Showing 60001 words to 63000 words out of 136570 words
red sai yazamana yayi red and black key din motar shi yadauko sannan yafito falon inda yabarsu anan ya tadda su,
Ƙarasawa yayi kusa da Ammi yace "Ammi na yane yakika ganni nayi ko banyi yafada tare da daga mata gira daya,
Baki asake Ammi tace "To nashigangadina yaran wai me kuka maida ni,ni kakar kuce da kuka rainani haka rungumeta yayi tare da manna mata kiss a chest dinta sannan yace Ammi tamu mukwa na Allah natafi kimin addu'a sai nadawo yafada yana nufar qofar fita daga falon,
Ammi dan girgiza kai tayi tare da cewa Allah yanunan ranar da zakai hankali kaine babba amma in kana abu kamar qaramin yaro.... dawowa yayi da baya yafasa fitar da yake qoqarin yi kusa da ita ya sake dawowa yace Ammi inde wannan abun da nake miki shine yarinta to har abada bazanyi hankali ba bari ma kigani yana gama fadar hakan yazauna akan cinyarta tare da qara rungume ta yana mata kiss ta ko ina yamata yafi guda goma ita ko mutuwar zaune tayi lalle yaron nan da gasken bashida hankali hannu ta daga ta daddage ta buga mishi dundu abaya ai bashiri ya miqe daga kanta yace Ammi da zafi fa tace uwar zafin kawai wani qaton gardi da kai gotai gotai dakai zaka wani zauna min akan cinya salon ka karyani abanza kabar ni da jinya Aysha ce da su yasmin da furaira da suke gurin suna kallon abun da yayan nasau yakeyi daman yasaba sai yazo yay tayin irin wadannan abubuwan amma su basu isa sunyi ba sai yace ze hukunta ka waishi babba ko kunya bayaji faruq da mimi basa falon da abun sai yafi haka jin suna dariya sai yawani hade rai tare da juywa yana kallon su kollon irin ku shiga hankalinku...
aikwa haɗiye dariyar su sukayi sunayi aciki Ammi ce tace sai sunyi din da wayace kayi abun da kayi ba dole suyi dariya ba zaka wani hade rai kana kallonsu,
Ammi "naga alama so kike su rainani ko kina goyan bayansu, ai kam tace duk ma abun da akayimaka ai kai kajawa kanka tunda baka iya jan girman kaba agabansu zakai duk abun da kaga dama kaga kwa suma dole suyi maka abun da suka ga dama girgiza kai yayi yace wlh kwa da na karkarya mutum tace karka kuskurama kafara tabamin ya'ya wlh yanda nake hakuri dakai ban karya kaba dole ne kaima kayi hakuri,
Jijjiga kai yayi bece mata komai ba yasa kai ze fita daga falon ya kusa fita kenan Ammi tace Aliyu dawo kutafi tare da furaira yanajin ta amma ko waiwayowa beyiba tace ba magana nake makaba amma ina lokacin da take wannan maganar har yabar gurin itama daman tsokanar sa take tasan baze dawo ba a fili kuma sai tace zaka dawo kasameni agabanta zan hukuntaka,
yasmin ce tace Ammi wai dan Allah wace za'adauko baki gaya mana ba fa Aysha ma ta dora dacewa nima tambayar da nake so inyi kenan naji sai magana akeyi anbarmu a duhu furairah de bata ce musu komai ba saboda wataran bata iya sakewa idan Ammi nagurin tana danjin kunyarta amatsayin ta na surukarta.
Ammi tace intazo idonku yagane muku sukace to Allah yakawo ta lafiya, Ammi tace "ameen"
yana fitowa tunkan yaqarasa gurin motar yasa linzamin dake hannu sa yabude motar yana zuwa yafigi morfin motar tare da afkawa ciki yana shiga bayan ya zauna yaja murfin yarufe tare da tayar da ita, yayi rivers tunkan yaqarasa yake dokawa gate man horn dasauri me gadi ya tashi tare da wangale masa wawakeken gate din yaturashi yatafi luuuuu yana gama budewa yazo yawuce aguje dan jinshi yake yi kamar yatashi sama yagansa acikin gidan su haka yake ji saikace bashine yagama yiwa wani maganar gudu ba dazu amma shi yanzu yakeyi yana hawa kan titi yaqara sa giya yana tafiya yana over taken duk wanda yaga baya gudu kuma yatsaya masa agaba ze buga masa horn me qara koma yadanne gurin horn din ahaka de yaringa tafiya cikin ganganci Allah ne de kawai yakiyaye shi har ya qaraso unguwar su tagaban gidan su Rasheeda yazo ze wuce sai kuma yadan dakata yace bari sugaisa daman sunkon biyu ko waya ma yanzu basu fiyayi ba saboda daman itace me kiranshi idan kuma takira sau daya ko sau biyu be daga ba sai tayi zuciya tadena kiranshi sai kuma ta wuce dan kanta sai taqara kiranshi,
Zaro wayarsa yayi ya lalubo number ta dayayi saving da baby😍 yana kira kwa two ring kawai wayar tayi aka daga ana daga wa yace kifito ina qofar gidan ku be jira amsar taba ya katse wayar tare da ajiye ta kan kujera shikuma ya dan kwantar da kansa ajikin kujerar yana jiran fitowar yanayi yana duba agogon hannun sa dan yana tunanin idan yayi five minutes bata fito ba tafiyar sa kawai zeyi haka ya ta zama har fave minutes din tacika yaqara qara bata wata five minutes din amma still de bata fito ba dan haka kawai yatayar da motarsa yaqara gaba yana tafiya kuma sai gata ta fito fitowar ta ke da wuya taga qofar gidan nasu wayam babu kowa burki taja ta tsaya agu guda tana tunanin kode qarya yake daman bezo ba wayar ta ta dago ta danna masa kira yana dagawa tace gani nazo banganka ba ko baka qaraso bane at the other side yace mata I'm so tired for waiting tace like how just ten minutes fa nadauka banfito ba ina kallon agogo yace oh really so now go back to home danni har na riga da nayi nisa daman wani gurin zani nabiyo kekuma kika bata min lokaci shiyasa kawai natafi nadawo gobe kitanadar min abun dadi kinji baby na tsabar ta kaici dajin haushin maganganun sa takasa magana,
Sai yasake cewa baby naji kinyi shiru what happened to you dear? Uhm uhm kawai tace mishi sannan ta kashe wayar tasan halinshi yanzu ya qunsama bakin ciki sannan daga baya yazo yana maka dadin baki,
Juyawa tayi da niyar shiga gida amma sai ta tsaya cak tana qarewa motar kallo tabbas wannan motar bossay ce kuma aqofar gidan su yarinyar da tafi tsana kaf duniya sai kuma tasaki wani irin killer smile duk alokaci daya sannan ta karkada kai tare da cewa to muzuba mugani in mai zai dafa shinkafa tana gama fadar haka ta shige gida ranta fari tass tama manta bacin ran da take ciki (tofa Rasheeda me kike shirya mana irin wannan murmushi haka daga gani bana gaskiya bane tode muga alkhairi)
Bossay dake cikin mota yana tafaman yi mata dariya yasan tunda yaji ta kashe wayar yasan ta shaqa ba qarya shima rama rashin mutuncin da tayi mishi yayi ko uban me ta tsaya yi har tafi minti goma mtsww yaja tsaki tare da bude motar ya fito yana shiga daga bakin qofa ya tsaya yayi sallama amma shiru ba amsa yaqara wata nanma ba amsa kai tsaye ya shiga cikin gidan yana qara wata sallamar amma da alama kuma kamar suna ciki tunda de ga takalmansu aqofar dakin,
Ameesha ya shiga kwalawa kira nan beji ta amsa ba qarasawa yayi har bakin qofar dakin nasu yanzu ma be shiga ba saida yaqara wata sallamar jin shirun yasa shi daga labulen ya shiga cikin dakin gaban shine yayi wata irin mummunan faduwa, zaro ido yayi cike da tashin hankali take yaji jikin sa na ɓari ba komai yasa shi wannan faduwar gaban ba illa ganin bayin Allah nan kwance a qasa kamar ma basa numfashi jikin shi na bari ya qarasa gaban su durqushewa yayi aban Ameesha tare da daga hannun ta sai yaji ya saki yaqara dagawa nan ma yasaki alamar kamar mutum ba rai ajinkin shi cike da tashin hankali ya kara kunnen shi daidai satin hancinta jiyayi ba numfashi jijjigata ya shiga yi yana kiranta, shiko takan Dadda ma dake yashe gefe guda itama bebi ba
Ameesha kawai yake ta faman jijjigawa yana cewa ki tashi dan Allah karki mutu karkimin haka ki tashi dago kanta da zeyi yaji hannun sa ajike kamar ruwa dubawar da zeye yaga jini wata uwar qara yasaki cikin fitar hayyaci muryar sa na rawa da ƙarfi yace "NO..! NO..!! NO...!!! Ameesha Ameesha AMEESHAA..!!!!!!!!!
Bari inbarku ana kada qara tafasa muku kunnuwa🥵
[21/12, 3:00 pm] #yaya Azeema#: 💅SARKI SAMEER.....💅
By
Yaya Azeema😎
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
Bismillah.........
37&38
"""""""""""""""""""""
'Cigaba yayi da bubbuga ta yana kiran sunan ta amma shiru no response miqewa yayi yakoma gurin dadda dake kwance a qasa amma ita ga dukkan alamu babu wani ciwo ajikinta kamar ma suma tayi yana zuwa gabanta yatabbatar da ranta kwasa yayi aguje yafita waje ruwa yadebo yadawo duk yabi ya rikice ya fita hayyacin sa yanazuwa ya yayyafawa dadda aikwa tasauke wani dogon numfashi tunda yaga haka be bi takanta ba yaqara komawa kan Ameesha yana qara kiranta amma ina dadda da tadawo daga doguwar suman datayi ahankali tafara bude ido amma bata gani radau sai dishi dishi jin kamar ihun mutum adakin kuma kamar muryar namiji yasata qara rife idon tare da dan murzashi sai ta qara budewa sosai yanzu tagani sai yanzu kuma abun da yafaru dasu yashiga dawomata a brain asukwane ta mike kamar wacce aka tsikara bossay nagani ta miqe yayo wajenta yace dadda me yafaru daku waye yaayi muku haka ankashe ta fa Ameesha ta mutu sai nakashe duk wanda yakashe ta saina kasheshi da hannuna yafada yana nunawa dadda hannu dadda datayi mutuwar tsaye jin abun da bossayn kecemata sai kuma tashiga girgiza kai hawaye na rigerigen fitowa daga idanunta muraya na rawa tace bata mutuba bata mutuba kar kaqara cewa ta mutu ni jikata bata mutuba nasan bazata mutu tabarni ba tafada tana qaraswa inda Ameeshan take akwance itama jijjigatan tayi amma abun da bossay yaji yagani itama haka tagani qamewa tayi awajen ta kasa koda daga hannuta ko motsi takasayi bossay dake bayan ta shima ya qame din sai kuma can daga bisani yazabura yayo wajenta yace tare da daga ta yasakata akafada yace dadda muje asibiti shi sai yanzuma ya tuna da asibitin rudewa tasa duk yama manta da wani asibiti said yanzu be jira cewar dadda ba yafice da sauri dadda ma ai da sauri tabiyo bayansa ko mayafi bata daka ba bare tayi tunani saka takalmi atare suka qaraso gurin motar back seat yabude yasaka ta dadda ma tashiga bayan shikuma yakoma gaba da sauri yatashi motar yajata a tsiyace da gudu idonsa ya rufe kawai gudu yake kwararawa akan titi dan alokacin da wata motar zatasha gabansa inajin baze tsaya ba dan ze iya bi takanta tunkan yazo waje yake dokawa mutane horn wanda yake son ransa kwa ya matsa ya basa hanya duk wanda yaga irin gudun da yakeyi kamar a filin tsere sai ya jinjina masa ko tsoro ma bayayi yaje yadaki wani gurin wasu suce Allah yakiyaye wasu kuma suce Allah yasa ya bugu da wani abun saboda wannan gudun da yakeyi yayi yawa bekamata yaringayi ba kowade da abun da yake cewa akansa duk inda yazo wucewa
Oho shi bema san sunayiba shide kawai tafiya yake ahaka de har yaqarso batate da wata matsala tasame suba sunzo lafiya lafiya yana zuwa yabuga wa gate man din horn shima da wuri akabude shikma yadanna cikin hospital din da yabari dazu saigashi yanzu ya dawo ko parking be gama daidai tawaba yafito ya bude baya yayi saurin bide baya ya cuccubota daman ba nauyi garetaba yana fito da ita yayi ciki da ita dadda nabinshi abaya yanashiga da ita nurses din dake gurin sukai saurin zuwa aka dakko gado aka dorata akayi emergency da ita sukuma ka tsayar dasu awaje da wuri nurses din sukayi saurin rufawa kanta suna bata taimakon gaggawa dan ganin tadawo hayacinta yayi da awaje kuma bossay yake ta faman zarya yakasa zaune yakasa tsaye sai kuma can yadauko wayar sa yakira Ammi ya sanar da ita cewa suna hospital Ameesha ba lafiya dagana kuma yakshe beyi mata kwakwaron bayani ba wata nurse ce tafito daga cikin dakin dasauri dukan su sukayi kanta suna cewa ta farfado girgiza musu kai tayi tace A'a haryanzu ba wani sauyi zamuje musanar da doctors suzo su dubata saboda munkasa taimaka mata tana kaiwa nan tayi gaba dadda ta dora hannu aka tana kuka tana cewa shikenan sunkasheta sun huta suncuce ni bossay ne yayi qarfin hali yace dadda dan Allah kidena wannan maganar in Allah ya yarda bata mutuba zata dawo muci gaba da rayuwa tare sannan yakamota yazaunar da ita akan kujerun tare da ruqo hannun ta sannan yace dadda suwaye sukayi muku haka suwaye suke qoqrin rabaku da duniya kigaya min dadda shiru dadda tayi takasa bashi amsa qara tambayarta yayi nanma shiru tayi tana tunanin mezatace mishi ya yarda dan bazata iya gaya masa gaskiyar abun da yafaru dasuba saboda ba hurimun sabane abun su ya shafa ba shiba dan haka bazata sakashi aciki ba saida ta yanke shawarar abun da zatace Mishi sannan tafara cewa wasune suka shigo fuskarsu duk a rufe suka shigo suka jata zasu fita da ita nikuma natashi na ruqeta ina roqonsu ina riqeta sai wani ya makama min abu tare da jafar dani tundaga nan kuma banqara sanin meke faruwa ba saida kazo tagama bashi labarin tana Matsar hawaye yayi mamki da jin hakan yace dadda kuma bakisasu ba to ku a ina suka sanku tace nima bansani ba nide kuma nasan ba harkar kowa nake shiga ba bare wani yace namishi ba dede ba yace dadda dan Allah wai ku suwaye kuma daga ina kuke baku da dangine ya qarasa maganar yana qare mata kallo yana jiran yaji me zatace amma kawai sai ta juya masa baya batace mishi komai ba ganin hakan yasashi qara juyowa inda tajuya din yace dadda baki ce komai ba hade rai tayi sannan tace wai da tambayar ka zanji koda halin da jikata take ciki tana fadar haka ta mike ta bar masa wajen ta canza guri tazauna tare da tafka tagumi
shide kawai binta yayi da ido yana kallonta da mamaki shibega wani abun jin haushi ba anan daga tambaya kawai shima zama yayi be qara yunqurin binta ba suna ahaka doctors din da suka shiga tun dazu basuga shigar suba sune suka fito yanzu suna fitowa sai bossay yatashi da sauri ya qarasa girin su yana tambayar yajikin nata doctor yace ina iyayenta dadda ce tayi saurin qarasowa gurin tace gani doctor yakalleta tundaga sama har qasa yaga ko takalmi babu gata ba mayafi ajikin tsofe tsofe da ita zata wani ce itace mahaifiyar yarinyar kai yagirgiza bece komai ba yajuya yakalli bossay yace kaifa wanene dinta sai yace yayan tane yace to kai kasame ni a office yana fada ya wuce gaba shikuma ya bishi abaya suna shiga yayi yazauna sannan yanuna mishi kujera yace have a seat zama yayi yana fuskantar shi saida yadanyi jim sannan yafara magana yace agaskiyar magana yarinyar ku tana cikin mawuya cin hali garin ya akai haka tafaru kukayi sake hartaji wannan babban ciwon haka bossay yace wlh nima bansan me akai mata ba ina shigwa gidan natarar da ita awannan halin amma yanzu dr. meye abunyi metake bukata dr. Jamil ya nufasa yace munsha wahala gurin gano ina matsalar take sai da qyar muka iya ganowa amma de mutabbatar bata mutuba ahalin yanzu da sauran numfashin ta saide kuma tana tsaka me wuya dan da qyar ne inzata tashi saboda sai anyi mata aikin kwakwalwa wanda yake da riski wala mutum ya tashi wala kuma yarasa ransa kuma koda yatashin ma ze iya mantawa da komansa da kowa ina akaci sa'a kuma zata tashi lfy qalau saide wataran za ana kasa gane kanta idan abun yajuya mata bade yanda bata yiyuwa bossay ne da yaji gaba daya duniyar tamishi zafi yace sir amma me yasamu kwakwalwar tata yace mishi jini ne ya shiga ciki dan haka dole sai an fidda shi
Ya salam bossay yace sannan yaqara cewa to ba matsala yanzu aikin zekai yaushe da fara shi da gama shi doctor yace mishi a kwana daya ma za a gamashi to amma babbar matsalar itace wanda ze mata aikin baya nan yayi tafiya shine babban likitan amma da sauqi naji ance nan da two weeks ze dawo inyaso mu sai muyi mata allurai da zatai ta bacci harzuwa lokacin da ze dawo hakan ba matsala bane saboda mu bamu da ikon akan bangaren wannan aikin saide mujira da wowarsa yanzu zamu cigaba da bata kulawa anan har zuwa yadawo sannan yace ze iya tafiya ko kuma zasu iya tafiya gaba dayan su saboda bawanda ze samu damar ganinta daga nan har zuwa lokacin da za ayi mata aikin dan haka ba buqatar suyi tazama anan hakannan duk halin da ake ciki za ana sanar dasu......
Jinjina kai bossay yayi sannan yayi masa godiya tare da miqewa jiki asanyaye babu kwari yabar office din yana fitowa ya nufi inda dadda take yana zuwa kuma sai yaci karo da su Ammi ita da faruq da yakawo ta suna ahigo kuma sukayi qoqarin kiranshi danjin a inda suke sai kwai sukai karo da dadda anan Ammi tayi mata magana sai take gaya musu yaje wajen dr. sai suka zauna suma suna jiran fitowar tashi yana qarasowa gabansu duk suka dago suna kallonsa ganin jikinshi duk amace yasa dadda cewa ta mutu ko dannan sun kasheta ko sun rabani da ita takarasa fada tana qara sakin wani marayan kukan Ammi ce tace haba dadda kiyi hakuri mana ki tsaya musaurari me zece bata mutuba in