Showing 102001 words to 105000 words out of 107296 words
de bansan wane hukunci xand'aukaba wallahi tun da akai haka na sak'a na ware,nasak'a na ware nakasa samin mafita"
"HasbunAllahu wani'imal wakil,kiramin ita khadijan da magajiyan muji daga bakinsu kafin musan hukuncin daxamu d'auka"
"To Yaya"captain Adam yace hakan had'e da mik'ewa yafita,
Cikeda tausayi Yaya Sameer Kebin captain Adam da kallo naganin harya d'an fad'a shikuma haka Allah ya tsaro masa tasa rayuwar,wani bang'are na xuciyarsa kuma sake yaba tawakalli irin na captain Adam d'in yake ganin yadda ya fawwalawa Allah lamuransa.....
Captain Adam cikin sassarfa yake tafiya har ya k'arasa part d'in magajiya don rabonsa da xuwa tun kwana hud'u da suka shud'e lokacin da yad'akko baby Kay daga hotel gabansa se fad'uwa yakeyi hailala yafarayi yana had'iyewa yakusa shiga babbar k'ofar yaji muryar baby kay na waya cikin rad'a rad'a;
"Don Allah dagaske kike cooley?! Aswr nagwada sau biyar kenan,wallahi da pregnancy tip d'inde,narantse da Allah gashinan b'aro b'aro yanuna akwai ciki,no serious cooley sau d'aya fa kawai ace har ciki yashiga?nashiga uku yanzu yaxanyi idan baffa yaji haka?tam xankiraki idan nasamu kud'in gwara kawai acire"tana katse wayar d'ago kanta daxatai suka had'a ido da baffanta,jikinta yafara kyarma,
Ba'abinda yai mata kallonta kawai yake yi yadda ta rame tad'ashe sak alamun masu ciki sun bayyana atattare da ita,kotakanta bebiba yak'arasa shiga cikin parlorn xaune yasamu magajiya tad'aga kanta sama ita kuma muna_b se zagaye parlorn take tana magana ita kad'ai tana ganin captain Adam takwaso da gudu tayo inda yake tana magana tana susar jiki batada maraba da tab'abb'iya;
"Boka Namuduka shine yaiwa hafsatun captain Adam asiri kishiyar magajiya ta haukace,mu ne mukai mata kurciya tashiga duniya muka cire mata tunaninta"tafad'i hakan tana rawa,
Girgixa kai kawai captain Adam yai cikeda takaici yake kallon magajiya dake tsiyayar hawaye
"Kuxo babban parlor na yaya sameer nason ganinku keda khadija,abu nabiyu kuma nace maki kisan yadda xaki kinemo dangin matarnan sutafi da ita"bejira cewarta ba ganin tafara kama fatar mak'ogaro xatai magana yasashi hanxarin fita abinsa.
Kafin yak'arasa wurin Yaya sameer tuni baby kay tariga shi xuwa da alama taji sanda yake fad'awa magajiya hakan,yana shiga parlorn ya hangota a rakub'e cikeda tsoro tafara gayda Yaya sameer muryarta har rawa take;
"Baffa Sameer ina kwana?!"tagayshe da Yaya Sameer jikinta se rawa yake,
"Lapia qalau khadija,inaso kifad'amin keda wa kukaje hotel kwanakin baya?!yanxu khadija harkinkai wannan lokacin daxakuje keda saurayi ku kama d'aki kuna aikin alfasha?!Ina tarbiyyar da aka baki? Kuma saboda yarena miki hankali ma yagudu yabarki daga k'arshe wanda kika bulawa k'asa a ido shiya biya kud'in,yanxude inaso insan wanene shi?!"
Shiru baby Kay tai tana ware ido na marassa gaskia se rawar baki take tace;
"Baffa k'arya hotel service d'in yakemin da...da k'awata mukaje"tak'arashe xancen idonta yaciko taf da hawaye,
Mik'ewa Yaya sameer yai kamar xe kai mata duka yai kanta dama be iya fad'a ba in aka kaishi k'arshe,xare mata idanuwa yafarayi nata shiga taitayinta,
"Dan gidanku xa'ai maki k'arya ne?!ko kinxata ba'a lura da takunki?!to bari kiji kode kibud'e baki ki fad'i da uban wanda kukaje hotel d'innan ko kuma yanxunnan kiga abinda xe faru"yafad'i hakan yana xaro wayarsa yafara dannawa,
Cikin sauri baby kay tasake matsowa inda yake sanin halinsa yasanyata fara hawaye tana rok'onsa;
"Baffa Sameer dan Allah kayi hak'uri xan fad'a"
"Ina saurarenki"
"Baffa wallahi wayo yamin"
"Kamar ya wayo yamaki?!"
"Baffa cayamin a al'adar su kafin ai aure dole se se...."sekuma tai shiru tana shashshek'ar kuka.
"Ke bakida wayo ne?!ko bakisan Allah yayi hani da hakan ba harse kunyi aure?!wanene shi?!"
"Baffa sunanshi kamal yazeed amma wani yacemin wai ba haka sunan shi yake ba"
"Kamar yaya banganeba?"
Nande baby Kay taxauna tafad'awa su Yaya sameer din farkon had'uwarsu da yadda yai mata xambo cikin aminci yarabata da martabarta tareda d'oriyar ashe mak'aryacine,girgixa kai kawai yaya sameer yake,babu wani b'ata lokaci aka kira mus'ab so called abokin bobon nata yaxo,ganin xe iya shiga wani hali idan yai masu k'arya yasashi gyara xama yafad'a masu komai tareda d'oriyar ai tanimu mudi(Bobo)mugun d'an k'aryane kuma ba'asan ma d'an wani gari bane yanxu haka cases d'in kansa sunyi yawa ya yaudari ya'yan mutane yayi masu raping ya kuma gudu ba'asan inda yakeba bayan yagama fad'ar komai ne suka sallameshi yatafi itade baby kay se raba ido take alokacin magajiya tashigo tana tafiya dakyar ta rame dakyar take d'aga k'afafuwanta,kallo d'aya captain Adam da Yaya sameer sukai mata suka d'auke kansu,atsakure taxauna agefe bayan ta gaisheda Yaya sameer, Adam yai gyaran murya;
"Yaya wani hanxari ba gudu ba,d'axu dakace naje nakirasu dama so nake naji ko xata fad'a ashe kuwa baxata fad'a d'inba,naji khadijan na waya da k'awarta,ashe ciki ne da ita gatanan inajinta tana wayar idan na mata k'arya"captain Adam yace hakan cikeda takaci,
"Ciki kuma?!"Yaya sameer yace hakan yana ware ido,cikin murya me rawa yake fad'in;
"Waye me cikin?!"
"Khadija"cewar captain Adam,
"Baffa Allah kuwan banida ciki,k'awatace me shi" baby kay tace hakan tana raba ido.
Salati yaya sameer yafara rafkawa wannan wacce irin rayuwace?!juyawa yai yana kallon magajiya dake raba idanuwa kamar mujiya yace da ita;
"Ko kinsan tanada ciki?!"
Saurin girgixa kai tayi alamun bata saniba,
"To ya akai baki saniba?!"
Fatar mak'ogaran ta tarik'e tafara magana ahankali;
"Wallahi yaya bansaniba bata fad'amin abubuwanta yanzu"
"To yaxa'ai tafad'a maki bayan kema kina b'oyewa maigidan abinda kike ciki,ko angaya maki cutar cancer bata nunawa?!ai ga irin tanan"
Shiru magajiya tai tana saukar da kai k'asa,xaro wayarsa Yaya sameer yai cikin k'ank'anin lokaci yakira DR SAMEER AMEER babban consultant dake kano,dayaxo yaduba khadija yaga ko tanada ciki?ba ajima ba likitan ya iso,baby kay tafara rantse rantse seda Yaya sameer yai mata jan ido sannan tayadda likitan yafara mata gwaje gwaje,minti talatin cikakku ba'aiba yadawo da result b'aro b'aro kan lalle tabbas baby kay nada ciki na sati biyu,musu tafarayi ita kan lalle ba na tabane,likitan yatabbatar mata da cewa ai shi ciki rana d'aya yake shiga akuma lokaci d'aya bawai d'aukar kwanaki yake ba,godia Yaya sameer yai masa sannan suka sallameshi yatafi,sallah suka tashi sukai dayake la'asar tayi sannan suka dawo suka sake sabon xama,alokacin Hafsat tashigo bayanta kuma y'ar aikinta ce d'auke da foodflask kala kala cikeda abinci,se wani tafkeken jug garai garai kana iya hango frozen xob'on dake ciki yasha cucumber slices se k'amshi ke tashi na food aroma daya cakud'e da k'amshin turaren khumran dake jikin hafsat d'in,lumshe ido captain Adam yai yabud'e yanasake jin son Hafsat yana ratsa b'argon jikinsa.cikin sauri tafara serving d'insu had'add'iyar fried rice tayi datasha hanta da veggies se sauce na green pepper dakuma French salad da soup na kaza,se sanyayyan zo'bo me sanyaya zuciya,ci sukai suka k'oshi banda magajiya da baby kay da akai masu tayi sukace sun k'oshi bayan harga Allah yawunsu ya tsinke girman kai nede kawai irin nasu,Hafsat harxata fita bayan tagama serving d'insu abinci Yaya sameer yace taxauna itama ayi maganar da ita tunda ba bare bace...
____Bayan sungama cin abincinne lokacin captain Adam yamik'e yad'akko bowl yakawowa Yaya sameer hand wash ya wanke hannunsa aka doko sallama cikin parlorn su muhannad ne da iyayensa suka shigo,kyakkyawar tarba su captain Adam d'in sukai masu aka gaysa kamar babu wani da ya tab'a shiga tsakani.Gaban magajiya se dukan uku uku yake tana adduar Allah yasa ba asirin su ne xe tonuba,shide muhannad kansa a k'asa yasa hannu yana wasa da gashin jikin center carpet dake malale a tsakiyar parlorn.
"Alhaji dama gurinka mukazo,mu wlhy se jiya mukejin wata magana ta daban da bamu santaba"mahaifin muhannad ke fad'in hakan yana me kallon captain Adam,
"Babu komai,xance ya wuce Alhaji abinda yarinya ma hartayi aure tana gidan mijinta"
"Munsan da haka ai,abinda ma yakawo mu kenan don maganace yanxu tataso kuma muna fatan bayan komai ya warware xa'a yafe masa"
"To muna sauraro nan duk family ne"cewar Yaya sameer.
Nande muhannad yadawo tsakiyar parlorn yaxauna yafed'e bindi harda wutsiya tareda d'oriyar shi kansa ba a hayyacinsa yai yunk'urin hakanba shide yasan kansa yana ta ciwo daganan kuma yaji xuciyarsa da jikinsa ba'abinda suke zumud'in so se jikin Ummi Aisha,bayan nan kuma besake sanin meyafaru ba,koda yakalli video d'in da captain Adam yasaka betuno komai ba se bayan and'au lokaci yafara mafarkai akanta kuma tunaninsa yadawo akan abinda yai yunk'urin aikatawa yak'arashe maganar yana hawaye yana kuma rok'onsu dasu yafe masa sukuma sa Ummi Aisha tayafe masa shikansa yason don baya neman tsari daga Allah ne hakan take faruwa akansa,
Ana cikin haka su Ummi Aisha da Ashraf suka shigo cikin parlorn turus sukai ganin mutane fal aciki da alama wani abinne yafaru,gaisheda kowa sukai suka nemi waje suka xauna,nande aka taso da maganar abinda muhannad yace,shin abinda yafad'a gaskiane?akace Ummi Aisha tafad'i abinda tasani,fad'ar komai tai tareda d'oriyar tabbas muhannad be rabata da martabarta ba yadeyi yunk'urin hakan amma Allah bebashi sa'ar cin galaba akanta ba,suna cikin tattaunawa muna_b tashigo da gudu tana soshe soshe,ganin haka yasanya su duka mik'ewa tsaye,nuna Ummi Aisha tafarayi da hannu se kuma ta nuna muhannad tafara magana;
"Ya akai haka?! boka namuduka yatabbatarmun xaku rabu ya akai kadawo?nacacce bayan munsa ka rabata da budurcinta seda kasake dawowa?!"
Ganin xata sake fad'ar wasu maganganun captain Adam yakorata waje tafita,kafin tasake kunya tasu,
"Ashsha ba hankali ko?"cewar mahaifin muhannad dayabi muna_b da kallo,
"Ehh"kawai captain Adam yace a tak'aice,
Sake xundumowa da gudu muna_b tai tana magana tana rawa;
"Mune muka sanyawa hafsatun captain magani acikin nono tasha hankalinta ya gushe tabar gidannan shekara da shekaru ba'asan inda take ba,mune muka sanya mata karkashi ta zume tafad'i akan cikinta lokacin daxata haifi Ummi Aisha,kuma muka xubarda cikin ta nabiyu"tak'arashe maganar tana kyalkyalewa da daria,
Parlorn yai tsit kamar ruwa yacinyesu,magajiya tai shiru gumi se keto mata yake dukkoda sanyin dake ratsa parlorn,
"Akwai k'ashin gaskia a maganar matar nan"cewar Yaya sameer,
"Tanada tab'in hankali fa yaya"captain Adam yace hakan yamik'e tareda sake kora magajiya waje yakira lamunde yaje karta barta tasake futowa...
Baby kay dake gefe a xaune ta tashi tadawo kusa da mahaifinta tana kuka,kallon diyar tasa captain Adam yai sekuma yakauda kansa gefe,ajiyar xuciya tai tafara magana da courage;
"Baffa abinda Aunty muna_b ke fad'a gaskiane,tabbas ni suka saka nadinga xubawa muhannad magani acikin abinci har tsawon kwana uku,nak'arshe kuma acikin lemon kwakwa naxuba masa yasha duk dande yai raping Ummi Aisha karta auri Ashraf kuma plan d'intane tasa akai video aka kai maka,dukdan kada kowa yasota ya aureta but bayan haka gaskia bansan komai ba akai nasande aunt muna_b na influencing ummah tana sata tana abubuwa marassa kyau,nikuma abinda yasa nai haka don inason Ashraf ne saboda farko shiya nuna yana sona ashe yayi hakanne don Ummi Aisha,dan Allah Baffa kuyi hak'uri kuyafe mana dan Allah nide na tuba"
Tuburewa captain Adam yai kan lalle sesu magajiya da baby kay suntashi sunbar gidan,seda Yaya sameer yai dagaske kafin captain Adam ya hak'ura se huci yake,wa'azi sosai Yaya sameer yashiga yi akan rayuwa sosai yan parlorn kowanne yai shiru saboda yadda wa'azin ya tsuma zukatansu ya k'ark'are da fad'in;
" Ke magajiya da idonki yarufe kikewa Hafsat SIHIRI yanxu wake jin dad'in xaman dunia cikin keda ita?!abu nabiyu y'arta da kuka sanya agaba kukai meyiwuwa don ganin anmata fyad'e gashinan sharrin da kukai mata yaxama alkhairi,dama wani sharrin idan akai maka shi to alkhairinsa yana gaba,duk abinda kuke jefansu dashi yanzu yadawo kanku,gashinan cuta sama da kala uku itace ajikinki,raping da kuke fatan yasamu ajikin yarta akan y'arki yak'are gashinan ita harda ciki ajikinta ita k'awar taki dake saki akan hanyar ta gashinan ta haukace ai,dukde abinda kuke fatan yaxama akan Hafsat da Ummi Aisha daga k'arshe duk masifar tadawo kanku ko kunya bakyaji kisamu mace da mijinta kice xaki rabasu?kai tirr da masu hali irin naki,Allah ya kyauta dama ance duniya makaranta kukam duniya ta koya maku hankali seku nemi gafararsu koxasu iya yafe maku abinda xan iya cewa kenan"
Kuka Ummi Aisha take shab'e shab'e Ashraf ya rungumo abarsa yana bata haku'ri ko kunyar su Adam bayaji, muhannad shiyai k'arfin halin magana kan cewar shide shida iyayensa sunyafe abinda akai akansa kuma yana fatan Allah yayafesu gaba d'aya kuma don Allah Ummi Aisha tayafe shi,nantake tace tayafe masa itama yayafe mata,baby kay ma ta matso wajen Ummi Aisha tana nemanta gafara tuni Ummi Aisha tace tayafe mata,takoma bang'aren Hafsat itama tace tayafe mata captain Adam ganin duk sun yafe mata yasanya shi shima yayafe mata,magajiya tataso tadawo kusada Hafsat tana kuka;
"Don Allah kiyafemin hafsatu,nasan na muxanta maki arayuwa kuma dede da rana d'aya baki tab'a ramawa ba don Allah kiyafeni"tafad'i hakan tana rusgar kuka,
"Niban rik'e ki ba magajiya Allah yayafe mana"
"Nagode sosai"cewar magajiya sannan ta juya b'angaren captain Adam
"Yaya dan Allah kayafemin kaji?!"
"Wa'enda kikaiwa hakanma sun yafe maki bare ni,kije nayafe maki amma kisani zamana dake ya k'are ki d'au y'arki kubarmin gidah"
"Baxa'ai haka ba Adam,hukuncin sakin daka yanke yayi amma batun tatafi da khadija duk bataso ba tunda yarinya nan gidan sune ko ba haka ba?"yace hakan yana kallon mahaifin muhannad
"Hakan dakace shiyafi"cewar mahaifin muhannad.
A hakade aka yayyafi juna,captain Adam ya yarda baby Kay xata xauna amma lalle se magajiya tafuta tabar masa gidansa,bayan komai yad'an lafa su muhannad sukai masu sallama suka tafi bayan sunyi godia,sosai d'an xaman dasukai da mahaifin muhannad dasu captain Adam har sunyi exchanging numbers donsun lura shid'in mutum ne me dattako.Yaya sameer se tambayar Ashraf yake ya ya xamansu bade wata matslar ko?sukace babu suka fara haramar tafiya Yaya sameer ya tsayar dasu yafara gyaran murya;
"Sakamakon duk jin abinda yafaru,Alhmldh dukda komai ya lafa,nakuma yaba da yadda faradd'aya Hafsat keda d'iyarki Ummi Aisha kuka yafewa su magajiya dukkoda tarin bala'in da suka shigar daku a rayuwa babu abinda xance sede fatan Allah yasa kwita ganin alkhairi har k'arshen rayuwarku,ina kuma fatan Allah yasa kuyi kyakyawan k'arshe Amiin,abu nabiyu na yaba k'warai da yadda khadija tafuto ta fad'i gaskiar al'amari kuma da niyyata kafin ai haka musamo wani a k'auye muhad'ata aure dashi,amma tunda tai wannan kyakkyawan halin Insha Allah cikin ARFAAN KO MUS'AB xan xab'a mata miji acikinsu"
Kowa nagurin yaji dad'i bayama i baby kay datasan su arfaan d'in yangayu ne na k'arshe da suka goge da boko da kuma addinin islama,tunba yauba takejin crush akansu data kasa gane shin wannan menene SO KO SHAK'UWA?tana kuma fatan Allah yasanya alkhairi Allah yabiye bakin baffan ya aikata hakan don itakam duniya takoya mata hankali babbaaa,sallama su Ummi Aisha sukaiwa su captain Adam da Yaya sameer dake shirin bin jirgin dare ya koma kaduna shima,b'angaren Hafsat suka nufa nanta sake baiwa Ummi Aisha shawarwari kan yadda xata rik'e mijinta takuma bishi sau da k'afa yi nayi bari na bari,suna tafiya captain Adam ya kad'a kan magajiya da muna_b yasasu a mota jirgi driver yajasu se kaduna,bayan captain Adam yace xeturo mata motar kayanta yabar mata ,takwashe kayan gidan kadunan ma shima yabar mata halak malak.Ita kuma baby Kay tadawo bang'aren Hafsat daxama har Allah yasa afara maganar aurenta da ARFAAN KO MUS'AB,kuma Yaya sameer yayiwa DR SAMEER AMEER waya kan xa'akawo baby kay suyi mata abinda yadace idan wankin cikin xa'ai idan kuma magani xasu bata to dukde suyi abinda yafi.
•
CASTLE OF LOVE;
Suna komawa gidah Ummi Aisha tafad'a kan gado se bacci ba ita ta tashi ba seda aka fara kiraye kirayen sallar magrib,da sauri ta mik'e tashiga band'aki tayo wankanta tayi brush taxura doguwar rigarta da wando tad'ora hijabi akai tafara sallah,bayan ta idar tajanyo qur'ani tana karantawa tayi addua tashafa jitake kamar wata sabuwar rayuwar aka sake mata daddad'a,tana gama addu'ointa tashafa taname k'ara neman tsarin Allah a lamuransu yakuma k'ara dank'on soyayya tsakaninta da mijinta,
Kitchen ta nufa don d'ora abincin dare tana cikin kiciniyar had'a tuwon shinkafarta taji an sak'alo mata hannuwa anrugumota ta baya,ta k'amshin turaren hugo boss d'insa tagane cewar shine,juyowa tai tana kallonsa,kafin tasa hannu taxame hannunsa daga k'ugunta;
"Ashraf barni na samu nadafa mana abincin dare mana ko?!"
"Life partner banasan kina wahala kibari mana xamuyi take away"
"A'a Wlhy,kabari kawai nadafa mana"
"Me xaki dafa ne?!"yace hakan yana bin ruwan data d'ora da kallo
"Sphagetti ne dan Allah kaje parlor kaxauna nagama pls"tace hakan don batason yasan tuwo xata dafa,
"Shikenan tunda korata kike"yafad'i hkan hardasu kalar tausayi sannan yafice daga kitchen d'in,
murxa muk'ulli tai tarufe k'ofar kitchen d'in,ba ita tafuto ba se bayan sallar isha'i lokacin har Ashraf yafita masallaci,tatass tagama tuwon shinkafarta miyar kuka datasha daddawa da manshanu tai saurin b'ararraka soup d'in kayan ciki tareda had'a lemon kwakwa sannan ta jere a dining ta bulala turaren wuta,ta nufi sama tasake wanka tai sallah sannan tacanxa kaya cikin bumshort dakuma wata yaloluwar riga iya cibiyarta kawai ta rufe,kanta ba d'ankwali tasakko k'asa taxauna tacanxa channel xuwa fox series tana kallon series d'in empire se k'amshi ke tashi ajikinta,bata jima da xama ba Ashraf yadawo baki,hanci,ido haka yasakesu yana kallon Ummi Aisha yadda tai kyau ba kad'an ba da sauri yanufi inda take yaxauna akusa da ita tareda sa hannu ya d'agota yad'ora akan cinyarsa,batare da b'ata lokaci ba yasa bakinsa cikin nata yana bata warming kisses dakyar ta iya kwatar kanta ta sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da farcenta ahankali yad'ago fuskarta yana kalla;
"My whole world changed the second i looked into your eyes,inasonki inasonki banson yaxance makiba"yak'arashe maganar yana k'asa da kansa,
Sa hannu Ummi Aisha tai tad'ago hab'arsa mexata gani? hawaye ne ke reto a fuskar Ashraf,kid'imewatai tana dubansa;
"SubhanAllah Ashraf meyafaru?!menai maka"
Kasa bata amsa yai illa had'a bakinsa da nata dayai yafara aika mata da sak'onni hakanne yatabbatar mata da cewar lalle tsantsar soyayyar dayake matane haryasanyashi kuka dakyar ta iya mik'ewa tsaye tana janye da hannunsa kamar k'aramin yaro kan kujerar dining tajamasa yaxauna,janyota yai kan cinyarsa yana mata rad'a;
"Ga wajen xaman kinan life partner"yace hakan yana mata nuni da cinyarsa,
Murmushi tai cikeda kunya tace;
"Abinci xan xuba mana"
"To xubamana"
Tana fara bud'e foodflask d'in Ashraf yadaka tsalle be dire ko'ina ba se bayan dispenser
"What the f^ck,miyar kuka agidan nan?!"yace hakan yana toshe hancinsa
"Uhm uhm sweethrt karmuyi haka dakai"cewar Ummi Aisha hardasu langab'ar dakai
"But life partner sarai kinsan banacin miyar kuka infact tuwon gaba d'aya baso nake ba"
"Trust me candyboo Wannan miyar dabance"duk dan yaci take kiransa da sunaye kala kala
"Uhm uhm ba xakimin wayo ba"
"tunda baxakaciba nima nak'oshi"tace hakan