Showing 84001 words to 87000 words out of 104242 words
narke mata, " no my heartbeat karmu makara fa, idan nadawo naci abinci kawai....."
Bata bari ya k'arasaba ta tashi daga jikinsa tana tura baki gaba. Saurin rik'o hannunta yayi ya maidota baya yana fad'in sorry my beat karki fushi, haba Amintacciya 'ya daga ALLAH, banito nasha ko kad'anne".
Tad'an kalleshi tana turo baki gaba, a shagwa6e tace, "really?".
Gira ya d'aga mata kawai danya kasa magana.
hannunsa takamo suka fito galo, ta zaunar dashi a kujera sannan tad'iba furar a frighte d'insa tasaka suga kad'an ta motsa, kusadashi tadawo, (hummm) mai makon ta zauna gefensa saita zauna a cinyarsa tana kashe masa ido d'aya.
Wani lalataccen murmushi ya sakar mata, ya sak'alo hannunsa a k'ugunta, " my beat karfa kimin Squeezing da kaya nida zanje masallaci".
Kofin furar tasaka masa abaki tana 'Yar dariya. amma batace komaiba.
Haka taita basa furar saida ya shanye bai saniba, ta ajiye kofin a Center table tana fad'in Uncle kafa shanye tas".
Bakinta ya sumbata, "yazanyi tunda 'Yar shagwa6a ta turkeni".
" wato Uncle turkekama nayi ko? Shikenan munyima fad'a karka kumamin magana harka dawo masallaci ehe.
Da sauri yakamota yana dariya, ya manne bakinsa kan nata. (Hummm dagananfa.....babu ruwana🤭).
Da k'yar tasamu ya saketa yafice yana kashe mata ido d'aya da d'aga mata yatsun hannunsa biyu alamar bye bye.
Gira ta d'aga masa itama tamasa alamar I love you da hannunta.
Tsayawa yay cak yana kallonta, harya d'an juyo zai dawo takoma bedroom d'insa da gudu tarufo k'ofar, tasan inhar ya kamata bakinta saiyaci k'aniyarsa, gashi time d'in masallaci nakuma k'urewa.
Sauka yay yana murmushi, dakumajin k'aunar Amatallah dake Shiga jininsa da 6argo. har yanzu yaran Na falo inda yabarsu, Shiga yay 6angaren Fateema suka gaisa, sannan yashiga wajen Aneesa itama, dukda tanata shamasa k'amshi bai damuba danyasan laifinsa.
Yana masallaci amma dukkan tunaninsa naga Amatallah, burinsa kawai a idar Yakoma gareta............✍🏻
_Ama.... kina zamani, walla banga laifinkiba,😉 murd'a kanbunki dak'yau karki saka wasa🤸🏻♀😻🤸🏻♀._
🤩👎🏻
One Luv my sweet fan's
*_ALLAH ka gafartama iyayenmj🙏🏻😭_*
[1/19, 10:20 PM] Aysha Galadima: *_Typing✍🏻_*
*_HASKE WRITER'S ASSO..._*💡
_{home of expert and perfect writer's}_
*_SIYASA KO K'ABILANCI_* ⁉
_(Hattara matasa)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
____________________
*_Number 35_*
____________________
Kafin su Uncle su dawo masallaci Amatallah tagama had'a abinci a falon k'asa data kuma gyarawa ta kunna turaren wuta. wanka taje tayi, tsaf ta d'auki gayu cikin wata light popul d'in atanfa da ratsin pink sai bak'i kad'an ajiki, yauma dai kwalliyar bawata mai yawa bace, amma tayi d'as da ita, tasha d'aurinta mai k'yau, ga k'amshinta mai rikita Uncle dasu Aneesa yana tashi ajikinta.
Zamanta tayi a falonta ta kira matan kawunta hafizu da kawu hamza Anty furera da anty sadiya sukasha hira abinsu, saikuma ta kira Asiya, suna tsaka da hirane tajiyo horn!. tashi tayi da sauri tana fad'in "ke 'yammata shugana yadawo sai munyi waya next time". bata saurari dariyar da Asiya ke tuntsura mataba ta yanke wayar, d'aukar k'aramin gyalenta tayi tasaka sannan tasaka takalminta flat kalar gyalen, saika rantse budurwace zata fita (😉lol).
Gate d'in tabud'e yashigo sannan tarufe, motar tasa tanufo cikin takunta Na nutsuwa da sanyi, yara harsun fito, shikam yana zaune yana kallonta ta madubi yakasa ko kwakwkwaran motsi saida ta bud'e masa k'ofar, murmushi suka sakarma juna, ahankali ta furta "welcome sir!". kasa amsata yayi, saiwani mayen kallo dayake binta dashi, badan yaransaba da babu abinda zai hanashi rungumeta a wajen, yakan rasa tantance watafi wata iya ado acikin matan nasa? Dan kowa gwanace a dressing. ganin yana k'ok'arin fitowa tamatsa baya kad'an, wayoyinsa yamik'o mata sannan yafito, yara suka kwashi ledojin fruits da chocolates d'in da aka siyo musu sukai ciki.
Ganin yaran sun shige yakai hannu zai kamota ta zille tana dariya, shima dole yadara yana fad'in " my best! rowar kanki kikemin? babu damuwa zan rama ai".
Dariyarta tacigaba dayi tai gaba abinta, shima sai yabi bayanta yana murmushi.
A faloma wasu taurarin yaci karo dasu, Dan tuni Fateema da Aneesa ma sunfito, kowacce cikin kwalliyar d'aukar hankali da birgewa, atare suka masa sannu da zuwa, ya amsa cikeda shauk'in ganinsu cikin ado, kowacce saida yakashe mata ido d'aya tareda mata alamar jinjina. duk sukayi murmushi kowacce najin kanta on top da tunanin itace zinariyar gida😀.
Kallonsu yayi yace, "bara nad'an rage kayannan ko?". yay maganar yana k'yaftama Amatallah idon. Murmushi tayi dantasan miyake nufi.
Saida yafara hawa steps d'in sannan tabi bayansa, suna shiga falo ya rungumeta, Dan yakasa hak'uri.
" humm Uncle kai d'innan ko! ALLAH bakada dama".
Yay guntuwar dariya da jawo hannunta suka zauna a kujera, tana saman cinyarsa "my best minayi kuma?".
" humm babu komai, ai abin bana fad'a baneba. mika rok'omin a masallacin?".
Kansa yad'aga sama alamar tunani, saiya kaleta yana k'ayataccen murmushi, "k'anwa na rok'o miki, naga gidannan kowa yanada k'anwa bandake, sainaga ba girmanki bane hakan, gara nayo amarya ta hud'u kema kisami 'Yar k'anwa ko? dama wata yarinya tanata bina a bayar...".
6ata fuska tayi kafinma ya k'arasa, ta yunk'ura zata tashi daga jikinsa..
Rik'eta yayi da sauri yana dariya, " ooh my best! Inakuma zakije? aiban gama fad'aba, Dan harda twins Na rok'o mana masu kama da brother".
Murmushin takaici ta sakar masa, cikin dakewa tace, "Su Aunty's fa suna jiranmu da yara".
Kuma fashewa yayi da dariya tareda k'ank'ameta ajikinsa yana fad'in oh god, my best! Kishinki mai ajinefa, kina burgeni over wlhy".
Mintsininsa tayi a hannu tana fad'in "waya gaya maka kishi nakeyi?".
ya saketa da sauri yana fad'in "Uchh!, my best wannan muguntarfa?".
Yanda yayi da fusaka saiya saka Amatallah fashewa da dariya tana mik'ewa a jikinsa tace, " saika taho ".
Yana kiranta amma ko waiwayensa batayiba tafice abinta.
Kansa ya jingina da kujera yana murmushi, da shafa Inda ta mintsinesan, dan yaji zafifa, ahankali ya furta "oh my Khadee ked'in Special ce acikin mata".
Can kuma Amatallah data fita dariya takusa kasheta, ganin idon Fateema da Aneesa duk yana hanyar saman, murmushi tayi ta k'arasa cikin falon, " Sorry my Aunty's mun shanyaku, wlhy Uncle".
Fateema dai murmushi takaici tayi, Aneesa kuwa saitaja siririn tsaki tana kauda kanta gefe.
Murmushi Amatallah ta kuma yi tafara had'a abincin a babban fleet, Dan yau tare takeson suci abinci su duka har yaran.
Daga Aneesa har Fateema kallon mamaki suke mata, mizatayi da wannan abincin?.....
Shikansa Uncle dake sakkowa kallonta yakeyi, ya canja kayansa zuwa dogon wando Na jeans da blue d'in T-shirt.
Yana gama sakkowa tana gama zubawa, ta sakama kiwa cokali sannan ta kallesu, ''to bismillanku, Sahib, Saifudden Abulkhairi kutaho ina Ummita?".
"Anty taje fitsari". Cewar Saifudden.
Abulkhairi yace, " lah Anty, yau harda Abbu dasu momy zamuci abinci?".
Kanta tad'aga masa tana murmushi.
"Yau kuma tare family zamuci abinci kenan?". Uncle yay maganar yana zama.
Amatallah tad'aga kanta alamar eh, kafin tace " wai musami albarkacin juna Uncle, suma yara suyi farinciki sunci abinci da iyayensu, kumama cin abincin tare yana k'ara dank'on k'aunar juna da zuminci mai k'arfi".
"Gaskiyane my best! ALLAH yayi miki albarka".
" Amin Uncle".
Fateema da Aneesa dai sai sukaji gingirin, Dan sudai basu ta6a wannan tunaninba. duk suka danne kishinsu suka nuna goyen bayansu akan abinda Amatallah d'in tayi.
Uncle yaji dad'in goyon bayan Nasu kuwa, shima duk yasaka musu albarka. yanajin dad'in idan wata acikinsu takawo shawara mai k'yau kowani Abu yaga sun taru sun bata had'inkai, bawai kishi yasasu gwaletaba.
Abin sha'awa da birgewa sukaci abinci tareda 'ya'yansu a nuse kamar yanda suka horar dasu, family ya had'u abin zaakk'yau😉🤩.
Bayan sun kammala Amatallah ta gyara wajen, daga nankuma sukayi zaman hira, yaran sunata wasansu sukuma suna hira su hud'u. dolene kagansu su burgeka, gasu cikin kwalliya, kuma kowa a nutse take hirar babu hantarar juna ko habaici wa juna irinnan kishiyoyi, dukda kuma kowacce kishin nacinta a zuciya, amma duk suka danne suke hira cikin son faranta ran mijinsu, shima kuwa cikin kulawa da soyayya yake amsawa kowaccensu, babu nuna wata tafi wata, nunawa yake duk matsayinsu d'ayane a zuciyarsa.
*_(Wlhy Ma'aurata munada matuk'ar gyararraki a gidajen aurenmu, wani fannin saikaga laifin maigidane wajen tarwatsewar zaman lafiyar gidansa, saboda rashin adalci namiji agaban abokiyar zamanki saiya dizgaki da nuna tafiki matsayi a gunsa, hakan ba daidai baneba, inhar maza zasu gyara zaman takewar gidajensu suyi adalci wlhy sai ansami raguwar zafin kishi Na mata, Dan wani abun mazanne ke haddasashi ga zamantakewar matan, zakiga wata Uwargidan tanada sauk'in kai, to amma mijin yagama 6atata ga amaryar tunkan ta shigo gidan saboda son zuciyarsa, kunga koda ta shigo bazataga darajar uwargidanba, to mijin yanuna uwargidan tagazane shiyyasa ita yakawota, kokuma ita amaryar yadinga munafuncinta ga uwargidan Dan kawai yanason uwargidansa Dason faranta mata, saiya fara gulmar iyayen amarya akan kayan d'akin ko gararta ko kud'in daya kashe a aurenta kokuma yace iyayenta suka manna masa ita Dan anga yanada hali Kodai yayta 6ata amaryar itama ta hanyoyi dadama, koya zama MUNAFUKIN MATA a tsakaninsu hakan ba daidaibane, wlhy maza kusani akwai hisabi, kuma duk Wanda ya gagara adalci a tsakanin matansa aranr lahira zai tashi 6arin jikinsa shanyayye, kuma babu makawa sai an antayashi a wutar jahannama, idan kuma bak'in cikinka yasaka mace bin malamai da bokaye wlhy kaima Kanna da wani tsagi Na zunubi aciki, bawai inabin bayan mata su aikata bane, amma mafi yawan mata sukanbi malan tsubbu ko bokaye saboda rashin adalci da k'untatawar mazajensu, saikiga suna Neman hanyar 'yancinsu, wlhy maza kuji tsoron ALLAH. Tawani fannin kuma laifinmu ne mu matan, wai Dan muna kishiyoyi bazamu zauna hira da junaba, inma anci sa'a an zauna d'in zakiga mafi yawa hirar habaicine da gugar zana, shin wannan kishine kokuwa jahilci?, nifa azatona kishi shine gogayya wajen k'yautatama miji da Neman soyayyarsa shine kishi, bawai shirme tsakanina da kishiyaba, kawai muzuba competition kowacce ta nemama kanta 'yanci awajen Wanda ya ajiyemu, bawai mu zauna hassada wa junaba, Dan kishin yanzun hassada tafi yawa acikinsa wlhy, nabaku Assignment ku gwada salon kishin su Ama.... Kugani wlhy koda kad'anne aciki, na tabbata kobayan babu raina saikun tunani, Dan kishi baya hana abama abokiyar zama hak'inta Na matsayin 'Yar uwa musulma, akwai hak'k'in k'yautatama juna tsakaninku, akwai Na mutunta juna, wlhy karkuyi zaton ALLAH bazai muku hisabi akan zamantakewa ba kawai, kafinma azo kan cutarwa ga juna nabin malamai da bokaye, muguwar kirsa dan kawai miji ya tsani abokiyar zamanki wannanma zalincine babba, idan ance kiyi kissa bawai ana nufin ki cutar da 'Yar uwarki wajen 6atata wajen miji ba, hakan ba daidai bane, kowa tata ta fisheta kawai, kinemi fadarki Na nemi tawa, amma babu dalilin 6atanci da juna. ALLAH yasa mudace yakuma shiryemu baki d'aya, komai dai zamuyi mudinga tuna mutuwa mai zuwa babu d'an aike, kwanciyar kabari da tambayoyin cikinsa gaskiyace, sannan kuma Ubangiji yatanadi wuta da aljanna, kuma kowacce zata samu mazauna cikinta, sai muyi hattara karmu bari kishi aikin banza ya kaimu wuta, wanima kishin abin kaitaima maiyinsa kukane, dan mijinma zakiga wata bai damu da'itaba balle yasan muhimmancin kishinsa datakeyi, kullunma mahaukaciya yake kallonta, wlhy mata musan inda kemana k'aik'ayidai mu Sosa, dawanan shirmen kishin damuka maida jinin jikinmu gara muduk'ufa ga ubangiji domin ku6uta daga azabarsa, saifa ka shuka alkairine zakaga alkairin🤷🏽♀, shawara tarage gamai shiga rijiya🙅🏼)._*
Basu bar falonba saida aka kirayi sallar La'asar, yatasa yaransa gaba suka tafi masallaci, sukuma su Ama...kowacce tanufi d'akinta dantayi.
Koda aka idar da sallah saiya kwashi yaran suka nufi gidansu, tashin motarsa kawai su Amatallah suka jiyo.
Hakanne yabama Amatallah damar shiya abincin dare, harta kammala tadawo falo inda Fateema da Aneesa suke zaune suna hira, zama tayi itama suka cigaba dayin hirar atare, dukdai bata wuce hirar rayuwaba da abinda ba'a rasaba.
Uncle kam yana gidansu, su Abulkhairi sunata wasansu, shikuma suka tattauna akan maganar auren Jabeer da Nazeefa, harma baba yace shima Shehu kawai idan yanada matar aure a hannu ayi gaba d'aya a huta kawai.
Uncle yace shikenan, hakanma yayi d'in, ALLAH ya tabbatar da alkairi.
Nace amin.
Saida akayi sallar isha'i suka shigo gidan, yaran kowannensu yay d'akin uwarsa, Uncle kuma yashigo d'akin Amatallah.
Zaune ya isketa kan abin sallah tana addu'a bayan ta kammala karatun alkur'ani mai girma. ya zauna saman doguwar kujera suka shafa tare. juyowa tayi tana kallonsa, "Uncle sannunku da zuwa, sai yanzu ake ganinku?".
Ya had'e hannayensa a waje d'aya " tuba nake my best!. Babane yarik'eni akan maganar aurensu Jabeer".
"Lah Aure zaiyi ya Jabeer d'in?".
" uhm, harma da Nazeefa da shehu".
Tad'an zaro ido waje "da gaske Uncle?".
" insha ALLAH my heartbeat ".
" masha ALLAH, ashe munada shan biki kwanannan".
Murmushi yamata yana d'aga kansa da lumshe ido.
Tashi tayi tanad'e abin sallar da maida alkur'anin inda yake tana kuma nuna farincikinta, ta cire hijjabin tafita dan kawo masa ruwa.
Babu dad'ewa tadawo, center table tajawo gabansa ta ajiye jug d'in data had'a kunun aya mai matuk'ar dad'i, kallonsa tayi yana kishingid'e a kujerar yana danna wayarsa, da alama wani Abu mai muhimmanci yakeyi.
Bata katseshiba, bayan ta zuba masa a k'aramin cup saita zauna kusadashi kad'an a kujerar.
d'agowa yayi ya kalleta suka sakarma juna murmushi, yad'an shafi kumatunta ya maida hankalinsa kan wayar.
Batace dashi komaiba tad'an kwanta a jikinsa tana kallon abinda yakeyi, sak'onni yake amsawa a WhatsApp, da alama wad'anda suka shafi k'ungiyarsune.
Kusan mintuna 15 ya d'auka yana amsa sakwannin sannan yakashe datar yazauna da k'yau.
Kallon Amatallah yayi datuni tatashi daga jikinsa takoma kujerar gefensa tana game a wayarta. "My best badai fushi kikayiba ko?".
Murmushi ta sakar masa, " Uncle miye abin fushi, suma sunada buk'atar lokacinka koyaya aii, nakawo maka abinci nan?".
"Wayyo my best ni zanma iya cin abincinnan kuwa? Har yanzu cikina yakasa sauka".
Langa6e kanta tayi gefe, " yanzu nan Uncle duk wahalar girkinnan danasha bazakaciba kenan?".
Ya had'iye kunun ayar daya kur6a kafin yamik'a mata hannu alamar tazo.
Babu musu tataso tazo, kusadashi ta zauna tana zun6ure-zun6ure, ya ajiye kifin kafin yajawota sosai a jikinsa, "sorry babyna mikika dafa to?".
" tuwo miyar d'anyen karkashi".
"Humm har kinsa yawuna ya tsinke my best, namiki alk'awarin da safe ki d'umama min zanyi break fast dashi".
" da gaske Uncle?".
"Yes my best".
Daga nan tasaki jiki sukaita hirarsu cikin so da k'auna, sai wajen 10 yatashi zuwa 6angarensa. hannunsa tarik'e tana marairaice face.
" ya yadai my best? ".
" Uncle please mu kwana anan mana".
Yay murmushi "tofs my best!, nan kuma? d'akinafa shi laifinmi yayi yau?".
" nidai babu laifin komai, kawai anan nake sha'awar kwana".
Yaja hancinta yana fad'in "hakan yayi my best, k'ilama ki samo mana twins yau....."
"Kai Uncle nifa ba yanzu ba?".
" kamarya ba yanzu ba?, sai yaushe kenan my best? "
"Uncle saina kammala karatuna, duk yaushe muka shiga level 2".
Shiru yad'anyi kad'an yana kallonta, ya sauke numfashi da d'ago ha6arta suna kallon juna, " my best kodai kinashan wani abune dan karki samu ciki? Please karkimin haka Dan ALLAH, inason ganin 'ya'yanki jinin brother d'ina danawa cakud'e awaje d'aya my best please ".
Jikin Amatallah saiyayi sanyi, ta maida kanta ta kwantar a k'irjinsa " Uncle wlhy bana shan komai, banma ta6a tunani irin wannanba,