Showing 138001 words to 141000 words out of 209154 words

Chapter 47 - GIDAN ARO COMPLETED HAUSA NOVEL

13 Jul 2025

3071

tintini Malam Sadi ya tada mota ke ake jira..” Ta k’arashe tana janyo Ajidden daketa faman waigowa tana kuma duban hoton Musaddiq daketa sakin murmushi. Mamaki fal Zuciyar Ajidde Wai jikan gidan ne.. Shine yace mata shi ba d’an gidan bane babu abinda ya had’asu Sai abota da yake da d’an gidan.. Wato k’arya ya mata kenan.. Toh Maiyasa ya mata k’arya.. Maiyasa ya b’oye mata asalinsa.. Duk sai taji babu dad’i.. Jikinta gaba d’aya sai taji kaman an zare mata laka.. Duk da wauta da shahshashanci irin nata sosai taji zafin abinda Kuran tashe yai mata na b’oye mata kansa da yai, sannan tana son sanin Maiyasa ya mata hakan.

Ranan haka Ajidde har Ta koma gida tunanin da take kenan b’oye mata kansa da Musaddiq yai.. Sunansa kuwa ranan kaman biya karatu haka taita nanatawa.. Yanzu Kyallu batada lokacinta sosai dan tana samun majinyata da take kwantar dasu a nan gidanta akai akai.. Idan ta baiwa Ajidde maganin Gidan Gona bata kuma bi takanta.. Hakan sai yafi ma Ajidde dad’i da bata yini a gidan balle taga yanda ake shirka ma Ubangiji da sunan magani. Ko safiyan Washe gari ma da zata fice taga wata mata an kawota bata cikin hayyacinta Kyallu tace a kawo Bak’in zakara da budurwa Baru a masu barbara sannan aka buga kan bak’in zakaran da dutse wanda saida ya mutu jini ya soma zuba Kyallu tace Jinin za’a baiwa matar sannan a shafe jikinta da sauran shine maganin ciwonta..

Ajidde Ta girgiza kai kurum kafin ta fice ta nufi gidan Malama Hafsah.

Daga yanda Malama ta ganta Jiki a sanyaye ta fahimci wani abu na damunta.

Malama ta tambayeta meke faruwa.?

Ajidde tai shiru tana duban Malama bata sanar da ita abinda Musaddiq yai mata ba Sai ta soma sanar da ita abinda taga Kyallu tayi.

Malama Ta nusa kad’an tace “Da yawan irin wad’ann bokayen sun ari sunayen masu magani na gargajiya suna fakewa suna yin bokancinsu Ajidde.. Tabbas akwai masu magani na gaskiya na gargajiya wanda ubangiji ya huwace masu ilimin sanin magunguna.. Sannan akwai Malamai masu magani da ayoyin Ubangiji bisa tsari da shari’a.. Sannan akwai wad’anda suke fakewa suke bokanci suna yanka dabbobi bada sunan Allah ba suna bawa mushirikan Aljanu jini.. Sai kiji ana cewa a kawo bak’in jaki za’ayi magani, a’a a kawo faran tinkiya za’ayi magani.. Irin wad’ann masu maganin Ajidde duk sun b’adda kama suna shiga cikin na gari suna bokanci da tsafi.. Suna shirka ma Ubangiji da sunan magani.. Akwai majinyata da ciwo zaik’i ci yak’i cinyewa.. Aita kawo masa sunayen masu magani gari wa gari.. Idan ba’ayi sa’a ba har a fad’a hannun irin wad’ann masu maganin wad’anda bokaye ne masu shirka ma Ubangiji ba wai maganin sukeyi ba wasu ma kawai sai su had’a ‘yanuwa gaba suce wane ne yai maka jifa alhali k’arya ce kawai bokanci ne da tsafi... Abu na farko da majinyaci zai saka a ransa shine jinyar nan Bautan Ubangiji yake.. Kuma jarabawa ce da Allah ya jarabcesa da ita domin yaga zaiyi hak’uri yaci jarabawa kokuwa zai kauce wa rahamarsa.. Duk zafin jinya zunubi ake kankare wa majinyaci.. Sannan suma masu jinyar wann majinyacin jarabawa ce da Allah ya jarabcesu da ita kuma duk d’awainiyar da sukai wa mai jinya lada suke samu wanda Allah shi zai biyasu wanan ladan na hak’uri da kuma d’awainiyarsu.. Hadisi yazo ingantacce Manzon Allah (S.A.W) yace babu wata cuta da Allah ya sauk’ar saida ya sauk’ar mata da maganinta. Ko wata iri ce kuwa... Neman magani ba haramun bane kuma godiyan Ubangiji shine ka saka dukiyanka ka nemi lafiya da Ita, amma saidai kar garin neman magani ka kai kanka ga halak’a.. Kar kaje wajen boka domin ya baka lafiya.. Babu mai warkarwa sai Allah.. Shi yake saka cuta kuma shi yake yayewa.. Idan yaso ko baka sha komai ba Sai ya baka lafiya dan shine mai bayarwan. Idan baiso ka sami lafiya ba ko zaka zaga duniyar nan Sai k’a k’arashi neman maganinka baka samu ba.. Tauhidi itace abu na farko da majinyaci yake buk’ata Ajidde.. Ita ce magani na farko da majinyaci zai sha.. Ya saka a ransa Allah shine mai yi kuma shine mai hanawa.. Idan ya tsira da tauhidinsa ko da Ubangiji ya k’addari wann jinya ba na tashi bane sai yayi fatan ya d’auki ransa yana mai imani ba yana mai kauce ma Ubangijinsa ba.. Sau tari zakiga anje wajen irin wad’ann masu maganin anyi bori anyi yanka ma aljanu sannan an halak’a daga k’arshe ba’a samu biyan buk’atan ba dan basu sukeyi ba Allah shine mai yi.. Ba’a samu biyan buk’ata ba Sannan an mutu ana kauce wa Ubangiji.. Allah ya shiryemu gaba d’aya ya kuma datar damu.. Ya ba ma marassa lafiyanmu lafiya, ya tsare mana imanin mu da tauhidinmu.. Ya d’auki rayuwarmu yana mai farin ciki damu..”

A hankali Ajidde ta jinjina kai tana fad’in “Ameen Malama..”

Malama Hafsah ta mik’o mata ruwa addu’a da take bata sannan ta had’a mata da garin Habbatussauda tace wannan hayak’insa zaki mata a cikin d’akin da take kwana.. Yana koran shaid’anu.. Sannan yanada kyau mutum ya dinga hayak’in habbatussauda a cikin gidansa lokaci zuwa lokaci domin yana kore shaid’anu daga gida.”

Ajidde ta jinjina kai tace “Toh Malama Allah ya saka da alkhairi ni zan wuce..”

Malama ta jinjina kai tace “Allah ya nufemu da dacewa ya kuma bawa Nuratu lafiya..”

Ajidde ta amsa da Ameen kafin sukai sallama da Malama ta fice.

**

ABUJA

Yau kusan kwanaki uku kenan bata sanyasa a idanunta ba, tinda ya tafi ranan da dare bata kuma ganinsa ba, gashi harta waya ma bai mata ba.. Haka zatai ta kallon lambarsa taji kaman ta danna kira amma sai ta fasa dan batasan mai zata ce masa ba.. Kasancewar laraba tayi ya sanya take ta jin wani Farin ciki cikin zuciyarta dan tafiyarsu Alhamis ne kaman yanda yace. Harga Allah ba Farin cikin tafiyar take ba amma tasan tana Farin ciki ne sabida zata gansa.. Tai shiru tana tuhumar kanta Maiyasa take jin haka akansa..? A baya zata iya cewa bata tab’a jin irin hakan ga kowa ba harta kuwa Sagir da suka kusan aure.. Ko dan lokacin abin hannayensu take so ba Su d’in ba..? Toh Maiyasa yanzu da bata son abin hannun kowa take jin haka gameda Inspector..? Kar fah maganan Aunty Larai ya tabbata cewa son Inspector take.. Cikin sauri ta d’ago kai tana duban fuskarta cikin dressing mirror.. Ta kuma tambayar zuciyarta.. Sai kuma ta rintse idanunta cikeda tsoron ansar da Zuciyar nata ke bata.. Ta k’ura ma fuskarta idanu cikin mirror kafin tace “Are you messing with my heart now Mr Inspector..?” Cikin sauri ta lumshe idanunta tana jinginuwa jikin gini.

Aunty Larai dake lab’e bakin k’ofa tana dubanta murmushi saman fuskarta, a hankali tai knocking da yatsarta guda.

Sadiya tai saurin tattara natsuwarta tana kintsa kanta.

Aunty Larai ta shigo sallama saman bakinta, hannunta rik’eda had’in Kankana..

“Maza Zo ki shanye wann..” Ta fad’i tana zama gefen gado.

Sadiya ta d’anyi rau rau da idanu dan kusan kullum Aunty Larai da irin had’in da take bata.

Ta d’an dubeta kafin tace “Bari dai na miki bayanin menene a cikin wanann.. Kinga akwai Kankana K’wallo d’aya sannan sakwai sabuwar tsamiya k’wara hud’u sannan akwai tafarnuwa curi d’aya.. Ita Kankana tanada tasiri jikin ‘ya mace sannan tsamiya magani ce itama.. Tafarnuwa kuwa Antibacterial ne.. Duk wata cuta da ta shafi mara tana maganceta.. Yana da kyau bayan lokaci ki dinga yi ma kanki wannan had’in dan takan bada kariya daga cuta na sanyi da ya addabemu a gidajen aurenmu.. Sannan ita wann had’in ko wanda ke fama da cuta na sanyi zai iya had’awa ya dinga sha da izinin Allah za’a samu waraka. A had’asu waje guda a dafa a dinga sha safe da yamma.. Kinga ba wani abu mai cutarwa na baki ba maza d’auki ki shanye.”

Sadiya ta d’auka ta kafa kanta ta shanye. Duk a kwanakin had’e had’e iri daban daban masu inganta lafiya da matantakanta Aunty Larai ta dinga bata.. Wasu Ta mata bayani wasu kaw bata mata bayani saidai ta sanyata cinyewa ko shanyewa.. Ga gyaran fata na musamman da take mata ita har Ta fara tinanin kodai had’a baki Inspector sukai da Aunty Larai shisa ya dena zuwa gidan.. Taga har alhamis Yayi babu Inspector babu batun tafiyarsu.. Abin har dai ya soma damunta gashi Aunty Larai bata fasa mata abu guda da take mata ba.. Fatarta ya kuma murjewa har wani kyalli da shek’i yake.. Jikinta ya kuma cika dan tana iya jin hakan tattare da ita.. A tak’aice ita kanta tana jin kanta Ta kuma canzawa. Idan ka kalleta dole kaso sake kallanta.. Wasa wasa saida akai kusan sati Inspector baizo gidan ba.. Ba abin Ta tambaya ba bama zata iya ba.. Idan ta zauna haka zatai ta kallon lambar wayarsa tana tinani.. Wasu lokutan ta kwab’i kanta tace k’ila ma ya mance da ita.. K’ila ma ya d’auki d’aya matarsa sunyi tafiyar.. Wannan tunanin shi yafi d’aga mata hankali.. Kardai ya d’auki d’aya matar tasa sun tafi ne tinda yace bazai kuma tilasta mata komai ba.. Maganganun Aunty Larai suka shiga zuwa mata cewa namiji baya son taurin Kai da kafiyar masifa da kuma musu, wad’ann abin sosai suke rage darajan mace wajen mijinta.. Sannan Ta bawa mijinta dama ya zamto babban abokinta kuma abokin shawarinta.. Yanzu ita da Mr Inspector Wai har zasu zamto manyan abokai irin yanda Aunty Larai ke fad’i..? Ta kuma duban fuskarta a madubi kafin zancen Aunty Larai ya kuma zuwa mata cewa Great Mission d’inta shine rayuwar aure dake gabanta, dan aure ibadah ne kuma bautan Ubangiji ne. Duk abinda Ta gani cikin gidan aure ibadah take.. Ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali kafin ta isa ta kwanta hoton fuskar mijinta cikin idanunta.

A ranan da yammaci Aunty Larai tazo da mai lalle Ta zana mata bak’i da ja hannu da k’afa.. Sosai k’unshi yai kyau ya amshi fatarta musamman da shike fatar tata ta d’auki gyara sosai.

Idan ka ganta kaman wata sabuwar Amarya ga wani k’amshi na musamman da take duk yanda Ta gifta..

Habeeb ya dubeta yace “Aunty Sadiya kunyi kyau sosai kaman ana bikinki..”

Gaba d’aya suka d’an dara Habeeb na kuma cikasu da sururtu. Kafin dare mai kitso tazo tai mata dan harta wanke kai da drying saida Aunty Larai tai mata.

Safiyar Washe gari litinin Aunty Larai ta sanyata ta shirya tsaf cikin wani embroidery atampa mai kyaun gaske ruwan cikin k’wai wanda ya tafi da kalan jikinta, d’inkin riga da skirt ne da ya masifan mata kyau cikin kayyakin da su Aunty Larai suka d’inka mata a nan cikin foundation d’in. Dama tin kwanakin baya Aunty Larai ta d’au measurement d’inta ashe Mu’azzam ne ya bama Aunty Larai tai mata d’inkuna masu kyau na zamani.. Sai gani kawai tai Aunty Larai dasu Farida ‘yanmata masu koyar da sana’ar d’inki a foundation d’in suna shigo da kayayyaki kama daga laces zuwa atmapopi hardai irinsu Dubai materials d’in nan.

Aunty Larai tasa Farida tai mata light makeup a fuskarta. Dik yanda Sadiya bataso ba haka dole akai mata mai sauk’i dama ita ba gwanar kwalliya ma fuska bace tin tana amsa sunan Sady pretty.. Kaidai barta da gayu ma jiki sai ka rantse d’iyar wata hamshak’i ne.. Dama bata faye fente fuska ba.. Yau d’in Sai abin ya zama na musamman abinka da wacce bata saba ba. Tayi kyau har ta gaji, Farida ta d’aura mata d’ankwalin daidai da kanta. Sai santin kyaun da ta k’ara suke.. Ita dai batace komai ba sai fad’uwa da gabanta keyi dan ko Aunty larai bata sanar da ita ba tanaji a jikinta Inspector ne zaizo, ga Umma ta kauda kai abinta bama ta saka masu baki cikin al’amaransu.. Toh kodai baiyi tafiyar bane.? Ta tambayi kanta tana duban kanta a mirror bayan an ida shiryata. Tabarakallah Masha Allah shine kawai abinda taji zuciyarta na ambata. Ta fito tsaf da ita kaman wata sabuwar Amarya.

Tana tsaka da tinanin wayar ya soma ruri. Ta juya tana duban wayar kan gado gabanta na kuma fad’uwa. Tasan idan bashi d’in ba babu mai kiran wayar Dikda cewa ba da lambar da ya sanya mata ba yake kiran.

Ta k’arasa a hankali hannunsa sai k’aran awarwaro yake kafin ta d’auki wayar.

Bata furta komai ba daga d’aya b’angaren ta sinkayo muryarsa cikin sallama.

Ta lumshe idanunta a hankali tana tinanin yaushe rabon da taji Muryarsa. Sallamar tasa ma a zuciya Ta iya amsawa.

Shiru kaman babu mai kuma cewa komai. Nan ta sinkayo muryarsa yana fad’in “Are you ready for your next mission..?”

Murmushi ne taji yazo mata wann karon.. Sai ta d’an murmusa tana rufe fuskarta da hannu guda.

Mu’azzam yaji sautin murmushin nata ta cikin waya. Shima murmushin yai kafin yace “Ki fito ina jiranki a parlor.”
Daga haka k’it ya katse kiran.

Ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali tana kuma duban kanta. Mayafinta kalan kayan dake aje saman gado ta d’auka ta yafa kaman mai tsoron ganinsa ko kuma wacce basu tab’a had’uwa ba haka nan taji.. Ta kasa fita saima komawa da baya da tai tana sauk’e ajiyan zuciya a hankali.

Kusan minti biyar ta kwashe kafin ta daure ta fito cikin taku a tsanake.

Tin daga nesa yake dubanta dan musulmin k’amshin da take ne ma ya soma yima k’ofofin hancinsa sallama.

Cak ya daina shafa wayar da yake ya mik’e tsaye yana dubanta sanda take k’arasowa.

K’afafunsa ta fara hangowa itama nan ta fahimci yau d’in shigar manyan kaya yayi.. Ta d’ago idanunta a hankali tana dubansa. Jampa ce jikinsa kalan ruwan k’asa sai hularsa Wanda ya dace da shigar tasa.. zata iya cewa wann shine karo na farko da ta gansa da idonta cikin manyan kaya tin bayan hoton aurensu da ta gani shida Safeenah a gidansu. Sosai shigar ya amshesa ita zata iya cewa irin wann shigar ma yafi amsar Sa. Ko kuma dan ta kwana biyu bata gansa bane shiyasa taga hakan bata dai sani ba. Kaman wacce aka tsunkula Ta kuma maida kanta k’asa tana jin kaman bazata iya ci gaba da tafiya ba sabida irin kallon da yake mata.





SameenaAleeyou📚
[9/3, 8:36 AM] My mom: *GIDAN ARO*




*45*




*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*





Kasa k’arasowa tai saima tsayuwa da tai daga can nesa kanta a k’asa. Gabanta na wani irin fad’uwa musamman da ta jiyo sautin footsteps d’insa alamun yana k’arasowa.

Saida ya tako kusanta kafin yaja ya tsaya yana kuma k’are mata kallo lokaci guda yana tsarkake mahaliccinta.. Cikin ransa yake fad’in Maiyasa suke kiranta Pretty...? Beauty ta cancanci su kirata ba Pretty ba domin kuwa she’s truly beautiful.. Ya k’arashe zancen zucin nasa yana mai kuma k’arasowa kusanta, dab kusanta ya tsaya yana duban tsakiyar kanta sabida ratan tsawo dake tsakaninsu.

K’amshin dake jikinta na kuma tasowa yana bugan k’ofofin hancinsa, hannayensa ya bud’e had’ida rungumeta cikin jikinsa idanunsa a lumshe. Itama d’in lumshe idanunta tai tana jin wani irin salama had’ida nastuwa na ratsa zuciyarta.

Sun d’an jima a haka kafin ya rik’o hannunta suka zauna saman kujera. Ta d’an duk’a ta gaishesa kanta a k’asa.

Ya tsareta da idanu yana duban Bak’on Al’amari a wajenta. Gaba d’aya shi gani yake ma kaman an canzata.

Ya amsa ba tareda ya janye idanunsa daga kanta ba. Suka d’auki lokaci a haka Sai k’are mata kallo yake, har ta soma gundura tana tinanin bazai kuma cewa komai ba, dan tasan mai hali baya fasawa. Nan kuma ta sinkayo muryarsa yana fad’in “It seems to me you’re ready.. For your next mission.. Kin shirya komawa GIDAN ARO..”


Sai sann ta d’an dubesa kafin ta maida kanta wani b’angaren, d’an juyowa tai tana dubansa murmushi saman fuskarta kafin ta jinjina kai tace “Of course Inspector.. I’m super ready to carry out my next mission.. But only for Inne..” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta.

D’an tsimewa yai kafin yace “Aw sabida Inne zaki yarda ki bini ba wai dan kina son bina ba.. Didn’t you miss me at all..?”

Sunkuyar da kanta tai tana murmushi. Sai kuma ta girgiza kai alamun a’a.

Kafeta da idanu yai sai kuma yace “Idan bakiyi kewata ba bazaki min Duka wad’ann kwalliyan ba..”

Dubansa ta kumayi, sai ta murmusa kad’an itama tace “Unfortunately ba sabida kai nai ba Inspector.”

“Toh sabida wa kikayi.?” Ya tambaya yana dubanta.

“Inne of course..” Ta basa amsa kai tsaye.

Mamaki ya cikasa ganin bataji haushi ba, yasan da da ne da yanzu hiran ya k’are yana sako mata zancen mission.

Ya jinjina kai kad’an kafin yace “Ki shiga ki masu sallama we are leaving now.. Akwai yanda zamu biya.”

Ta d’an d’ago tana dubansa a d’an tsorace wann karon “Da gaske kake yanzu zamu tafi..? To.. To.. Bakaci komai ba.. Should I bring something for you..?” Duk sai ta wani daburce lokaci guda.

“Calm down.. I’m not hungry.. I’m ok..” Ya fad’i yana mai kamo hannayenta da zanen k’unshi ya k’ara masu kyau.

Jiki a sanyaye take duban yanda ya sakale yatsun hannunta cikin nasa “I thought you said Kin shirya ma mission d’inki na gaba.. Why are you panicking then..?” Ya k’arashe yana mata wani salo cikin tafin hannunta.

So take ta cire yatsun hannun nata daga nasa amma ta kasa, ga tsareta da idanunsa da yai. Saida ya tabbata ya kashe mata jiki lak’was kafin ya d’anyi gyaran murya yace “Jeki masu sallama na k’agu a fara wann mission d’in..”

Gabanta ya fad’i tai saurin d’agowa tana dubansa, sai gani tai yankashe mata idanu guda “Go now.” Ya fad’i murya a hankali yana mai mata alama da idanu.

Jiki a sanyaye ta mik’e ta nufi ciki yayinda Mu’azzam ya d’au wayar salulansa

Tana shiga ciki maimakon ta sanar dasu d’aukanta yazo, sai ta soma masu kuka. Ta duk’a saman cinyar Umma tana kuka.. Aunty Larai ta duk’a tana lallashinta had’ida bata baki “Haba Sadiya saikace tafiyar da bazaku dawo ba, dukda duka bazaku shige sati biyu ba.. Tashi abinki kayayyakinki ma an fitar miki tintini.. Tashi kar ki b’atawa mijinki lokaci kinji koh.”

Ta d’ago tana duban Umma, kwantattun hawaye ta hango cikin idanun Umman. Basu iya furta komai ba Sai rungume juna da sukai.

“Allah shi maku albarka.. Allah ya tsareku daga dukkanin abin k’i ya azurtaku da zuri’a d’ayyiba.. Tashi kije Sadiya na yafeki duniya da lahira.. Allah yajik’an mahaifinki ya miki albarka..” Ta k’arashe suna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login