Showing 3001 words to 6000 words out of 107296 words
dake rakube da nonstick spoon ahannunta tai tsuru tsuru daga bisani kuma ta tsugunna har kasa ta gaida addah sadeeyan,wadda dakyar ta amsa tana kokarin bude tukunyar sekuma ta fasa Tana kallon haule"ke idan Kingama kixubo manashi duka a foodflask kikawo parlor ,"Sannan Ina wannan juyar take?!haule tace ta..tana daki batada lapia ne..addah sadeeya tai tsaki Allah yakaro Wata akai ta mutu Ma shegiya mayya Uwar taurin rai,sanann ta fice takoma parlor ,"haule tai tagumi oh ya Allah yaukuma da wacce sukaxo haka?!Allah karabamu da mugun hali ameen!
"Haule nagama faten tajuye duka a flask seda tafaki ido taga basanan Sannan ta samu wani madedeci taxuba ciki tarufe taboye cikin kitchen carbinets dan tasan yadda auntyn kesan faten dankali.sannan tanufi parlor takai masu,"addah safeeya tabude foodflask din tana wani baje hanci kamar mayya iceko baki rage kokadan ba ?!dan Wlhy idan nagano kinrage senaci ubanki merabani dake agidannan Se Allah,haule ta sadda Kai kasa a'a duka najuyo maku shi dama badayawa naiba namune nidasu modu,addah sadeeya tace Toh xaki iya tafiya ,seda sukaci sukai nak suka kora da lemon donsimon dake freedge din parlor din Sannan suka mike suka nufi dakin da Hajia Hafsat take.."suna shiga addah safeeya tafara salati eh lalle Yayi Kyau sadeeya kalli yadda sanyin AC ketashi jiyadda juyar nan ta bararraje kan royal bed dinnan shegiya sede taci,tasha,takwanta tai barci.addah sadeeya ta takarkare tadaga hannu sama ta duma mata duka abaya jikake duuuuuum yadda Kasan drum akadaka.bashiri "Hajia Hafsat tamike Tana salati sekuma tasa kuka,addah safeeya tai tsaki Sannan taja kafar Hajia Hafsat basu direta ko'ina ba Se tsakiyar parlor sosai suka gurje mata jiki akasa saboda janta dasukayi..
Sehaki suke kmar Wanda sukai gudun fanfalaki,Hajia Hafsat tadago raunannun idanuwanta dasukai ja saboda azaba ta aza akansu "Dan Allah mena tsare maku?!wannan kiyayya har ina.."addah sadeeya tai tsaki ubanki kikai mana,sosai sukahau dukanta tako'ina tun Hajia Hafsat nabasu hakuri har azaba tasa tadena Se ajiyar zucia datake ,addah safeeya tai wulli da wayar charger datake dukanta da ita akasa sannan taxube akan kujera tana maida numfarfashi,addah sadeeya tahau ruwan cikin Hajia Hafsat taxauna tana Dariar mugunta "gwara mukashe ki mukashe banxa da wofi,haule me aiki dake lekensu tasaki kuka ahankali tareda jingina a drawer din kitchen "wannan wacce irin tsana ce haka?!
•••••
Capt Adam yai murmushi ,"yakalla driver dinsa dake tukinsa daga airport din Aminu kano xuwa gidansa sardauna crescent ,jirgi (yadda suke kiransa kenan Dan ya iya gudu na bala'i)"iceko bakacewa Hajia yau xan dawoba Dan suprise nake san mata,jirgi yakada Kansa "kodaya oga banfada mata kosu modu da hannafi basusan da xuwankaba..Capt adam yace "Yawwa jirgi nagode kwarai..sosai suke hirarsu har suka Isa kofar gidan ,"Capt adam yace Yawwa basekashiga da motar ba danxan aikeka nan shop rite .yabasa kudin shikuma yasakai yashiga sosai modu da hannafi sunji dadin ganinsa Sannan suka mai sannu daxuwa..modu yakalli hannafi "kan bala'i yau akwai ruguntsumi kenan,"hannafi yai Daria aigwara haka dama hausawa nacewa rana dubu ta barawo rana daya tame kaya!
Capt Adam Se murmushi yake yau xeyi toxali da sanyin idaniyar tasa kwana biyun dabe sata cikin idonsa ba jiyake kaman shekara biyu yai,,"da sallamarsa yashiga parlor din Yana kwala kira my hafsat...my ha..karaf idanuwansa sukai toxali da hafsat dinsa kwance akasa ga kanwarsa safeeya kan ruwan cikinta gefe daya kuma sadeeya ce tsaye da Waya ahannunta..
nanahafsat.wordpress.com
WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;MISS XOXO👄
[4/18, 11:56 PM] Asy Khaleel: 22/12/2016. 4;00pm
•✨UMMI_A'ISHA✨•
(THE MAGNIFICENT)
4
©•MISS XOXO
👄
DEDICATED TO
UMMI_A'ISHA👌🏼
•✨•✨•✨•✨•✨•
Note;narubuta kanwar Capt Adam da SURAYYA a farkon page,pages na biyu Dana uku..inatasaka SAFEEYA,,wannan yafarune sanadiyar wajen typing Wanda wayata take samun haka..Ayi hakuri pls,xandawo saka SURAYYA karnai confusing mutane.inafatan xaku gane🙏🏽
•✨•
"Karaf idanuwansa sukai tozali da Hafsat dinsa kwance akasa ga kanwarsa surayya zaune daram kan ruwan cikin Hafsat din,gefe daya kuma sadeeya Ce tsaye da wayar charger a hannunta.."bude idanuwansa yai yakara rintsewa shin wannan mafarki yake kokuwa dagaske ne?! Addah surayya naganinsa tamike tana noke kai sosai saura kadan fitsari yaxubo mata Dan tsabar tsoro ita dinma sadeeya saurin sakin charger dake hannunta tai,suka koma gefe daya suka tsaya zuciyoyinsu Se harbawa suke abinka da marassa gaskia tuni idanuwansu suka firfito waje suna jiran abinda xefaru ..
"Capt Adam ya ajiye Kayan hannunsa Sannan ya fice waje bebi takansu sadeeya dasukai tsuru tsuru ba,Yana xuwa yace"modu ku kullemin gidannan da kwado kada kubude harse nabaku izini,Sannan xankiraku xaku amsa min wasu tambayoyi,bejira tacewarsu ba yajuya yasoma tafiya dayake da dan taxara tsakanin gate din da kuma cikin gidan,"modu yakalla hannafi,yace yaufa xa'ayita kenan agidannan inaga watan sallamarmu ne yai shikenan,jar miya takare Se kuka koriya shar,kuma yau Se kauyen garin dau"hannafi yai shiru Yama kasa magana kwata kwata Se zare Ido yake musanman dayatuno kauyen na garin dau dayadda tuwo ne kullum ba fashi miyar nan koriya ko dandano babu,"yanxu kuwa saboda Allah yasaba cin jarmiya mehade da kaji..
"Kafin Capt Adam ya isa cikin parlor din,addah sadeeya takalla addah surayya dake faman xubar hawaye sekace tsohon famfon dayaki kulluwa.. "kede banxa ce wallahy Banda mukullawa shegia sharri,"addah surayya tasa gefen mayafi Tana share hawayen fuskarta tareda fyace majina",kyaleni sadeeya wannan duk baxeyiwuba kawai de Se abinda Allah yayi .amma yau me karbarmu a hannun Yaya Adam Se Allah!tana cikin magana "Capt Adam yashigo gurin Hafsat dinsa yanufa ko kallonsu beyiba,sosai yasa hannu ya ciccibi abarsa yakaita daki yabata agajin gaggawa dayake akwai first aid box agidan ..sannu ahankali tafarfado daga suman datayi Sannan yadan sa ruwan dumi ya gaggasa mata jikinta ,"dakyar take magana hayatee yaushe kadawo ?!"capt Adam yajuya Yana goge hawayen daya xubomai dan bayasan tagani,sosai yau yatabbar da cewar wannan shine dalilin dayasa rannan daxe tafi yaga jikinta yayi sanyi ,kuma tabbas duk tsahon shekarunnan inde yatafi yadawo yake ganin Hafsat dinsa kullum da sabon tabo da sabon ciwo ..sosai tabashi tausayi dakyar yagyara mata kwanciya bayan yaballi magani yatemaka mata tasha "ahankali yake fadin calm down my hafsat,dama nace maki baxanyi kwana 3 ba if you can recall,yanxu de kiyi bacci akwai abinda xanyi .."hannu tasa tarike rigarsa pls hayatee kakyalesu ni na yafemasu wallahy Dan Allah banasan abinda xehadani da gwaggo.."Capt Adam yaxaro Ido nakyalesu fa kikace?!axo har gidana agina wannan rashin mutuncin kice baxandau mataki ba,"my Hafsat muna Bawa junanmu shawara nidake muna dauka muyi amfani da'ita.."amma kiyi hakuri da rashin shawararki dayau xansa kafa nashureta,wallahy yau sadeeya da safeeya sesun gane gonar wasuka shigo!beko jira mexata ceba yasakai yafice,"Hafsat tasa kuka Dan batasan tashin hankali,kuma batasan ace itace sanadiyar hada yaya da kanne ,"gashi jikinta kwata kwata ba kuxari balle tace xatabi bayansa haka tahakura tafara yan'adduo'in kwantar da musibar datashigo gidan,harde bacci dadda'da yai awun gaba da ita..
"Capt Adam nakomawa parlor yanemi kujera three sitter yaxauna yaharde kafafuwansa kamar betaba Daria ba,sosai yatsura masu Ido Yana kallon yan'uwan nasa Wanda Sukai masa abinda ko amafarki betaba xatan yan'uwansa najini xasuyi masa shiba,"yai gyaran murya yace surayya kece babba,babbar banza babbar kwabo shashasha mekwakwalwa irinta kifi,wadda kanwarki taxauna Tana juyaki ubangiji Allah yakyauta,"Sannan yakalla sadeeya datai kasa da Ido sekace mumina,yace ke dago idonki karamar munafuka ,dama ke tunda annamimiyace..yanxu kafin Komi yakwana kafin inmuku dukan kawo wuka Wanda xaku gane wannan shine babban kuskuren dakuka tafka a rayuwa.."inasan kufadamin uban meye yake kawoku gidana shekara da shekaru kunacin mutuncin matata?!
"Sadeeya tai kasa da Ido Yaya bafa lefin mubane,ita batasan ana zumunci yauma damukaxo takamamu da kokawa kanse munfita daga gidan shi...kafin takarasa Capt Adam yabata wani kyakkywan mari "Yana huci kamar xaki Yana nunata da yatsa you knw me sadeeya I dnt tolerate nonsense ,natambayeku magana kufadamin gaskia xaki sako makircin dakuka saba to kisani nasan matata ciki da bai,,,Capt Adam yace naku wasane Sannan yadaga murya yace "haule xonan parlor yanzu kome kike ki ajiye kixo..a Dari haule tashigo parlor din bayan tayi sallama ta kwashi gaisuwa Sannan takoma gefe taxauna ,"Capt Adam yace Yawwa haule fadamin gaskiar al'amari akan mekika sani gameda wa'ennan kada kiji tsoransu ko suyi maki jan Ido kikasa fada,fadi Komi tun shekara goman dakikai kina aiki a gidannan nasanki da amana,haule tadaga Ido Tana kallonsu,atare suka maka mata harara,sosai haule tahadiye yawun tsorata amma yata iya inde tanasan yan' cin auntynta Hafsat dole ne tafadi gaskiar lamarin..
"Haule tace abba gaskiar al'amari xanfada tsakanina da Allah daya halicceni,shekara ta goma kenan Ina aiki agidannan,amma bantaba ganin farin cikin Aunty ba harse kana gidannan,inde kayi tafiya to farin cikin Aunty yakare kenan kuma bawani abunne yasaba face addah surayya da addah sadeeya,,sune xasuxo ranar dakai tafiya yawanci da kwana daya ko a rana tabiyun wani lokacin har ranar daka tafi Ma,sukanxo sau biyu duk a yan'kwanakin,"kuma insunxo bawai xuwan mutunci suke ba a'a suna xuwa xasu fara gasa mata bakar maganganu na juya ce bata haihuwa sede taci,ta sha,tai kashi ta kwanta tai bacci,Sannan bayan wannan bakar maganar kuma Se su lakada mata dukan kawo wuka sosai suke jibgarta agidannan wani lokacin idan nazo rabiyar fadan dani suke hadawa suyiwa dukan ,Sannan wancan tafiyar dakai Ina shigowar dakai kaga goshin Aunty ya kumbura ga parlor dinnan yayi kaca_kaca?! "Capt Adam yakada kansa yaname kallon haule,sosai idanuwansa sunfirfito,hakama jijiyar kansa dukta fito.."haule tacigaba da cewa Yawwa Toh ranar sune sukaxo inda sukai mata duka fitowata daga kitchen kenan naji Kara ashe addah sadeeya ce tahankada aunty tabige kan tiles,"sannan wannan satin yau kenan,daxu sukaxo da safe lokacin Aunty tacemin xatasha magani kanta ciwo yake tace namana faten dankali ,Toh nashiga kitchen nadora yakusa dahuwa kenan segasu sunshigo addah tashigo kitchen tace idan yadahu naxuba masu duka a foodflask kada narage ko kadanne,Sannan tacemin Ina wannan juyar take ?!nace mata batada lapia Tana dakinta,bayan nagama nakai masu seda sukaci suka koshi Sannan suka shiga dakin Aunty ,"nide sena koma kitchen danbaxan iya ganin mexasu mata ba,Se yanxu daka kirani.."wannan shine abinda nasani tsakanina da Allah abba..
"Capt Adam sosai yake kuka harda shassheka ,yadedeta muryarsa yace amma haule meyasa baki taba gayamin haka ba??"haule tace Toh gaskia inaso ingaya maka amma Aunty setace karna soma fada babu ruwana batasan tahadaka da yan'uwanka,shisa kawai banfadaba amma wllhy Ina addua Allah yakawo ranar daxaka gani da idonka,Capt Adam yace Toh shikenan haule nagode xaki iya tafiya amma kafinnan kiramin modu da hannafi yanxu kutaho tare,..ba ajimaba modu da hannafi suka shigo duk suka xauna akasa,"Capt Adam yace Yawwa tambayar daxanmku inasan kugayamin gaskiar lamarin,"shin mekuka sani gameda wa'ennan kannen nawa?!modu shekara tafi 18 muna tare dakai kaikuma hannafi shekara 10 kenan kada dayanku yamin karya tunda baci ko sha suke Baku ba inajinku,"modu yace toh gaskia de mude abinda mukasani wa'ennan mata yan'uwankane Sannan kace mana inde yan'uwanka da yan'uwan matarka sukaxo kada mikokarin hanasu shiga,toh akwai Wata rana inaga ranar asabar ce,Hajia tafito xata unguwa ,jirgi harya tada mota ,sega su sunshigo suna xuwa suka janyota daga cikin mota suka fara duka ,dakyar muka rabasu muka fitar dasu daga gidannan,to bayan sati biyu sesuka Kara zuwa nahanasu shiga shine surayya ta mareni tareda gayamin maganganu marassa dadi,bayan suntafi Se Hajia tafito tabamu hakuri tareda doriyar mukyalesu duk abinda zasuyi Allah Yana sane dakomi Sannan karmu sake mufada maka batason ta hadaka da yan'uwanka wannan shine abinda muka sani."Capt Adam yai shiru Se ajiyar zuciya yake Yana magana azuciarsa Hafsat wacce irin zuciya ce da ita haka duk irin tozarcin dasuke mata amma bataso afadamai saboda kada tahadasu da yan'uwansa?!dakyar"ya'iya furta shikenan xaku iya tafiya nagode..
•✨•
5
"Muryarsa narawa yake fadin" hakika kun tozartani kun ha'inceni kuma kunnuna baku sona bakwa son abinda nakeso,dan kiyayyar dakukewa my Hafsat Wlhy tallahi ba ita kukewaba ni kukewa,Ina ganin ko Allah yakarba rayuwata inada family din dasuke son matata Ashe duk karyace,"dama hausawa sunce makashinka na *****,to yau na Kara tabbatarwa da hakan,banmasan mexan maku ba saboda duk hukuncin daxan dauka akanku mesaukine,me Hafsat tamaku inbama tanada kyakkyawar zuciya ba ,wacece xaku mata haka tai shiru taki fada shekara da shekaru?!!! Badan Allah yaso nashigo ba shirin kasheta kukeba.,harda zama kan ruwan cikinta,ke kuma yasa hannu Yana nuna sadeeya harda rike charger waya kingama dukanta kenanko??
"Toh da farko de ke sadeeya Ina gidan kajina dake hannunki Wanda nace kidinga saida kwan kina aikawa dakudin kaduna,Wanda gwaggo tarufa maki asirine Wlhy bakya kaiwa,Toh kibani mukullin gurina wallahy tallahi nakarba abuna dama bakyauta nabaki ba,"sannan ke surayya tunba yau ba narufa maki asiri shekaru kenan da mijinki yasakeki saki uku narufa maki asiri nabaki gida kike xaman ya'yanki to wallahy tallahi sekin bar gidan nan asatinnan tunda bana ubanki bane,nasan ance hannunka baya rubewa kace xaka yanke ka jefar,to nidai xanyadda nawa hannun tunda yarube wari yakeyi daga yau nayanke...addah surayya taxube akasa tana kuka Dan Allah Yaya Adam kayi hakuri Wlhy banida inda zanzauna Kasan Yaya sameer baxebari nakoma kaduna naxauna ba wurin gwaggo.,.ko kallonta Capt Adam beyi ba sema Danna wayarsa daya keyi ,"sadeeya Ta lallaba tarike kafarsa Yaya kaimin rai Dan Allah kajanye maganar dakai wllhy tanan muke samin abin ci da sha,kasan suhail(mijinta)baya aiki yanxu ankoreshi har kudin makarantar su basmah aciki muke biya.."Capt Adam yajanye kafarsa yai Daria kadanma kuka gani dagake har suhailun,..
"Sannan abu na biyu kada daya daga cikinku,dukkan kuma kada ku Kara takomin kafa kuxo gidana ,babu wannan zumuntar nayanke ta wallahy,addah surayya tasunkuya har kasa Yaya Dan Allah kayi hakuri baxamu sakeba,wani makokon bakin ciki yatsaya amakogaron Capt Adam,dasauri yasa kafa yashureta tafadi kasa tadauje baki Sannan yasa hannu yatsinketa da bahagon mari yaciro belt yahau dukanta,Sannan yakoma kan sadeeya itama yahadata da bango yahau dukanta ,seda yamasu lilis Sannan yajefar da belt din agefe Yana huci,hannu yasa yanuna masu kofa"xoku futa yan'iska marassa mutunci ya'yan Fata,ya'yan Allah bani narokeka,shegu Wanda basuyi halin iyayen suba,Anya Ma ku yan'gidan mune kuwa?!ina tantama inku jinane,bashiri addah surayya da addah sadeeya suka fice kowacce fuskarta tayi suntum,abinka da farare tuni fatarsu tai ja saboda duka..binsu yai abaya yadaga murya"hannafi kubude masu gate su fice yanxunnan,komasu kama dasu kuka sake budewa Gidana abakin aikinku!!!tuni su modu suka aikata hakan,ya yinda su addah surayya suka fice daga gidan,"surayya takalla sadeeya da gefen bakinta yafashe Se jini yake,"yanxu Ina muka nufa?! "Sadeeya tace yanxu abinda yarage Se plan b kuma,yanxu gwaggo xamu samu kawai shine best solution..tuni suka haye Dan sahu yakaisu tashar Kano line inda sukahau motar kaduna ,dama gurin mutum biyu ne kawai yarage,mota tadaga daga kano tadabo tumbin giwa koda mekaxo anfika..xuwa kaduna garin gwamna,garin dabasu da sarki se gwamna..
"Kodah Capt Adam yakoma ciki,kuka yaxauna yanayi shabe shabe sekace karamin yaro,sosai yanayi Yana goge hawayen Yana ci gaba,wannan wacce irin kiyayya ce sekace Wanda suka hada uba daya dasu,shekara kusan 20 suna mata wannan abin?! Amma tace ayi shiru saboda karta shiga tsakanin yan'uwa lalle Hafsat tacika matar kwarai wadda kowa xeso yasamu amatsayin mata uwar ya'ya..yanayi Yana lekawa dakin sosai haryanxu baccinta take peacefully ,yadade Yana kallon kyakkyawar fuskarta Sannan yaja bargo yasake rufe mata jikinta sosai,yarage AC din dake dakin din Sannan yakoma parlor yaxauna,wayarsa yakalla yaga Tana haske seyanxu yatuna Ashe a silent yasakata,7missed calls duk na mutum daya bakowa bane Se abokinsa DR NAUFAAL,tuni yafadada murmushinsa Sannan yakirashi,"aslm alykm mijin husnah,angon naja'atu,.,
"Dr NAUFAAL yayi Daria bayan ya amsa sallaman "na Hafsat badakanka asare kaje gidah kace ya fadi,Ina miko gaisuwata xuwaga uwar gidah ,sarautar mata..
"Capt Adam yace wannan haka yake,Yaya kadawo daga tafiyan ne?!,
"Dr NAUFAAL yace nadawo daxu shysa nakiraka,naxo da albishir ma,insha Allah gobe da safe xanshigo gidan naka..
"Capt Adam yace kanada kyauta kenan babba,Allah yakaymu goben lafiya..Sannan suka danyi hirarsu sukai sallama..sosai Capt Adam yamatsu yaji albishir dinann Yana kuma Fata Allah yasanya alkhari akoma menene..
"Bayan hour 1 da mintina,Hafsat tatashi daga bacci,sosai Capt Adam yatemaka mata tayi wanka tai sallah,inda haule tai reheating faten dankalin,sosai taci takora da ruwa ,Capt Adam yanata mata hira me dadi,Sarai yaki Gaya mata yadda sukai dasu addah surayya ,,,kalamai masu sanyaya zuciya yake fada mata harde tamanta da duk wani abu da yafaru,wunin ranar Yana gidah Se da akai la'asar Sannan yaje masallaci yadawo inda suka Dora daga inda suka tsaya na hirarsu!!!
"Su addah surayya na Isa kaduna suka xayyanewa gwaggo abinda yafaru amma duk karyace na abinda suka fada,sosai suka badawa idonsu kasa suka karkace suna xuba karya idan surayya tagama seta kalli sadeeya ita kuma tadora datata karyar harde gwaggo tayadda tacika tai fam,tadanna Waya takira Capt Adam "Yana dagawa tace lalle yataho kaduna yanxu kome yakeyi ya ajiye Tana nemnsa,lokacin Capt Adam xaune suke shida Hafsat suna kallon tashar CNN sunajin news din Donald trumph"Yana ajiye wayan yamike Yana gyara hula"my Hafsat Bari naje nan kaduna nadawo wai xankarbo sabo nakawowa Baffa imam(kanin mahaifinsu)sosai yafadi hakan danbayasan yadaga mata hankali,Hafsat tai murmushi tuni tagano abinda yafaru Sarai tasan su addah surayya ne sukaje suka xuga gwaggon abinda take gudu kenan,amma yata iya dole tadanna xuciarta tai kamar bata gane ba"murmushi tai Sannan tamike tana gyara masa hannun rigarsa "Toh hayatee Allah yakayka lapia yadawomin dakai lapia agaidamin dasu gwaggon kafin naxo ,"Capt Adam yace insha Allah my Hafsat xan isarda sakonki ,mekikeso na kaduna?! Hafsat tai daria "ba abinda nakeso Se Allah yadawomin da mijina lafiya,"Capt Adam yai murmushi Sannan yadago habarta tareda bata peck a kai,insha Allah xandawo lapia my Hafsat ,amana addua Sannan yasakai yafice..
"Hafsat takoma kan kujera taxauna bayan tayi addua tashafa na Allah yakai duk Wanda suke kan hanyar tafiya lapia yakuma dawo dasu lapia...Sannan taxauna Tana naxarin abinda ke shirin faruwa