Showing 72001 words to 75000 words out of 107296 words
meke faruwa ba da alama koma menene babban tashin hankali ne wannan tuhumar dayakewa UMMI AISHA duk yadda akai akwai wata a 'kasa,
"Hayatee wai menene ni kunsani a duhu"
Dafe kansa yai yana girgixa kansa,se shima yasoma hawayen yana shesshekar kukan,
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiun"
Shine abinda hafsat take furtawa,tashi tai tadawo kusa dashi tasa hannu ta rungumoshi tana dafe da bayansa tana bashi ha'kuri,
"Bansan menene ba amma koma meye dan Allah Hayatee kayi hakuri,ka yafemata dan Allah kasan Bakada ishashshiyar lapia likita yahanaka yawon damuwa,dan Alllah badan niba kayi hakuri mu kar'bi koma menene amatsayin kaddara dan Allah"
Cikin muryar kuka captain adam ke bata amsa
"My hafsat,UMMI AISHA ta 'bata halinta,ta 'bata tarbiyyar da muka'dau shekaru muna mata,ta 'bata sunana,ta 'bata rayuwarta,ta 'bata mutuncin ta,ta rushe duk wani mutunci da kamala da daraja da ake gani akanta a matsayinta na 'ya mace kuma budurwa wacce batai aure ba wacce xatakai mutuncinta da martabarta gidan mijinta"
"Innalillahi wa'inna ilaihirrajiun,Allahumma ajirniy fi musibatii wa'aklifli khairin minha"
Shine abinda Hafsat ta fa'da tane dafe da kirjinta,
Jakarta da cd disk 'din su captain adam yaciro yasaka akan center table,sannan yabawa Hafsat disk 'din,
"Sakashi yanxu"
"Hayatee baxan iya ganiba"
"Saka Ita tagani tunda baxata fa'da da bakin taba"
Jiki da hannu na rawa hafsat ta karba cd din tasakashi cikin dvd sannan takoma taxauna ita kanta hawayen take,wannan wacce irin jarabawa ce daga rabussamawati mabuwayi gagara misali?!komawacce irice Allah yabasu ikon cinta danko qur'ani aka bata xata iya rantsewadashi kan UMMI AISHA baxata ta'ba aikata hakan ba,gefe 'daya kuwa UMMI AISHA ce ke kuka ha'de da ajiyar xuciya,a take cd yai loading yafara viewing video dede lokacin da UMMI AISHA tafito da number 'dakin suite 20 da yadda gashin kanta yai kaca kaca da yadda take bleeding da yanayin tafiyarta uwa uba yadda rigarta take a kacaccale,da cikin parlor 'din da kan gadon da yadda jini yai staining take hafsat ta 'dauke kanta tana hawaye shi kansa captain adam 'dauke kansa yai yana hawayen shima,
"Ki gayamin kedawa kuka aikata wannan 'danyen aikin?!"
UMMI AISHA bata bashi amsa ba illah kukanta daya tsananta,
"Okay fine!ai nasan data dawo baxata rasa cemaki wani abinba"
Yafadi hakn yana kallon hafsat dake share hawaye da tissue,
"Wallahy batacemin komai ba saboda lokacin dana dawo kwance nasa meta naxata ma kanta ke ciwo ko xaxxabi saboda yanda jikinta yai zafi,nan nabata pain killer bayan tasha ne alokacin ka aiko shafi'u naje 'dakko sa'kon kafin nadawo bacci ya 'dauketa shine kadawo katarar tanayinsa"
"Nace waye yamaki haka?!"
Yafa'di hakn a tsawa ce.
"Baffa,ni ban..ba.."
"Tambayarki nake ba bayani nace kiyimin ba"
"Ya muhannad ne"
Ido suka ware dukansu daga shi har hafsat 'din,
"My hafsat kirashi yaxo har gidannan,se a ha'da ayi masu aure Allah ya kyauta"
Hannu narawa hafsat ta'dau waya ta kira muhannad har sau uku be 'daukaba,
"Kira mahaifiyarsa"
Dialing number Hajia sakeena tai mahaifiyar muhannad 'din tafara kiranta ,ringing biyu ta 'Dauka a handsfree hafsat tasaka kamar yadda captain ya umarceta datayi...!
•✨•
75
Wannan page 'din nakune; 'Kawata billyn abdul❤tareda tawajena khadija candy,ban manta dake ba rano theorist,kina raina walicious🍂
______"Assalamu alykm!"
Hafsat tai sallama tana 'ko'karin kwantar dakanta kar Hajia sakeenan tagano kuka take,
"Wa'alykm salam maman UMMI AISHA,ko ince Maman muhannad,ya ya kikaje gidah?!yanxu nakeso nakiraki kinrigani"
Dariar datafi kuka ciwo hafsat tai ahankali dukdande tanuna hankalinta a kwance yake dukkoda cikin zuciyarta Banda 'kuna da 'bacin rai ba abinda ke damunta,
"Alhmdlh yaya mai jego?!"
"Lapia qalau Alhmdlh,tana miki bangajiya kafin taxo itama"
"Allah sarki ina amsawa,nace muhannad nanan kuwa?!"
"Yau kuma ni ake tambaya"
Tafa'di hakn tana daria,sannan tacigaba,
"Lalle naciri tuta kenan,yau 'dan gidan naki kuma ni ake tambaya,be da'de dashigo waba,bakisameshi a waya bane?!"
"Ehh Wallahy na kikkira be 'daukaba nace kila ko yashiga rungutsumin suna"
"Muhannad 'din dabayason taro ai 'dakinsa yashiga ya kulle,amma barin dubo maki shi,shima be da'de da shigowaba"
"To Shikenan nagode"
"Yawwa"
Sannan sukai sallama ko wannen su ya kashe wayar,Hajia sakeena na ajiye wayar ta mi'ke tai hanyar 'dakin muhannad 'din,knocking tafarayi don tasan 'kofar a rufe take,a malale muhannad 'din yake akan gado yayi ruf daciki yana kallon bango idonsa biyu,
"Yasss"
Yace dayaji knocking 'din yayi yawa,
"Bu'de min 'kofar yanxu"
Da sauri ya mi'ke jin muryar mahaifiyarsace yasa key ya bude kofar yana sosa 'keya,
"Kullum de cikin kulle 'kofa sekace marar gaskiya"
Takashe maganar tana shiga cikin 'dakin,
"Banason hayaniyar sunan nanne shysa"
"Babu wani hayaniyar suna,kullum haka kake,kaiba namiji bane Meyasa baxaka fitaba?!kasande saboda kai ka'dai ranka baxamu 'ki yin shagalin suna ba kaima fa'de kake.ina wayarka take?!"
"Waya?!"
Se asannan yatuno da wayarsa ma da sauri yasa hannu yana duba kan gadon can karshen gado wayar take a silent take ga missed calls nan rututu na mutane,
"Gata"
Yace yana mi'kawa mahaifiyar tasa
"Mexanyi da Ita?! Maman UMMI AISHA ce ta kikkiraka baka 'daukaba shine takirani ko lapia ?! Nace kadawo gidah ma yanxu seka kirata kaji ko?!"
Tafadi hakan tana ficewa daga 'dakin
"Toh"kawai yace
Sannan yasa hannu yana dialing number hafsat 'din ringing 'daya tadauka bayan sungaysa take cemasa yaxo yanzu,tayi mamaki 'kwarai dataji muhannad 'din yacemata gashinan muryarsa fes kamar kullum babu alamar tsoro ko rawar murya irin na wanda ya aikata rashin gaskiya,
"Yace gashinan xuwa"
Hafsat tace da captain adam haka,
"Ke kintabbata shine kuwa?!"
captain adam ke tambayar UMMI AISHA hakn batace komai ba illah 'daga kanta datai sama haryanxu ba tadena kukan ba idonta ya kumbura yayi sumtum Lokaci 'daya kamanninta sun canxa kamar ba Ita ba,
Ba awani 'dau Lokaci ba muhannad ya 'karaso fuskarsa fes se murmushin daya saba yake,kamar kullum suka gaysa da kowa yanayi yana kallon UMMI AISHA da idonta sumtum,da Kansa captain adam ya mi'ke yasaka video 'din nan yana kallon mood 'din muhannad da ko ka'dan becanxaba,bayan video 'din ya 'kare muhannad ya juya yana kallon UMMI AISHA kallon tuhuma kallon Meyasa xata aikata wannan mummunan aiki kamar ita mace me kamala wadda duk inda nutsuwa,tarbiyya da kamin Kai na 'ya mace yakai UMMI AISHA ta kai hartaso ta xarta danata irin mu'amalat 'din,
"Muhannad ko xan iya sanin kafin kuje gidan suna Ina kukaje da UMMI AISHA?!"
"Ni kuma baffa"
Muhannad yafadi hakan yana kallon UMMI AISHA da ke kallon gefe,
"Eh!kai"
"Baffa nide nasan naxonan 'daukarsu UMMI AISHA inda tatafi ta shrya Ita kuma baby kay muna hira da Ita,alokacin kaina yafara ciwo ko ammi banwa sallama ba natafi gidah"
"Kama nufin baka 'dauki UMMI AISHA kunfita ba?!"
"Ehh baffa da de dasu xamu fita sekuma natafi saboda banajin da'di"
"Ki kace dashi kuka fita"
Captain Adam ke tambayar UMMI AISHA hakan
"Wallahi Allah baffa dashi muka fita alokacin kan nasa yana ciwo,ya muhannad katuno har kacemin da abokinka xamu gaysa a ni'imah semu wuce gidan suna seku.,,se..,ku..ma"
Bata 'karasaba tashiga matsinancin kuka,
"Anyi haka muhannad?!"
"Gaskia bani bane baffa"
"Allah shine shahidi,kana nufin bakasan komi kan wannan video 'din ba?!"
"Wallahy Allah baffa bansaniba"
Nanfa muhannad yadinga rantsuwa yana rantse rantse kanshi befita da UMMI AISHA ba har baby Kay aka kira shin kotagansu sunfita tare?!itama kaikaicewa tai tana xubo nata 'kararrakin kan Wallahy batasaniba lokacin ita suna tare da 'kawayenta ma,aka kira masu gadi suma tasu amsar itace sallah suke lokacin da muhannad din yafita,i adole captain adam yacewa muhannad yaje ya sallameshi,kukan da UMMI AISHA tai babu kama hannun yaro,kukane take yinsa wanda xe tsuma zuciyar duk Wanda ya saurara kuma dole ya tausaya mata,
"Yanxu menene abinyi anan hayatee?!"
"Wallahy banida tacewa tunda nide bana gidah balle in fa'di abinda nagani kuma ankira sheda agabanki tafa'di yadda akai,shin mexance akai?!ko kuwa caxanmai dole shine?!yau da annunoshi a video 'dinnan Wallahy tallahy har court semunje to babushi babu kuma Wanda aka nuno face ita,idan ma 'Karya yake shida Allah,wata shari'ar se alahira ku kuka 'dau gaskiya da aminta kuka 'dora masa yaxamto kamar wani 'dan uwanku aiga irinta nan"
"Yanzu babu yadda xa'ayi?!"
"Akwai kuwa yadda xa'ayi,nide nine mahaifinta Kuma nayanke shawara aure xanyi mata aure shine yaka maceta"
"Amma Hayatee kanajin abinda yace yanxu dawa xa'a ha'data?!"
"Dawa kuwa xan ha'data ko so kike tunda 'ya tace nace lalle se ARFAAN KO MUS'AB wani ya aureta acikinsu?!sam bada yawuna ba yadda take 'ya ta wanda nine silar kawota duniya haka suma nakejin su a jinina tunda 'ya'ya nane da mahaifinsu da ni Uwa 'daya uba daya muke shiya saki mama na kama,babu xalunci a tsakaninmu wanima baxanyi masa hakaba ballantana su"
Mi'kewa tsaye yai yana gyara karin hularsa ya 'dora akansa,sannan yafara fa'din;
"Alfarma 'dayace xanyi mata alfarmar kuwa bakomai bace fyace aure,Wallahy baxan xauna da Ita cikin gidan nanba kafin axumin nan tafito da mijin aure ayi mata ko kuma na ha'data da duk Wanda naga dama kamar yadda hadisi yace budurwa a xa'ba mata miji bazawa ta xa'ba da kanta"
Sannan yasa hannu yanamai nuni da UMMI AISHA
"Kinci sa'a nasan 'kaddarace ta ubangiji ta fa'domiki da wallahi hukuncin daxan xartar miki harki koma ga ubangijinki baxaki manta daniba,saboda haka shawarar daxan baki shine ki bu'de Idonki sosai Ki hana Idonki bacci tunda duniya takoya maki hankali Ki dage da addua Allah ya xaba maki miji Wanda yafi alkhairi domin aurar dake shine mafificin alkhairi......!"
Sannan yasakai yai ficewarsa be jira yaji daga bakin UMMI AISHA ba ko Hafsat 'dinsa
•✨•
Duk naga comments 'dinku kan cewar nasa anyiwa UMMI AISHA fya'de,wasunku sun nuna bankyautaba wasu sunce hakan danai shine dede domin basusan fa'dakarwar daxanyi akaiba,wasuma sunce sundena karantawa😅nide baxaku ji komai daga bakina ba tunda bangama littafi ba...fatana Allah yabani ikon 'karasa abinda nadakko tun farko amiin,
Ina Kuma fatan xaku bani ha'din kai....
WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;NANA HAFSAT.....
[4/18, 11:58 PM] Asy Khaleel: •✨UMMI_A'ISHA✨•
(THE MAGNIFICENT)
76
©®MISS XOXO
👄
DEDICATED TO;
UMMI_A'ISHA👌🏼
nanahafsat.wordpress.com
•✨•✨•✨•✨•✨•
Tunda captain adam yafice Ummi Aisha da Hafsat suka bude sabon shafin kuka,Ita Ummi Aisha kukan ta akan meyasa muhannad xe mata haka duk yardar da ke tsakaninsu amma yaci amanarta haka?!ita kuwa hafsat nata kukan tanayinsa ne kan abinda muhannad yaiwa tilon 'diyar tata da Kuma yadda rayuwarsu ke shiga halin tsaka me wuya,har lokacin bacci basu dena kukan ba sede suyi su tsagaita su cigaba babu me tausar wani dakyar Hafsat tadanne zuciyarta taiwa Ummi aisha nasiha me shiga jiki tareda bata wasu addu'oi daxata dingayi saboda kariya daga shaidan dakuma sharrin masu sharri..,
Bayan kwana biyu da abinda yafaru kafin kace me Ummi aisha ta rame tashiga damuwa tunma baga hafsat dinba itama tata ramar ta bayyana sosai sefa mama da mjay ne ke tausar su,Ummi Aisha ko abinci bataci kullum se amminta tamata dagaske sannan take iya tsakula taci yawanci tafishan oats shima dan bayadda xata yine,ko makaranta ta'ki zuwa aganinta kowa yanxu yasan xancen 'kawayenta sunxo sunyi kiran amma fafur ta'ki komawa, ashraf ma yakira ya kira taki 'dauka daga karshe ma kashe wayar tata tayi tun Hafsat na matsa mata kanta shrya taje makaranta Kar awuceta a abubuwa har ta kyaleta domin intace tajema kukan takeci gaba dashi ba ''kak'kautawa shiysa kawai ta kyaleta tasaka mata ido tana Kuma mata adduar Allah yakawo 'karshen wannan abu da yafaru,gaba 'daya tacanxa kamar ba Ummi aishan ta ta da ba ta rame taxama kmar wacce aka canxawa kamanni ,dama haka magajiya keso Itako zaman iddar dake kanta badamunta yaiba dukkoda saura wata biyu da 'yan kwanaki ta tattara tabar gidan,Ita kawai rayuwarta tafuso ta bu'de ido taga rayuwar Ummi Aisha da hafsat acikin ba'kin ciki(Allah ya karemu daga sharrin masu sharri)
A ranar muna_b taxo da safe lokacin baby kay nashiri xata makaranta bayan sun gaysa muna_b ke tambayar baby kay;
"Tana xuwa makarantar kuwa?!"
"Bata xuwa ko'ina ai ko 'kofar gidah"
"Ah'to dama ina xata da wannan abin kunya dole se xaman gidah ai,Yaya asharf din kuna magana kuwa?!"
"Ba lefi muna magana a matsayina na 'kanwar budurwarsa ba,sister in law yakecemin"
"Se ahankali xata fita ransa"
"Allah aunty kullum seya tambayeta fa wai yana kiranta bata 'dauka wai tama kashe wayan nata gaba daya lapia kuwa?!nace ai sunyi tafiya daxan gaya mashi abinda yafaru sena fasa saboda karma yace xezo gidah ya ganta yaji tausayinta"
"Gwara da kika fasa tunda anga yayar kice xa'ace da'di kikeji har sugano wani abin kibari ahankali xamu fitar da komi kowa yagani Kinga shima daga lokacin xata fita ransa"
"Sosai kuwa,barin tafi sch aunty"
Takarashe maganar tana gyara mayafin jikinta
"To Shikenan sekin dawo"
Baby Kay nafuta muna_b tadawo kusada magajiya,
"Yaya 'kawata lapia kika kirani bade jikinneba?!"
"Ai asibiti xaki rakani dubi gashina gaba daya ya xaixaye babu komi akaina"
Tafadi hakan tana bu'de 'kwanyar kan nata da babu ko silin gashi kamar kan namiji dayasha 'kwal'kwal,jimami muna_b ta mata na ganin yadda kan nata yaxama sannan suka fita xuwa asibitin standard dake kan titin tarauni,bayan likita yagama gwaje gwajensa kenan ya dago ya kalli magajiyan datai zuru da idanuwa 'can tace;
"Likita me result 'din yabayar?!"
"Dafarkode xan lissafo signs na ciwon ki duk Wanda kike irinsa seki gayamin ko?!"
"To dr"
"Ko kinajin new onset or change akan yanayin ciwon kan Ki?!"
"Sosai dr kusan kullum seya canxa"
"To,ciwon kan naki gradually yake becoming more frequent and more severe?,sannan kawai kina samin kanki cikin nausea ko vomiting?!"
"Wallahy duk abinda ka lissafo inayi 'daxun nanma nagama amai"
"Allah ya kyauta to yanayin ganinki fa shin kina ganin abu blurred ko double vision?!sometimes harda pheripheral vision?!"
"Wallahy Ina gani da naxata ma yanayin ganinane ya 'Karu harxan koma wajen optometrist 'dina"
Shiru yai yana rubuce rubucensa 'can ya 'dago yana kallonta;
"Shekara nawa kikai kina cancer?!"
Baki,hanci,Ido haka magajiya da muna_b suka saki suna kallon likitan kafin muna_b tai karfin halin magana;
"Likita kaf gidansu ba mai cancer fa"
Likitan yai murmushi kafin ya ajiye biro din dayake rubutu
"Karki sako jahilci mana aciki,karki manta ko yatsu da Allah ya tashi yinsu seya yisu wasu sunfi wasu,sannan komai ki kaga yafaru da bawa mu'qaddarine daga Allah,ze kuma yiwu genetically tasamu gashinande Allah ya kadai yabarwa Kansa sani"
Itade magajiya shiru tai tana kallonsa takasa kodah motsi,dan ko amafarki bata ta'ba kawo wa kanta cutar cancer ba,sannan likitan yacigaba da magana;
"Ki godewa Allah ma dayasa brain cancer/tumor ce,sede taci 'karfin ki sosai"
"Yanzu dr surgery xa'a mata ko me?!"
Muna_b ke tambayar hakan,
"Treatment de na irin cancer 'dinsu should be individualized for each patient,sannan shekararta nawa?!"
"49"
Muna_b tabashi amsa
"Toh kuma bayan cancer batada wani ciwon?!"
"Banajin akwai se mahaifa da aka cire mata"
"To fa,to yanzude gashi ga size din tumor din da inda yake a kan nata dakuma grade na yadda tumor 'din yaci,gaskia tayi sakaci da bataxo da wuri anyiwa gurin riga kafi ba yanxu gashinan tumor din yacinye gashin kanta tas,yanxu xamu fara bata chemotherapy treatment tunda abin yayi worst daga baya Kuma xamu yi mata surgery radiation"
"Toh dr"
Magajiya in Banda kuka ba abinda takeyi najin abinda likitan yace Wai cancer,har sukabaro asibitin bata dena kuka ba da wanne xataji da cire mahaifartata da akayi koda sabon tashin hankalin da taji yanzu Wai brain cancer'?!har suka koma gidah bata dena kuka ba yanxu me xatagayawa Yaya adam?!dakyar muna_b tamata sallama tatafi,wunin ranar haka magajiya tadinga kuka kamar wacce akaiwa mutuwa,(ka'dan ma kika gani da yardar Allah,duk 'karshen me sharri da yardar Allah baxeyi kyauba)
Da yamma lis Waliyya tai sallama part 'dinsu Ummi Aisha,bayn sungaysa da Hafsat tatashi tabasu waje,Waliyya tajima tana kallon Ummi Aisha ganin yadda ta rame ta jeme kamar ba 'Ita ba,
"Tawan dan Allah banasan kukan nan dakike,jiya muna waya da jamil ashraf dinki ya karba Wai ance kinyi tafiya?!nace wacce irin tafiya kuma amma xanduboki nagani"
"Shi yasani"
"To shikuma meya miki bawan Allah dashi?!"
"Ke 'kyaleni da xancen maxa pls nacire su kaf a policy 'dina"
"Wai kina nufin dagaske muhannad....ya"
Bata 'karasaba Ummi Aisha ta katseta
"Na miki 'karyar dana saba"
"Meyai zafi tawan nayi shiru amma dama tunfarko ni muhannad 'din nan kam se a slow kuma kinyi shirme da kika bishi ke ka'dai"
"Hakama baffa yace,to saboda Allah aibansan gaibu ba kuma Allah zemana hisabi ranar gobe 'kiyama"
"Nace kode yanada ta'bin hankaline??"
For the first time tunda akai wannan abin se yanxu Ummi Aisha tai daria,sosai taci daria harda siraren hawaye,kafin tabawa Waliyya amsa;
"Xe iya yiwuwa,tunda nanfa yaxo ya 'karyatani gurin baffa,naji mamaki 'kwarai matu'ka kuma koyanxu nai sallah nasa goshina a 'kasa senace Allah yabimin ha'k'kina"
"To yanxu mu sako maganar ashraf 'dinki Wallahy guy 'dinnan yadamu yana sonki soyayyar da ko a littafi Wallahy da wuya a samu irinta"
"Kai,innalillahi wa'inna ilaihirrajiun,bestie kina shiga min rayuwa dayawa nace maki nacire maxa kaf a zuciyata gaba 'daya banasan zancensu"
"To kince baffa yace maki lalle kifito da mijin aure aganinki waxa kice??"
"Addu'ata kullum itace Allah ya za'bamin abinda yafi alkhairi kawai,nikam nagama tsorata da maxa xaki trusting namiji kibashi zuciyarki daga karshe yasa kafa yai fatali da Ita kuma babu yadda kika iya fyace rungumar 'kaddara"
Hakade sukaita hirarsu itada Waliyya suna bawa junansu shawarwari kan yadda xasu 'bullowa al'amarin...dakyar da da'kyar'kyarewa Ummi Aisha ta yadda ashraf yaxo,
___Washegari da rana ashraf yaxo bayan sungaysa da ammi tatashi tabasu waje setabar 'yar 'kanin babanta kawai wata 'Yar karamar yarinya da taxo hutu jiya anakiranta da sajeedah,Ummi Aisha bayan gaisuwa bata karawa ashraf magana ba se shine yaketa faman yiwa sajeedah wasa dayagade abin bana 'kare bane yace;
"Life partner kinyi shiru wannan ba halinki bane,Wai meke faruwa dake kwana biyu?!ko makaranta bakya zuwa why?don Allah nikam kinsani cikin wani Hali Dan Allah Kiyi magana karki azabtar da xuciata pls"
Ummi aisha looked up quickly batace dashi komai ba dama kanta a 'kasa yake,ahankali take kallon kyakkyawar fuskar ashrf dake kallon gefen tv he was sad and in pain gaba 'daya shikansa ya rame kamar ba shi ba,a hankali murya narawa take masa magana;
"I'm sorry ashraf niyanxu bandace da kaiba"
Ashraf ya ware ido yana kallonta lokaci 'daya yanayinsa ya canxa,
"WTF,Life partner you belong to no one but me forget your beloved muhannar yake kowa?!nasan akanshi kikace haka"
Sekuma yasakko daga kan kujera yasa gwiwoyinsa a 'kasa idonsa yaciko taf da hawaye muryarsa na rawa yake mata magana wanda ba Ita ba har 'karamar yarinyar dake gurin sedata tsaya tana kallonsu;
"You don't have