Showing 75001 words to 78000 words out of 107296 words
to say anymore you are different from the others,life partner you r MAGNIFICENT...dan Allah kitausayamin Wallahy baxan iya rayuwa bakeba,
Sirririn tsaki Ummi Aisha taja ahankali tana takaicin kalmomin maxa da irin salon yaudararsu akan mata,a hankali take 'ko'karin furta masa magana wadda baxata tadar masa da hankali ba;
"I belong to no one but my self, ashrf kayi ha'kuri pls mu rabu da juna bawai bana....ba wai..,"
Sekuma tasa kuka,ashrraf ya mi'ke daga dur'kushen dayake,
"Noo don't cry pls,pls Kiyi shiru idan wani laifi nayi dan Allah Kiyi hakuri idan wani halina nane beyi makiba nayi al'kawarin xan canxa,dan Allah kibar kukannan pls kinji dan Allah idan kuma nine bakyason gani xantafi sena dawo daga baya i can't take it anymore yanda kike xubar da hawayen nan pls"
" ashraf!muhannad ya...muhannad ya"
"Me muhannad 'din yamaki?!"
"ashraf,muhannad yayi raping 'dina"
Shiru tai tana jiran kalmomin ha'kuri da tausasa zuciya daga bakin ashraf,shirun dataji yayi yawa yasa ta'dago kanta ganin ashraf tai yana girgixa kansa alamar taci amanarsa 'dinnan bece Mata komai ba illah girgixa kan takaici dayai sannan yasa takalmansa yafice ko takan yiwa hafsat sallama bebiba...takaici goma da ashirin ya tsayawa Ummi Aisha ha'de da wani makokon bakin ciki suka dunkule waje 'daya suka tsyar mata da abu a ma'kogaronta harwani jiri takeji Lokaci 'daya kanta yafara ciwo,sabon kuka tafarayi ahankali me tsuma zuciya kukan da bashida sauti sede xubar hawaye..
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiun allahumma ajirni fi musibati wa'aklifli khairn minha"
Shine abinda Ummi Aisha taketa maimaitawa dama ashraf basonta yakeba kenan,tana cikin kukanne hafsat tafuto daga kitchen duk taji abinda sukai ahankali tasa hannu tarungumo tilon yar tata,itama hawayen take,
"Kiyi hakuri ummi Aisha Allah ka'dai yasan abinda ya 'boye duk naji komai kibar kuka Allah ya kawo maki Wanda yafi alkhairi amiin......!"
WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;NANA HAFSAT......
[4/18, 11:58 PM] Asy Khaleel: •✨UMMI_A'ISHA✨•
(THE MAGNIFICENT)
77
©®MISS XOXO
👄
DEDICATED TO;
UMMI_A'ISHA👌🏼
nanahafsat.wordpress.com
•✨•✨•✨•✨•✨•
Kwana 6 kenan da fya'den ummi ,gaba 'daya Ummi Aisha ta shiga tsananin damuwa ta rame manyan idanuwanta sun shige ciki kamar ba itaba,yan makarntar su sun zazzo dan ganin ko lapia?!har professor tajuddeen shima yaxo danjin anya lapia kuwa UMMI AISHA(THE MAGNIFICENT)bata xuwa school,ganin ramewar datayi hakan yabasu tabbacin batada lapia ne,ma'kasudin ramewar tata kuwa yawanci kan tafiyar da ashraf yai jiya bebata amsa bane ta'dau hakan ta ajiye amatsayin 'kaddara da kuma yaudara na halin mazan yau'
•LAMIDO CRESCENT;
Kwance ashraf yake a kan gadonsa yana kallon saman p.o.p 'din 'dakinsa shikansa ya rame kamar bashi 'dinba,wayarsa ce take ringing kamar baxe dauka ba sekuma ya 'dauka dan ganin jay ne ke kiransa,
"Yo man,yh ina gidah ina ciki mana"Sannan ya katse kiran ya ajiye wayan agefe,
Jay ne yashigo cikin 'dakin da sallamarsa,
"Dude thought yau akwai school bakajeba kenan"
"Uhm" ashraf yace hakan yana gyara kwanciyarsa yakalli damansa,
"Wai meke faruwa ne dude?!nifa banganeba,bansan menayiba ko ince bansan meka janyo minba my woman(waliyya)tadena 'daukar wayana tamin text wai kayi deceiving best frnd heart 'dinta Wai itama tarabu dani shiyasa kaganni da safe haka dude ko ishashshen bacci banyiba jiya dan Allah menene?!"
"Play boy Allah yakama ka kenan kaine me playing da zuciyar 'ya'yan mutane thank goodness daka kasa baccin"
"Dude ba wasa nakeba,dan Allah me ya'daku da Ummi Aisha?!"
Ashraf yai shiru yana tunanin shin yafa'da abinda muhannad yaiwa Ummi Aisha ko ya ya?!girgixa Kansa yai alamar hakan be kamata ba,to Kuma ai yana bu'katar shawara nanmade sake girgixa kansa yai yana fezar da iskar bakinsa ha'de da sa hannu yana shafa kansa,
"Ba abinda ya'hadamu" yafa'di hakan with full confidence,
" 'karya ne wallahi akwai abinda ya ha'daku my woman baxata maku 'karya ba ai"
Ashraf yai murmushin da kyakkyawan dimples 'dinsa suka lotsa ya da'de yana kallon jay ganin yadda jay 'din yashiga damuwa sosai after all play boy ne na 'karshe inde yaudarace jay yayi degree akanta segashi yasamu wadda take tamaule da tasa zuciyar,
"My lips lie not jay,I'm damn serious ba abinda yaha'damu da ita kawaide kasan halina sometimes bansan hayaniya shysa ko school bana zuwa"
"To nide pls Kasan yadda xakai my woman ta'dau wayata ko muryarta ne naji"jay yafadi hakan yana marairaicewa sekace Wanda xeyi kuka
"Seka bari inkaje wajenta seka marairaice mata murya ba feminine gender bane abeg bu'de muryanka"
"Pls"
"Naji nace"
"Thanks dude"yakarashe maganar yana mi'kewa tsaye sannan yaiwa ashraf sallama yatafi wajen aiki dayake yariga ashraf din gama degree tun a umyuk yanzu haka aiki yake a ministry of education...
Ashraf ya jima yana sa'ke sa'ke azuciarsa sannan yatashi yashiga ban'daki ya 'dauro alwala yafuto yai sallah raka'a biyu ta nafila da niyyar Allah yasa abinda yasa agaba alkhairine idan ba alkhairi bane Allah yasa abin baxeyiwuba dama kullum yana sallolin darensa yana ro'kon Allah mabuwayi gagara misali kan yaxa'ba masa mafificin alkhairi cikin halin dayake ciki,Kuma dama yakira mahaifiyarsa awaya yaso yaje yasameta ma besamu Lokaci ba seya kirata awaya yashedamata abinda akeciki takumayi na'am tareda sanya albarka yakuma gayawa Hajia aisha(abokiyar xaman mahaifiyarsu wadda suke xaune a wajenta)itama tasaka albarka 'kwarai tayi murna Kuma ta amince kan xata shige gaba tayiwa abban nasu magana..... Ayush 'kanwarsa Ita tashigo cikin 'dakin nasa bakinta 'dauke da sallama ganin addua yake yasanyata jiransa sedata bari ya 'daga hannu xeshafa itama tadaga suka Shafa atare sannan tace,
"Yaya ashraf kazo injisu abba suna parlor"
"Toh kice ganinan"
Seda ya ninke sallayar tsaf ya ajiyeta akan stool Sannan yafice yanufi parlor 'din,gaisheda iyayen nasa yai yasamu gefe daga 'kasa ya xauna,
"Babana yau babu makarantar ne?!"cewar mahaifin nasa
"Akwai abba banajin da'dine shyasa banjeba kuma ma munyi covering revision akeyi"
"Allah yatemaka"
"Amiin abba"
"Duk karame ashraf nace muje asibiti ka'ki,Allah de yabaka lapia" maman tafadi hakan tana jinjina kanta,
"Ba komai mama kawaide major stress ne na makarnta inyai yawa dama haka yake seyasa mutum kullum cikin rashin 'karfin jiki"
"To Allah yatemaka"
"Amiin"
Alhaji kabeer mahaifin ashraf yai gyaran murya yana gyara xamansa,sannan yafara magana;
"Babana munyi magana da iyayen naka(hajia barira da Hajia aisha)kuma na amince 'dari bisa 'dari na abinda sukace,kuma Ina adduar Allah yasanya albarka aciki,kun fahimci junanku da itane Kuma shin mahaifin nata yasan kana Neman 'yar tasa?!dukko dade babu matsala amma Kasan Neman aure acikin wani aure babu kyau a musulunci karmuje da magana muji yarinya anbada Ita ko ko??"yakarashe maganar yana kallon hajia aisha,
"Wannan haka yake alhaji,Kuma nima natambayeshi hakan yace babu matsala yarinya batada wani bayanshi Kuma sun fuskanci kansu gashide hakan yace" Hajia aisha ke fa'din hakan,
"To Masha Allahu,babu de wata matsala ko babana kun dedeta da yarinya??"
"Babu abba" ashraf yafadi hakan Kansa a 'kasa jiyake kamar yafuto yafadi abinda muhannad yamata sede bayasan tona mata asiri,
"To shikenan abu yaxo adede kenan dama kaga gobe asabar semuje in Allah yakymu yanxu xankira su kawu sale nafa'da masu yadda akeciki jibi kuma Insha Allahu xanje katsina can sena gayawa mahaifiyar taka da kuma su baffa na lagos,seka maida hankali kan karatunka ka kuma fara xuwa company 'din kafin ka 'karasa makarantar asan gurbin daxa'a maidakai Allah yasanya alkhairi"
"Amin abba nagode"
"Yawwa babana xaka iya tafiya"
Ashraf ya du'ka yasake godia sannan yatashi yatafi,bayan yatashi yatafi ne alhaji kabeer yake cewa;
"Lalle neman aure me canxa mutane yasunan yarinyar ma?!gashi tacanxa halayyar babana tsaf"
"Ummi Aisha sunanta akwai halin kirki da tarbiyya ai,duk arrogants 'din ashraf gashi yanxu babu dama niya birgeni sosai tunda dama Idan yaro yanuna yanason aure gwara ai masa sekaga idan ba'ayi dinba irin shine yara ke jefa kansu cikin wani hali,ga 'ko'kari Kuma itace kwanaki aka bata award 'din danace maka xamuje aka bata babban title ma 'THE MAGNIFICENT'"
"Hakane sosai nima nayaba da hankalinsa anan 'din,to Allah ya basu xaman lapia Allah yasa matar sace .Ai komai yaxo da sau'ki naji da'di ba ka'dan ba tunda mahafinta amininane sosai Kuma mahaifiyarta munyi xaman mutunci da Ita lokacin da taxauna a katsina"
"Allah sarki hafsatu ba"
Hakade alhaji kabeer suka xauna sunata maganar da Hajia Aisha,sun sanya albarka yafi a 'kirga Kuma sun amince sunyi na'am da abin atake a alokacin yakira yan uwa yafa'da masu dakuma aminansa da xasuje goben suyi tambayar...
•✨•
78
WASHEGARI;
___da safe da misalin 'karfe 10 aminan alhaji kabeer 'kwara biyu sun hallara alhaji ateeku da alhaji barau se 'kanin alhaji kabeerun da ake cewa saje su kenan dayake yayyun alhaji kabeer a katsina suke da xama wasun su Kuma suna yola shiyasa ya hutashshesu yace su zauna tunda sun manyanta.Bayan sun gaggaysa ne alhaji ateeku abokin alhaji kabeeru ke cewar;
"Amma de harda ku'din nagani inaso xa'akaiko base anje Kuma asake komawa akai ba"
"Eh to gaskia da kawai tambayar xamuje kudin kuma sedaga baya xa'a Kai"
Alhaji barau dake gefe yana shan kakkauran shayi yai saurin girgixa Kansa tareda fa'din;
"Yadda ateeku yace shine wannan duk wahalane Ai tambaya Kuma akoma daga baya akai kudi amma yanxu atafi da ku'din kaga anjefi tsuntsu biyu da dutse 'daya kenan ko ya kagani??"
"Hakane kuma hakan yayi,yamafi sau'ki to kamar nawa xa'a Kai kenan??"
"Dubu 'dari yayi alhaji barau??"alhaji ateeku ke fa'din hakan yana kallon alhaji barau
"Eh to ammade da 'dari biyu aka kai kudin zance dubu 'dari ku'din nagani inaso dubu 'dari yafi a mutince"
"Ehh yayi sosai to Allah yashige mana gaba ameen"
Atake alokacin alhaji kabeer yaciro wrapper 1k notes kwara biyu,nande alhaji atiku da barau sukace yabada dubu 'dari inda suka cika hamsin hamsin kowannensu kan cewar sunyi hakanne a ka'dan daga cikin gudunmawarsu,bayan sun gama tattaunawa ne Sannan suka tashi suka shiga mota suka nufi gidansu Ummi Aisha,ashraf dake le'kensu ta window se asannan yasaki labulen yakoma yakwanta akan gadon wani 'bangare na zuciyarsa cike da farin ciki da Kuma hagunta'
•SARDAUNA CRESCENT;
Captain adam ne zaune akan kujerar parlor 'dinsa dayake asabar ce babu aiki kansa asama da alama tunani yake dama duk kwanakin nan haka yake tunane tunane sunmai yawa shiyasa dayaje asibiti tashin farko akace bp dinsa yayi high yarage damuwa,damuwar kuwa aksari akan Ummi Aisha yake yinta,kusan kullum shi kadai haka yake yiwa kansa magana yanzu yarinyar nan shikenan yaron nan yacuceta ya latata mata rayuwa kenan?yanxu waye xe'aureta,addua kuwa kullum seya yiwa iyalinsa kan Allah yatsaresu yakuma karesu daga sharrin masharranta amiin,yana cikin tunaninsa yaji ana knocking 'kofar,
"Waye?!"yafadi hakan yana xaune saboda bayasan tashi shiko parking 'din motar da akai bejiba saboda tsabar tashin hankalin dayake ciki,
"Damuna....."
Da sauri captain adam ya mi'ke yana murmushi sanin waye,sannan yasa hannu yabude kofar,
" 'dan kabiruwa"sekuma yasa hannu yarufe bakinsa
ganin yan ajinsu da shekaru kenan basu ha'duba
"Su ateeku nake gani ko ido nane?!"
Daria aka hau yi sannan suka shiga cikin parlor 'din gaggaysawa sukai tayaushe gamo?suka hau tsokanar junansu kowa ana fadar yarintarsa lokacin suna barewa college,captain adam yakira hafsat awaya kan tasa akawo drinks da snacks takuma 'dora abinci yayi ba'ki na musanman,da axama hafsat ta mi'ke tashiga cikin 'dakin Ummi Aisha don takirata tatayata da wani aikin,lokacin xaune Ummi Aisha take akan gadonta tana karanta littafin 'Americanah na chimamanda ngozi adichie'
"Ummi Aisha" amminta ta kirata bayan tashigo cikin 'dakin
"Na'am ammi"tafadi hakann tana ajiye littafin hannunta,
"Ya kan naki yayi sau'ki?!"
"Yayi sau'ki ammi gashi harna 'dakko littafi ina karantawa"
"Allah ya 'kara sauki dama wani abin xaki kamamin a kitchen baffankine yai ba'ki yace adafa masu abinci"
"Toh ammi"
"Yawwa yanxu kiramin habule(me wankinsu)yaxo yakai masu drinks 'din"
Mi'kewa Ummi Aisha tai tafita kiran habule tare suka shigo dashi ya'dauki drinks yakai ya sake dawowa ya'dau snacks yakai dayake weekly hafsatun keyin snacks ta ajiye saboda irin haka shi yasa captain adam din baya shiga fargaba saboda yasan tana fitar dashi kunya barin girki da sauri xata gama Kuma tayishi me 'dan'dano atsaftace cikin foodflasks 'cikin awanni 'kalilan hafsat da Ummi Aisha suka gama ha'daddiyar jollof rice 'dinsu datasha duk wani ingredients daya kamata sannan sukai sauce na kayan ciki da vegetables,gefe 'daya Kuma soup sukai na kaji dayasha tafarnuwa da kuma gashashshen kifi dayasha dankali da 'yar sauce harwani lemon 'bawo akai slicing agefe,lemon gargajiya sukai na zo'bo mesanyi da 'kan'kara se ha'din salad dayasha 'kwai da sauran Kayan ha'di gefe 'daya Kuma egg into egg sukai da kuma lemonade na ayaba(don't mind me I'm hungry*lol*)suka 'debi na ba'kin abokan captain aka zuba a tsaftatattun warmers sannan suka 'debi nasu inda akajera akan food holder akakai part 'din captain adam se hira suke sha bayan habule ya jere musu abincinne suka hau kan dinning sunaci se asannan sukai tsit da alama dadda'dan abincin hafsat yafara aiki a ma'kogaro,bayn sungama cin abincinne sunyi godia alhaji ateeku ke fadin;
"Mufa neman aure muka zo,munxo neman auren 'yarmu awajenka"
Captain adam yai murmushi,
"To awajena kuma?!wacce daga ciki kasan yaran biyune"yakarasa fadin hakan yana dubansu amma azuciarsa babu wadda yakawo se baby kay'
Alhaji barau yakalli alhaji kabeeru,nan alhaji kabeer yace,
"Ummi Aisha de ta farin itace mukaxo nemawa ashraf aurenta"
Murmushin dole captain adam yai yana kallon alhaji kabeer,sekuma yai shiru yarasa abinda xe ce,
"Tanada wani ne a 'kasa?!"alhaji barau yafadi hakan ganin shirunda captain adam yayi
"Babu kowa kawai de..."bekarasaba alhaji kabeer yai saurin katseshi
"Base kace komai ba damuna,yarinyar nan koni inada ikon aurarda ita ko bandashi?!"
"Kanadashi mana 'dan kabiruwa"
"To saboda haka,duk wani abu ashraf komai yafadi Kuma babu matsala Allah yasanya albarka munji mun amince nasan Idan ana neman aure ba'asan a'boye komai Kuma duk munsan yarinyar nan munsan halinta saboda haka mun amince" alhaji kabeer yai saurin fa'din hakan axatonsa ji yake captain Adam xece basu shrya bane ko makamancin hakan,
Jin hakan captain adam yai xaton ashraf yafada masu halin da Ummi Aisha ke ciki,sosai yaji da'din wannan abu yakuma 'Kara godewa Allah azuciarsa,
"To shikenan Allah yasanya albarka aciki banida bakin godia sede nace Allah yasanya alkhairi Amiin"
"Mune da godia damuna Allah ya albarkacesu amin yasanya albarka acikin auren"
"Amiin"
"Sannan da ku'din xance mukaxo fa dan mu ashrye muke"
"To to Shikenan sede nika'dai xankarbi kudin kenan?!"hannu yasa a aljihu yaciro wayarsa yakira yaya sameer 'din hamdalah yayan yayi najin wannan abu don yaji xancen Ummi Aishan Kuma shi dama 'daukar hakan yai ya ajiye a matsayin kaddara,yakuma ce yakarbi kudin babu komai Allah yasanya albarka,
Atake awurin akai komai suka ciro kudi suka bayar captain adam yace yayi yawa dakyar ya yarda ya karba don sunce Wallahi baxasu koma dasu gidah ba,sannan akatsaida biki kafin axumi Idan ankawo lefe se a tsaida ranar 'daurin aure da saurin shagalin biki,shima yabada tukwici da kuma sauran abun motsa baki sannan suka mai sallama suka tafi cikeda jin da'din anbasu aurenta shima yakoma part 'din su Ummi Aisha zuciyarsa fes nadaga abinda yafaru yanxu yakuma ajiye hakan amatsayin wata baiwace daga rabbus samawati,
•✨•
79
Yana shiga da sallamarsa yasamesu a parlor suna kallon sunnah tv,amsa sallamar sukai inda Ummi Aisha ta mi'ke xata bar wajen captain adam yai saurin dakatar da ita,
"Tsaya akanki zanyi magana"
"Toh Baffa"Sannan ta nemi waje a 'kasan carpet ta xauna gaba daya gabanta faduwa yake don batasan wacce maganar bace,
"Nace menene tsakaninku da ashraf 'dan wajen alhaji kabeeru?!"dukkoda yasani so yake ya tabbatar da hakan daga bakinta
"Baffa...."sekuma tai shiru,
"Saurayin tane hayatee"Hafsat tafadi hakan don tasan Ummi Aisha baxata iya bawa uban amsa ba tanajin kunya,
"Kunyi magana dashi ne kan ya turo iyayensa?!"
"Baffa bamuyi ba,yazo de nan shekaran jiya saboda yaga bana zuwa makarnta Kuma bana picking calls,shine yaxo yaji ko lapia?!nace masa lapia qalau shine nafa'da masa abinda yafaru to kumade ko magana beyiba yatashi yafita"
"Wani abunne yafaru Hayatee??"
"Dana kiraki nace ki 'dora abinci nayi ba'ki ai alhaji kabeerun ne yaxo da 'kaninsa da abokananmu 'kwara biyu inda sukaxo nemawa shi ashraf 'din auren ita Ummi Aishan maganar da nake miki ma ga ku'din aure sunkawo dubu 'dari biyu kudin nagani inaso da ku'din xance muntsaida biki ma kafin axumi Insha Allahu tunda ba wani bincike xa'ai ba nasan mahaifinsa shima yasanni yaro yanada abinyi danma yayiwa Kansa shirme datuni ya hada degree dinsa"yakarashe maganr yana ciro ku'din a 'aljihunsa ya ajiye akan center table din dake tsakiyar parlorn..
"Alhmdulillah ya rabbi for the unlimited blessings lalle"take awajen Hafsat tai sujjada tana hawaye,
Ita kanta Ummi Aisha dake gefe wani nauyayyan abune yatafi mata daga ma'kogaro xuwa ciki ta tsaida hakan a amtsayin damuwarta ce ta fa'da,ita kanta tarasa mema xatai don da'di kamar taje ta rungume iyayen nata haka takeji,take wata zuciyar tafara raya mata to kuma ai ashraf 'din bece mata xa'axo tambaya ba hasali ma tunda yatafi basuyi waya ba ko 'dan text 'din daya sabar mata da,to me hakan ke nufi?!Allah ka'dai yabarwa Kansa sani,captain adam ya jima yanawa Ummi Aisha nasiha sannan yatashi yafice xuwa masallaci,nanne hafsat ta 'dora da tata nasihar daga inda captain 'din yatsaya,hawaye sha'be sha'be kwance a fuskokinsu na farin ciki,bayan hafsat tagamaiwa Ummi Aisha nasiha tajanyo waya tafara kiran yan 'uwa da abokanan arziki kan kawo ku'din tilon 'diyar tata da akayi ana gama gayawa Mjay tace gatanan xuwa ba a waya xaai xancen ba,ba'afi mintina ka'dan ba ta 'karaso dayake se bayan sallah xata koma can capetown 'din bayan sungaysa ne Mjay tabi Ummi Aisha da kallo Ita Kuma tasaukar da kanta 'kasa irin kunyar nan,
"Ja'ira harkin fara kunyar amarcin?!"
Itade Ummi Aisha shiru tai tana daria 'Kasa 'kasa,
"Kingani ba ko ya hafsa dama nace maki Allah yana tare da me gaskiya gashi adduar da muke Allah ya 'karbi kukamu"
"Hakane kuma to Allah ya 'Kara karemu da kariyarsa ameen"
"Ameen ya rabbi"
"kince kafin azumi ko?!"
"Eh haka baffansu yace to Kinga kuwa ba doguwar rana xa'asakaba kenan"
"Ai nima na'ki jinin saka doguwar rana jide bikina sati biyu akasa kintuno?!"
"Natuno lokacin da cikin Ummi Aisha ne"
"Tabbas hakane ashe fa ba'a haifeta ba"
"Ba'a haifeta ba mana lokacin de da cikin yatsufa a lokacin ni inaga bayan bikin da sati biyu ne nahaihu"
"Tabbas natuno lokacin Ina can banxoba seta skype naga baby"
"Ehh"
"Bari tun wuri mu fara dashi