Showing 33001 words to 36000 words out of 104242 words

Chapter 12 - SIYASA KO KABILANCI COMPLETE HAUSA NOVEL

04 Oct 2024

16053

sai yanzu katashine kokuwa?".
Nazeefa tayi saurin " fad'in ALLAH Yaya sai yanzunne yatashi, da asuba babu irin bugun da ya Jabeer bai masaba amma yak'i bud'ewa, hakama innani".
Harararta Shehu yayi, amma baice komaiba.
Cikin matuk'ar 6acin rai Uncle M.A yace, "wai Shehu mikakeso kazamane kaikuwa? Wannan wace irin rayuwace kaza6ama kanka? gwargwadon iko kowa k'ok'ari yake dakai agidannan kan kazama mutumin kirki, amma gakanan tamkar wanda bakin iyaye ke d'auniya dashi? yanzufa ka kalli agogo kusan 7:30 amma bakayi sallar asubahiba, amatsayinka na matashi mai lafiya, ko baba dake kwance yana jiyya kullum saiyabi jam'i a gida, kaje kayi tayi wlhy, rayuwarkace, idan ka gyara kaine zaka anfana, idan kabari ta lalace asararkace, shekarar k'arshe kake a makaranta amma yanzu haka yau kunada exam, kana kwance kana barci k'ilama ko karatu bakayiba?".
" Yaya nafayi, dad'ewama danayi ina karatunne yajamin makara.....
"Rufema mutane baki kafin na sa6a maka kammanni wlhy, ina k'ofar gidan su Rabi'u kazo ka wuce kaida abokanka kunata warin sigari, nasan baka ganniba ai, kuma koda na dawo gida kwance na iskeka kana barci zakace wani karatu kayi. walhy Yaya idan yaronan bai tsallakeba wannan karon karka kuma 6ata kud'inka akansa, banza kawai Mara amfani wa kansa bare waninsa".
Jabeer ne mai maganar cikin k'unar rai da bak'incikin halin d'an uwan nasu daya biyema abokan banza suna shashanci.
"Abinda dama na yanke kenan Jabeer, ka duba shekarun da yaronnan ya d'auka a makaranta, tunfa Nazeefa na ss2 a secondary, gashi harzata kammala degree d'inta tareda dashi, k'ilama takuma barinsa....
''Dan ALLAH Yaya karkace haka, insha ALLAHU zan dage nabar jami'a wannan year d'in, kodan naga kunyi farinciki, kuyi hak'uri Dan ALLAH, kucigaba damin addu'a".
ALLAH sarki, d'an uwa rabin jiki, sai kuma tausayinsa ya kamasu, a raunane Nazeefa tace,
" please ya Shehu ka canja mana, kodan k'ok'ari da Yaya Muhammad keyi a kanmu kullum shida ya Jabeer, ga halin da baba yake ciki, ALLAH abinda kakeyin nan yana k'ara saka damuwa a ciwon baba, kai abin baya damunka ne?".
''Ya za ayi ya damesa Nazeefa? tunda duniya da abokan banza na kaimasa yanda yake buk'ata, ALLAH ya shiryeka Shehu, kawuce kaje kai Salla rana na kumayi, ni bara na wuce kasuwa".
"Yaya nagama karin kumallo fa, kazauna kaci dan naga yanda kafito da safen nan dawuya idan kayi a gida".
"No auta, karki damu, ina saurine yau kayanmu suka iso, gashi zanje office yau, inada meeting da lecturers".
Bai jira cewartaba yabama Jabeer hannu sukayi musabaha ya fice.
Dariya Jabeer yayi yace, " auta kema kinsan Yaya da abinci aii, nidai bani nawa na d'ora natai aiki".
Itama dariyar tayi kawai tanufi ketchin.
Abincin kowa ta zuba takaikai musu, sannan ta d'auki nasu itada Amatallah.

Baba da innani duk sunajin abinda ke faruwa a tsakanin 'ya'yan nasu. hakama Amatallah tana jiyosu, sai hakan yasata kewar families d'inta, dajin sha'awar inama tanada k'anne ko yayye itama, ko babu komai ai zasu tattauna akan matsalolinsu suji sanyi, wannan tunanin ne yasata kuka sosai. motsin shigowar Nazeefa yasata saurin share hawayen tacigaba da shinfid'a bedsheet a kan katifar.

"Anty Nazeefa kin ganni har yau ban gama gyaran d'akinba".
Dariya Nazeefa tayi tana ajiye tiren hannunta, "inafa za'a gama mana gyaran d'aki, kunyi bulum keda Yaya a d'aki kamar bakwa gidan kunata shan soyayya".
Cikin zaro ido waje Amatallah tace, " kai Anty Nazeefa, soyayya kuma? Uncle nefa". 'tak'are maganar kamar zatayi kuka'.
Sosai Nazeefa take dariya, "yo Amatallah ai yanzun yatashi daga Uncle, yakoma miji, ba laifi bane idan anyi soyayyar. Kinsan kuwa bala'in dacewar da kukayi keda ya Muhammad? wlhy karki bari damarnan ta ku6ce miki, ya Muhammad garas yake tamkar wani d'an 30years, yandama yakeda k'aramin jikinnan wasu d'auka suke ma Anty maijidda ce babba, kofa ya Jabeer yafishi jiki. wama zaice ya Muhammad yanada mata biyu, koda yake uku fa yanzun". ta d'agama Amatallah gira.
Baki Amatallah ta tura gaba, " Anty Nazeefa kibari Dan ALLAH, nifa ALLAH Uncle d'inane" ta matso hawen dasuka taru mata a ido tunda Nazeefa tafara maganar.
Kusada ita Nazeefa ta zauna, ta dafa kafad'arta, "kiyi hak'uri Amatallah, nasan anan gaba kad'an zakiso ya Muhammad amatsayin miji ba Uncle kad'aiba. na tabbata saiya nuna miki soyayya maiban mamaki, dan soyayyar dayakema Yaya Isma'il duk zai tattara yahad'a da wadda yake miki, ya Muhammad yanama ya Isma'il k'auna maiban mamaki, to yakike zaton kuma kasancewarki matarsa jinin masoyinsa ya Isma'il?, gakuma ke kanki dama yanda yake sonki sosai tamkar 'ya'yansa. lokaci kawai muke jira na ganin hankalinku ya kwanta dagake harshi, dan har yanzu duk kuna cikin rud'anine na abubuwan dasuka faru, amma nabaku shekara d'aya zuwa biyu kacal, insha ALLAH sai kunzama abin kwatance a duniyar masoya. Ke dai kawai ki koyi yanda zaki zauna da matansa, dan gidan ya Muhammad zama akeyi namasu ilimi da kissa, kowacce jitake da kanta akan tayi karatu mai zurfi, saiki dage sosai akan karatunki, tunda inada tabbacin yaya bazai barkiba kema, zai maidaki makaranta, fatana dai kirage wannan sanyin naki, dan zama dasu Anty Aneesa sai jaruma, kuma mai wayo. Zan cigaba da baki haske a zaman mu, yanda kema zaki kwaci 'yancinki a hannun mijinki, harma kizama tauraruwa fiyeda kowa a zuciyarsa kinji".
Kai kawai Amatallah ta jinjina mata, tasaka hannunta biyu ta share hawayenta, sai dai k'asan zuciyarta tana tunanin yanda za'ayi ta zauna da Uncle d'in nata a matsayin miji, bayan zuciyarta tana girmamashi tamkar mahaifinta, tabbas maganar Anty Nazeefa gaskiyace, babu wanda zai kalli Uncle yace yakai shekarunsa, saboda k'aramin jiki da ALLAH yabasa, baza'a kirashi siririba, hakama bashida k'iba, sannan yana tsaka tsaki a tsawo, ba dogoba ba gajereba kuma........
Girgiza tan da Nazeefa tayi ne yasata sakin ajiyar zuciya.
Nazeefa tace, "kinga bar aikin mu karya tukunna ko".
" to".
Kawai Amatallah tace tamik'e, MacLean da brosh ta d'auka tafita.
Nazeefa tabita da kallo a sanyaye, tausayinta na kuma ratsata, a fili tace, "insha ALLAH zakiyi farin ciki a rayuwarki Khadija, nasan ya Muhammad zai kawo sauyi a duniyarki, ALLAH dai yak'ara baki hak'urin jurewa wannan jarabawa tarashin iyaye lokaci d'aya, kuma yakawo mana sauk'in rikice-rikicen dasuke sanadin wargaza farin cikinmu a k'asarnan. ALLAH ma yay miki gata ke, tunda yabarki da Ya Muhammad, a kwai yara irinki masu yawa dasuka shiga halin k'uncin rashin families d'insu ta sanadin irin wannan rikice-rikicen *SIYASA KO K'ABILANCIN*, amma rashin gata damasu tallafa rayuwar tasu yasasu shiga k'angin wahala da tarwatsewar rayuwar tasu suma, ALLAH ka kawomana iyakar wad'annan matsaloli dai."


Nace, "amin Nazeefa😭🙏🏻.



____________________________

Tunda yafita sai Aneesa tafad'a gadonsa ta hau rusa kuka, tabbas sunada aiki agabansu, yarinyarnan bama ganinta yakeba a shekarun baya yasuka k'are, kullum zancenta na bakinsa, inaga yanzu ta dawo kusa dashi, tana amsa sunan matarsa kuma.
Tunda k'addara ta dawo da Amatallah Kano basu sake samun kan mijin suba, motsi kad'an yana gidansu, dasunyi magana saiyace yaje duba jikin babane, insunyi k'orafi akan Amatallah yace basuda tausayi.
Tasan yarinyar nabata tausayi, amma gaskiya tana matuk'ar kishin mijinta, taso ace daga ita sai shi da 'ya'yansu zasu rayu, amma tunkamma tazo gidan saita taras wata tarigata shiga, maimakon abarta taji da zafi d'aya, gashi kuma rana tsaka ankuma aura masa wata, k'aramar yarinya ma, sa'ar k'anwarta ta biyu.
Dolene ta d'auki mataki wajen ninka soyayya da kulawar datakema mijinta fiyema data dacan, dan tafison yasota fiye da kowacce acikinsu. jibafa tunda tayi sallar asubahi taketa kaida kawo wajen ganin tahad'a masa break fast mai rai da lafiya, saboda ganin kwana biyu bayacin abinci sosai saboda damuwar dayake aciki tarashin amininsa. (Duk da dama shi bamai yawan cin abinci baneba) Amma dan wulak'anci shine yafice wai sauri yakeyi, yanzu haka kuma yanacan wajen bak'ar yarinyar can.
saita kuma rushewa da kuka kuma.


Nace, ''bantan uba, Aneesa kinada aiki wlhy🤣, zan bama Xoxo kwangilarki😜".


Ita kanta Fateema abin yabata mamaki, ganin yafita cikin fushi ko d'akinta bai kallaba, bayan kuma k'a idarsane duk Safiya zai shiga d'akin wadda ba itace da girkiba su gaisa, hakama idan yadawo aiki zai shigo miki, yaji ya lafiyarki keda yara, da darema kafin a kwanta zai shigo yamiki sai da safe yama yaransa addu'ar barci. Amma yau ko yaran bai sauraraba, saima k'arar bud'e gate da rufewa sukaji.
Cikin damuwa tagama musu shirin makaranta ta turasu wajen Aneesa suyi break fast, amma sai suka dawo suna sanar mata momyn batanan, kuma ko Saifudden ma ba'ama shirin school ba.
Tashi tayi tafito, ta lek'a 6angaren Aneesa batanan, har bedroom sai Siddiqa dake barci a kan gado, tad'anyi knocking k'ofar toilet amma shiru, saifudden ne kawai kwance afalo lullu6e da towel, da alama wanka aka masa ba'akai ga shiryashiba ma, dan ga uniform d'insa nan a gefensa da manshafawa da turare.
Kallon Sahib tayi tace, "Sahib jeka saman Abbu kagani kotanacan tana sharane".
" to Umma". Sahib yafad'a yana fita da gudu.
Babu dad'ewa ya dawo yafad'a mata tana d'akin Abbu tana barci.
"Barci kuma? lafiya kuwa?".
fita tayi tana fad'in " Abulkhairi tada Saifudden ka shiryashi ina zuwa".

Sai da tayi sallama kusan sau uku sannan Aneesa ta amsa.
Fateema tashigo d'akin idonta akan Aneesar.
"Momyn yara lafiya kuwa?".
Tashi Aneesa tayi zaune, tayi kwafa sannan tafad'ama Fateema abinda yafaru, dan aganinta wannan matsalace dazasu raba tare sukuma d'auki mataki akanta.
Fateema tace, " Humm momyn yara kenan, nimafa haka yaymin ranar da yarinyarnan ta farfad'o, gaya mikine kawai banyiba".
Aneesa takuma yin kwafa, tace,
"Wana mataki kike ganin zamu d'auka? inba hakaba yarinyarnan saitama kiremu daga kan 'yayanmu wataran, dan naga rawar jikin dayake akanta tayi yawa tunkanma tashigo gidan, raina mana hankali kawai akayi, za'ace wani babanta yarok'eshi ya aureta, wlhy dama can son yarinyarnan yakeyi, shima Baban nata ya gane hakanne shiyyasa ya k'ak'aba masa. nifa har mamakin yanda babanku yayarda yama Muhammad wakilcin auren nakeyi, bayan kuma yasan keza'ama kishiya".
Duk da maganar Aneesa ta k'arshe ta 6atama Fateema rai haka ta danne saboda kishi na cinta itama, tace, "miye shawararki to akai? Nasan dai Muhammad bazai ta6a sakin Amatallah ba, kodan k'aunar mahaifinta dayakeyi".
''Yo idan shi bazai iya sakintaba, ai ita saimu sata masa bore tace bata sonsa, ai dole dai ya barta ko".
" hakane, amma tayaya zamuyi hakan?".
''Muyi tunani na kwana uku, abinda kowa ya yanke saimu tattauna yiwuwarsa mugani kawai, koya kikace?".
"Hakan yayi d'in, yara sun shirya, ke suke jira karsu makara".
Mik'ewa Aneesa tayi suka sakko k'asa tare, a gaggauce suka bama yara break fast dan mai keke napep d'in dake kaisu makaranta yazo................✍🏻


Nace, " humm, wai Fateema da Aneesa ne yau a inuwa d'aya😂, lallai Amatallah da k'arfinta tashigo💪🏻🤣.



🤩👎🏻

Rashin comments d'inku kesani wannan laziness d'in, buk'atar typing d'ina kullum yana hannunku☹✋🏻, inkun gyaran nima zakuga sauyi a gareni🤷🏽‍♀😏.
🚶🏻‍♀





*_ALLAH ya jik'an iyayenmu😭🙏🏻_*
[1/16, 1:30 PM] Aysha Galadima: *_Typing✍🏻_*


*_HASKE WRITER'S ASSO..._*💡
_{home of expert and perfect writer's}_





*_SIYASA KO K'ABILANCI_* ⁉
_(Hattara matasa)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


____________________
*_Number 16_*
____________________

Da gudu ta wuce Furera matar kawunta yayan Ammi dake tsakar gida tana wanke-wanke.
"Ke Amatallah lafiya kuwa?". Anty Furera tafad'a a tsorace tana zare hannunta daga ruwan wanke-wanken, ganin tawuce d'aki itama tatashi da gudu ta shige inda Amatallah tashiga harda rufe k'ofar.🤣
Ganin haka da Sadiya tayi matar k'anin Ammi itama saita afka d'akinta ta banke k'ofa harda sakata.
Sufa duk zatonsu wasune suka biyo Amatallah d'in, gashi mazan gidan duk basanan sun fita.

Tashi Amatallah tayi daga kwanciyar datayi a gadon Anty Furera danjin tarufe k'ofa.
''Lah Anty Furera lafiya kuwa kika rufe k'ofar?".
" keza'a tambaya Amatallahi, miyafaru kika shigo gida da gudu haka?".
Sai yanzu Amatallah tatuna da yanda tashigo, dariya tashiga tuntsurama Anty Furera, dan ganin jikinta har rawa yake saboda tsoro.
Sai da Anty Furera tamata magana sanan ta tsagaita da dariyar datakeyi, "Anty Furera babu komaifa, wai da kina zaton minene?".
Ajiyar zuciya Anty Furera tasauke, " kai Amatallahi kin d'auki hak'ina wlhy, kinsan garinan ba lafiya yacikaba, har yanzu a d'ar-d'ar kowa yake, waya biyoki haka to?".
Guntuwar Dariya Amatallah tayi, ''kai Anty Furera haka kike da tsoro ashe?, babu komai wlhy, bud'e kiga wayarda Uncle ya siyamin".
Amatallah tayi maganar donson kauda tanbayar da Anty Furera kemata.
Bud'e d'akin tayi, sai lokacin itama Anty Sadiya tabud'e nata.
Fitowa tayi tana tambayarsu ko lafiya taga sun shiga d'aki?".
Labari Anty Furera tabata, Amatallah bata bari zancen yayi tsawoba tabasu kwalin wayar suka shiga kallo da yaba k'yanta.


***********

Uncle M.A kam haka yabar jos cikin farin ciki da kewar brother d'insa, dan baibar garinba sai da yabiya ta gidan su.
Komai ya k'one, da Alama ma ankuma sakama gidan wutane, dan randa abun yafaru gobarar bako ina ta cinye hakaba, amma yanzu harda gidajen makwaftansa, bayan kuma waccan ranar wutar bata ta6a kowanne gidaba, anguwarma gaba d'aya tayi kaca-kaca.
Mota yakoma yatafi kawai, wani 6angare na zuciyarsa na tuno masa abinda yafaru tsakaninsa da Amatallah, sai yakanyi murmushi, lokaci-lokaci kuma yakan kama d'an kwalinta dake kan cinyarsa ya shak'i k'amshin.
Haryaje Kano ribbon d'inta na a tsintsiyar hannunsa. sai da zai shiga gida yacire d'ankwalin yasaka ribbon d'in ciki ya nannad'e ya tura a aljihu.
Yau girkin Fateema ne, dan haka ita tabud'e masa gate. yauma kamar kullum a cikin kwalliya take, hakama yaransa suna gida saboda Alhamis ce babu islamiyya kuma ana hutun boko, itama Aneesa cikin kwalliyar tafito tamasa sannu da zuwa, suduka basusan ma inda yajeba.😜
Da taimakon Fateema yay wanka, sanan ta shirya masa abinci, bai ciba sai da suka dawo sallar Magrib shida yaransa.
Suna kammala cin abinci suka fita sallar isha'i, daga can gidan su yawuce da yaran gaba d'aya, suka gaida kakanninsu.
Sun dad'e agidan suna hira shida Jabeer da Shehu da Nazeefa, Rabin hirar duk akan tafiyarsace dakuma Amatallah, innani dai bata saka musu Baki sosai, amma tana saurarensu, baba kam tunima yayi barci, dan babu laifi jikinsa da sauk'i.
Basu koma gidaba sai da yaga plashing d'in Fateema, dole yatafi shi kad'ai yabar yaran nan, dan dare yayi, kuma duk sunyi barci, gashi a Napep sukazo ba motaba, shima mashin d'in Jabeer ya kar6a yatafi a kai.


___________________________

Gobene takama tafiyar Uncle, duk abinda yakamata ya kimtsa yayisa, abinda ya danganci gidansa dana mahaifansa duk yamik'ashi hannun Jabeer, hakama lamarin kasuwa, dukda akwai yara masu kulada shagunan, amma dole sai da mai kulawa lokaci-lokaci.
Abu d'ayane ke damunsa arai dabai samu koda kafa harsashin saba, yarasa wazai fara tunkara da batun? Dan bakowa baneba yakeda zuciyar irin wannan jihadin, musamman ma daya kasance abune da sai an ta6a aljihu.
Zuciyarsace tashiga bashi shawarar kiran Sabi'u m Ali. Wayarsa ya d'auka sai dai zuciyarsa na fad'a masa yakira ko karya kira, danya kai tsawon wata 10 rabosa da waya dashi, dama can yafisu k'ok'arin kira a waya dama zumincin dagashi har marigayi.
Shawara ya canja, yafara masa test massage. kusan mintuna 15 saiga kira yashigo. Wayar ya d'auka yana k'aramar dariya, Dan ganin Alhaji Sabi'u ne. Sai da ta tsinke sannan shi ya kira. Alhaji Sabi'u na d'agawa Uncle M.A yafara bashi hak'uri kawai.
Dariya Sabi'u yayi daga can yace, "ya zanyi daku, kai da Isma'il ko kad'an bakwason zuminci dani na lura".
" a'a wlhy, ba haka baneba, amma amana afuwa kanmu bisa wuya".
"Hhh shikenan ya wuce aii, ya gida ya iyali?".
" duk lafiya lau muke".
''To Alhmdllh".
Gyaran murya Uncle M.A yayi, sannan yace, "wlhy maganace a bakina, gashi kuma ban saniba ko kana kano?".
" eh ina Kano, ai munma dawo gaba d'aya, zirga-zirgan ta isheni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login