Showing 87001 words to 90000 words out of 136570 words
dauko su ba wlh Ammi ce tayi saurin dakatar dashi daga maganar da yakeyi tace kul naqara jjn irin wadannan maganganun abakin ka kanaso karasa ladan niyar dakayi duk irin abun da zata aikata agidan karkataba yin wannan tunanin zamuci gaba da ruqesu kuma muyi mata fatan shiriya kayi mata uzuri saboda akwai tsufa daman duk abun da zakayi domin Allah yabaka lada to dole sai ka fuskanci qalubale daban daban wanda sai ka kai zuciyar ka nesa Inbahaka ba zakai ta samun ladane kana zubar dashi ayanzu bata da wasu aduniyar nan da ya wuce mu tunda muka je muka dauko su dole ne mutsaya akan duk abun da ze shafe ta bawai muzuba mata ido ba dole mujawota jikin mu sosai daga nan ma watakil musamu wani haske agareta nasanin ko ita wacece idan zakayi abu kawai kayi dan Allah kar ka tsaya bin halin mutum idan kace haka zakai to kwa bazaka taba taimakawa kowa ba saboda kowa da ka ganshi da irin tashi matsalar arayuwar nan,
Bossay ne ya katsamata zancen ta dacewa shikenan Ammi komai ya wuce Amma fa Ammi wallahi matar nan a kwai abun da take boyewa bataso kuma kowa yasani Ammi ni na dade da fahimtar ta duk wani abu da take tanasane takeyin sa tana cikin hankalimta watakil kawai taku ne Ammi tace koma me tatake boyewa wataran dole ta tonoshi watan wata rana kawai muzuba mata ido kar wanda ya tambayeta game da ita ko wacece ko daga ina take ita da kanta wataran zata fada,
Bossay yace yauwa Ammi daman inso intamabye ki a ina kika santa dannaga lokacin da kuka hadu kun nuna kunsan jiuna sosai manatawa nayi intambaye ki tun alokacin
dan nufasawa Ammi tayi sannan tace nasanta amma bansan wai ko ita wacece ba kawai shekarum baya tun wannan yarinyar tana yar qarama kai kuma lokacin katafi karatu faruq kuma yana boarding su aysha su kuma suna yara ba fahimtar komai suke ba,
na hadu da ita akan titi tana ta faman gudu goye da Ameesha abayanta kamar de biyo ta akeyi saboda tana gudu tana waigen baya ganin hakanne yasa nayi parking agabanta nace ta shigo intaimaka mata bayan tashigo nakawo ta gida kwananta biyar agidan tace mun zata tafi tagode nayi nayi da ita ta zauna amma taqi dana tambayeta me yafaru da ita wacece ita kuma a ina take tafadan nikuma zantaimaka ta Amma fur taqi yarda sai tace munma irin wadannan tambayoyi suna daya daga cikin dalilin da bazesa ta zauna ba dan haka gwara ta tafi babu yanda na iya da ita dole nabarta ta tafi tunda nayi niyar taimaka mata sai nabata kudi masu yawa da nasan zasu taimaka mata sosai tundaga tayi min sallama da godiya banqara ganinta ba sai ranar da mukaje da kai dan nayi mamaki ma da ta yarda zata ta dawodin to kaji ta yanda akai kaga ranar da mukaje munsan juna saboda banmanta da ita ba itama kuma bata manta dani ba koma maiye mubi asannu zamu sani,,.....
cike da gamsuwar labarin da Ammi ta bashi yajinjina kai tareda cewa shikenan amma dole musani ko waceca ita saboda kinga baze yiyu ace kana zaune da mutum tsawon loakaci ba amma bakasan ko shi wanene ba kuma be yarda dakai ba kinga ko in abba yadawo yagansu agidan nan kinsn dole sai yasan ko suwaye duk da ze taimaka musu din amma sai yafara sani tukunna ko kina ganin baze tambaya ba ?
jinjina masa kai tayi sannan tace nasan dole yatamba duk dade munyi maganar dashi a waya kuma ya amince da zaman nasu saide kuma be tambaye ni ko daga ina suke ba kaiwai yace ai nasan daidai idan na aminta dasu kawai zan iya dauko su amma nasan inyadawo ze tambaya saide mubari muga dawowar tasa idan ya matsa akana sanin to sai tagaya mishi watakil idan taga shi namiji ne ta iya fada mishi inkuma taqi bansan wane matakide ze dauka ba saide mujira din kawai yadawo tafada cike da damuwa kamar ance mata idan yadawo zasu bar gidan,
faruq ne yace ai abba baze qima amincewa ba koda taqi gaya masa baze koresuba kunsande halinsa da tausayi nasan ze rabu dasune kawai amma ba abun dazeyi ku kwantar da hankalin ku yanagama fada yadora sa cewa yanzu yakamata kuje ana qara bata lokaci ba asan kuma yanzu me takeyi a asibitin ba ,
Ammi tace gaskiya ne yakamata mu gaggauta zuwa kar muje ta qara jawo wata matsalar bossay yace to shikenan mutafi din gaba dayan su suka fito daga dakin suka sauko downstairs,faruq yace Ammi wai ina su yasmin ne naga duk bangansuba tace ai basa nan sunfita da furairah zasuyo shopping ranar monday zasu koma makaranta yace "ok" to bari inbiku mukoma tare dan bazan zauna nikadai ba agida kamar maye,
Ammi tace kacede tsoro kake ji kamar ba namiji ba ka rage tsora wallahi in mukai maka aure idan matar bata nan kace baza ka iya kwana kai kadaiba agidan ko?
lokacin da take mai maganar har sun fito daga falon sun qaraso waje bude motar sukayi Ammi ta shaga baya sukuma suka shiga gaba bossay ya tayar da motar
yar dariya faruq yayi sannan yace Ammi ai ba inda zani anan gidan zan zauna idan nayi auren ga dakina sai a gyarashi tsaf muzauna da matar bossay yace dake bakada hankil gote gote dakai ubanwa ze barka ka zauna da mata acikin gida kai zakaje ka nemo kudi ka gina gidan ka da kanka sannan kabar mana gida munsallame kai da gida kuma saide ka kawo musu ziyara itama matar baza ta yarda ba ko tayardama iyayenta bazasu yarda ba saboda zasuso suyiwa yarsu kayan falo dana kitchen da duk abun da akeyi wa matar aure idan kuma kace adaki daya zata zauna duk sauran kayan ina zakace ta sakasu?
"Eh Ku ma fa hakane to sai ingina mata wani daban awaje ta ajiye kanyanta sai ta kwaso na sa warta muyi zaman mu anan muringa kwana a dakina ko Ammi ai hakan yayi?yafada yana kallon Ammi dan tabashi goyon baya akan maganar shi Ammi tace eh mana hakan za ayi tunda nono ka kesha da bazaka bar gidan ba kuma can din da zaka gina meye amafanin sa ai gwara karkayi kawai kayi zaman ka ana sai ma in kwashe kayana ita ta zuba nata anan gidan shikena mubar maka gidan gaba daya sai mukoma gefe muna kallonku ko ai inaga hakan sai yafi maka dadi,
juyowa yayi daga gaban motar yace a'a ammi ai baza ai haka ba kuyi zamanku nide kawai abarmin dakina muzauna da ba inda zani ina tare da ku tace to shikenan ai Allah yakaimu lokacin da rai da lafiya cike da jin dadi yazata da gaske take yace Amin Ammi na daman nasan ai bazace sai na bar gidan ba saide masu bakin ciki su mutu zaman mu daram ko anaso ko ba aso,
Ammi ta riqe baki tace oh ni yarnan yanzu da wakake wannan maganar yace nifa bada kowa nake ba Ammi kawai da duk wanda zemin bakin ciki
yafada yana satar kallon bossay ta gefe,
Bossay dakejin shi kuma yasan dashi yake yace zanyi maganin ka ne kar kaga kayi tsaho ba wahalar duka zakamin ba tsaf zan kamaka in nada maka na jaki tunda baka da kunya,
qasa qasa yace tabb aikwa da any doke doke saide kowa jikinshi yagaya mishi,
Bossay yace me kake cewa sai yace nikam me zance haka nace yi hakuri babban yaya,kai bossay ya jin jina yasan bahaka yace ba ammade besan me yaceba saboda bejishi ba shide yaji yana magana kawai,
Ammi tace kai kafa kiyaye ni banaso shirmen banza kai abun naka ma kullum gaba yake kana girma hankalin ka na raguwa to wlh kafita daga idona duk da bata jiba itama amma tasan wata rashin kunyar yayi shiyasa ta tsawatar masa ,hade rai yayi yana turo baki irin beji dadin fadan da Ammi tayi mishiba acikin ranshi sai faman qunquni yake kuma be qara magana ba dukan suma ba wanda yasake magana har suka qaraso hospital din bayan sun shiga kowa yafito suka rufe qofar sannan suka nufi ciki kai tsaye Suna zuwa inda suka saba zama suka nufa,
Allah sarki suna qarasawa suka ga Dadda ta hada kai da gwiwa sai faman kuka take tagaji da zaman gurin amma kafiya ta hana ta tashi daga wajen kuma tun fitowar ta ba wanda yazo gurin ta ita kadai ce awajen kamar mayya abun dunniya duk yabi ya isheta tayi danasani yafi cikin carbi😂
(maganinki kenan kafiyar tsiya Allah yaqara qarawa Allah yasama karyayi mata din muga ta tsiya).
[23/12, 4:39 pm] #yaya Azeema#: 💅SARKI SAMEER....💅
. By
Yaya Azeema 😎
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
Bismillah......
57&58
'jitayi andafata da sauri ta dago tana binsu da kallo sai kuma tasake sakin wani kukan gaba dayansu saida tausayinta yakama su musamman faruq na hannun damarta sai yaji be kyauta mata ba da yatafi yabarta itakadai.
Ammi ce ta tsugunna tare da rungumeta tace daddda dan Allah kiyi hakuri kikwantar da hankalin ki yazaki zauna ki ta kuka anan gurin so kike ki haifarwa kanki damuwa shiru tayi bata iya cewa komai ba har Ammi tagama ta saketa tare da zama akusa da ita tana qara lallashinta har tasamu tayi shiru amma taqi yarda ta kalli kowa hakan nan taji abun da tayi yasa taji kunyar su bayin Allah duk abun da take musu amma basa taba gajiyawa gurin taimakonta,
faruq ne ya tsugunna agaban ta yace dan Allah dadda kiyi hakuri kinji Sweet heart dina bazan qara tafiya inbarki ba nasan duk ni najawo miki wannan kukan nazata zaki taho idan kikaga natafi ashe bazaki iyaba I'm sorry sweetheart dan shafa kansa tayi sannan tace ba komai dan albarka ni baka min komai ba ni yakamata ma na baka hakuri koma meye ni najawa kaina sannan ta juya gurin Ammi tace ba abun da zance muku saide addu'a Allah ya biyaku da irin kulawar da kuke bani iya haduwa ta daku bazan taba mantawa daku ba harqarahen rayuwata duk abun da nake muku baku da buri saina kuga kuna kwantar min da hankali batare da kunsan ko ni wacece ba kun rukemu hannu bibbiyu nida jikata Allah yasaka muku da alkhairi yabiyaku da gidan aljanna ni yanzu tawa ta qare tunda nasan Ameesha bazata rayuba zan dauke ta mukoma inda muka fito sai ayi ta axiyarta acan nikuma daga yau zan rabu daku amma alfarma daya nake nema agurin ku kutaimaka ku fito min da ita sannan kudora mu amota ku bada kudin idan kun koma gida a kwai kudi adakin danake kwana a qarqashin kayana ku dauka na barmuku su gaba daya inkukai min wanna ma kadai ya isa kar kuma.....
Bossay ne ya dakatar da ita dacewa haba Dadda wace irin magana kike yi ne kina fadar abun da baze taba yiyuwa ba, ba inda zaku kuma Ameesha bazata mutu ba a yau ko gobe za suyi mata aikin ki kwantar da hankalinki dan Allah kibar waɗannan surutan,tace hmm wanda ze mata aikin yace baze yiba kuma ance idan yafadi magana ba ya canzawa magana daya yake kuma ni naga alama saboda idan kaga mutumin kamar ba mutum ba ni watakil ma aljanine masu shigar mutane daga ganin shi ba imani a tattare dashi be da tausayi ko kadan duk jiran da mukayi mishi fa wai yana zuwa ya kwanta yakama bacci hayaniyar muce ta tasheshi wannan qaramin dalilinne ma yasa yace baze yiba dan bashi da tausayi yarinya a kwance kusan sati biyu amma yanzu yace baze yi mata ba hmm daman wasu masu kudi haka suke,
ni inaji ajikina yarinyar nan bazata tashiba dan haka kar ku wahalar da kanku kawai kubar ni intafi da ita tafada tana share hawayen dake zubo mata,
faruq harda hawaye yace dadda dan Allah kibar wannan batun in Allah ya yarda zata tashi tayi rayuwa kamar kowa,bossay ne yadora dacewa ko nawane zan kashe akanta ko sunqi yiamata zan dauke ta ko qasar wajene inkaita ayi mata sai inda qarfina yaqare akan samun lafiyar ta yanzu bari inje inyi magana dasu asan abunyi yana kaiwa nan amaganar sa yayi hanyar zuwa office din dr.jamil,
Ammi da gaba daya jikin ta yayi sanyi ta bude baki da qyar tace hakuri zaki amma ba inda zamu taba bari ki tafi kina tare da mu in sha Allah saide mutuwa ta raba mu yanzu bari yadawo muji yanda za ayi amma kicire duk wani tunani aranki kabar damun kanki da yardar Allah Ameesha kamar tasamu lafiya zakici gaba da rayuwa da ita kamar da kinji tafada tana share mata hawayen da ya zubo mata,
murmushin yaqe dadda tasaki domin maganganun da suka fada tareda da nuna kulawar su agareta dan haka be kamata tayi jayayya dasu ba gwara kawai tabisu yanda suke so hakan sai yafi musu dadi dan haka kawai sai tace to shikenan Allah yasa nagode sosai da kulawar ku Allah yayi muku abun da kukai mana Allah yatai makeku akan duk halin da kuka tsinci kanku Allah yabiyaku da gidan aljannar Firdausi da ameen duka suka amsa mata sannan Ammi taci gaba da bata baki akan ta maida komai ba komai ba dahaka de har suka samu ta dan sauko tasaki ranta........
bossay yana qarasawa office din yayi nocking akabashi iznin shiga sai ya tura qofar tare da shiga ciki da sallama abakin shi abayan yaqarasane ya niqawa dr.jamil hannu suka gaisa bayannan kuma yafara yimasa bayanin abun da ya kawo shi shikuma sai yace mishi ai yanzu bashine me kula da itaba ya miqa file din gurin dr.shettima shikuma zebawa Sam wanda zeyimata aikin saide yaje yasame shi yace ok tare da miqewa yana mishi godiya har yakai bakin qofa sai kuma ya dakata tare cewa yau dan Allah ko zaka kwatan ta min inda office din nashi yake dan bansan shiba dr. jamil ya kwantan ta mishi kamar yanda ya bukqata godiya yaqara yi masa sannan ya fita directly ya nufi inda aka kwatan ta masa din kwankwasa qofar yayi aka bashi iznin shiga bayan ya shiga ya tadda su aciki shi da saleem yagane fuskar saleem saboda ranar da ya taimake su dan haka be manta fuskar shiba yana shiga da sallama dukan su suka amsa mishi sai yagaida dr.shettima shikuma saleem ya miqa mishi hannu suka gaisa sannan yazauna aka kujerar da take facing din saleem saida yadan qara nutsuwa sannan yafara bayanin ko shiwane da kuma abun da yakawo shi,
saleem ne yace gaskiya a kwai matsala yanzu maganar da nukeyi kenan yanda za a shawo kansa ya amince amma kuma matsalar itace yama qi daga wayar bare asan halin da akeciki abashi hakuri gashi ba asan inda yake ba itama tayi kuskure wallahi gashi yanzu kowa ya shiga damuwa,
dr.shettima ne yace yanzu mafita daya ce kajata kutafi gida inyaso kubani zuwa gobe zan nemoshi duk inda yake zuwa gobe kuma in sha Allah zanyi iya bakin qoqarin ganin ya amince duk hanyar da zanbi ya yarda zanbi kuje gida kawai sai zuwa gobe idan daso samune ma kubari sai nakiraku dan Allah kar kusake zuwa da wannan rikitartiyar tsohuwar duk yanda mikai dashi zankiraka insanar dakai inaganin hakan sai yafi kawo mana solution ko yakuka gani?
Bossay ne yace hakan ma yayi wlh Allah yasa adace gaskiya muna godiya bari inje kawai ka kiranin zuwa goben Allah yasa ya amin ce suka ce ameen sannan yafita daga office din yana qara yi masa godiya dan baqaramin dadi yajiba sai yanzu yadanji sanyi aransa"yana qara sowa gurinsu ya yagaya musu duk yanda sukayi amma yadanyi wa maganar kwaskwarima saboda dadda ta kwantar da hankalin ta aikam taji dadi dukan suma sundan ji dadin hakan dan haka cike da murna duk suka tashi suka wuce gida ran kowa fess saboda yar qaramar qaryar fa bossay yayi musu yace ya hakura kuma tun ayau ze fara dubata zuwa gobe za agama komai amma ance kar wanda yaje sai ankira su saboda anaso sai ta dawo cikin hankalinta sannan zasuzo suganta dan haka suke ta jin dadi musamman dadda da bakinta yama qi rufuwa,
Saleem yakalli dr.shettima yace yanzu kana ganin ze amin ce din ni ina ganin kamar kawai ka sallame su anan sai sukaita wani tunda kace baya magana biyu kuma tunda yayi haka har yaqi daukar wayar ka ai kasan dole yaji haushin kuma ba lalle bane ya amince
Saida yadan numfasa tare da furzar da isaka daga bakinshi sannan yace dole ya amince zan hadasa da wanda ya isa dashi a gida inde shi yace yayi mata to baze taba bijirewa umarnin sa ba zeyi mata din ko yana so ko baya so kaf duniyar nan shikadai yake daga qafa da jin maganar sa saboda yaba ganin girman shi dan haka kar kadamu yanzu gida zan tafi zanje insame shi acan nasan watakil yakira waya anzo andauke shi, Yanzu bari inje gida in shirya sai in wuce can din yafada yana miqewa tare da fara har hada kayansa,
saleem ma tashi yayi yace to shikenan sai gobe Allah ya kiyaye hanya Allah yasa adace yace mishi Ameen atare suka fito waje qulle office din yayi sanna yanufi hanyar fita yana zuwa ya shiga mota yabar asibitin yana kan hanya yana tafiya sai yazaro wayar sa ya lalubo wata number da naga ansaka my sister kira yadanna mata ana dagawa yace yauwa sister yakk tace lfy lau yayana nikadai sannan yace bakya nemana ko tace wlh aa bahakabane kawaide abunbuwane sukai dan min yawa, yace dan Allah fa aiki kike zuwa ko yayanane dake bamusani ba,
Dariya tayi sannan tace 'yaya kuma ina yar qaramata a ina zan samo 'yaya yace bawani nan nide fushi nake dake daga can tace I'm sorry bro sai yace nadeji zankama ki yanzude nakiraki ne in dan