Showing 78001 words to 81000 words out of 136570 words
zanyi bari muje mu dawo juyawa sukayi atare sunkai qofa zasu fita kenan dr.shettima yace qanwata ba sallama muna hirar mu me dadi qwaro yazo ya katse mana indan kundawo sai inbaki magani jan idon ya washe da wuri sannu fa kinji gsky wannan kwaron be kyautaba da yataba mana lafiyar qanwarmu, duk wannan surutun da yakeyi bata kulasaba tasakai tayi ficewar ta zuciyar taf da takaici, saleem sai faman murmushi yake ta faman saki baki yaqi rufuwa ganin yanda ya nuna kulawar sa akan qanwar sa yaji dadi sosai dan haka godiya yaqara yi masa sannan ya fita yana fita dr. Shettima ya zube akan kujerar office din tare da kwanciya akan ta yana faman lumshe ido yakeyi sai kuma abun da yafaru ya shiga dawo masa tundaga farko har zuwa qarshe sai kuma ya saki murmushi acikin zuciyar shi yake cewa ashe de macen ce daga gwaji ina neman wuce gona da iri da bankai zuciyata nesa ba da tuni nayi abun kunya sai kuma ya fashe da dariya a fili ba koami yasashi dariya ba sai lokacin da yakawo bakinsa daidai nata yana so yayi kissing dinta sai kuma yafasa sai yanzu yake tunanin dama yayi yaji me ake ji danshi yaune karon sa na farko da yafara yiwa mace haka arayuwar sa inba a rashin sani bama sai ya rantse shi be taba maceba ko hannu ma be taba ruqewa ba da niyar jin dadi ko wata manufar daban to shi inba kannen sa bama yaushe ma mace taga fuskar da zata tunkare shi da nufin ta tabashi ko kuma shi ya tunkareta dan shi tawani bangaren ma tsoron mata ne dashi baya kulasu saboda besan me zece musu ba shiyasa yake rayuwar sa shikadai baya soyayya duk da inyana gani a film ko in wasu sunayi abun yana burgeshi to sai gashi yau wai shine harda shafa bayan mace da rungumeta har yana qoqarin yin kissing dinta lalle yau yabawa kanshi da kanshi mamaki yau yakafa tarihin da baze taba mantawa dashi ba arayuwar sa,
wani murmushin yaqara saki sannan ya mike yafito dan ji yayi zaman office din duk ya isheshi bayan su yabi saboda hakannan kuma yarinyar da akace ankwantar ta ringa fado mishi arai so yake yaganta yanaso ya tabbatar wa kansa yarinyar dayake tunani ce ko ba ita bace hakan yasashi nufar inda yake da tabbacin annan aka kwantar da ita yana shan kwana yaganta amma ta juya mishi baya tana ta kiciniyar mayar da bra din da yacire mata amma takasa harda hawaye so take tayi sauri ta mayar kafin saleem yadawo amma taqiyi saifama take tayi gashi idan tace zata barta ahaka bazataji dadi ba gashi ita bata iya zama ba bra ba bare ta cireta to idan ma ta cire a ina zata ajiye tunda bata dauko jaka ba dan haka baze yiyu taita yawo da ita a hannun ta ba tana cikin kiciniyar taji anjata tabaya zatayi ta tsorata sosai dan haka ta bude baki zata kurma ihu taji an rufe mata baki,
yana shiga da ita ya rufe qofar juyo wa tayi zatayi magana ya dora mata yatsansa akan lips dinta tare da cewa shhhhh kar kiyimin wata maganar banza anan idan bahaka ba kuma zanmiki abun da bazaki taba mantawa ba taimaka miki kawai zanyi in badan halinki ba darajar yayanki zaki ci yana gama fadar haka bejira me zatace ba yajawota yasata a faffadan kirjinshi sannan da hannu daya ya riqeta dayan kuma yayi qasa dashi yana qoqarin daga mata hijab din jikin ta da sauri ta kai hannu ita tare da riqi nashi hannun cikin kuka tace wai dan Allah me na tsare makane daga haduwa kabi ka takurawa rayuwata banaso banaso banaso kasake ni nace ta qarasa fada cikin daga murya tare da fashewa da wani irin kuka me tsuma zuciya dan zuwa yanzu kuma ta karaya tafara tsorata dashi ta ajiye makaman sosai takeyin kuka shiru yayi yana sauraron ta sai kuma yaji ta dan bashi tausayi ahankali yakai bakinshi saitin kunnen ta yace is ok naden ba abun da zanmiki mayar miki zanyi da ita tunda ni nacire ta dole inmayar kai ta girgiza mishi alamar a'a bata so be bi takanta ba ya kwace hannunsa daga ruqon datayi mishi sannan ya qarasa daga hijab din sai da ya kawoshi daidai saitin wuyanta sannan ya tattareshi guri daya yanda ze samu damar ganin bra din qara hadata yayi da jikinsa sannan ya dora kansa akan kafadar ta yana ganin farar fatar bayanta sannan yakai hannu ya kamo ma ballan bra din yafara qoqarin saka mata har zesaka awaje na farko said kuma wani tunani yafado masa ko ba anan take sawa ba dan haka sai yace aguri na farko ko na tsakiya ko na qarshe banza tayi mishi bata bashi amsaba hakan yasashi dakata wa yace ok ba kyaso agama da wuri kenan to ai sai mitazama ahaka daman na fahimci hakan kikeso, dasuri ta dago kai tana qoqrin barin jikinshi amma sa yasa hannu ya mayar da ita yace Allah in baki fada ba ahaka zamu zauna aikin banza mutum yanaso yana kaiwa kasuwa yafadi hakan saboda yanaso yaga ta qara hawa ranta ya baci sannan yace ke nake jira fa,
Itade taga takanta yau ta hadu da gamonta babu yanda ta iya dole tayi yanda yace inbaso take yi suci gana da zaman ba kamar yanda yafada din da haka ahankali ta bude baki tace ana qarshe sarai yaji mai tace amma sai kawai yace me kikace nifa banji ba ki daga murya kina wani maqe murya sai kace kina tare da saurayin ki,
Shiru yayi yana jiran jin me zatace bata kulashiba illa kwai maimaita masa din kamar yanda yakeso dan tasan yajita kawai de wulakancine irin nasa dan murmushi yasaki sannan ya maida hannun sa kan bayan nata tare da mayar mata da bireziya din sannan ya zuge mata zip din rigar ya mayar mata da hijab dinta yanda yagansa sannan yasake ta suna qoqarin fitowa kenan suka jiyo muryar saleem da dr.jamil saleem nace mishi wlh anan na barta bansa ina tayiba gashi batasan ko ina ba yau tafara shigowa kartaje ta shiga wani wajen yaqarasa fada cike da damuwa kamar ance mishi ta bata,
jin hakan da Azeema tayi hankalinta ba qaramin tashi yayi ba gabanta sai dukan uku uku yakeyi yanzu idan suka gansu tare a daki daya me zasuce tashiga uku yau yazatayi wlh bazata taba yafewa wannan mutumin ba duk shi yajefata ahalin da take ciki tunda tazo yake bata mata rai,
"juyawa tayi tana kallonsa taga shi ko ajikin sa ganin tana kallonsane yasa shi dage mata gira daya tare da cewa yade ni ba ruwana idan suka ganmu zance kece kikace dan Allah inzo in gyara miki rigar nonon ki ta tsinke waro ido tayi kamar zasu fado qasa jin batun da yakeyi ko kunya na bayaji zeyi mata sharri hannu yasa da niyar bude qofar tayi saurin shan gabansa tace wai meye hakan dan Allah kai inbakajin tsoro to ni inajin tsoron yayana gashi kuma zakaje kamin sharri ko kunya bakajiba yace kunya kuma akan me zanji kunya daga fadar gaskiya ko nayi qaryane a maganata bayanzu nasaka miki ba zakice zan miki sharri zatayi magana kenan ta qara jiyo muryar saleem yana kwala mata kira dr.shettima ne ya bude baki da qarfi zeyi magana yace gatanan ganin hakan yasata tayi saurin saka hannun ta akan lips dinshi ta rufe mishi baki dan tasan kadan daga halinsa yayi abun da yayi niya dan haka tayi saurin rufe mishi baki tsayawa yayi yana kallonta tare da bin hannun ta dake kan bakinshi da kallo............✍
[21/12, 8:30 pm] #yaya Azeema#: 💅SARKI SAMEER....💅
By
Yaya Azeema 😎
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
Bismillah......
49&50
""""""""""""""""""""""""""""""""""
"Ahankali yadaga hannunsa ya dora akan nata amma kuma be janye shi daga kan bakin shiba da ta dora ganin hakan yasata qoqarin janye hannun ta amma sai yariqe kam tare da manna mata kiss akai da sauri ta fusge hannuta tana hararar sa wai kai dan Allah me ka medani me ka daukeni to wlh inka qara tabani ka taba wutar jahannama kuma Allah ya isa na taqara sa fada tana doka mishi harara shi abun natama dariya yabata dan haka ya dan dara sannan yace au hakama kikace to na yarda bari inqara tabawa yafada yana tunkarota da sauri tayi baya tana girgiza mishi kai da qyar ta iya bude bakinta tace dan Allah kayi hakuri wlh bazan qara fada ba yace kima qara aini imnai niyar abu sai na aikata bani kikeyiwa Allah ya isaba kuma idan na tabaki na tanba wuta ko to bari intaba wutar inji da zafi ko babu zata iya qona ni,
cike da takaicin maganar sa tace ai ba ajikina zakaji zafin ba sai ka mutu Allah ze babbaka ka awutar jahannma kalidina fiha abada baza kavtaba fiyowa ba tunda burinka ka ringa taba matan da ba muharraman ka to wlh kaji tsoron Allah kadena halin da kakeyi tunkafin lokaci ya qure maka ka mutu a loda maka qasa tifa guda ko ma biyu sannan kasha azabar qabari daga nan kuma ranar tashin alqiyama ka shiga wuta kuma wlh.....
Bata qarasa ba taji dal abakinta saurin sa hannu tayi ta dafe domi ba qaramin zafi taji ba saboda har saida kwalla ta tafito daga idon ta,
Kallonta ya shiga yi tundaga qasa har sama sannan yace ni kike cewa dan wuta ko to ai kema kinzama yar wutar tunda kema yanzu kika tabani kinga tare za asakamu awutar ko,
tace ai ni iya bakinka nataba kuma ina da dalilin shiyasa yace ohhh daman baki ba ajinkin mutum yake ba kenan zakizo kinawa mutane maganar banza yen yen yen to saide ke kishiga amma baniba yaqara sa fada shima yana galla mata harara shiru tayi bata qara tanka mishiba dan tagaji da shi wlh so take kawai ta fita barinshi tayi awajen sannan ta nufi qofar dan budewa tayi ahankali ta leqa dan taga su saleem sun tafi ko suna nan, aikwa tana lekawa tagano shi amma yajuya mata baya da sauri ta mayar da qofar ta rufeta ahankali tana juyawa tayi karo da mutum dagowa tayi tana kallon shi shima ita yake kallo sai kuma ta hade rai tare da cewa malam lafiya tafada tana bin ta gefenshi zata wuce har tayi gaba sai tajishi yana qoqarin bude qofara asukwane ta qarasa gurinsa tare da shiga gabansa tace me kake qoqarin yi har yanzu fa suna wajen dan Allah kar kafita kasama mana mafita yanda baza aganmu ba tunda tafara magana ya zuba mata manyan idanun shi yana kallon ta saida yaji tayi shiru sannan yace ya kikeso ayi nibanda wata mafita da ya wuce infita dan bazan tazama anan gurinba saboda ke ina da aikin yi marairai cewa tayi sannan tace dan Allah ka tsaya mune mi mafita wlh ina tsoron yaya saleem kuma sai yaje yagayawa mama taqarasa fada tamkar zata fashe da kuka tausayin tane yadan kamashi dan haka sai yadakata daga qoqrin bude qofar da yakeyi sannan yace to naji kinsan me za ayi yanzu ni zan fita ke kuma ki buya idan na fita zanja hankalin su gabadaya mu koma wani bangaren ke kuma sai kifito sannan kitana di qaryar da zakiyi ki kare kanki idan an tambayeki kingane ko kai ta jinjina mishi sannan tace to a ina zan buya yace can gurin ya nuna mata qarshen wata kusurwa idan kinga na dade da fita sai ki leko idan kinga ba kowa sai kifito kawai da to ta amsa masa sannan ta juya ta nufi inda yace mata din batace mishi komai ba shima be qara kulata ba ya bude qofar ya fita yana fita yaga ba kowa agurin ajiyar zuciya ya sauke tare da hamdalah saida yakalli ko ina ya tabbatar da ba kowa sannan tasake bude qofar ya dan daga murya tare da cewa kiyi sauri kifito ba kowa yana gama fada nata yayi saurin barin wajen ya nufi wata hanyar da ya tabbatar da baza su hadu da suba,
"cikin tafiya sauri sauri gudu gudu har yaqarasa gaban office dinshi yana qoqarin budewa yaji ance sir cak ya tsaya tare da juyowa saleem ne yaqaraso gurinsa da sauri yana cewa sir tundazu nake zuwa wajenka bana samunka dan Allah ko ka ga qanwar nan tawa danazo da ita wlh tundazu nake nemanta duk inda nasan zata iya shiga naduba amma banganta ba
Wata boyayyiyar ajiyar zuciya yasauke sannan yace ayya gsky bangan taba tunda kuka fita dinnan banqara ganinta amma gsky abun da mamaki kuma kunduba ko ina har dakuna kunduba saleem yace bamu duba ba gsky amma bari yanzu inje induba yafada yana qoqarin barin wajen sai yayi saurin dakatar dashi tare da cewa muje in taya ka amma inaji ajikina ba abun da yasame ta kuma tana cikin girin nan ba inda taje...
Saleem yace to Allah yasa
tare suka jero suna qara duddu bawa dr.shettima ne yace saleem yanda zamufi sauri kai kabi tana nan hanyar ka duba na bangaren ni kuma bari in duba nan saleem kwa yaji dadin hakan da yace mishi koba komai yasan ya taimaka mishi dan haka godiya yayi masa sannan ya wuce dr.shettima saida yadan dara ganin harda yi masa godiya sannan ya nufi inda take kai tsaye yana zuwa yaga bata wajen sai kuma yafara tunani to ina ta shiga dan dube dube yara yi sannan sai ya hangota can nesa da gurin ta zauna aka kujera tare da yin tagumi tana jiran taga ta ina saleem ze bullo,qarasawa yayi wajen ta sannan yazauna akusa da ita dan neman magana kawai sai yadora kansa kan kafadar ta da sauri ta miqe dan ita tsoro ma yabata bataga zuwan shiba bare zaman shi kawai sai jin ankwanta mata akafada da tayi ,
dafe kanta tayi tare dacewa nikam yau naga takaina me kuma yadawo da kai wai baza ka rabu da rayuwata bane shima miqewa yayi yana kallon ta sai kuma ya hade rai kamar be taba dariya ba abun har mamaki yabata dan har ta fara tunanin kode aljanune dashi muryar shice ta katseta da cewa ke dalla can rufewa mutane baki dan kinsamu ma ina kulaki shine zakina wani yimin duk maganar da tazo bakinki,kasake tayi kamar sokuwa tana kallon sa dan magan ganunsa ba qaramin bata mamaki yayi ba tama kasa magana, da
Dorawa yayi da cewa yanzu zankaiki gurin yayanki zance nasamoki a wani daki kina bacci dan haka sai ki canza mood dinki zuwa kamar wadda ta tashi daga bacci sannan kibiyo ni dan ba jiran shirmenki zan tsaya jiba yana kaiwa nan yayi gaba abunsa bushewa tayi awajen tabi bayansa da kallo takasa koda kiftawa har saida ya bacewa ganinta sannan ta dawo hayyacinta da gudu ta kwasa tabi bayanta saboda bata da mafita da ya wuce tayi yanda yace tayi sa'a kuwa tana beyi nisa ba dan har ta cimmasa yana tafiya tana binshi abaya har suka kai office dinshi budewa yayi yashiga itama ta shiga yana shiga ya dauki waya yakira saleem yana dagawa yace mishi gata kazo office dina yana gama fada ya kashe wayar tare da dauko wani file dake gabansa yafara dubawa ko kallon inda take beqara yiba kamar ma besan da ita a office din ba tayi mamakin wannan canjin da yayi lokaci daya bayan yagama tattabeta zezo yana wani ciccin magani saikace tayi mishi laifi bata san lokacin da tsaki ya subuce mata ba dagowa yayi yana kallon ta karaf suka hada ido da sauri ta rufe bakin ta tare da cewa ni ba da kai nake ba tafada tana turo baki har zeyi magana sai saleem ya turo qofar tare da sallama hakanne yasa shi yin shiru sai ya amsa sallamar sa sannan yace gata nan acan nasamo ta tana bacci
"Saleem yace haba auta kinga yanda kika daga min hankali kuwa daga cewa kijirani sai kitafi wani wajen ki kama bacci yafada yana kallon ta fuskar sa ba walwala dan har ga Allah yaji haushi yana nan yana ta faman nemanta amma ita tana can ta sharar bacci hankalin ta kwance,
ahankali tace dan Allah yaya kayi hakuri wlh bansan baccin ze dauke ni gajiya nayi da tsayiwa kuma wajen ba kowa shiyasa kawai na shiga dakin kusa da wajen dan injiraka aciki sai kuma bacci ya daukeni sorry pls shiru yayi mata sannan yacewa dr..shettima
Sir nagode sosai Allah yabar zumunci bari kawai inje in dorata a napep ta tafi gida kar inje kuma ta qara jamin wata wahalar dr.shettima yace a'a karabu da ita kawai yau daya de naga ai ko gurin qawar tata ma bata shiga ba kuma zece ta koma gida hakan ai be dace ba kabarta yanzu muje dukan mu nima inaso inga marar lafiyar yafada tare da miqewa,
Saleem beyi masa musuba yace to sannan itama ta miqe suka fito a tare saida suka fara zuwa wajen dr jamil suka taho tare dashi sannan sukaje wajen Ameesha suka duba ta sannan suka fito Azeema sai faman matsar kwalla takeyi da ta tausayawa bestyn tata addu'a tayi mata Allah yabata lafiya office din shi sika qara komawa dukan su bayan shigarsu ne saleem yace sir bari inje kan aikina anajirana ke kuma saura ki qara yin wani wajen kiga yanda zanyi dake anan yana gama fadar haka ya fice daga ciki dan har yanzu haushinta yake ji,haka ta qari zaman ta shiru ba magana dan har yanzu be kulata ba ko kallonta ma beyi ba har aka kira sallah ya miqe yana niyar fita yace kishiga ciki akwai toilet aciki zamuje masallaci yana gama fada be jira amsar taba ya fice ajiyar zuciya ta sauke da daman duk atakure take dashi zaman da sukayi waje daya sai