Showing 54001 words to 57000 words out of 209154 words
k’ok’arin k’arasowa kusan Inne dan yanzu har wani shiri ne na musamman ya shiga tsakanin Musaddiq da Innen tinda ya fara watsar da rayuwarsa ta baya.
“Gidado na Zo ka shige abinka kaji fita sha’aninta..” Inne tace tana duban Musaddiq d’in.
“Toh Inne na..” Ya fad’i yana gwalo ma Safeenah had’ida kashe mata idanu.
K’wafa Safeenah tai ba tareda tace komai ba dan harga Allah alla alla take Masoyinta Mu’azzam ya shigo Ta gansa.
Aiko bata ida tinanin ba ta hangosa yana tafe ya nufo k’ofar parlorn, yana sanye cikin k’anan kaya dark blue polo shirt da faded pants. Idanunsa na kan wayar salularsa dake hannunsa, hasken k’wan wutan manya manyan wutan lank’arki da suka k’awata gaban gidan sun haske masa fuska tarau, gani tai kaman ma zuwansa nan ya k’ara haske da kyau ne babu damuwar CID akansa babu komai.. Ta saki murmushi a hankali dan tama mance da abinda ke fuskarta. Idanunta akansa tana sakin murmushi har yai sallama ya shigo parlorn.
, idanunta naga masoyinta wanda shima ita yake duba cikeda mamakin bak’in dake fuskarta dan sam bai fahimci wacece ke zaune wajen ba har saida ta bud’e murya tace “My Halal.!”
“Safeenah.!” Ya furta a hankali yana mai kuma shigowa parlorn mamaki fal fuskarsa, har lokacin idanunsa na kanta. Bama mamakin bak’in fuskar nata yake ba, mamaki yake yaushe Safeenah tazo.
Inne ce takatsesu da fad’in “Yauwa k’araso dama kai nake jira.. Kazo ka sanar dani idan kai ka bata lasisin Ta dinga gantali saman kwalta da sararin samaniya Ita ba tsuntsuwa ba, tana a matsayin Amarya wacce ko tarewa batai ba.. Ai Iyayen naku ma basuda hankali da suka zuba maku idanu haka.. Toh ni bazan lamunci wannan asaranci ba.. Kafin Dangi su fara k’anan magana tinda shi Marwan ya zuba maku idanu kuyi yanda kuke so da rayuwarku ni zan masu abinda suka kasa.. Zaku tare a nan. Idan yaso a miki sabon jere a nan..Tinda abin naku ya zama haka sai a gyara maku d’aya b’angaren ki tare a nan.” Ta k’arashe tana duban Safeenah da ta saki baki tana jin Innen Wai zasu tare a nan.
Safeenah zatai magana Inne tace “Rufe mun baki.. Ba shawarinki nake nema ba.. Bazaku bar mun abun fad’i a dangi ba.. Na riga na gama magana.” Ta k’arashe tana mai mik’ewa da zummar barin parlorn.
Sai kuma ta juyo ta dubi Safeenah tace “Ke kuma Ki tashi kije ki wanke wann bak’ar fuskar taki kafin Ki razani mijin naki da ita..”
Sai sannan Safeenah ta tina da bak’in dake fuskarta, tai saurin Kai hannu zata tab’a sai kuma ta kasa ta shiga muryar kuka tana fad’in “Oh my gosh.. Eww.. I can’t touch it, It stinks.. My Halal please help me get rid of it.. Wllhi I can’t touch it..” Yanda take da fuska da hannu Kai kace kashi aka watsa mata.
“Meye a fuskarki..?” Ya tambaya yana dubanta.
“I don’t know.. Wllhi wata mahaukaciya ce ta watsa min.. Inne tace wai magani take bawa Mamy.. My Halal wllhi Mahaukaciya ce ka koreta.. I don’t trust her around Mamy..” Ta k’arashe tana kuma yatsina fuska da hannu.
“Biyoni..” Ya fad’i yana mik’ewa tsaye. Babu musu Safeenah ta biyo bayansa..
D’akinsa suka shige ya maida k’ofan ya rufe. Ya nuna mata hanyar bathroom “Shige muje..”
Ta d’ago tana dubansa da mamaki sai kuma ta shige sim sim.. Mu’azzam ya take mata baya.
Washbowl suka nufa yace ta saka fuskarta, tanaji ya d’auko sabulu yana wanke mata.
Yana ida wanke mata ta d’ago fuskarta tana duban mirror saidai to her surprise Mu’azzam ta hanga ta cikin mirror d’in yana rage tufafin jikinsa.. K’akk’arfan suffarsa da yasha training irin na Force ya bayyana. Ta zaro ido a tsorace had’ida juyowa tana dubansa, tana ganin ya soma nufota Ta soma k’ok’arin komawa da baya..
Fincikota yai ta fad’o jikinsa hakan yai daidai da tab’a makunnin shower dake kansu ai kuwa ruwa ya soma zubowa kansu. Tana jin hannunsa saman zip d’in rigarta yana k’ok’arin zugewa.. Har lokacin ta kasa janye idanunta daga duban fuskarsa da ruwa ya wanke tas Wanda sam babu walwala..
Zuciyar Safeenah yaci gaba da tsinkewa.. Cikin sauri kaman wacce aka zabura, tamkar wacce ta tina wani abu tai saurin rik’e hannun nasa ta hanasa tana mai girgiza masa kai ga idanunta da sukai rau rau.
Wani irin duba yake mata, lokaci guda ya kamo hab’arta had’ida d’ago kanta kad’an ruwan na zubo mata a fuska. Tsoro da tsananin firgici ya hango saman fuskar tata wanda dik a nasa tinanin tsoran kasancewa dashi take a matsayinta na budurwa sabuwar aure da bata tab’a sanin wani d’a namiji ba..
“Why.? Ba abinda kike so bane..? Ba abinda kike bibiyata sabida shi ba kenan.. Well na shirya baki yanzu a nan idan har zaki k’yaleni na gama binciken mutuwar ‘yaruwata da nake in peace ba tareda Kinyi causing mun distraction ba.. Fine zan baki sai ki daina bibiyata har na natsu na ida binciken da nake..”
Lokaci guda hawaye ya soma zarya saman fuskar Feenah.. Ta shiga girgiza kai hawaye na gangaro mata “No ni dai ba haka bane.. Dama dama kawai I was missing you ne.. That’s why I followed you here..” Tai maganar hawaye gauraye da ruwa saman fuskrta.
Ya tsareta da idanu yanda take shivering.. Janyota jikinsa ya kuma dikda tsananin rawa da jikin nata keyi, saitin kunnenta yake rad’a mata “Really..? Did you miss me that much..” Ya fad’i yana mata wasu salo irin nasa wanda tuni sun kashe mata jiki.. Lokaci guda yaci gaba da furta “Dama baki shirya ba kiketa bibiyata..?” Tai saurin girgiza masa kai tana hawaye.. Zatai magana ya rufe bakinta da nasa. K’arar wayarsa dake cikin aljihun wandonsa ya dawo da hankulansu.. Yai saurin zaro wayar yana duba mai kira, ba kowa bane face abokinsa kuma colleague d’insa Assad. Yai saurin kashe ruwan kafin ya shiga janyo Feenah yana fad’in “Zo ki fice..”
Ta dubesa da mamaki yanda yake fuzgota saikace ba shine ya nuna San kasancewa da Ita yanzu yanzu ba “Mu’azzam a haka zan fice.. Duba fah ka gani from head to toe a jik’e nake fah..”
Har saida suka k’araso k’ofa kafin ya turata ya janyo k’ofar ya rufe ba tareda yace mata komai ba.. Baki sake Feenah ke dubansa da tsananin mamaki.
Yana rufe k’ofar ya d’aga wayar Assad “Hey Officer, hope all is well with you..” Mu’azzam yace yana mai tsane jikinsa da towel.
Saida suka gaisa kafin Mu’azzam d’in ke tambayarsa “How are things at the CID.. Mai da mai kukai discovering so far..?”
Assad ya d’anyi gajeren tsaki yace “Things are getting tougher here, tinda ka tafi.. And Chief Jaja ya bud’e mana wuta mu kawo Danger within 2 days... Jiya ya mik’a team report d’inmu office d’in Chief Superintendent a General meeting d’in da akai, and babu wani progress har yanzu and he was even insisting bamuda case against Danger.. Saifa da nai presenting final report d’inmu ne ya tabbata Danger’s involved toh shine ya hura mana wuta mu kawo masa Danger yanda ya shiga ya fita..Ga dukkan alamu so yake case d’in ta lalace a haka ba tareda an sami wani improvement ba.. And Danger is no where to be found.. Dik wani hideout da muke tinanin zamu samesa bamu samesa ba, duk wasu masu criminal records da muke tunanin zasuyi linking d’inmu to Danger still babu wani haske har yanzu..”
Fuzar da huci Mu’azzam yai yana tura yatsunsa a sumarsa da suke wet.. “That scumbag I’m pretty sure he’s up to no good again.. Babu wanda ya isa ya rufe case d’in matuk’a ina numfashi.. Sai mun Kai har k’arshe yana so ko baya so.. Assad yarinyar nan itace kad’ai key d’inmu.. Inada tabbacin Babanta kashesa akai ba ordinary accident bane da ya saba aukuwa.. They’re after her family, I’m pretty sure bazasu k’yalesu haka nan ba.. Ya kamata muyi monitoring duk wani abinda ahalinta ke ciki.. Sannan Kai zaka fara tinda ni bana nan.. Go there, find out everything about them.. Dik information d’in da ka samu nasan zai ma investigation d’inmu amfani.”
Assad ya jinjina kai kaman yana ganinsa “Copy Sir..”
Lokaci guda ya k’arada “Baka tambayeni mutuniyar ka Maleeka ba.. Ita kaw kullum cikin missing d’inka take.. Tana counting days har zuwa randa zakai Reporting back to work.”
Gajeren tsaki Mu’azzam yai yace “Banida lokacinku daga kai har ita..”
Assad ya tintsire da dariya dan dama tsokanan abokin nasa yai niyya.
Sallama sukai kafin Mu’azzam ya zauna saman gado rik’e da wayar yana fuzar da fuci.. Zama bai gansa ba, yasan da biyu Chief yasa aka dakatar dashi dan ya samu sauk’in cimma burinsa cikin sati biyun idan baya nan, yasan muddin yana nan sai yanda k’arfinsa ya k’are bazai tab’a iya stopping d’insa ba.. Fuzar da fuci ya kuma yana jin zuciyarsa na masa zafi.
A b’angaren Safeenah kaw kafin ta isa d’aki wayarta ce dake cikin jakarta tai ruri, Meema da fitowarta kenan daga shower taji sautin waya na tashi daga cikin jakan Feenah. Kaman bazata d’aga ba dan tasan bazai wuce Mommy ba k’ila sunyi waya da Inne. Bata shirya ma fad’an Mommy ba. Amma jin wayar ta k’ara ruri ya sanyata k’arasawa jikin jakan ta d’ago wayar tana dubawa. Lamba ce Babu suna..
Meema dai samun kanta tai tana mai sliding kiran da ake.. Lokaci guda ta k’ara a kunnenta ba tareda tace komai ba.
Daga d’aya b’angaren Barr Ameer ya murmusa yace “Kin zaci zaki gudu mun ne Safeenah.. Dik yanda kikaje sai na biki.. Bazan tab’a barinki ma D’ansandan nan ba Safeenah.. You are mine.. Ked’in tawa ce ni Barr Ameer.!”
D’if Meema ta katse kiran tana kuma duban wayar k’irjinta na wani irin bugawa. “Barr Ameer..?!” Ta nanata a hankali.
Daidai lokacin Safeenah ta turo k’ofa ta shigo da jik’akk’un kayanta sai rawar d’ari take.
Da mamaki take duban Meema da tai tsaye rik’eda wayarta. Ta soma saurin nufo Meemar tana fad’in “Meye kikai wani tsaye a wajen sororo haka.. And why are you holding my phone.. bani kayata..”
Saidai kafin ta mik’awa Feenah wayar saida ta tabbata ta goge kiran.. Feenah ta fuzge wayarta tana aikawa Meemar mugun kallo “Waye ya kira..?”
“Babu mana.. Naji kaman wayar tayi ringing ne nazo zan d’auka, nayi tinanin Mommy ke kira Kinsan tawa babu charge.. Nasan dole zata nemu..”
Meema tace tana mai bud’e suitcase d’inta.
Tsaki Feenah tai tana mai neman towel take fad’in “Sabida kin mata sallama sanda zamu taho Ko..”
Meema ta d’an tab’e baki tana duban ‘yaruwar tata. Sai sannan ta kula da jik’an dake jikin Feenar..
“Addah Feenah.. Ya haka..? Ya na ganki a jik’e..?”
Tsaki Safeenah tai tana mai nufa hanyar bathroom..
Dariya Meema Ta soma tana fad’in “Kardai horon watsa ruwa yai miki a sanyin daminar nan.. Amma wannan miji naki anyi bak’in mugu wllhi duk wani salon mugunta ya Sani.. Koda yake ba laifinsa bane dama D’ansanda ne ya karanci sharri Da mugunta.. Allah ya cecen wann karon ba’a had’a dani ba..”
Ko amsata Safeenah batai ba ta shige toilet kayanta.
**
Washe gari sassafe Safeenah ta nufi d’akin Mu’azzam, dan tasan ya fice sallar asuba. Tana shiga ta fad’a kan gadonsa ta lume cikin bargo ta lumshe idanunta kaman mai bacci. Tasan babu yanda za’ai idan ya dawo sallar asuba ya samu tana bacci d’akinsa ya koreta dole ya k’yaleta su k’arasa kwanan tare.
Aiko koda ya dawo yasha mamakin ganin Feenah na bacci saman gadonsa, bai tasheta d’in ba ya kwanta daga can gefenta dan jiya bai wani samu bacci ba kusan kwana yai yana tinani tin bayan wayar da Assad yai masa yanda zai b’ullowa al’amarin Danger da Chief Jaja wanda idan yayi wasa zai iya rasa case d’in mutuwar k’anwarsa da ya d’aukarwa mahaifiyarsa alk’awarin kafin ta farka daga wannan jinya nata da izinin Allah sai ya gano waye ya kashe mata d’iyarta. Hakan yasa tuni bacci yai awon gaba dashi.
Safeenah tanajin alamun bacci yayi gaba dashi ta mirgino ta dawo jikinsa, zuciyarta fari k’al ta mak’ale cikin jikin mijinta tana shak’ar k’amshinsa dake rikitata.. Baccin ne itama yai gaba da ita.. Ba ita ta farka ba sai wajajen k’arfe bak’wai da rabi na safe sabida iska da aka soma sosai alamun za’ai ruwa hadari ya rufe sama gaba d’aya.. Ta saki murmushi tana duban yanda Mu’azzam ya rik’eta sosai cikin jikinsa alamun shi kansa yana enjoying baccin nasa. Ta k’ura ma kyakkyawan fuskarsa idanu tin daga sumarsa da suke kwance luf har zuwa idanunsa da suma suke a rufe, ta gangaro da idanunta tana duban hancinsa zuwa lips d’insa.
Iskan da akeyi shi ya bud’e k’ofar d’akin.. Ajidde da Ta biyo corridor d’in dan zuwanta kenan, nan tazo zata shige k’ofar d’akin Mu’azzam dan kafin ka isa d’akin mahaifiyarsa sai ka wuce wasu k’ofofi ciki harda d’akin Mu’azzam.. Da mamaki take hangan k’ofar a bud’e ta tina sanda ta shiga zata masa sata ya kusa kamata.. Ta soma sauri tana fad’i cikin zuciyarta bari tai sauri ta shige k’ofar d’akin kafin ta hango wannan jakar tasa.. Tana tafe bata fasa lek’en d’akin ba aiko nan ta hango matar nan ta jiya data watsa mata ruwan magani zaune gefensa saman gado tana shafa sumarsa zuwa fuskarsa.. Ajidde ta saki baki da hanci tana duban ikon Allah.. Ji tai bakinta na furta “Kaga ‘yaniska.. Toh asirinku ya tonu tinda kuka mance k’ofa a bud’e..” Bata ida shan mamaki ba saida taga matar nan ta kifa fuskarta kaman dai sumbatar juna suke.. Jikin Ajidde ya d’auki rawa babu shiri ta kwasa a guje ta nufo parlor..
Tana k’arasowa tsakiyar parlorn ta saki wani irin azabebben k’ara wanda idan akwai masu bacci da basu tashi ba ma tabbas sai Sun tashi.. Ihu Ajidde take tana tsalle tsakiyar parlorn tana fad’in ta shiga uku.. Inne dasu Hindu dake kitchen suna karin kummalo Inne na monitoring nasu kaman ko Yaushe, babu shiri suka nufo parlorn..
Mu’azzam cikin bacci shima yaji ihun har tsakar kansa.. Ya mik’e yaga Feenah tareda shi itama da alama ta firgita da ihun da ake.. Cikin sauri ya mik’e yana janyo jallabiyar sa yana fad’in “Mamy.. Mamy na.. Something happened to Mamy..” Abinda yake fad’i kenan yana k’ok’arin zira rigar dan itace maras lafiya a gidan dole kowa yai tunanin jikinta ne ya tashi koma aka rasata gaba d’aya. Ko tsaya bi takan Feenah dake tambayarsa Ina zaije bai ba ya matsarta gefe kad’an ya nufo yanda yake jiyo ihun cikin sauri.. Tuni Feenah ma ta take masa baya tana mai rufa siririn rigar baccin nata da na saman.
Musaddiq ma dake bacci a nasa d’akin babu shiri shima ya fito a birkice..
Aunty Shemau da tayo rakiya wa Uncle Salman zai wuce Factory dan wataran da wuri yake zuwa, nan Suma suka soma jiyo ihu daga sashen Inne. Babu shiri suka nufo sashen suma duk a birkice dan a tinanin Shemau Nuratu ce Allah ya mata cikawa.
Harta Meema dake ta faman susa ta kasa bacci dan dama tanada allergy irin na daminan nan balle tazo gidan Gona ga dabbobi ga shuke shuke tuni allergy d’inta ya tashi.. Ta d’an samu baccin kenan itama ta soma jiyo ihun.. Ta fito rai b’ace tana soshe soshe..
Gaba d’aya aka hallara parlor ana duban Ajidde dake ihu tana tsalle idanunta a rintse.
Musaddiq kam daga nesa yaja ya tsaya yana jiran yaji ruwan da Ajidde ta b’allo wannan karon.
SameenaAleeyou📚
[9/3, 8:35 AM] My mom: *GIDAN ARO*
*20*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ikon Allah, wannan ya dubi wannan wancan ya dubi wancan kowa na mamakin haukar yarinyar. Inne Ta k’arasa ta rik’eta tana fad’in “Ke Ajidde.. K’alau kike..? Lafiya kiketa zunduma ihu haka..? Ko wani abu ne ya faru..?”
Ajidde ta Ware idanu tana kallon mutanen da sukai cincirindo a parlorn Kowa ya zuba mata idanu. Ta kai dubanta ga Mu’azzam wanda yakai mak’ura wajen had’e rai kafin ta maidoda da dubanta ga Safeenah wacce ke tsaye tana aika mata mugun kallo ko ba’a ce ba kasan shak’e take da ita.
Inne ta dubi Mutanen da Ajidde ke duba Wato Safeenah da Mu’azzam, sai kuma ta maidoda dubanta ga Ajidden “Ajidde lafiya kike.. Wani abu ya faru ne..?” Ta tambaya tana mai tsareta da idanu.
Cikin sauri Ajidde ta jinjina kai alamun Eh.. Inne tace “Mai ya faru.. Ko wani abin ne ya sami Nuratu..?”
Ta girgiza kai a hankali tana duban Safeenah da har lokacin huci take tana aika mata mugun kallo ga Mu’azzam dake gefe shima yana aika mata razanannen kallo hannayensa hard’e ta baya.
Matsawa bayan Inne tai cikeda tsoro still idanunta naga Mu’azzam da Safeenah take fad’i a hankali “Inne Allah ne ya toni asirinsu..”
Inne ta kuma dubanta da mamaki “Asirin Su Wanene ya tonu..?”
Ajidde tai saurin shigewa bayan Inne tana lek’en Mu’azzam da Safeenah wanda kallon mutanen parlorn ya dawo kansu.
Mamaki ya mugun cika Mu’azzam ganin yanda yarinyar nan ta tara masa jama’a sunata kallansa babu gaira babu dalili.
Aunty Shemau baki sake take duban Ajidde Cikeda takaici tace “Da sukayi mai..?”
Ajidde Ta dubi Inne sai ta kuma dubansu, lokaci guda take girgiza kai..
A kufule Safeenah tayo kanta tana fad’in “Ke yarinyar nan na kula kanki rawa yake.. Tin zuwanta gidan nan kike shiga hurumina.. Cikinmu wanene sa’anki da zaki tara mana jama’a.. Zo nan ki fad’a Uban mai mukai..”
Inne Ta tare Ajidde tana fad’in koda wasa kar Safeenah ta tab’ata..
Lokaci guda Ajidde dake tsalle bayan Inne take fad’in “ Inne wllhi Allah ne ya toni asirinsu, ni ba lek’ensu nayi ba k’ofa suka mance bud’e shine na gansu suna abinda ‘yaniskan turawa suke a tv.. Wllhi Inne Shi naga sunayi bari ma kiga..” Ta juya Ta manna ma garu kiss tace “Wllhi Inne haka naga sunayi...”Tai maganar cikeda gadara irin ita ga mai gaskiya. Cikin zuciyarta kaw duban Mu’azzam take tana ayyana dama dik wannan famkam famkam d’in nasa na K’arya ne da bogi iskancinsa yake a b’oye.
Meema baki sake take dubansu ta kuma dubi Ajidde ga wani irin dariya dake taso mata Wai abinda ‘yaniskan Turawa keyi a tv.. Kai wann yarinya anyi shashasha Ta bugawa a jarida. Babu hali Meema tai dariya ganin yanda Mu’azzam ya gumun had’e rai yana aikawa yarinyar razanannen kallo.. Sad’af sad’af Meema ta shige tana kuma k’unshe bakinta da dariya keta k’ok’arin kufcewa.
Uncle Salman ya girgiza kai kafin ya dubi Mu’azzam dake tsaye kaman wanda aka dasa idanunsa sunyi jazir, ya maido da dubarsaga matarsa Shemau yace “Ni na