Showing 36001 words to 39000 words out of 122205 words
bugawa tamkar za ta tsaga ƙirjinsa ta fito dummm!.
Cikin damuwa ya ce "Lowalli, sai ka ƙara gudu fa, kar ya mace mana, bugun zuciyarsa raguwa fa yake yi. Kuma ka san idan ya mace mana mun shiga uku mun lalace"
Lauwalli ya jinjina kai yana ƙara gudun motar. Ya ce "In sha Allah a raye za mu kai shi, ba za a samu matsala ba. Dan dai ka ƙi yarda ne, da na ce mu tsaya a Asibiti".
"Kai dalla ka daina maganar tsayawa a wani Asibitin nan. Ka yi ka hanzarta mu cika umarnin nan, mukaɗai ake dako"
"To shikenan, mun kusa in sha Allah" ya yi maganar yana ƙara gudun motar.
****
Antin Yusra ce ta kalle ta, ta ce "Yusra duk wannan kwalliyar fa? Ta karɓar baƙon ce?"
"Eh mana Mami, yana hanya ma ai" ta yi maganar tana tafiya ɗakinta, ta fesa turare.
Wayarta ce ta fara ringing, ta ɗaga wayar tana murmushi ya ce "Gani a layin"
"Duba lambar gidan, za su buɗe maka"
Ya ce "Ok"
Bayan mintuna goma sha biyar, ta fito ta ce "Mummy na tafi"
"To a gaida baƙon, ya tabattar mana da alkhairi"
Kawai ta fice tana murmushi. Tana zuwa ta gan shi a tsaye a cikin falon, yana kallon ƙaton frame na hoton mai gidan, da yake retired soja.
Ganin abin take tamkar a mafarki, wai Sagir ɗin ta ne a gabanta.
Jin ƙamshin turarenta ne ya sanya ya waiwaya.
Da gudu ta ƙarasa inda yake ta faɗa jikinsa.
Babu tunanin komai, Sagir ya ƙanƙame ta a jikinsa, bar siririn mayafin da ta yafa a kanta, yana zamewa gyararren gashin kanta, da yake ta ƙamshin mayuka ya bayyana.
Ya din ga shafa bayanta yana murmushi, kawai ya ji tana sheshsheƙar kuka. A ɗan rikice ya ce "Lafiya, kuka kuma Yusra?"
Ya zauna tare da ita a jikinsa, ya ce "Ina ta murna zan zo na gan ki, amma in zo ki din ga kuka, ko ba kya son ganina ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To mene ne"
"Ka daina so na, tun da ka sake ni ba ka ƙara nema na ba" Ya ɗago fuskarta su na kallon juna yace "Da na daina son ki, ba zan zo nan ba Yusra, kin san yadda rabuwarmu ta kasance, ban daina sonki ba, ban kuma daina tunanin ki ba"
"Almost three years, ba ka sake nema na ba"
Sagir ya marairaice murya ya ce "To yanzu ba gani na zo har nan saboda ke ba? Haba wifey" ta zumɓura baki cikin ɗabi'arta ta shagwaɓa. Duk da ya zuciyarsa na tunatar da shi, tare da gargaɗin sa a kan Yusra ba muharramarsa ba ce, amma ya kasa yaƙar kansa, ya ƙyale ta a jikinsa yana jin yadda ya yi kewarta.
"Talk mana, na zo kuma kin haɗe rai?" Tashi ta yi daga jikinsa, ta zauna a kusa da shi ta ce "Ya hanya?"
"Alhamdillah, ki na lafiya ya jikin naki?"
"Da sauƙi"
"Kin warware?"
Ta girgiza kai ta ce "Bayan ƙin yadda ku ka yi da gaske ba ni da lafiya. Sai ga shi na haɗu da wata Nana, ita ma tana irin ciwon da nake ji, ai ita ta san ba ƙarya nake yi ba."
Ya ce "To yanzu dai duk ba wannan ba, i miss you Yusra, irin sosai da sosai ɗin nan fa"
"Bayan ka yi aurenka, ba wani missing ɗina da ka yi" ta yi maganar tana tsiyaya masa lemo a cup ta miƙa masa.
Ya karɓa ya kai bakinsa yana tsare ta da ido. Ta kalli screen ɗin wayarsa da ya kawo haske, hoton Haidar ya bayyana a kan screen ɗin. Ta ɗauki wayar tana kallon yaron ta ce "Waye wannan?"
"Ɗanki ne Haidar, recently ma ta kuma haihuwa ɗan ya rasu" ta yi masa wani kallo, da bai tantance na mene ne ba ta ce "Da tuni nima wataƙila na haihu"
Ya yi murmushi ya yi shiru, yana cin abincin da ta zuba masa. Cikin hikima ya karkatar da zancen suka ci gaba da hira.
Wayarsa ce ta fara ringing, ta ajiye masa ganin hoton heart a kan sunan. Ya ɗaga wayar tare da yin sallama "Hello love"
"Ka sauka lafiya?"
"Alhamdillah am good dear"
Shukura ta ce "To sai ka dawo, Allah ya tsare mana kai, take care"
Ya yi murmushi ya ce "In sha Allah dear" wani abu ne ya tokare wa Yusra a ƙirji, ta zuba masa ido.
Ya ajiye wayar, bai kalle ta ba ya ce "Yusy, kin san na yi missing ɗin girkinki over?"
Jin ta yi shiru ya sanya ya ɗaga kai ya kalle ta, ya ga tana hararsa. Ya yi murmushi ya ɗebo Abincin ya kai bakinta.
Ta murguɗa masa baki ta tsuke fuska.
"Smile, haba sweetheart" ta buɗe bakin ya saka mata Abincin. Haka ya ribace ta, suka ci gaba da hira.
A nan ya yi sallar la'asar, sannan ta fito raka shi.
A jikin motarsa suka tsaya, tana yi masa wani irin kallo mai ƙayatarwa.
"Tom sai yaushe zan dawo?"
"An jima kaɗan"
Ya yi murmushi ya sake kallon ta ya ce "Yusra"
Ta ce "Na'am"
"Yaushe za ki dawo gidana, ji nake kamar na ɗauke ki, na tafi da ke Kano, ina kewar ki sosai da sosai. Yaushe za ki dawo gidana?"
Ta girgiza masa kai ta ce "Ba zan dawo ba"
Cikin mamaki ya ce "Saboda me?"
"Ka auri wata, kuma Hajiyarka ba za ta bari na dawo ba, su Mami ma ba za su bar ni ba, kuma ma haryanzu ban gama warkewa ba"
"Haryanzu ki na so na?" Ta kalle shi ta sunkuyar da kanta ƙasa.
"Idan ba kya so na, me yasa ki ka nemi lambata, ki ka kira ni? Kuma har ki ka ba ni dama na zo?" Ta sunkuyar da kanta ta ci gaba da murza yatsun hannunta.
"Yusra Sagir ɗin ki ne fa, ɗago ido kalle ni" Kawai ya ga hawaye na bin fuskarta.
"Sagir ɗina, da ya rabu da ni, saboda ba ni da lafiya ba" Ta yi maganar tana sheshsheƙa. Ganin babu kowa a gurin da suke, ya sanya ya janyo ta jikinsa, ya ɗago kanta yana kallon idonta ya ce "Yusra, ki na so na haryanzu?" Ta yi shiru hawaye na ci gaba da bin idanunta.
"Ki na so na har yanzu, shi yasa ki ka neme ni. Dan haka batun ina da aure, Hajiyata ba za ta bari ba, 'yan uwana ba sa son ki, haryanzu ba ki da lafiya, duk ba ta taso ba. Za ki dawo gidana a karo na biyu in sha Allah. Haryanzu ina son ki Yusra"
"Amma...
"Babu amma tsakaninmu, believe me zan dawo da ke gidana in sha Allah" Jikinta ya yi sanyi. Ya cika ta a hankali, ya shiga motarsa. Ta tsaya ƙyam tana kallonsa, shi kansa da kyar ya tafi, tamkar ya ɗauki Yusra ya tafi da ita.
Har ya kama hanyar Kano, zuciyarsa cike da tunanin ta ina zai fara. Dan shi har ga Allah yana son matarsa, ba a son ransa ya rabu da Yusra ba. Yanzu kuma da ya ganta, gaba ɗaya ya ƙara rikicewa ba abin da yake sai tuno soyayyar da suka yi, daga saurayi da budurwa zuwa auren su.
Ko da ya je gida, Shukura ta karɓe shi tana yi masa sannu da zuwa.
Amsa mata ya yi yana kallon ta, kafin ya ƙaraso ta kira shi ya fi sau biyu, yana zuwa hatta ruwan da zai yi wanka ta tanadar masa.
Ya cire kayansa ya shiga wanka, kamar ta san ba zai iya salla ba, sai ya tsarkake jikinsa, saboda rungumar da ya yi wa Yusra.
Tana cikin tattare kayansa, hancinta ya ji ƙamshin turaren da ba na sa ba a jikin kayansa. Turarensa ɗaya ne da ta san shi da shi. Jikinta ne ya yi sanyi, domin ta daɗe da karantar alamomin rashin gaskiya a tattare da shi. Wani abu ne ya soki zuciyarta amma ta yi ta maza ta haɗiye tare da ajiye kayan.
****
Aka shiga kwana na biyar, ba tare da jin ko ɗuriyar Sayyid ba.
Nana duk ta fita hayyacinta, ba ta iya cin abinci, ba ta bacci. Ga Uwani tun tana rarrashinta, ta koma yi mata faɗa tana ganin ta ƙi tawakalli ta ci gaba da addu'a.
Ga shi ta hana ta komawa gidan nasu, a nan gurinta take zaune tare da ita.
Yanzun ma Uwanin ce ta miƙo mata kofi da fura a ciki ta ce "Ungo ki samu ki sha furara nan Nana, ko ɗan cikinki ya samu wani abu shi ma. Rayuwa ba za ta yiwu a haka ba kina zaune babu Abinci, ga juna biyu ba. Idan wani gurin mutumin nan ya tafi, idan da rabo zai dawo ai"
Nana ta karɓi kofin, tana ajiyar zuciya. "Maza ki shanye, kan na fito daga banɗaki" Nana ta jinjina kai tana kallon kofin.
Uwani na shiga banɗaki, Nana ta ɗauki mukullin da aka kulle gidansu, ta tafi.
Gani take kamar tana shiga za ta tarar da shi a inda ta bar shi. Ƙofar dama a lanjare take aka rufe ta.
Ta shiga ɗakinsu, amma ta tarar wayam babu kowa a ciki.
Ta kalli kan katifar su, ta ga abin hiraminsa na rawani a kai. Ta durƙusa a kan gwiwoyinta, ta damƙi hiramin nan, da yake ta ƙamshin turaren sa. Tamkar ta damƙi Sayyid ɗin. Cikin kuka ta ce "Haba Sayyid, daga cewa na je na dawo, sai ka tafi ka bar ni? Haba Sayyid yau kwananka biyar ba ka tare da ni. Da mutuwa ka yi na san wannan hukuncin Allah ne, dole na tawakalli, amma me yasa zaka tafi ban san halin da ka ke ciki ba. Haba Sayyid Haba Sayyid Nana ce fa" ta din ga soki burutsu tamkar zararriya. Wani irin kuka take yi mai haɗe da gunji da ƙunar zuciya.
Ba ta san lokacin da Uwani ta shigo ba, tare da abokiyar zamanta Sabuwa ba, sai ji ta yi ta taɓa ta ta ce "Nana shi ne sai da ki ka fito ki ka zo ko? Ba na ce kar ki fito ba?"
"Uwani. Sayyid ya tafi ya bar ni, na zata mafarki nake yi, me yasa zai tafi ya bar ni?"
"Ke ki ji mini 'ya da rashin ta ido, yo ina zan san dalilin da ya sanya ya tafin ni? Ke ba za ki iya dakewa ki kama kanki ba, idan guduwa ya yi fa?"
Sabuwa ta ce "A'a Yaya, su fa yaran birni su na nunawa junansu kulawa, ya za a yi mutum mara lafiya a neme shi a rasa, ki ce hankalinta ba zai tashi ba? Kina kallon yadda take tiri-tiri da shi take nula da abin ta ke kin san ba ƙaramin so take yi masa ba, ai da tausayi"
Uwani ta ce "Kuma haka ne, amma tun da shi ya tafi nima jikata nake yi wa kar wani abu ya same ta, ga ciki. Ke Nana kuma ba garinsu ya tafi ba bai gaya miki ba? Ba kin ce ɗan Nijar ba ne?"
"Ba shi da lafiya fa, ba zai iya wannan tafiyar ba"
"A'a kar ki ce haka, idan ki ka bibiya ma, can ɗin ya tafi, amma yanzu ki yi haƙuri ki tashi mu tafi gida"
"Uwani, dan Allah ki yi mini alfarma ki bar ni na kwana a nan"
"To ya za ki kwana a gida ke kaɗai haka ake yi?"
"Ni dai dan Allah ki bar ni a nan, wallahi da safe zan dawo na yi miki alƙawari"
"A'a sai dai na turo yarinya ɗaya ta tayaki kwana" Nana ta amince da hakan, aka turo mata yarinya.
Tuni yarinyar ta yi bacci, Nana kuma kwana ta yi aikin kuka.
Lokaci Lokaci, sai ta yi tasbihi tare da ajiyar zuciya.
Washegari da sassafe Uwani ta zo ta kawo mata abin karyawa.
Yadda idanun Nana suka kumbura, ya sanya ta fahimci Nana ba ta yi bacci ba.
"Wai ni Nana, babu wani wanda za ki kira, ki tambaye shi ko yaje? Ko kuma wani guri da za ki je a duba?"
Jiki a sanyaye Nana ta girgiza mata kai. "To shikenan sha kunun nan da ƙosai, kar su huce"
Nana ta karɓi kunun tana kurɓa a hankali, ji take tamkar tana shan magani, saboda wani irin ɗaci da take ji kunun yake yi mata a bakinta. Amma saboda ba ta son faɗan Uwani, haka ta din ga shan kunun nan da ƙyar.
Ta ɗan saci kallon Uwani ta ce "Uwani, ina ga gobe in Allah ya kaimu zan shirya na koma Kano"
"Gurin wa?" Uwani ta jefe ta ta tambayar.
Nana ta ɗan yi shiru, Uwani ta ce "Gurin wannan masoron Ubannaki da bai san ciwon kansa ba balle ya san naki? Ya kasa tallafa miki da larura ta samu mijinki, yanzu ne idan kin koma zai tsinana miki wani abu? Ga cikin fari ke ba sanin kan abubuwa ki ka yi ba, ga wannan shu'umar matar tasa, da ƙafa duk dama ba tsayawa za ta yi ta kula da ke ba?. Ban ƙi ba ki kira shi, ki sanar masa abin da yake faruwa a matsayin sa na ubanki ba, amma ba dai ki koma wannan gidan ba. Ki yi zaman ki a nan ki haihu, ki yi biƙinki idan mijin naki bai dawo ba, a san abin yi"
Tabbas Uwani tana da gaskiya, idan ta koma gidansu rayuwarta ta sake komawa baya, ta san babu wani abin kirki ko kulawa da za ta samu a gidan, wataƙila ma a kore ta. Ummi kuma ta yi mata ɗawainiya da yawa, tana jin nauyin ta sake koma mata da matsala.
Kuma ba ta ji a ranta za ta iya sake ko nufar hanyar gidan Alhaji Zailani ba, saboda yin hakan tamkar cin amanar Sayyid ne, kuma ita ba dolensu ba ce, da za ta je ta ɗora musu ɗawaniya. Dan haka Uwani na da gaskiya. Amma zamanta a nan ɗin ma, shi ma dai ɗawainiyar ce.
Ta sake ɗago kai ta ce "To ina son na je Bauchi gurin Mamana"
"Kai Nana ki na da gardama, gurin nawa ne dai ba za ki zauna ba, kin ƙallafa rai tun da mijinki ya bar garin nan kema sai kin bar shi?"
"Ba haka ba ne Uwani, ina da dalili dan Allah ki bani damar hakan"
"Shikenan Nana, ba zan matsa miki ba, Ubangiji Allah ya tabattar da alkhairi, amma ki bari kamar nan da sati ɗaya, ki ɗan ƙara samun nutsuwa. Nima na lalubi na mota na baki"
"Ai ina da kuɗin mota"
"Nima na san ki na da kuɗin motar, na ce zan baki ai" Nana ta ja bakinta ta tsuke.
****
Jamila ta yi shirin fita, tana tsaye tana latsa wayarta ta ce "Baba har ya fita ne?"
Mama ta ce "Tun da uwar kashinsa ta cika ya fita. Da dai bai ci ba da yanzu yana nan yana bin bango yana zabga hamma yana faɗa da ƙadangaru da bokitai"
Jamila ta basar ta ce "Sonake ya bani cikakken kwatancen Buda, zan saka a kai ni, na je na ga Nana"
"Wai ba za ki bar maganar Nanan na ba ko Jamila?"
"Mama meye laifi idan na je na gan ta ne wai?"
Nasiru ya ce "Laaa rannan kuwa wannan ɗan uwan mijin nata, da suka zo a ka kaita gidanta ranar biki, suka zo shi da wasu mutane, suka ce mini wai yanzu Nana a ina suke. Na dawo daga makarantar allo, na ce musu tana Buda can garin su Baba, shi ne ya ce na gaida Baba"
Mama ta ce "Ikon Allah, amma yarinyar nan ta ce 'yan uwansa an neme su an rasa. Kai Nana muguwar makira ce ta ƙarshe"
Jamila ta ce "Amm na tafi sai na dawo"
"To Allah ya tsare, a gaida Hajiyar"
" Za ta ji" ta amsa a taƙaice ta fita.
Nana ta zauna ta haɗa kayan da za ta buƙata a cikin jaka guda ɗaya.
Tattara sauran guri ɗaya, ta ɗauki jakar gurin Sarkin Baka, da kuɗin Nijar ɗin da suke ciki. Ta tattara sauran kuɗin da suke ɗakinta, tana tunanin ta tafi ko da Uwani ba ta sani ba.
Ta tattara kayan kitchen ɗin ta, ta ce wa Uwani sayarwa za ta yi.
"Me yasa za ki sayar da kayan ki Nana?"
"Kawai kuɗin nake buƙata ne"
"Gaskiya ba za ki sayar da kayan nan ba, ki bari ranar kasuwa, zan kai Tinkiyata kasuwa, na baki kuɗin amma ba za a sayar da kayan ba" Gaba ɗaya Nana ta ji ta damu yadda ta ɗorawa Uwani ɗawainiya.
"Uwani kar ki sayar da Tinkiyarki dan Allah, gara a sayar... "Za ki rufe mini wannan dogon bakin naki, ko sai na kwaɗe ki? Ke ki ka sani na sayar? Ke dai akwai gardama"
Babu yadda Nana ta iya, haka ta haƙura sai ranar kasuwa, aka sayar da Tinkiyar. Uwani ta ɗauki dubu talatin a kuɗin ta bawa Nana ta ce "Ban san iya adadin kuɗin da ki ke buƙata ba, amma ga wannan kya jalauta. Dan Allah ki kula da kan ki Nana, duk inda ki ka je idan kin ga akwai matsala, ki dawo mini nan ni zan riƙe ki na kula da ke" Nana ta din ga juya kuɗin, ta kalli Uwani idonta fal hawaye ta ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka miki da mafificin Alkhairi na gode"
"Babu komai, Ubangiji Allah ya sauke ki lafiya, ya bayyana mijinki cikin aminci. Nan ma za mu ci gaba da jiran jami'an tsaro ko za a samu wani labari daga gurinsu. Allah ya bayyana shi"
Nana ta amsa da Amin. Jin washegari Nana za ta bar garin, ya sanya 'yan uwa, suka din ga kawo mata abin alheri cikin mutunci da karramawa, tare da yi mata fatan alkhairi.
Washegari da sassafe, Nana ta yi sallama da su Uwani, aka ɗauke ta a babur aka kai ta tashar ƙauyen. Aka kaita Garko, daga nan ta hau motar Kano. A Kano ta hau motar da za ta sada ta da garin Bauchi.
Tsawon awanni huɗu da aka shafe, ana tafiya a motar, babu abin da Nana take yi, banda tunani ta saƙa wannan ta kwance wancan. Tunaninta a wani hali yake ciki, ya jikinsa? Su waye suka ɗauke shi? Mene ne makomarta idan bai dawo ba.
Lokaci-lokaci ta kan shiga hijjabinta ta yi kuka, ta share hawayenta.
Da ta sauka a tasha ƙarfe sha biyu na rana, ta samu abin hawa, har sunan unguwar da Mamanta take ta sani, sai dai ba ta san takamai ina ne gidan ba. Shi ma daga tashar zuwa garin da maman nata take, sai da aka yi tafiyar awa ɗaya da rabi. Ƙafafun Nana duk sun kumbura, da ƙyar take jan su. Ta ɗaukko wayarta ta kira lambar Anty Fati, ta ji ba ta shiga. Ta kira