Showing 84001 words to 87000 words out of 136570 words
brown dinsa da ta wani fidda shap kamar anyi shaving dinta asaite take gata baqa kamar ansaka mata kwali sai gashin kansa da yake akwance luf yasha gyara dan harya zubo kan goshin anyi masa wata kanan nada yayi kamar macaroni sai Bluetooth da ya maqala akunnen shi guda daya hannunshi daya a cikin aljihun rigar jikin shi dayan kuma yana ruqe da trolley ahankali yake tafiya kamar bayaso da sauri dr.shettima yaqarasa gurin sa tare da yin hugging dinshi tare da cewa you are well come my man I'm so happy to see you I wanna miss You too much duk wannan abun da yake besamu arzikin anyi mishi magana ba kuma yana tsaye ko motsi beyi ba bare kuma yamayar masa da hugging din dayayi masa saida yagaji dan kansa sannan yataba jikin shi danashi yana ta faman sakin murmushi da gaske de yaji dadin dawowar tasa kuma qin kulasan dayayi be damesa ba hannu yasa yakarbi trolley din hannun sa sanna ya ruqe hannun sa suka fara tafiya har suka qarasa wajen motar sannan ya bude mishi ya shiga sai ya bude back seat yasaka trolley din sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver yazauna tare da yiwa motar key tare da yin reverse yasai ta kan mota sannan yafara tafiya a tsanake dan juyawa yayi ya kalle sa saiga ya kwanatar da kansa jikin hannun kujera ya lunshe idon sa kamar me bacci ganin hakan yasa shi yin shiru shima dan yasan tunda yaganshi haka to ko meze ce mishi ba amsa ze samu ba dan haka gwara kawai yayi shiru shima,,
ahaka bawanda yayi magana har suka qaraso hospital din yana gama parking yaqara kallonshi tare da kiran sunan shi yace SAM muqaraso fa shiru ba amsa kuma har yanzu be bude idonsa ba saida yagama shan qamshin shi sannan ya bude idon sa yadan kallishi batate da yace komai ba kuma yabude motar yafita da shima budewa yayi ya fito yarufe qofar yazagayo ya koma kusa dashi yace ka tsaya ko sai na dauke kane sai yanzu ya bashi amsa shima ba bude baki yayi ba kwai uhm yace mishi dr. shettima sai yadanyi murmushi yace ai zan iyane kar ka ganka wani qato dakai ba wahalar dauka zakamin ba jinjina mishi kai yayi sannan yafara tafiya ba tare da yabashi amsa shima bayansa yabi dake kowa yasan da dawowar sa yasa ba kowa awaje kowa yakama aikin gabansa gudun jawa kai matsala any mistake game over qaramin abu zakayi yayi firing dinka dan haka kowa yake taka tsantsan idan yazo dan surabu lafiya tunda ba dadewa yakeyi ba idan yazo,
yana tafiya yana kallon asibitin har suka shiga ciki nanma kalla yaringayi office dinshi asama yake dan haka direct suka nufi sama saide suna dab da fara hawa benen saiga dadda tsudum abayansu tan cewa to yaza kutafi bayan kasan tundazu muke jiran ku tsayawa dr.Shettima yayi saboda yagane muryarta amma banda dayan dan har ya qarawa motarsa mai be tsaya sauraron taba duk da yasan dasu ake magana dr.shettima ne yace kiyi hakuri baiwar Allah yanzu yadawo kinga dole sai yadan huta tukunna ze samu damar fitowa kuqara hakuri tunda saboda aikin nata nema yazo nan da baze zo bama kujira kinji baba jiki asanyaye dadda tace to aishikenan yafito lafiya munade jiransa yace to karkidamu bawani dadewa zamuyi ba yana fada ya wuce shima dadda komawa tayi kusa da faruq, faruq na ganinta yace dadda yanaganki haka me ya sukace miki tace bansani ba din ni wlh banma san neye amfanin ka ba kazo kayi zaune nida nake mace ni nake qoqrin jin ba asi kaide anyi malalacin namiji ni kakiramin wancan yaron duk wulakancin shi yafika wayewa da shine da tuni yayi abun da yadace amma kai sai wani noqewa kakeyi saikace dan qauye kwata kwata baka wayeba sai iya shiganta ka anan kafi kauri dariya yayi sosai yace lalle dadda yanzu nidin ne ban waye ba ki kallenifa kina ganina kinga wayayye dan zamani yafada yana wani kada kai harda juya ido saikace mace kasake dadda tayi tana kallonsa tace ikon Allah kai abun naka kullum gaba yake ji yanda kake abu saikace mace wannan ce wayewar da ancuci wayewa wlh da ka waye ai baza ka tsaya anan ba ni wlh nama yi danasinin tahowa dakai daman wancan yaron na lallaba muka taho yace au yanzu dadda hakan ma danayi miki bazaki gode min ba saide ki ta kusheni kina yabon wani to bari intafi gida sai kikirashi yazo din yana gama fada ya tashi yana niyar fita daga wajen da sauri dadda tace la ai da wasa nake dan albarka tsokanar ka fa nake dawo muzauna ai yanzu komai yayi daidai tunda na tambayo kuma yanzu zasu fito tafada tana danyi murmushi kwabe fuska yayi yace Allah kisake ni intafi bazan zauna ba kuma daga yau bani bake munkunce tace haba dan albarka ai nasan baza muyi haka da kaiba ko baka so inbaka jikar tawa inde kanaso dole kazauna dani inkuma bakaso shikenan na yarda mukunce din kuma in munkunce baza mu sake daurawa ba tafada tana mika mishi hannu alamar sukunce din sai yamaqe kafada yaqi mika nashin yazata da gaske take dariya tayi sannan tace ja'iri ai nazata zaka yarda din ashe baza ka iyaba banza yayi mata ya koma inda yatashi yazauna tare da juya mata baya wai shi adole yayi fushi da ita itama kusa dashi ta dawo ta zauna tana dan dariya qasa qasa saboda kar yajita,
dr.shettima yana zuwa bakin qofar yadan kwankwasa sannan shiru ba amsa saida yadanyi jiran kamar 1 minutes sannan ya bude ya shiga ciki be wow aljannar duniya office iya office ya hadu iya hasuwa kamar ma ba office ba abubun ciki komai farine gashi yasha gyara tunkan zuwan shi daman kullum sai anshiga an gyara duk da bayana table din farine sai abubun kaine kawi suka kasan ce black sai kujeru guda biyu na zaman wan inya shigo ze zauna sai fridge shima fari saide shi sai fulawoyi da akayi ado dasu sai wani tamfatsetsan hoton shi da ke maqale da bango kana shigowa dashi zaka fara cin karo saboda yana facing din qofar shigowa suka dai ne aciki sai qofofi biyu danake da tabbacin daya kitchen ne dayar qofar kuma bedroom ne,......,
dr.shettima yana shiga ciki sai yaga baya nan dan haka sai kawai ya nufi bedroom din dayake da tabbacin yana ciki nan ma saida yayi nocking sanna yadan qara bashi lokaci idan ma wani abun yake ya gyara saboda yasan ba lalle yayi mishi magana ba kai tsaye ya tura qofar yashiga ciki da mamakin sa yana shiga yaganshi a baje akan bed ko takalmi be cire ba qarasawa yayi gabanshi ahankali yakira sunan shi amma shiru ba amsa saida ya kalleshi sosai sannan ya fahimci ashe har bacci yayi awon gaba dashi adan kankanen lokaci ysugunnawa yayi yacire masa takalmin qafar sa sannan yagyara masa kwanciyar sa yafito daga dakin har ze fita kuma sai dadda ta fado mishi tana can tana jiranshi gashi kuma me kankat din ya kwanta bacci besan kuma lokacin tashin shiba dan ze iya daukar lokaci yanayi gashi kuma qaidar shice idan yana bacci ba a tashinshi sai yaga damar tashi dan kansa,
fita yayi da har yazauna a office din nasa sai kuma ya miqe yafita da tunanin idan ma ta tambayeshi zece mata gashi nan yanzu ze fito daganan kuma yasan bazata ce zata nemo shiba dole ta hakura idan kuma ta gaji ta tafi da wannan shawarar yafito.
ilai kuwa yana zuwa yana shirin bin wata hanya caraf yajiyo muryar ta tana cewa ina dayan yake naga ka fito kai kadai juyowa yayi yana kallonta ganin tan dayayi sai kuma yaji kawai baze iya yi mata qarya ba dan haka sai kawai yace wlh ansamu matsala tsayawar danayi anan wai kafin inshiga har bacci ya daukeshi yanzude zamu jira yatashi idan yatashi zan sanar dake idan kuma kungaji zaku iya tafiya ai baza aitaba yimata aikin batare da saninkuba dole in anzo yi za akiraku asanar daku sai kuzo yagama fada yana kallon ta amma ga mamakin sa wai sai yaga tana hararar sa zaro ido yayi sannan yace wlh baba za akiraki kar kidamu wata hararar taqara maka mishi sannan tace ba inda zani shi waye da baza atasheshi idan yana bacci ko sarki ne ai bazaice karc atasheshi ba naga alamar sai kwana kwana kuke yi kuga yamin gskiya idan kunkashe ta sai kufada bawai kuyi ta jamana raiba,maganar ta taso ta bashi haushi dan jin abun da take cewa ranshi ya baci dan haka yace kinga mu ba mugaye bane kuma idan ma mutuwar tayi me zehana mu sanar daku ko tsoron ku zamuji ne mungaya miki iya gaskiya ta amma kuma kina wata maganar daban yafada yana qoqarin barin wajen tace to ko uban waye shi sai na tashe shi inga uban dazeyi min tun safe nake jira anan amma kuma yazo yayi wucewar sa ya kwanta yakama bacci to wlh sai na tasheshi tana gama fadar haka tafara hawa saman benen da sauri yace ke kinsan waye kuwa kike wannan maganar kinaso kirasa ranki ko to wlh duk yanda kike daukan kanki yafiki iyawa ko kulashi batayi ba duk da tanajin maganar da yakeyi mata wacce bata kwanta mata kuma zata dawo kansa yanzu so take tagama da dayan ganin taqi sauraron sa yayi saurin binta abaya yana kiranta amma taqi tsayawa,
Furuq ma dake can yana hangosu baya jin maganar dasuke yi da yaga de kamar ba lafiya ba yasa shi tasowa shima yabi bayan su,
dadda natafiya dr.shettima yana binta yana kiranta amma taqi sauraron sa sai magiya yake mata faruq da take jin maganar da akeyiwa dadda amma taqi tsayawa da gudu yayi yashi gabanta yana cewa wai dadda meye hakan ana tayi miki magan amma kinki tsayawa kallonshi tayi tace kai ka matsamin ko inbi takan ka yace walh bazan barki kije ko ina ba daga nan wajen tace to ubana,
dr shettima yaqaraso kusa da su yace dan Allah kiyi hakuri wlh ze iya jiyowa kun tsaya abakin office dinshi dadda kallon office din tayi taji dadi kwa da yafada mata saboda daman tunanin da take kenan saboda batasan inane office din nashiba amma yanzu tunda yagaya mata magana ta qare gurin ta nufa tana qoqarin shiga faruq ya ruqeta yana cewa dadda kibar fa suna cikin cecekucen su tana sai tashiga sukuma suna hanata da bata hakuri, ahankali suka ga anfara bude qofar dr.shettima ne yafara cewa ai shikenan hankalin ki ya kwanta kin ta sheshi qarasa bude qofar akayi shine ya bude yafito daga ciki be kalli kowa ba ahankali ya bude bakinsa yafara magna yana cewa kasallame su sudau yarsu sukaita sukaita wani wajen bazan duba taba yana kaiwa nan yayi gaba be tsaya jin maganar kowa ba....
Tabbbb........
[22/12, 8:46 pm] #yaya Azeema#: 💅SARKI SAMEER....💅
. By
Yaya Azeema 😎
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
Bismillah......
55&56
""""""""""""""""""""""""""""""""""
'Dr.shettima ne yakalleta yace tode kinji abun da yace dan haka sai kisan yanda zakiyi hankakinki ya kwanta saida nagaya miki bakisan halinsaba shi ba irin kowane mutun bane shidan qaramin abuma maidashi babba yake gashi kinzo kina mishi ihu a qofar office har ya tasheshi daga bacci yafada ranshi babu dadi yana kaiwa nan yafara qoqarin barin wajen,
dadda tayi saurin dakatar dashi tace to naji yanzu saikaba shi hakuri yazo ya dubata bayan kunbata mana lokaci kuma ina kuke so mukaita idan kuma kashetan kukeso kuyi saikuyi ai ku da Allah tanafada hawaye na zubo mata faruq yace dadda koma me yafaru ke kikaja idan ma mutuwar tayi kece sila tunda ke bakyabin komai ahankali duk maganar da tazo bakinki fada kike alahakin kuma ke kike neman taimakon yanzu wa gari ya waya mutumin nanfa daga wata qasar yadawo yau koma ince yanzu amma yafara zuwa nan saboda ya dubata din amma ke kuma kinzo kinayiwa mutane abun da bedace ba ni wlh tafita ma zanyi inkinga dama kizo mutafi in kuma baki ga damaba sai kikwana anan ni kinga tafiyata yafada yana bi tagefenta yayi tafiyar sa,
Dadda wani kukan ta qara saki sannan tajuya takalli dr.shettima da shima yake qoqarin barin wajen saitayi saurin riqe hannun sa tace dan Allah yaro kataimaka min wlh bazan qara cewa komai ba amma kabashi hakuri yazo ya dubata janye hannunta yayi daga nashi yace ni ba abun da zan iya yi miki lokacin da nake qoqarin ganar dake ai ƙin saurarata kikayi kuma shi in yafadi magana baya canzawa ya fadeta kenan dan haka ba abun da zan iyayi miki yana kaiwa nan yabar wajen shima,
Zama tayi awajen dirshen tafara kuka kamar wata qaramar yarinya sai yanzu take tunanin to yanzu insun dauketa ina zasukaita kuma kowa ma bazeji dadin abun da tayiba nan ma wani tunani yafado mata idan sukace ba ruwansu suma to ina zata samu kudin da zatakai ta wani asibitin kuma tasan kudin da za akarba ba qaramin kudi bane itade tayi da nasani dama batazo ba da tasan haka abun zefaru da qyar ta iya lallabawa ta miqe tana share hawayen ta yayin fa tafara tafiya tana saukowa downstairs tana gama fitowa taga bakowa agurin tana tunanin ina kuma zata nufa gashi dan albarka ma yatafi yabarta ga bata fito da kudi ba bare ta hau motar haya ta koma gida guri ta samu kawai ta zauna...
'Dr.shettima yana fitowa waje yayo yana duba inda zega sam amma beganshi ba waya yazaro yakirashi nanma beyi picking ba saida yakira yafi sau goma sha amma be daga ba hakan yasa ya hakura yana tunanin ina kuma ya shiga dan yasande ba gida yatafi ba tunda ga motar da ya dauko shi agurin kuna yasan baze taba hawa motar haya ba dole yana cikin hospital din amma besan inda yayi ba komawa ciki yayi yafara nemanshi amma beganshi ba hakan yasashi komawa ciki office dinsa ya koma yana qara gwada kiranshi amma still de bedauka ba hakaura yayi sai yatura mishi text har ya ajiye wayar sai kuna kira yashigo da sauri yadauki wayar dan azatonahi shine yakira shi dan ko duba suna beyiba yadaga tare da kara wayar akunne shi saidai kash bashi bane muryar saleem ne ta daki kunneshi lokacin da yace hello salamualakum aba yandan zeyi ya amsa masa daga can saleem yace tundazu nake nemanka banganka ba nazo har office bansame ka ba shikuma yabashi amsa dacewa ok yanzu ai ina office zaka iya zuwa daga can yace ok gani nan sannan ya kashe wayar ajiye wayar yayi yana jiran ko Sam zeyimishi reply amma shiru har yanzu,
'Faruq na fitowa kwa dagaske gida yatafi yana zuwa yatarar ba kowa afalo upstairs ya haura inda dakin Ammi yake yana zuwa yayi nocking aka bashi iznin shiga yana zuwa yaganta kwance kan gado ganinshi yasata tashi zaune tana jiran qarasowar sa yana qarasowa yasamu gefenta ya zauna batare da yace da ita komai ba kallon shi tayi tace ya akaine naganka haka me yafaru doctor din yazo ne naga kundawo kai ya girgiza mata cike da taqaicin abun da dadda tayi yace inafa Ammi waccen matar wallahi tana da matsala kamar me aljannu nifa ina tunanin wasu abubuwan da takeyi ba itakadai bace,
tace waccen matar kake nufi kuma yace wace kwa inba dadda ba taje tajawao ma kanta ruwan dafa kanta doctor din da zeyi mata aikin yace baze yiba mudauke ta mukaita wani wajen da sauri Ammi tace ya salam me taje tayi ina lillahi me yafaru yanzu tana ina yace na baro ta acan tace kamar ya nande y kwashe duk abun da yafaru yagaya mata aikwa itama bata ji dadin abun da tayi din ba tace amma yazamuyi dole muyi hakuri da ita watakil gigin tsufane yake sata yin wasu abubuwan amma inbanda halinta tunda ance za ayi ai kamata yayi ma kudawo gida nidaman tunfarko banso tafiyar nan ba dande ta dage akan sai taje din tace yanzu to da kataho meye abunyi kasan de ai dole akoma wake ta yanzu Allah ne kadai yasan me takeyi acan din katashi kaje ka duba idan Aliyu be fita ba ka kira min shi yazo muje can din muji yanda ake ciki inkwa sukace saide mudauketa to wallahi zamu sha wahala kafin musamu wani ba fata bama watakil kafin ma munemo inda zamu kaitan rai yayi halinsa tunda ba na'u'rorin ajikinta taqarasa maganar cike da rashin dadi miqewa yayi yace in Allah ya yarda ma zasuyi mata bari inje inkira shi din tace to Allah ya yarda bari inshirya kafin ya fito tafada tana tashi tsaye itama, shi yafita ita kuma ta nufi toilet,
yana fitowa kwa suka hadu da bossay yafito yana shirin fita daga falon faruq yadakatar dashi yace yaya Ammi nakiran ka tsayawa yayi tare da juyowa yace har kundawo kenan ai gurinku naked shirin zuwa ya kukayi da su baka kira kace mana komai ba da gyara tsayiwa yayi yace yaya wallahi maysala akasamu dan yanzu halin da ake ciki ma sunce bazasu dabata mudauketa da kallon mamaki yake binshi sannan yace meyasa yanda yayiwa Ammi baya ni shima haka yabashi labarin duk abun da ya faru dafe kai bossay yayi yace OMG wannan wannan matar akwai bada matsala wlh anya kwabata da tabin kwakwalwa abun da takeyi tafara yin yawa mtsww yaja tsaki tare da dawowa ya nufi dakin Ammin tasu shima faruq din bayanshi yabi suka shiga dakin atare dauke da sallama abakinsu Ammi ta amsa musu lokacin har tagama shiryawa tana ganinsu tace Aliyu kaji abunda matar nan ta jawo mana ko yace wlh yanzu faruq yake gaya min matar nan bata kyautawa kanta duk qoqarin da akeyi akanta bata gani danasan haka take ni da banfara