Showing 93001 words to 96000 words out of 209154 words
gaba da zama da ita matsayin mata ba.” Tana ida fad’in haka ta katse kiran tai saurin k’arasawa ta shige motar ‘yansandan.
Barr Ameer yai wata k’asaitacciyar murmushi yana furta “Now it’s your time to shine Ameer..! Good Job Officer Maleeka.. I knew it from the very start. You and I would make a perfect team, nasan zaki min amfani.. Good job Officer.”
Ya wani murmusa yana karkad’a k’afa guda kafin yaci gaba da fad’in “Yanzu za’a fara buga wasan tsakanin Lawyer da kuma Inspector.. I told you Safeenah, you are mine.. Ni Ameer ni ne mijinki nan gidan duniya.. Now it is time for me to play a perfect Attorney role..!” Yana ida fad’in haka ya bushe da muguwar dariya kafin ya mik’e yana sab’a suit d’insa.
**
Daddy na nan zaune waje aka soma bud’e gate, motar ‘yansanda da ya hango na danno kai cikin gidansa shi ya bala’in d’aga masa hankali. Badai Safeenah taje ta aiwatar da wani mugun abin ga matar Mu’azzam ba. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kurum Daddy ke iya nanatawa cikin zuciyarsa. Bai ida tinanin ba ya hango Motar Mu’azzam biyeda na ‘yansandan.
Daddy ya mik’e yana tambayar kansa meke faruwa.
‘Yansandan suna ida parking Mu’azzam ma yai parking a gefe. Saidai basuyi yunk’urin aiwatar da komai ba dan umarnin Mu’azzam d’in suke jira.
Mu’azzam yana fitowa daga mota ya hangi Daddy tsaye yana dubansa cikin rashin gane meke faruwa.
Take Mu’azzam yaji zuciyarsa ya masa wane irin rauni. Idanunsa suka soma k’ok’arin kawo ruwa. Ji yai k’afafunsa na barazanar gaza d’aukarsa.. Dik k’arfin hali irin nasa saida yaji zuciyarsa Ta gaza juran abinda ke faruwa. He looks shattered.
A hankali yake takowa yanda Daddy ke tsaye. Yana k’arasowa ya kifa kansa ba tareda ya iya ci gaba da duban Daddy ba. Shi kansa Daddy ya Sani ba k’aramin abu bane zai jefa Mu’azzam cikin irin yanayin da ya gansa ciki.
A hankali Daddy ya soma furta “Mu’azzam. Son, are you alright..? What’s the matter.. Talk to me Mu’azzam, meke faruwa..?!”
Daga nan yanda yake tsaye kansa na kife sai sautin fitar kukansa Daddy yaji jikinsa na vibrating kaman dai wanda aka jona masa electric shock.
Saurin kamosa Daddy yai cikin tsananin kad’uwa da tashin hankali “Mu’azzam.. Son.. Talk to me.. Mai ya faru Mu’azzam.. Dan Allah ka mun magana..!”
D’agowa Mu’azzam yai yana duban Daddy sai kuma ya rungumesa yana kuka sosai, kukan dake tare cikin k’irjinsa wanda bai iya fitarwa ba.
Jikin Daddy ya gama sanyi Mu’azzam d’in na rungume cikin k’irjinsa.
Abinda kawai Daddy ya kawo shine kodai Nuratu ce ta rasu.. Kar dai Sun kuma rasa ahali.
Daddy ya kasa jurewa, kafad’un Mu’azzam ya damk’e sosai ya shiga jijjigasa kad’an “Mu’azzam tell me.. Tell me it’s not your Mom.. Talk to me Mu’azzam.. Please talk now..!”
Mu’azzam ya d’ago gajiyayyun idanunsa yana duban Daddy, tausayinsu gaba d’aya ya rufesa. Cikin rawar murya yake furta “It’s Safeenah..! I’m sorry Daddy.!”
Ya sunkuyar da kansa ba tareda ya iya ci gaba da magana ba.
Cak Daddy ya tsaya ya daina jijjiga Mu’azzam d’in.. Ya dai San yanzu Safeenah ta bar gabansa ta shige gida.. Toh mai kuma ya faru.
Ya girgiza kai cikin rashin gane ina kalaman Mu’azzam suka dosa.
“What happened to Safeenah..? I mean tana cikin gida, right.?”
Mu’azzam ya d’ago ya dubi Daddy cikeda tausayawa “Unfortunately Daddy.. We.. We are here to arrest Safeenah. Bincikenmu ya gangaro zuwa kanta Daddy..!”
Dummm!! Haka k’irjin Daddy ya buga. Mu’azzam yai saurin kama Daddy ya zaunar dashi.
Daddy yaci gaba da girgiza kai yana fad’in “Tell me mai Ta aikatawa matarka.. Ta mata wani illan koh..?”
Girgiza kai Mu’azzam yai yana duk’e gaban Daddy. Hannayen Daddyn rik’e cikin nasa yake fad’in “Bata aikata mata ba.. Amma ta aikata ma Ikram Daddy.!”
“Ikram kuma..?!” Daddy ya tambaya cikin tsananin kad’uwa.
Mu’azzam ya jinjina kai a hankali.
“But.. But.. Mai kake nufi Mu’azzam.. Ikram ta rigayemu gidan gaskiya.. A ina Safeenah zata ganta.. What.. what is all this Mu’azzam.?!”
Mu’azzam ya kuma damk’e hannayen Daddy cikin nasa kafin yace “Safeenah is now our prime suspect game da case d’in mutuwar Ikram Daddy.!”
Wannan karon cire hannayensa Daddy yai daga cikin na Mu’azzam yana girgiza kai yake duban Mu’azzam d’in “No Mu’azzam.. You must have got this wrong.. Safeenah.. Safeenah would never do something terrible irin wannan.. Mu’azzam ka mun magana yanda zan fahimceka.. Ikram da Safeenah duka yarana ne.. Bazai yuwu hakan ta kasance ba.. Safeenah nada kurakurenta a rayuwa amma bazata tab’a zama makashiya ba.. Right Mu’azzam.. She’s your wife. You should know better, bazata iya kashe Ikram ba.. Mu’azzam wannan wasa ne ba gaskiya ba.!”
Mu’azzam ya shafi fuskarsa da duka tafukan hannayensa kafin ya girgiza kai yace “Daddy I wish ba gaskiya bane nima.. But... Gaskiyan kenan..!”
Daddy yaci gaba da girgiza kai hawaye mai zafi yana gangaro masa.. Daidai lokacin da Mu’azzam ya kifa kansa k’asa.
Muryar Daddy ya sinkayo yana fad’in “Ku shiga ku tafi da ita a binciketa..
Go Mu’azzam.. Go ahead.. Jeka kayi aikinka..!”
Mu’azzam ya d’ago yana duban Daddy.. Kafin ya kuma furta wani kalma Daddy yace “Bazan hanaka ka bincike Safeenah ba.. Sannan idan har an kamata da laifi nayi maka alk’awarin zata biya abinda Ta aikata.. Go ahead now.. Ku shiga ku tafi da ita.!” Yana ida fad’in haka ya kauda kansa gefe yana k’ok’arin maida k’wallan da suka taru idanunsa.
Lokaci guda Mu’azzam ya juya ya dubi su Assad yai masa alama da kai.
Jiki a matuk’ar sanyaye Assad ya jinjina kansa kafin ya dubi su Maleeka da d’aya ‘yar sanda macen mai sanye da uniform yace su shiga su fito da Safeenah.
Maleeka ta jinjina kai kafin ta dubi sergente d’in tace suje.
Tashin hankali wanda ba’a saka masa rana, yau Wai Safeenah aka Zo arresting ana tuhumar Ta da zargin kisa. Wane irin tashin hankula ne suka tsinci kawunansu ciki wanda za’a iya cewa yazo masu bagatatan babu zato balle tsammani. Aunty Shemau kam Ta kasa daina mamakin abubuwan tashin hankula dake kan faruwa tun bayan zuwanta. Babu wani abin arziki da faru tinda tazo.
Mommy masu shirin maka Mu’azzam a kotu sai gashi su ake shirin makawa.
Safeenah ta ci gaba da b’oyewa bayan Mommy tana fad’in “Mommy wllhi ba gaskiya bane.. Wllhi ban kashe Ta ba.. Mommy I can’t go to jail.. Na shiga uku.. Daddy please help me.. Na rantse da Allah bansan komai ba.. Wllhi Allah I’m innocent..!”
Maleeka tayo kanta tana fad’in “Idan munje Headquarters zaki k’arasa bayananki.”
Safeenah ta rapza mata crutch akai tana fad’in “K’arya kike k’aramar Karuwa kinyi kad’an kiyi arresting d’ina.. Bak’ar munafuka Kema kina cikin Karuwan nasa..”
Sergeant Teena ta k’araso tana fad’in “Madam you’ll be charged for attacking the police officer.. Ki shige muje..”
Mommy ta shiga tsakani ta tare d’iyarta tana fad’in “K’arya ne..! Wllhi babu ubanda ya isa yai arresting ‘yata.. My daughter is not a killer.. Ku fice mana a gida ko muyi suing naku for trace passing..!”
Maleeka ta mik’o mata takarda a linke tana fad’in “Hajiya, we have the warrant of your Daughter’s arrest.”
Mommy ta fuzge takardan ta yaga tai kaca kaca dashi tana fad’in sunci ubansu dasu da warrant d’in.
Daidai lokacin Mu’azzam ya shigo, idanunsa kan Safeenah dake b’oye bayan Mommy tana kuka.
Mommy taci gaba da k’are Safeenah tana fad’in “Mu’azzam ta nan ka b’ullo dan ka guje ma laifinka.. What kind of a monster are you.. You’re not taking my daughter.. Kai ko kunya bakaji ba ka tattaro ‘yansanda ka kawo mana gida.. Haven’t you thought of our family’s reputation.. Haven’t you thought of what people might say.. Zakayi arresting matarka kuma ‘yaruwarka kana tuhumarta da kisan k’anwarka.. So kake sunan ahalinmu ya lalace ko mai.. So kake mu tafi kotu muna shari’a ana nuna mu da yatsa.”
Da rinannun idanunsa yake duban Mommy wannan karon kafin ya girgiza kai yace “Mommy, Safeenah should’ve thought about that before committing the crime..! And yes kafin nace za’a tafi Kotu kin riga kowa cewa zamu tafi Kotu muyi shari’a. Idan ban mance ba yanzu kika gama fad’a mun a waya, ashe idan mun tafi Kotu da sunan ahalin nan ba komai bane wajenki. Abinda kike so ne.. Kuma ina mai tabbatarki zamu tafi Kotu, kuma za’ayi sharia..!” Yana ida fad’in haka ya kamo hannayensa Safeenah yana zira mata handcuffs. Lokaci guda yake furta “You have the right to remain silent. Everything you say can be used against you in the court of law. Kinada damar da zaki d’aukarma kanki lauya.. Idan kuma baki dashi the Authority will assign one for you.!” Ya ida maganar sanda ya gama rufe hannayenta.
Shaye da tsananin mamaki Safeenah ke dubansa. Bakinta na tsananin rawa take girgiza kai tana furta “I.. I didn’t do it.. Na rantse da Allah ban aikata ba Mu’azzam.. You need to believe me.. How can you arrest your wife..? Mu’azzam ni ce Safeenah.. Kaga abinda ka min.. Haba my Halal, Please don’t do this.. Wllhi I’m innocent. Maiyasa zan kashe Ikram..? What could be my motive.!”
“Ki ajiye bayananki har sai munje ofishinmu.!” Ya fad’i cikin kad’uwa kafin ya dubi Maleeka yace “Take her.!”
Wane irin k’ara Safeenah ta saki wanda saida ya firgita kowa dake cikin gidan. Su Kiki da dake d’aki basusan wainar da ake toyawa ba ihun Safeenah ne ya fiddo dasu gaba d’aya.
Tashin hankali bisa tashin hankali. A fujajan Mommy tabi bayansu Safeenah tana fad’in Mu’azzam bai isa yakai mata ‘ya ofishin ‘yansanda ba. Dik abinda ake bama tai zaton Daddy na gidan ba. Ta zaci ya fice.. Ta dubi Meema hanaki tashe tace “Call your Dad right now..!” Ta kuma duban Aunty Shemau da tuni ta d’auko mata mayafi tana rufa mata. “Muje Shemau..!” Ta fad’i suna ficewa cikin sauri.
Wani irin wawan birki Mommy tai ganin Wai da sanin Daddy Mu’azzam yazo d’aukan Safeenah. Kuka Mommy Ta fashe dashi sanda Safeenah ke sanar da Daddy cewa batada laifi cikin kuka.
Daddy ya girgiza kai yace “‘Yansanda zasuyi aikinsu.. And if you are proven guilty.. Ki mance kinada mahaifi Marwan Gamji. I do not have a daughter for a criminal.!” Yana ida fad’in haka ya juya cikin gida yana matsan k’walla.
Mommy Ta bisa da kallo baki sake. Lokaci guda ta isa tana janyo Daddy “She’s your daughter.. You should believe her.. Kasan Safeenah bazata tab’a aikata abinda ake zargin Ta ba.. Wllhi our daughter is not a killer.. She can be anything.. But not a murderer.. You can’t neglect your daughter.. She needs you now.. Kai tunanin sunan ahalinmu.. Wannan zai b’ata maka sunanka da sunan ahalinmu ne.. Mu’azzam ba d’an halak bane tinda har ya shigo da ‘yansanda cikin gidan nan akai arresting Safeenah.”
Sai lokacin Daddy ya juyo ya katseta da fad’in “Ina jin kin mance cewa kafin Mu’azzam ya tsaya akan case d’in nan ni ne mutum na farko da yai failing case d’in mutuwar Ikram ma ‘Yansanda.. Kin mance cewa ni ne nan nai k’udirin za’a bincike mutuwar nata dukda cewa ga sakamon da ya bayyana cewa mutumin da ya kasheta ya riga ya kashe kansa.”
Mommy cikin kuka Ta katsesa da fad’in “Amma ai duk mun amince mutumin da ya kashe Ikram ya kashe kansa.. Mu’azzam neman wanda zai d’aura ma Alhaki kawai yake..” Ta k’arashe cikin kuka.
Daddy ya jinjina kai yace “Ki k’yale ‘Yansanda suyi aikinsu Hajara.” Daga haka Sa kai yai ya shige.
Mommy ta soma kururuwa ta nufi mota tana fad’in driver yazo ya tuk’asu itada Aunty Shemau, dole subi bayan ‘yansandan idan Daddy bazaije ba.
Meema da Kiki kaw kuka suka dingayi suna ganin Bak’on al’amaren dake faruwa cikin ahalin nasu. Wai Ya Mu’azzam yai arresting Addah Feenah kuma wai da kisan Ikram ake tuhumarta. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.
Cikin sauri Meema ta shiga neman layin Musaddiq dan Ta sanar dashi abindake faruwa dashike baya gida.
**
Mu’azzam ya k’ura mata idanu sanda aka barsu su biyu a interrogation room saiko d’an mindow mai kaman glass wanda abokan aikinsa zasu iya hangosu daga nan.
Idanunsa jazir yake duban Safeenah sanda ya nuna mata lambar wayarta da time da date da komai da komai na lokacin da aka tura mata sak’on.
Safeenah taci gaba da girgiza kai tana furta “Na rantse da Allah bansan komai ba Mu’azzam..”
Tsawa ya daka mata yana mai buga table d’in da ya raba tsakaninsu “Don’t you dare lie to my face.! You received this text message a ranan d’aurin aurenmu.. Admit it Safeenah.!” Yai maganar idanunsa tar akanta wayar Sagir rik’e cikin hannunsa yana mata nuni da sak’on.
Safeenah taci gaba da girgiza kai tana hawaye ba tareda tace komai ba.
Mu’azzam yaci gaba da furta “You were not yourself that day Idan ban mance ba. You were acting very strange.. I even asked you meke damunki, but what did you say..? Ce min kikai nervousness ne na barin gida sabida zakiyi aure.. Washe garin wannan ranan aka tsinci gawar Ikram... Haka ne..?!”
Ta kuma girgiza kai tana hawaye “Na rantse da Allah ban San komai ba..”
Wani Farin takarda Mu’azzam ya ajiye gabanta nan saman table d’in wannan karon cikin rawar murya yake magana “This is the autopsy result of Ikram’s death Safeenah..!” Muryarsa yaci gaba da rawa yana furta “Take a look Safeenah.. Ki duba autopsy result d’in.. Binciken da likita ta gudanar akan gawan Ikram.. She was raped Safeenah..!” Izuwa lokacin hawaye ne ke gangaro masa haka ma Safeenar wacce take girgiza kai tana duban takardan.
Mu’azzam yaci gaba da furta “My sister was raped and then shot.. An mata fyad’e sannan aka harbeta da bindiga.. An kasheta a wulak’ance. Wulak’ancin da ko dabba baza’a masa ba.. Idan kinada zuciya cikin k’irjinki Safeenah zaki sanar dani gaskiyan al’amarin.. Zaki sanar dani gaskiyar da kika sani..!” Ya k’arashe gumi na gangarowa daga cikin sumarsa zuwa goshinsa.
Safeenah taci gaba da girgiza kai tana hawaye “Wllhi ni bansan komai ba Mu’azzam.. Ka yarda dani.!”
Buga table d’in ya kuma da k’arfin gaske wanda saida ya storata Safeenah “Isn’t it enough that you’ve been fooling me for almost a month now.. You insulted my intelligence and my profession as a police officer.. Safeenah let’s not make this difficult anymore.. Ki sanar dani mai kika sani..”
Safeenah ta d’ago tana dubansa cikin huci wannan karon “Banfa mance abinda ka min ba Mu’azzam.. Dan Mommy tace zata maka ka a Kotu shine bari ka b’ullo ta nan.. Bazaka tsere ma laifinka ba.. Ka cuceni ka kai min mace cikin gidana.. Kana kwanciya da ita a saman gado na kai ko kunya bakaji ba.. Tell me mata nawa ka kai min gida ka kwanta dasu saman gadona.”
“Feenahh..!!” Ya daka mata tsawa yana mai d’ago hannunsa kaman zai mareta. Sai kuma ya sauk’e hannun nasa a hankali..
Safeenah taci gaba da kuka tana fad’in “Kai mugu ne Mu’azzam.. Azzalumi ne kai.. Ka cuceni Ka cuceni.!” Tai maganar tana k’ok’arin turasa tana kuka sosai tana bige bige.
Mu’azzam ya shiga k’ok’arin kame hannayenta dole Maleeka ta shigo tana taimaka masa da rik’e Safeenah dake Ta faman buge buge kaman sabuwar kamun hauka.
Ficewa yai daga interrogation d’in to get some fresh air, saida Safeenah ta daina bige bigen da take kafin ya dawo cikin tsananin tsimewa. Tai zaune saman kujeran tana sakin huci.
“Shall we continue.”ya fad’i yana dubanta.
Kauda Kai gefe tai kafin tace “Ina son magana da lawyer na. Ko shima banida dama.?”
Yai mata K’uri yana dubanta “Daddy yace lauyansa bazai tsaya miki ba. Kinada wanda kike so a kira miki in mind.”
Ta d’ago da mamaki tana dubansa jin abinda ya fad’i. Kafin Safeenah takai ga magana sukaji an turo k’ofa an shigo.
“I need to speak to my client. Mr Inspector.” Abinda ya fad’i kenan daga nan yanda yake tsaye cikin bak’ar suit d’insa.
Daga Safeenah har Mu’azzam juyawa sukai suna duban Ameer dake tsaye kansu.
Mu’azzam ya mik’e shaye da mamaki yana duban Brr Ameer dan tsaf ya ganesa tsohon saurayin Safeenah ne.
SameenaAleeyou📚
[9/3, 8:35 AM] My mom: *GIDAN ARO*
*32*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Mu’azzam ya girgiza kai yana duban Barr Ameer disbelievingly kafin ya kuma duban Safeenah wacce itama Ameer d’in take duba.
Lokaci guda Ameer ke takowa gaban Mu’azzam d’in muguwar murmushi saman fuskarsa. Ba tareda wani b’ata lokaci ba ya mik’awa Mu’azzam dake tsaye gaban yana dubansa hannu alamun musabaha “Inspector, long time no see.” Ameer ya fad’i still murmushin saman fuskarsa yana mai mik’a right hand d’insa ga Mu’azzam d’in.
Ganin Mu’azzam bai mik’o masa hannun ba ya sanyasa sakin wata k’asaitacciyar murmushin kafin yace “Nasan ka sanni by name so need na maimaita abinda ka riga ka sani. After all, your wife and I used to be very good friends.”
Izuwa lokacin zuciyar Mu’azzam takai k’ololuwa wajen b’acin, hannayensa kaw sai faman dunk’ulesu yake jijiyon jikinsa na kuma fitowa sosai.
Ameer ya kuma gyaran murya yana d’an gyara tsayuwarsa kafin yace “Aff ashe fa na mance ban maka murnan aure ba, everything happens so fast.. I couldn’t get the chance to congratulate you.. But wait.. Shin ka cancanci nai maka murna..? Wanne irin miji ne zai arresting matarsa..? What kind of a husband does that to his wife .? Aren’t you ashamed of yourself Inspector.? Kana tuhumar matarka da kisan k’anwarka..” Ya d’anyi fasali yana mai girgiza kai kafin yace “Don’t you have anything to say to me, Mr Inspector..?” Ya d’an tab’e baki kad’an kafin yace “Koda shike ba Kai bane abokin karawan nawa wannan karon. I rather speak with your Lawyer in court.. Sai muga waye kuma zai sha k’asa yanzu.!” Baikai aya ba yaji sauk’an naushi a hancinsa wanda saida ya kaisa k’asa.
Safeenah ta mik’e da sauri tana k’ok’arin tare Mu’azzam yayinda Maleeka da Assad dake dubansu ta cikin glass sukai saurin shigowa.
Assad ya k’arasa ya rik’e Mu’azzam d’in yayinda Maleeka ta duk’a tana tambayan Barr Ameer if he’s okay.
Barr ya mik’e yana kame bakinsa da Mu’azzam ya basa naushi wajen.. Yana fad’ida Maleeka “I’m alright.. Kar ki damu Officer.”
Assad yaci gaba da k’ok’arin janye Mu’azzam yana fad’in “That’s enough Mu’azzam..”
“You Stay out of this Assad.. Let me teach this moron some manners.” Yana maganar yana fincika Assad na kuma rik’esa.
Ameer yai wata k’asaitacciyar murmushi kafin yace “Can I speak to my client now..?” Yai maganar yana duban Mu’azzam dake aika masa razannan kallo. Ya kuma murmusawa kafin yace “In private.”
Mu’azzam ya kuma yowa kansa Assad yai saurin janyesa ya fice dashi.
Suna ficewa Mu’azzam ya finciki hannunsa daga rik’onda Assad yai masa yana mai shafe fuskarsa da tafukan hannayensa.
Assad ya jinjina