik’ewa kowacce tana neman hanyar gudu dan an canfa ance tanada Farin k’afa dik yanda taje Sai bala’i ya auku wajen.. Malama ta tsawatar masu da fad’in “Shin ba yanzu muka gama karatu kan yarda da canfi ba.. Canfi haramun ne a musulunci.”
Wata mata Ta d’aga hannu tace “Malama inada tambaya”
Malama Ta jinjina mata kai tace “Ina sauraronki..”
“Amma malama ai akwai Kambun baka.. Shin shi ba canfi bane..?”
Malama ta jinjina kai tace “K’warai Al’ainu haqqun. Akwai Kambun baka, harta a musulunci an yarda akwai Kambun baka, yazo kuma a sunna cewa akwai Kambun baka har an bamu addu’a da zamu dinga yi domin neman tsari daga sharrin Ido wanda ake cema kambun baka.. D’aura laya ko wani abu mai kama da haka da sunan neman kariya daga sharrin ido haramun ne a musulunci.. Yin hakan shirka ne inji Manzon Allah SAW, hadisin yana nan a cikin Musnad Ahmad 16969.” Malama ta d’an tsagaita kafin taci gaba da fad’in “Wacce dik take neman kariya daga sharrin ido ko Kambun baka ga abinda zatace ‘A’uthzu bi kalimatillahit taammaati min kulli shaid’anin wa haammaa wa min kulli ainin laammaa.’ Wannan addu’a ce ingantacciya datazo a sunna sannan zaki iya karanta ma yaranki ko wacce safiya da maraice domin nema masu kariya daga sharrin ido dama duk wani shed’ani ko abin sharri.. Babban darasin da nake so mu d’auka a nan shine wani baya tab’a sauk’ar maka da bala’i sai idan Allah yaso haka wani baya tab’a kawo maka nasara sai idan Allah yaso Kun fahimta..”
Gaba d’aya suka amsa da “Na’am Malama mun gane..”
Malama ta jinjina kai tace “Monita ki bud’e shafin da muka k’ara jiya ayi bitarsa kafin na dawo muyi k’ari.. Ku d’an ara min lokaci naji da Ajidde..”
Gaba d’aya suka jinjina kai suna amsa mata..
Malama ta janyo Ajidde suka fice zuwa tsakar gidanta..
Dik karatun kore shirka da aikata tauhidi da malama tai tsaf Ajidde ta saurareta, gaba d’aya jikin Ajidde yayi sanyi domin kuwa abinda Inna Kyallu ta d’aurata Kai kenan..
Malama ta nufi kitchen ta d’auko ma Ajidde abinci Ta bata tace ta zauna taci..
Saidai yau gaba d’aya jikin Ajidden a sanyaye yake babu sokancin data saba yima Malama.. Tak’i zama taci abincin ta fice sai waige waige take tana kuma duban Malamar rungume da kwanon abincin. Sauri sauri ta fice dan kar Inna Kyallu ta dawo ta tadda bata nan..
Malama Ta bita da kallo cikeda tausayawa har Ta b’ace ma ganinta.. Allah ya gani rayuwar yarinyar sosai yake bata tausayi..
**
Koda Kyallu ta isa gidan gonar sassafe tasa aka rufesu a