Showing 15001 words to 18000 words out of 122205 words
gida mu yi yaya ne? Nan ɗin ba dai magani ake baka ba ana kula da kai, komai sai ka nuna kai ba a kyauta maka ba, ba a iya ba haba dan Allah"
Jiki a sanyaye ya ce "Yi haƙuri, Allah ya baki haƙuri" daga haka ya sunkuyar da kansa.
Sai kuma jikinta ya yi sanyi, ta zauna a kusa da shi, tana tunanin ta yi magana. Ta ga yana share hawaye.
Cikin damuwa ta ce "Alhaji kuka ka ke yi? Dan Allah ka yi haƙuri raina ne a ɓace, amma dan Allah ka yi haƙuri"
Ya yi mata shiru, gaba ɗaya ta rikice ta rasa abin da za ta ce. Raudah ce ta turo ƙofa hannunta da towel ta ce "Daddy guess what?" Ta miƙa masa narkeken jaririn da Fadila ta haifa.
Hannunsa na karkarwa ya riƙe jaririn ya ce "Another Muhsin" ya yi maganar yana murmushi.
Ya din ga yi wa jaririn kiss, yana shafa shi kamar ba a taɓa yi masa haihuwa ba.
****
Fafur Sayyid ya hana Nana zuwa ko nan da can, har aka yi azahar.Uwani ta sake aiko musu da dambu, ta ce a cewa Nana ba za ta zo ba, sai ta zo da kanta.
Cikin damuwa ta ce "Sayyid dan Allah ka bari na je, na ji kiran me take yi mini" fafur ya sha kunu ya tsuke fuska.
Babu yadda Nana ta iya, ta zauna ta ƙi fita. Ta zazzage kayansu, tana ƙara gyara musu, ta fito da kayan wankin gashinsa, da turarrukansa da duk wata sai su Habu sun sayo sun kawo. Ta ɗaga kai ta ga ita yake kallo, ta ɗan yi murmushi ta haɗe su a guri ɗaya da combs ɗin sa na taje gashi.
Sai yamma bayan sallar la'asar, ta yayyafawa tsakar gidan ruwa, ta share shi.
Ta yi shimfiɗar tabarma a tsakar gidan, ta saka wa Sayyi fululluka ta kamo hannunsa zuwa waje.
Ya zauna, ta ɗaukko mayafin rawaninsa ta yafa masa a kansa.
Babu jimawa sai ga Uwani ta zo, tana faɗin "Tun da ba za ki zo ba, ni ga ni na zo da kaina"
Nana ta ce "Ba ƙin zuwa na yi ba Uwani, yanayin jikinsa ne sai a hankali, shi yasa ban fito ba"
"Koma dai mene ne gani na zo ai" Ta kalli Sayyid ta ce "Sannu ko" ya jinjina mata kawai.
"Dama kiran ki nake yi, na ji idan akwai wani abu da ku ke buƙata?"
"Eh, ina son yin sayayya ba mu da fitila sai ta waya, da kuma 'yan kayan buƙatu"
"To da kin sanar, ai da na saka yara sun raka ki, dama zan ce miki kuma idan an kwana biyu, yakamata ki zo a ɗan zagaya da ke cikin dangi, su san kina garin nan, tun da dama ba zuwa ku ke yi ba, dui ba sanin ku aka yi ba"
Nana ta jinjina kai ta ce "To in sha Allah"
"Wai ni Nana ina Mai jidda kuwa?"
"Tana can Bauchi inda take aure"
Uwani ta ce "Kuma tana zuwa?" Jiki a sanyaye Nana ta girgiza kai.
"Ai dama na san babu lallai ta zo, ko dan saboda baƙin halin Isa. Ai ya bamu mamaki. Ita ma tun da suka rabu ba ta sake zuwa garin nan ba. Kuma yakamata mu je na zagaya da ke, har inda danginta suke a nan"
Cikin mamaki ta kalli Uwani ta ce "Danginta kuma?"
"Ƙwarai da gaske, tushen Maijidda garin Buda ne. Kakanninta 'yan nan garin ne, can wajen unguwar Wanzamai, ƙarewa ma a nan garin suka haɗu da babanku. Ai kakarta aka raina a Bauchi, aka haifi babarta da ita a can.
Har an saka mata rana, suka zo garin nan, ke ma Babanki ya zo gida, suka haɗu a dandali. Aka yi ta ɗauki ba daɗi suka ƙulla soyayya. Ga shi can garinsu an saka mata rana da wani, ina ga shi ne mijinta na yanzu da take aure. Asali tun kan ta auri babanku da shi aka fara saka mata rana. Kakarta ta ce sai an warware wancan baikon ta auri babanku, ko ba komai sa din ga zuwa gida a kai kai. Haka aka mayarwa da wancan kuɗinsa ta auri babanku.
Ya Babanku ya so ta sosai da sosai, kuma aka ƙulla auren nasu da tunanin hakan ya ƙara kawo zaman lafiya a tsakanin zuriyarmu da zuriyar wanzamai kin san a tarihin garin nan ba zaman lafiya ake ba.
Kuma dai cikin ikon Allah sun fara zamansu lafiya gwanin sha'awa, amma Allah ya ƙaddara rabuwar su."
Nana ta yi shiru tana tunanin, kamar ta san wani abu mai kama da wannan labarin da Uwani take ba ta, amma sam ta kasa tunawa. Gaba ɗaya hirar ta Uwani ta gundure ta, saboda ta san shi kansa Sayyid a takure yake, ba ya son mutane ko kaɗan, balle uwa uba dogon surutu. Ita kuwa Uwani tamkar an ƙona ta a ka ko gajiya ba ta yi. Babu wanda ya taɓa ba ta wannan labarin, sai yanzu babu wanda ya taɓa gaya mata cewar mahaifiyarsu tushenta a garin Buda yake, sai dai kamar ta san labarin da Uwanin ta bata.
"Ga wata 'yar rama na zo muku da ita, sai ku ci kafin Abincin dare ya sauka. Wai shi mijin naki kurma ne?"
"A'a ai kin ga ba shi da lafiya ne"
"Eh gaskiya ne, Allah ya ba shi lafiya, amma a ina ki ka samo Buzu haka? Ni wai anya ma labarin da Rabi ta din ga bayar wa ranar bikinki nan gaskiya ne? Abin dai da mamaki. Allah ya ba shi lafiya bari na tafi, dan Allah idan ki ka samu lokaci kya zo a je a gaggaisa.
"To in sha Allah zan zo"
"Yauwwa, zan din ga turo miki yara, idan da aike kya din ga ba su, duk 'yan uwanki ne, 'ya'yan 'yan uwa ne. Kuma ki kwantar da hankalinki duk abin da ku ke buƙata ku sanar mini, da yardar Allah ba zai gagara ba"
Nana ta ce "In sha Allah, mun gode sosai da sosai"
"Ba komai, ki yi haƙuri ki riƙe mijinki ki kula da shi, sai ki ga kaf ayyukan ki, Allah bai karɓa ba, silar wannan jinyar ta sa ki shiga aljanna, a yi ta haƙuri yayata"
Nana ta tashi ta raka ta, ta ce "In sha Allah"
Ta yi ƙasa da murya ta cewa Nana "Dan ubanki, ki din ga ɓoye mijinki, kar ki bari 'yan mata su din ga zuwa su na kallon sa." Uwani ita iya rage muryarta kenan, amma Sayyid na jin ta. Nana ta ɗaga kai suka yi ido huɗu, ya yi murmushi yana sunkuyar da kai.
*****
Alhaji Fatuhu, farin cikinsa ya kasa ɓuya, duk da halin rashin lafiya da yake ciki, idan aka zo duba shi, sai ya yashe haƙoransa da sukaɗai suka rage farare a jikinsa.
Alhaji Zailani ya ƙura wa jaririn ido, ya kalli Alhaji Fatuhu da yake ta yashe baki.
Hajiya Sa'a ta ce "Kai Fatuhu. Sai ka ce ba a taɓa yi maka haihuwa ba, ji yadda ka ke washe baki, kana fama da kan ka"
Hajiya Suwaiba ta kwaɓe baki ta ce "Abin da na gani kenan"
Alhaji Zailani ya ce "A'a ku bar shi ya yi, ɗan mutum fa, kyauta ce Allah ya ba shi, da duk Duniya babu mai ba shi. Ni ba gani ba 'ya'yan duk babu sai biyu ne suka tsaya." Ya yi maganar yana zuba wa jaririn ido, yana tuna na Shukura. Tun da yake harkar ƙungiya, bai taɓa bayar da jinin da ya tsaya masa ya kasa mantawa ba, sai na Shukura. Mussaman idan yana tuna irin baƙar wahalar da ta sha.
Ya kalli Fadila, da take ɗakin a zaune, ga jego tana yi, amma ta tare a Asibiti da ɗanyen jaririn da ko suna ba a yi ba.
Ya yi ajiyar zuciya ya ce "Wane sunan za ka saka masa?"
"Muhsin ɗina zan mayar" ya yi maganar muryarsa ɗauke da rauni.
Hajiya Sa'a ta ce "Wai an din ga saka Muhsin ɗin kenan?"
"Sunan mahaifin Fadila ne, shi za a mayar mu ci gaba da kiransa Muhsin, ni na yi mata alƙawari shi yasa. Na so Muhsin ɗina da ya rasu sosai da sosai. Na ji zafin rashin sa, sai dai ina tausayawa wannan Muhsin ɗin. Ya zo lokacin da mahaifinsa ba shi da komai, ba zan iya ɗaukar nauyinsa na kula da shi ba. Wataƙila ma kafin ya yi wayon sani na na rasu. Ga shi ko hakika ba zan iya yi masa ba" ya yi maganar hawaye na zubowa daga idanunsa.
"Haba Fatuhu, ya haka? Dan dai Hakikar da za ayi wa jaririn nan, ka san ba za ta gagara ba, amma ya za ka zauna kana kuka kamar ƙaramin yaro, a gaban iyalinka da 'yan uwanka hakan bai kyautu ba ai".
Alhaji Fatuhu ya ɗago idanunsa da suka yi jawur ya ce "Zailani. Ka san me nake ji kuwa? Gidaje da motocin hawa nake da, ina kyautar maƙudan kuɗaɗe ba tare da na ji komai ba, da abu ya dame ni, zan sai ticket na tafi umara. Ina da shaguna dukiya Allah ya yarje mini, bayan gwagwarmaya da na sha ta rayuwa. Astagfirillah ba ƙarar Allah nake kawowa ba, ko rashin imani da ƙaddara ba, ina jinjina girman lamarin Ubangiji, kuma ina jin babu daɗi ɗa na na cikina, ba zan iya saya masa ko wando ba"
Fadila ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haƙuri. Mu na murna sauƙi yana samuwa, ga shi ka na ta magana sosai da sosai, kukan nan karya mana zuciya yake yi. Kuma da ka yi mana a baya, yanzu kuma da Allah ya kawo jarrabawa shikenan sai a yi haƙuri"
Su na nan zaune, sai ga ƙanin Baban Fadila, ya zo duba Alhaji Fatuhu ya kuma jaririn Fadila, wanda shi ne waliyyin Fadila. Sai dai shi ma ya tsorata da ganin Alhaji Fatuhu.
"Alhaji haka jiki ya zama? Subhanallah Allah ya baka lafiya"
"Amin kawu, amma jiki ya yi kyau Alhamdillah, tun da ina ta magana"
"Haka ne, amma menene takamaiman abin da aka ce ya same ka ne?"
Fadila ta ce "Haryanzu ba a gano takamaiman mene ne ba, yau a ce ƙodarsa ta kumbura, gobe a ce ko cancer ce, an yi gwaji ba ita ba ce. An yi gwajin zuciya shi ma lafiya ƙalau"
Cikin damuwa ya ce "Amma Fatuhu ana haɗa maka da na addini kuwa? Ka san muna da ido ne ba na ganin gari ba. Mussaman ku da ku ke shahararrun mutane da Allah ya ba wa wadata. Yakamata a yi na sihiri da shaiɗanu"
Alhaji Zailani ya ce "A'a ga likitoci su na kula da shi, ya za a yi a ce kuma a kawo wani abu daban? Magungunan gargajiyar nan kashe mutane suke yi ai, tun da ba auna su ake yi ba".
Alhaji Fatuhu ma ya ce "A'a ba wannan ba ne, wa ya damu da ni da zai yi mini sihiri. Larura ce kawai kuma likitoci na kula da ni"
"Kai, kalle ni da kyau. Duk bokon ka, nima ɗan boko ne, kuma na san ilimin addini, amma sihiri da shaiɗanu gaskiya ne. Tun da aka yi Annabi Sallallahu alaihi Wasallam sihiri, duk duniya ban ga wanda ba za a yi wa ba.
Ciwo ya ƙi ci ya ƙi cinye wa ai akwai alamar tambaya, ga lalacewar dukiya lokaci guda. A dai tsananta addu'a. Ya gama bambaminsa ya fita. Alhaji Zailani ya din ga ziga Alhaji Fatuhu, tare da kushe magungunan gargajiya. Ba tare da jin nauyin Fadila da take gurin ba.
Ya gama soki burutsunsa, ya tashi ya yi musu sallama, tare da cewa zai aiko da abin hakika.
Har ya kusa ƙarasa wajen motarsa, ya waiwaya ya ga Hajiya Sa'a ta nufo shi, ya tsaya ta ƙarasa.
Ya ce "Ya dai?" Ya yi maganar yana kallonta.
"Zailani"
"Na'am
"An sauke ɗan uwana daga shugabancin 'yan kasuwa an ɗora ka, ka saka an dawo da shi Asibitin nan, ƙarƙashin kulawarka, an ce a yi masa maganin gargajiya ka haƙiƙance kana kushewa.
Kar ka kuskura na tarar da sanya hannunka, a cikin wannan abubuwan da suke faruwa da ɗan uwana"
Ya gyara tsayuwarsa ya yi murmushi ya ce "Babu sanya hannuna a ciki. Ina ƙoƙarin zama aboki mai halacci ne kawai.
Sannan ki daina mazewa kamar ke ɗin mai ƙaunarsa ce, bayan sadaukar da 'ya'yansa maza da ki ke yi"
"Duk da haka, munin abin da na yi bai kai wanda ka ke aikatawa ba, ka fi ni sanin kai da me da me ka sadaukar, dan haka ka kiyaye ni". Ta juya ta koma. Bin bayanta ya yi da kallo, ya ji wani abu ya tsirga masa, tabbas idan Hajiya Sa'a ta ci gaba da wannan gigin, zai ɗauki matakin da ya dace a kanta."
*****
Cikin bacci, take jin hayaniya a bayan ɗakin, tamkar ana cin kasuwa. Ga wata irin sukuwa da take ji a roofing ɗakin, tamkar ta dawakai.
Tun da ta farka sai juyi take yi, bacci ya gagari idanunta, ayatul kursiyyu ce ta zo bakinta ta din ga maimaitawa, har ta samu nutsuwa daga razanin da take ciki.
Ta ruge idanunta, sai dai a maimakon ta yi bacci, sai wata irin kewar Sayyid take addabar ta. Ta rasa dallin da ya sanya, ba ya kula ta yanzu. Duk da ba shi da lafiya tana yi masa wannan uzurin, amma duk da haka da ya kan yi attempting sai ya ƙyale ta, yanzu kuma gaba ɗaya ya daina yinƙurin aikata komai ma.
Wanda da idan ya sako ta gaba, har takura take yi.
Ta tashi zaune ta gyara maganin sauro, ta taka a hankali ta ɗaga labulen ɗakin, saboda zafi. Ta dawo ta ɗauki fitilar wayarta ta kunna. Ta haska shi ta ga idanunsa a lumshe, yana bacci. Ta zuba masa ido, ta fara tunanin ko ita ce mai matsala gaya mata ne bai yi ba, ko ma sharrin Ƙaisar ne?.
Ta yi ajiyar zuciya, ta kashe fitilar, ta kwanta a gefen sa tana wasa da gashin ƙirjinsa. Zuwa na fuskarsa.
Ta sake matsawa a hankali, tana sumbatar leɓansa, tamkar mara gaskiya. Gaba ɗaya a tunaninta bacci yake yi, sai da ta ji ya sanya hannayen sa, ya zagaye ta, tare da ba ta damar sumbatar bakin nasa.
Nana za ta iya cewa, tun da Allah ya sa ta buɗi ido a duniya, ba ta taɓa jin kunya irin ta yau ba, cikin sauri ta fara ƙoƙarin rabuwa da jikinsa ta matsa, amma ya mirgina ya rungume ta gam a jikinsa yana numfashi a hankali.
Ayshercool
08081012143
56
Yana jin yadda jikinta yake tsuma, tamkar wadda aka kama tana aikata wani abin ashsha! Ko kuma wadda ake kaɗawa mazari.
Magana yake son yi mata, amma abu ya gagara, duk ƙoƙarin da ya yi amma abu ya ci tura.
Ya ƙara ƙanƙame ta tamkar wani zai ƙwace ta, ya din ga murza hannunta har ta fara jin zafin riƙon da ya yi mata. Yanayin ya ƙara ninka mata halin da take ciki, ta rintse idanunta.
A hankali ta ji yana hura mata iska a cikin kunnenta, tamkar yana zuba mata wani sindari, haka ta ji wani irin nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita.
Ƙamshin nan ta ji yana ratsa hancinta, ta buɗe idonta a hankali, kamar yadda ta yi tsammani, a wannan ɗakin ta gan su. Ta hau waige-waige. Ta wata ƙofa ta ga ya fito, ƙugunsa ɗaure da wani abu kamar zani, ya zauna a kusa da ita yana kashe mata ido.
"Sayyid ka warke?"
"Eh mana"
"Ka daina jin duk abin da ka ke ji?" Ya jinjina kai yana murmushi. "To ka yi mini magana mana"
"Ma vieee" ya faɗa yana ɗan jan maganar yana kwanciya a gefen ta. "Har na ji daɗi da ka samu lafiya, Allah ya ɗorar maka da sauƙin nan Sayyid"
"Amin rayuwata, matso ki kwanta mu yi bacci"
Ta noƙe kafaɗa ta ce "A'a"ya saki murmushi yana kama hannunta. Duhu ne ya gauraye ɗakin. Dariya ta fara jin Sayyid ɗin yana yi mata cakulkuli. Ta kasance da shi cikin wani yanayi mai tsayawa a zukata.
Ba ta iya tantance a wani hali take, ta daina ganinta a ɗakin, sai a libraryn Ƙaisar.
Ta tsaya tana kallon gurin, tana tunanin yaushe rabon da ta zo gurin nan.
Ƙaisar ta hanga, a tsaye yana gyara litattafan sa.
"Ƙaisar ka warke kenan?"
Yayi shiru yana goge wani littafi, ya gama ya ajiye littafin sannan ya ce "Eh, na warke. Waye ya ce ki je ƙauyen nan?"
"Ban gane waye ya ce na je ba? Zan kwana a titi ne? Ga mara lafiya ina da shi"
"Gaskiya ne, bai kamata ki kwana a titi ba. Wannan dalilin ya sanya tun a farkon auren nan, na din ga haska miki matsalolin da za ki iya fuskanta, amma gani ki ke yi kamar ƙarya nake yi, to yanzu sai ki san yadda za ki yi, ki rayu da ke da wannan lanjararren mijin naki, da duk larurar duniya ta ƙare a kansa".
A ƙule Nana ta ce "Larura Allah ne ya ɗora masa, kuma kun taka muhimmiyar rawa a larurarsa. Kuma ka daina ganin laifina. Zan tsallake shi ne a wannan yanayin da yake ciki, na bar shi? Mu bil adama mu na da bambanci da ku, mu na da tausayi da kuma nuna kulawa ga waɗanda muke ƙauna"
"A'a kar ki tsallake ki bar shi, amma ki yi ɗamara fiye da ta baya, garin Buda ki ka zo za ki zauna, ban sani ba ko kin fahimci abin da nake faɗa ko ba ki fahimta ba. Idan ma ba ki fahimta ba, za ki gane daga baya. Bil adama ku na tausayi da nuna kulawa ga wanda ku ke ƙauna, ku ke iya ɗaukar jinin makusantanku ku bayar, a yi muku tsafi ko? Da kyau matsala kuma ki sani, ba ki ga komai ba" Daga haka ya ɓace ɓat. Ta buɗe idonta a hankali.
Tana buɗe idonta, ta ji ana kaɗa kacakaura, da garaya a tsakar gidan su. Ana ta hayaniya tamkar ana cin kasuwa a tsakar gidan.
Sanyi ta fara ji yana ratsa ta, bugun zuciyarta ya ƙaru, fiye da da, waiwaya ta yi tana son ganin ta inda za ta ga Ƙaisar, ko makamancin hakan amma ba ta ga kowa ba.
Wata irin guɗa ta ji an rangaɗa da wata irin murya, mai sauti, sai kuma aka ce "Yeeee barka da zuwa wakilin rafi, ku matsa ku bayar da hanya ga ango mairamu ya iso" ta ji wata murya na faɗa, ana ci gaba da shewa da kaɗe-kaɗen garaya.
"Ku kawo Nono da suga, a kirawo 'yar Mairo ga mijinta ya iso. Ga farin