Showing 132001 words to 135000 words out of 136570 words
zata iya mutuwa yau ko gobe akoda yaushe ma zata iya rasa ranta dan haka inrabu da ita tun wuri kar nasake nace zan taimaka musu inrabu dasu a yanda nagansu nikuma sai nace masa gaskiya abun da bazeyiyu ba kenan saide dan nariga da nayi niyya kuma bazan iya fasawa va sai yace to shikenan inje inyi duk abun da nashirya din sukuma zanji nasu shirin saide kuma ga wata hanya mafi sauqi zasu bani duk abun da nake so duk adadin kudin danake so zasu bani abu daya zanyi musu zuwa uku idan nai hakan zansamu kudi kuma zasu rabu dani lafiya baza sutaba lafiyata ba in bahaka ba kuma bani kadai bama dangina ma sunshiga uku jin hakan yasa na tsorata sai nace musu nayarda wani abu suke buqata sai mutumin yace nafarko suna so idan na dauki yarinyar duk wani motsin ta irin ga gaya musu na biyu kuma koda yaushe zasu iya bukatar in kaimusu Ameesha gurin su sannan kuma idinga nuna mata so sosai innuna mata kaf duniya ba wacce nakeso irin ta saboda ta yarda dani sosai yanda kowa ze sheda hakan saboda koda anrasa ta ba wanda zeyi zargin ni nakaita saide kawai ace ta bata daga nan kuma kowama yamanta da ita sannan ba ruwana da me zasuyi mata na qarshe kama akwai wasu takaddu dasuke bukata agurin dadda suna so in lalabo inda suke suma inkai musu idan nayi musu haka to nagama yi musu komai kuma zasu rabu dani da dangina bawanda wani abun da zesamu daya daga cikin mu idan kuma nace zangaya wa wani to gabadaya dangina sai sun rasa rayuwar sa ko iyayena kar na kuskura nagaya musu wannan zancen inbarsa da nan kuma suna kula da ni idon su yana kaina koda wasa nayi wani kuskure to zasu aiwatar da abun da suka gayamin ba yanda na dole na amince musu alokacin saboda kubutar damu gaba daya saida yaqara jaddada min da zamin kunne akan kar inbari kowa yasan wannan zancen amma ni wallahi bawai na amince dan son rainaba kokuma dan inaso har cikin raina ba tsorone yasa ni amincewa kuma atake a lokacin ya karbi account number dita da kuma phone number na amma shi beban tashiba danace yaban sai yace baya bada number duk lokacin da ze kirani ze kirani da private number alokacin yasakamin 2.5 million aciki yace min wannan somin tabine idan nayi musu aiki yanda yakamata zasu bani ninkin baninkin din su kudi sai nace nagaji dasu kuma dangina bazasu qara yin talauci ba daganan har qarshen rayuwar mu sai lokacin na tsorata dasu sai naji dama nace ban aminceba tun farko bansan ta yanda yagane tunanin me nake yi ba kawai sai naji yace qaddara ta riga fata kar ka canza tunani ka riga ka amince kuma dole kayi ko kana so ko baka so in ba haka ba kuma hmmm a tsorace nace dashi ni nafasa zuwa ma dauko sun daga yau bazan qara zuwa inda suke ba sai yace dole inyi mun riga da mungama magana saboda yace min wai dadda taurin kaine da ita bata yarda ta zauna da kowa ba amma tunda sunga ta yarda damu to dole ta Han ya ta zasu qarasa aikin su da suke so nace masa dan Allah yagaya min me suka aikata masa kuma waye shi sai kawai yace min na kusan kusanka nan da wasu watanni wanda zezamo jigun rayuwar ka zamu kulla alaqa tajini kasanni kuma kasan waye ni nima kuma nasanka nasan waye kai dan haka kar ka wahalar da kanka akan gano koni waye dan zaka jefa rayuwar ka cikin garari shawarar da zan baka ka ajiye tunani akaina kayi abun da nasaka kawai kuma daga yau aikin ka zefara ka kula sosai ina tare dakai jin akoda yaushe hakan yasa naqara tsorata da lamarin sa wani kwarin gwiwa ne yazo min a lokacin zuciyata tabani kawai injanye abun dake fuskar sa dan ganin kowaye tunda yace nasanshi besan lokacin da nakai hannu na ba kan fuskar sa har na fara cire wa amma bangani ba atakaicede sai farkawa nayi naganni agadon asibiti bansan ma wa ya maida ni gida ba aranar shine lokacin da na tambayi Ammi tace in bari zata gaya min kuma haryanzu bata gaya min ba to kunde ji abun da yafaru iyakar gaskiyar abun da nasani kenan.....,
**********************
*Azeema*
yaya dan Allah kajirani mutafi tare kasande inason idan ta farka mu fara haduwa da ita amma tunjiya nace maka zanje kahanani kuma yau ma kace bazan jeba nide dan Allah ka yarda mutafi tunda mama tace bazan qara fita nikadai ba da sai inje kone kadai ce inma tafiyar ce dani baka sonyi kaji yayana nakaina Allah ya barmin kai,
tana sane take tayi masa haka saboda yaqi kulata tunjiya da tayi masa wannan abun wai shi adole fushi yake da ita shiyasa ma yayi mata haka na hanata zuwa gurin Ameesha yasan ta hakanne kawai ze iya hukun tata taji haushi,
cigaba tayi da takura masa har da ruqe qafar sa daman tana zaune akusa da qafar sa girgiza qafar sa tayi tana kwakwalo kukan muna furci dan hawayen ma yaki fitowa sai faman makyar makyar da ido take amma sunqi fitowa,
saleem dake gefen mama yana karyawa yace mama ki mata magana nace bazata ba kuma tana tafaman damuna wai danma kinci sa'a bantaba kiba ko yafada yana ture ta daga kusa dashi,
mama ce ta kalleta tace ke bakyajin magana ko tashi daga nan kibawa mutane waje cinki qunar rai ta tashi tana turo baki gaba zata wuce dakin ta sai aka kwankwansa qofar gidan nasu hartakai bakin qofa mama tace zo kibude gida ana kwankwasawa batare da ta amasaba ta juyo bata kalli kowaba ta wuce waje dan budewa me kwankwansawar tana zuwa kafin ta bude tace waye daga can taji muryar na miji yace nine dan daidai ta nutsuwar ta tayi sannan ta bude gidan binsa tayi da kallo saboda batasan shiba dan murmushi yasakar mata sannan yace sannu yarinya da fatan nasame ku lafiya tace lfy kawai, tana jiran qarin bayani ganin yayi shiru tace kayi shiru ko wani kake nema yace eh inason kimin sallama da mahaifiyar ki idan tana ciki tace eh tana ciki amma duk abun da zaka gaya mata nima zaka iya gayamin dan haka fadi maganr ka kanka tsaye kamar kana tsaye da itane nida ita duk daya muke bazato ba tsammani taji rankwashi a tsakiyar kanta juyawa tayi tana kallon saleem tace kai yaya me kuma nayi maka ni wai duk kabi ka tsaneni bansan me nayi maka ba kuma harar ta yayi yace dalla matsa nidaman nasan da abun da ya tsayar dake daga bude gida zaki zauna kina masa surutun banza ko sa'ankime da zaki gaya masa haka dan hade rai tayi sannan tace a'a kayi hakuri tana gama fada ta koma cikin gidan tana ta faman kunbura fuska,
Saleem ne ya gaida mutumin yace dan Allah kayi hakuri tazo tana yimaka shirme mutumin yayi murmushi yace ai yarinyace ba komai wallahi bata bata min ba, tunda gakama daman aikoni akai amma indamuwa inaso ka fara sanar da mahaigiyar ku sai mutattauna saleem yace ok ai ba damuwa shigo kawai muje yace a'a shigade kafara sanar da ita yace to shikenan bari inje yana kaiwa nan ya juya yaje ya sanar da mama tare suka fito tana sanye da hijab dinta har qasa tunda tafito take bin mutumin da kallo tanaso ta gano ko tasanshi amma taga batasan shiba ta danyi mamakin jin yana neman ta din alahalin bata sanshi ba fuskar ta ba yabo ba fallasa ba fusss ba asss suka gaisa sannan yace inba damuwa zam iya zama da zuciya daya ta karbe shi dan haka sai tace eh bismillah mushi ga daga ciki atare suka qara komawa cikin falon lokacin Azeema ta samu guri ta zauna tana jiran shigowar su,
Dylan su zama sukayi tare da zubawa wannan bawan Allahn da basu san daga ina yazo ba mama da ta qagara da taji maganar da takawo shi tace bawan Allah muna sauraron ka ka barmu a duhu dan qayataccen murmushi yayi sanna yace yanzu kuwa zakuji abun da yake tafe dani tace to munajin ka saida ya gyara zama sannan yace abun da ya kawo ni wajen ku daman shine an aikoni ne dan inzo in sanar daku halin da mahaifin ku yake yana nan da ransa da lafiyar sa gaba dayan su suka miqe tsaye atare dan yanda maganar ta dake su bazato ba tsammani maganar kamar a mafarki........✍
[29/12, 12:51 pm] #yaya Azeema#: 💅SARKI SAMEER....💅
By
Yaya Azeema 😎
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
Bismillah........
89&90
""""""""""""""""""""""""""""""""
____________*Azeema*
Azeema ce data rigasu dawo cikin hayyacin ta da sauri tazo gabansa tace dan Allah da gaske kake bawan Allah ba marki nake ba kamar yanda nasaba dan murmushi yayi yace bawani mafarki 'yarnan maganar da kikaji gaskiya ne yana ina dan Allah me yasameshi me yasa yaqi dawowa wajen mu meyasa ya tafi yabarmu duk tabi ta rude hawaye har sun fara wanke mata fuska mama ce tazo takamata ta zauanar da ita kusa da ita sannan tace bawan Allah munajin ka saida ya kuma gyara zama sannan yadan numfasa sannan yace me gidanki yana gidan sarki da mamaki suka maimaita gidan sarki to me yakaishi gidan sarki nasan zakuyi mamaki ko to nide abun da aka ce nasanar daku shine ku kwantar da hankali ku babu abubun da ze sameshi saide wani hanazari ba gudu ba a kwai babbar matsala dan baze yiyu kugansa ba ko yagan ku saboda inda yake din ko da wasa yayi qoqarin fitowa zasu iya kashe shi saboda basu da imani muta nen nan saide kawai kuyi hakuri kucigaba da addu'a har lokacin da Allah zesa yafito inkuka maida komai ga Allah sai kuga ya kawo muku mafita ta cikin sanyi saboda sun riqeshi yazama bawan su agidan kuma in kunga fitowarsa to saide a fito da gawar sa saboda inde suka maida kai bawa to babu shaka kazama nasu har abada nima yanzu fa kyar aka sanar dani inzo in sanar daku saboda ku dan samu kwanciyar hankali kudena wahalar neman sa tunda yace yaji lokacin ma da kuka bada cigiyar sa dan haka kutaya shi da addu'a dukan su babu wanda be zubda kwalla ba jin halin da mahaifin su ya koma saleem ne yayi qarfin halin tambayar sa dan Allah bawan Allah me yayi sukai mishi haka mutumin yace nima wlh bansani ba nide iya abun da aka gaya min kenan yace to waye ya aiko ka yace wani dan gidan ne shima bawane shine yasamu damar fitowa daman kuma nasan shi tunkan ya shiga gidan amatsayin bawa to shine yake sanar dani dan Allah inzo insanar daku shima kuma mahaifin nakune yace yazo ya fada asan inda yake amma ni baya ga haka bansan komai ba game da shi dan ko kamannin sama bansaniba mama ce tace Alahamdulillah Alahamdulillah hakan munji dadi sosai da jin baya nin ka mungode Allah ya saka maka da alkhairi yanzu hankalin mu zefi kwanciya dan akullin da kalar yunanin da mukeyi akan sa dan har muna tunanin ma ko ya mutu me ashe da ransa kuma in Allah ya yarda ze dawo gare mu mama bata gama rufe baki ba Azeema tayi caraf tare da miqewa tsaye tace in sha Allah mama sanin inda baba yake daidai yake da dawowar sa garemu ni da kaina zanje har cikin gidan kuma zan dawo dashi da yardar Allah dukan su zuba mata ido sukayi mutuminne yace a'a yarinya karkiyi haka kibari kar kishiga gidan nan saboda inde kika shiga to banajin kema zaki fito da lafiyar ki bayama in akasan me yakawo ki dan Allah nide shawarata agare ku itace kuci gaba da addu'a kawai saboda itace zata magan ce muku komai Allah ze kawo muku mafita amma ina ganin tunkarar cikin masarautar nan da daya daga cikin zeyi inaganin kamar zaku kuma jefa kanku cikin wani halin,
saleem yace gaskiya ne maganar ka gaskiya ce zamu ci gaba da addu'ar in Allah ya yarda kuma munsan Allah yana tare damu zai amsana mungode sosai da sosai sannan dan Allah idan kaje kagayawa wanda ya aiko ka kace mungode masa sannan yagayawa baba muna gaidashi kuma ya kwantar da hankalin sa muna cikin qoshin lafiya nama samu aiki kuma muna nan muna masa addu'a sannan kaima Allah yabika da mafificin alkhari Mutumin ya amsa da Ameen daga nan ya miqe tare da dan kallon Azeema yace jaruma ayi hakuri naga kin fusata da yawa ki kwantar da hankalin ki babu abun da ze samu mahaifinku matsalar de kawai itace da baze dawo wajen ku ta cikin sauqi saide addu'a dan kai ta daga masa kawai amma bawai tana jin zata hakura da zuwa ba kawai zata rabu dashi ne azin ta hakura din,
sallama yayi musu suka qarayi masa godiya sannan ya tafi zama sukayi gaba dayan su tsawon 'yan mintina ba wanda ya iya yin magana acikin su kowa da abun da yake saqawa,
Azeema ce ta katse shirun nasu da cewa mama yanzu kuna ganin hakan zamuyi mu zuba ido munazaman jiran dawowar sa alhalin bamusan lokacin dawowar sa ba kuma munsan inda yake nide gaskiya ina ganin gwara kawai inje din ko ya kuka gani mamace ta dan numfasa kana tace ke baki ji me yace bane mazama ya suka qare idan sun shiga bare kuma ke mace ina ganin kawai muci gaba da addu'a kamar yanda yace din ai ba abun da yafi qarfin Allah idan su sunfi qarfin shi suna takama da mulkin su ai Allah yafisu tunda shi yabasu kuma ze iya kwacewa dan haka kawai mucigaba da addu'a ta qarasa fada fuskarta ciki da damuwa,
saleem ne yace mama gaskiya be kamata ba mu tsaya zaman jira yanda auta tace ina ganin hakan shine kawai mafita ita macece zata iya shiga gidan batare da kowa yagane da wata manufa tazo ba inaganin kawai mushiryata taje ta gano mana shi inda yiyuwa ma zata iya fito dashi din koda za adau lokaci kuma zata tafi da waya duk halin da ake ciki sai ta ringa sanar damu in Allah ya yarda ba abun da zai sameta sai alkhairi kuma in Allah ya yarda zamuyi nasara akai mama tadan numfasa sannan tace to ni baqin yarda bane banayi ina guje mana abun da kanje yadawo kar muje ganin naiman gira arasa ido hakan yazo yazame mana wata masifar tundade kunji abun da mutumin nan yafada kuma yafimu sanin masarautar tunda kukaji ya hana kowannen mu zuwa to yasan masarautar tana da hatsari dan haka mubar komai agurin Allah,
Azeema tace mama dan Allah kar ki hanani in Allah ya yarda ba abun da zai farau kawai mude amincewar ki muke bukata danni a yanzu ma ashirye nake da tafiya dan ganin nagana da mahaifina ina so inganshi kuma koda bansamu gurin zama ba agidan ai zanganshi kuma lokaci zuwa lokaci zan ringa zuwa gidan daga haka har nasaba amma dan Allah mama kar ki hanani kinji mama mama shiru tayi bata ce komai ba shima saleem baki ya shiga bata suna tabata hakuri da roqon ta yarda ta amimce da zuwan nata,
bayanda ta iya dole suka shawo kanta ta yarda ta amimce saboda itama tanaso taji ahalin da yake da kuma wane irin aiki yake musu Allah yasade ba me wahala bane,
sunji dadin amincewar tata sosai Azeema harsa dan taka rawar jin dadi bayan tagama ta zauna kusa da yayan nata tace yaya to ya kake gani taya zan shiga gidan mama tace kingani ai shiga gidan ma madai wata matsalar ce tundade gidan sarauta ne dan haka ko ina za asa masu tsaro kuma suna ganinki dole sai sunsan daga inda kike da abun da gakawo insun tambayeki me zaki ce musu saleem ne ya gyara zaman sa yace hakan ba me wahal bane mama sannan ya maida dunbasa ga Azeema yace auta kinsa taya zaki shiga tace karkada masa kai tare da cewa a'a yaya cigaba yayi da cewa zakije qofar masarautar ne ki tsaya azin me neman alfarma dan kayan jikin kima sai kin canza ki samu tsofaffi sosai kisaka sannn kiyi kalar tausayi kar kibari wani me tsaron yaganki ko dan aikin gidan kibar har sai kinga wanda yayi kama da dan gidan wanda kina ganinsa kinsan daga ciki yake inda so samune ma kisamu mace mace sai tafi tausayin ki akan namiji idan kuma baki samu macen ba ki gwada yiwa namijin magana inbaki dace akansa zaki dace akan wani kingane me naked nufi tace eh yaya nagane kuma zanyi qoqarin yin hakan in Allah ya yarda shiga gidan kamar anyi angama ne mama de najin su har suka gama shirye shiryen su bata saka musu baki kawaide tana addu'a aranta Allah yasa adace batare da wata matsalar ta qara faruwa ba miqewa Azeema tayi tace bari inje inshirya yaya kallon ta mama tayi tace ke baki da hankali ya za ayi kije daga gama magana saurin me kike kibari sai gobe ko jibi ma ba sai a shirya komai a tsanake ba ki fita da sassafe tace mama yanzu ma ai rana batayi ba zan iya zuwa wlh ko yaya tafada tana kallonsa kai yadaga mata sannan yace hakane ai gwara ayi komai da wuri mama tace Allah ba inda zata yau sai gobe in kuma kuka takuramin a fasa zuwan ma gaba daya da sauri Azeema tace a'a mama baza ai haka ba na hakura zuwa goben wallahi naso zuwa yau din amma tunda baki amince ba to na hakura nabarwa goben mama tace karma ki yarda din ina ruwana saleem yace ti shikenan Allah ya kaimu