Showing 1 words to 3000 words out of 122205 words

Chapter 1 - BUZU BOOK2 COMPLETE 2

18 Jan 2026

571

BK 2

52
Jamila ta fashe da wani irin kuka tana tsuma, ta ce "Na shiga uku, yanzu Aljani ne ya kwanta da ni?"

"Eh amma a jikin bil'adama ya shiga, ya yi amfani da ke" ta gaya wa Jamila kai tsaye, ba tare da ta ji nauyin hakan ba.

"Na shiga ku, yanzu waye zai aure ni a haka? Ya zan yi. Na lalata rayuwata"

Hajiya Sa'a ta riƙo hannun Jamila ta ce "Na sha gaya miki, matsoraci ba ya zama gwani Jamila. Shi fa auren nan ba dole ba ne ba. Idan kina tare da ni duk abin da ki ke so za ki samu a tare da ni. Idan ma auren ki ke so miji sai kin zaɓa, kuma tsaf za a yi miki gyara babu wanda ya isa ya gane an taɓa amfani da ke. Kuma ƙungiya ta bayar da kuɗinki na shekara. Su na gurina zan din ga baki a hankali saboda kar a gane. Ki kwantar da hankalinki, ki ƙwarara jikinki, kar wani abu ya razana ki. Kuɗi kin same su kin gama ki saki jikinki ki mori duniya. Ke ce yarinya mafi ƙanƙanta a cikin ƙungiya. Ni dai ina matuƙar ƙaunar ki ne. 'yar uwakki na so na kawo, amma abu bai yiwu ba, ina tausayawa rayuwar da ku ke yi a gidanku ne. Ki cire duk wata damuwa daga zuciyarku, ki cire tsoro da tausayi baki ɗaya za ki je inda ba ki taɓa zato ba.
Jamila ta ɗaga kai ta yi wa Hajiya Sa'a wani irin kallo, da ita kaɗai ta san ma'anarsa. Ta share hawayenta ta ce "To shikenan"

Hajiya Sa'a ta yi murmushi ta ce "Yauwwa Daughterna, tashi mu je na gasa ki, ki karya likitan ƙungiya zai shigo ya duba ki" Jamila ta ja jikinta da ƙyar, Hajiya Sa'a ta kama ta suka je banɗaki.

****

Yau kwana na huɗu kenan, Sayyid yana cikin wannan yanayin. Babban abin da yake damun Nana rashin cin abinci da kuma salla da ba ya yi, daga bacci sai zaman shiru. Ba ya cewa uffan, sai dai ya yi ta bin ta da kallo. Ta din ga Addu'a Allah ya taimake ta, ko Ummi ba ta zo gurin ta ba, balle ta san halin da suke ciki.
Ƙarfe tara na dare ta na zaune a ƙasa inda ta ajiye fulo tana kallonsa a kwance a kan katifar. Ta ɗaga hannayenta kamar za ta yi addu'a, ta karanta suratul mulk, da ayatul kursiyyu, da Suratul falaƙi da Nasi. Ta tofa a hannunta, ta ƙarasa kusa da shi a ɗan tsorace ta shafa masa a fuskar sa. Ta ja da baya tana jira ta ga abin da zai yi, amma ta ga bai yi komai ba. Ta nemi guri ta kwanta tana ta tunani a ranta.

A cikin bacci ta ji ana ture ta, ta buɗe ido da sauri, ta ga yana ƙoƙarin kwanciya a gefen ta, duk da yadda gurin ya matse su.

"Sayyid" ta kira sunansa.

"Na'am"

Wata irin ajiyar zuciya ta yi, ta riƙo hannunsa ta ce "Mene ne?"

"Na kasa bacci, kin bar ni nikaɗai a kan katifa"

Cikin farin ciki da kulawa, ta shafa bayansa ta ce "Gani na yi ka na numfashi da ƙyar, kamar na matse ka shi yasa na saukko nan"

"Ma vie"

"Na'am Shugabana"

"Yunwa nake ji, kamar ban taɓa cin abinci ba"

"Bari na yi sauri na dafa maka wani abin, amma zo mu je ka wanke bakin ka, ka ga yanzu tsakiyar dare ne"  Ya yinƙura ya tashi, ta kama shi, yana ta jiri, saboda yunwa ga rashin lafiya, ga kuma mutuwar jiki.

Ta kai shi banɗaki, ya wanke bakinsa, ta dawo da shi ya zauna.

Ta feraye doya a cikin ɗakin, ta ɗaukko gas ɗin ta, ta ajiye a bakin ƙofa ta ɗora.

Ta ɗaukko mafici tana ta yi masa fifita.

"Rayuwata"

"Sayyid"

"Kamar yau ba mu ci abincin safe ba ko?"

Nana ta ce "Kwanan ka huɗi fa ka na bacci. Babu abin da zan ce wa Allah sai godiya, da ka farka" ya yi shiru bai kuma cewa komai ba. Ta sauke doyar ta dafa masa shayi, ta ajiye tana jira ya sha iska, ta ba shi da kanta. Amma bai jira ta ba, ya din ga hannu baka hannu ƙwarya. Sai dai hakan ya yi wa Nana daɗi, ganin ya ci Abinci da yawa yau.

Ya gama ci, ta dafa ruwa ta kama hannunsa zuwa banɗaki, tamkar jaririn goye ta yi masa wanka. Shi kansa a lokacin ya din ga jin wata lafiyayyiyar iska na shigar sa. Ta saka ya yi alwala, ya fito ya zauna ya fara jero sallolin da ake bin sa.
Ta ce "Sayyid kar ka ce sai yi a yanzu duka, sallolin da yawa.ka bari ka din ga ramawa a hankali.
Ya jinjina mata kawai kawai, tun yana yi a tsaye ya kasa tsaiwar ya koma yi a zaune. Ta yi shiru tana kallonsa, ta wasu guraren suna da kamanceceniyar halayya ita da shi.
Duk yanayin da yake ciki, muddin ba hankalinsa ne ya gushe gaba ɗaya ba, ba ya wasa da salla ko kaɗan. Hakan ya sanya take jin ko a ainihin rayuwarsa haka ya siffantu da kiyaye salla a kan lokaci.
Har ƙarfe uku da rabi, dan kansa ya ce "Ba zan iya ƙarasawa ba, numfashina"

Ta ce "To ko za ka yi a kwance?"

Ya girgiza kai ya ce "Na fi so na yi a zaune, ko a tsaye"

Ta ɗage masa labule, ganin yadda yake ta gumi. Ta shimfiɗa masa sallaya a bakin ƙofa, ta jera masa fululluka, ya kwanta.ta zauna a gefen sa tana yi masa fifita. Ta ɗora hannunta a goshinsa tana karanta masa abin da Allah ya sa ta tuna a zuciyarta.

Hannunsa ta ji yana saka wa a rigar ta, duk da idonsa a lumshe yake. Murmushi ta yi ta ci gaba da abin da take yi. Jin yana yi mata cakulkuli, ya sanya ta kwanta a jikinsa tana dariya. Shi ma dariyar ya yi. Ya ce "Ki kwanta a kusa da ni" ya yi maganar yana nuna mata kusa da shi. Kafin ta yi magana ta ga an dalle su da fitila.
Cikin hanzari ya juya kansa, ya ɓoye fuskarsa a cinyar Nana, gashin sa ya kwanta a kan filon. Nana ta saka hannu ta kare fuskarta.
Muryar Barira ta ji ta ce "Yi haƙuri dan Allah, jin motsi ya yi wa na fara jin tsoro, shi ne na fito na duba, ku yi haƙuri.
Ta kashe fitilar ta koma ɗaki. "Sayyid ka yi haƙuri, na san ba ka ji daɗi ba, ka yi haƙuri"

Ya yi mata shiru, kuma bai ɗago daga kan cinyarta ba. Ta shafa gashin ta ce "Shugabana, ka yi magana mana, ko na ji daɗi, kwana huɗu ka na bacci, ba ka yi mini magana dan Allah kar laifin wani ya shafe ni"
Sai kuma ya juyo a hankali, ta ce "Yauwwa Rayuwata"

"Kin daina aman?" Ta ji ya tambaye ta babu tsammani.

"Eh na daina"

"Allah ya sa ki haihu wannan karon "

"Amin, kuma Allah ya baka lafiya na haɗa jariraina biyu, babba da ƙarami"

Ya yi murmushi ya ce "In sha Allah, kafin ki haihu, idan na ji sauƙi zan nemi aiki, na kula da ku da kaina"

"To Allah ya amince. Amma Sayyid ina kuɗin nan da na gani rannan, a cikin wardrobe ɗin ka? Da na haɗa mana kaya ban gan su ba. Da sai mu ɗauka a yi maka magani, kuma mu canza gida"

"Ai Habu ya karɓa, ranar da ya zo na ƙarshe, ya karɓi kuɗin Nigeria da yawa, ya bar mini wasu, ya ce na Nijar ne. Kuma da kin duba kayan nawa sosai, su na ciki"

"A'a ni ba na caje maka kaya, idan Allah ya kaimu gobe, sai a lissafa mu gani idan za su isa."

Ya ce "To. Kwanta ki yi bacci" ya yi maganar ya ƙara matsa mata. Ta kwanta tana murmushi.

"Sayyid, idan har ba a ga su Habu ba, ina ga da ni da kai zamu je Nijar, mu nemi danginka da kanmu"

Ya yi shiru bai yi magana ba, ta ɗan taɓa shi ta ji har ya yi bacci.

*****
Jamila a dole ta saki ranta, jikinta ta ɗan samu ƙwari, ya daina yi mata wannan mugun ciwon da yake yi mata. Raɗaɗin ma duk babu. Sai dai tana jin ƙasan zuciyarta kamar za ta yi bindiga, saboda damuwa da tashin hankali. Sosai abin da ya faru ya tsaye mata, ta shiga banɗaki ta sha kuka. Wai ita Aljani ya kwanta da ita, ta gaba da baya aka ci zarafin ta ta wannan mummunar hanyar.

Tana kwance a cikin bargo, Hajiya Sa'a ta fita shashashancinta. Wayarta ta fara ringing. Ta janyo ta ɗaga. Muryar Abba ta ji ya ce "Ƙanwata, wunin yau ban jiki ba, lafiya kuwa?" Wani irin abu mai zafi ya taso mata, ya haddasa mata karaya. Muryarta na rawa ta ce "Yaya Abba ba ni da lafiya"

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Me ya same ki?"

Rasa abin da za ta ce masa ta yi, kawai ta saka kuka. Aikuwa ya rikice ya din ga rarrashin ta.

Da ƙyar ya lallaɓa ta ta ce masa cikinta ne yake ciwo.

"To ina Mummyn take? Ba ta kai ki Asibiti ba?"

"Ta kai ni, an ba ni magunguna ma, dan Allah kar ka yi mata zancen, ta yi mini iya ƙoƙarin ta,kar ka yi mata zancen dan Allah"

"No ai ba zan yi mata ba, ba ta san ma ina da lambar ki, mu na magana ba. Ki kwanta ki samu hutu kin ji Ƙanwatax

"To shikenan na gode sosai" suka yi sallama ta ajiye wayar, ta kwanta hawaye na ci gaba da bin idanunta.

*****

Yana zaune a cikin mota, yana ƙoƙarin kunnawa, wayarsa ta fara vibrating. Ya kalli screen ɗin wayar, ya ga baƙuwar lamba. Ya ɗauki wayar ya ɗaga ya saka a kunnensa.
"Hello" muryarta ta doki dodon kunnensa. Ɗan waro ido ya yi, ya gyara zaman sa ya ce "Wa ke magana?"

A raunane ta ce "Beb abin har ya kai ka manta muryata ma? Shikenan na gode" ta kashe wayar.

Da sauri ya bi kiran wayar, amma ta ƙi shiga, ya yi ya yi, amma ta ƙi shiga, sai haƙura ya yi ya ja motar.

Shukura mamakin abin da ya zaunar da shi a cikin mota take yi, bai tafi ba har yanzu, sai dai tana ɗaga labule, ta hango ya ja motar ya tafi.

Video call ɗin Hajiya Amina, Shukura ta gani, ta ɗaga cikin fara'a tana faɗin "Hajiya Mummy, ya ibada?"

"Ibada Alhamdillah, Shukura dan Allah me yasa ba kya ji ne? Ina zaman zamana, ina ibada kin jawo mini ɓacin rai da damuwa"

Cikin rashin fahimta, ta ce "Ni ɗin kuma? Me na yi?"

"Baban ki ya kira ni, bai taho ba tukuna yana Abuja. Yana yi mini faɗan wai ke ba ki san ƙaddara ba ne? Doctor Sharif ya kira shi cikin damuwa, yana gaya masa a gaban mutane ki na cewa yana kashe mutane, haka ake yi a kan ki a ka fara rasa ɗa? Me yasa ba za ki girma ba ne Shukura"

"Mummy ki na ji na, network ɗin ki mai ƙarfi ne ko?"

Ta ce "Eh, ina jin ki, kuma ina kallon ki"

"Ina son idan kin je gaban ka'aba, ki yi mini addu'a, muddin a kan gaskiya ta nake, Ubangiji Allah ya shiga lamarina ya ƙarfafa mini gwiwa. Idan kuma ba a kan daidai nake ba, Ubangiji Allah ya kawar da kaina daga kai. Ya bani juriya da dangana na daina jin abin da nake ji a zuciyata.
Sai dai kin dawo amma akwai matsala ne fa."

"Shukura matsala wace iri ce, za ta sanya musulmi kasa yin tawakkalli?"

"Ki bari dai ki dawo ɗin"

"To shikenan, amma gaskiya mahaifinki ya yi fushi bai ji daɗin abin da ki ka yi ba sam"

Shukura ta lallaɓa ta, ta ajiye wayar.

*****

Nana tana jan ruwa a rijiya, tana zubawa a cikin bokitanta, za ta kai banɗaki.
Barira ta ce "Nana ki yi haƙuri dan Allah, jiya na haska ku, ba a son raina ba ne, kuskure ne" Nana ta ce "Babu komai"

Sajida ta ce "Uban me ki ka haska ki ka gani?"

Barira ta kwashe da dariya ta ce "Ni babu abin da na gani, duk da bai kyautu ba abin da na gani ɗin. Amma Nana mijinki balarabe ne ko bature?" Nana ta ɗaga ta kalle ta.
"Tun da ku ka zo dama bamu taɓa ganinsa ba, gashi na gani kamar na mace dogo sosai"

Nana ta maze ba ta kula ta ba, ta kwashi kayan ruwanta, ta nufi ɗakin su.

Sajida ta tuntsure da dariya ta ce "Maganinki da shegen shishshigi, ga shi ta gwale ki"

"Shegiya ba, ta fiye jin kan ta,kamar 'yar uban wani, kuma da 'yar uban wanin ce, da ba su kama hayar ɗaki ɗaya ba" Duk abin da suke faɗa a kunnen Nana, amma ta yi kamar ba ta ji ba.

Bayan ta gama wanke banɗaki ta fito, ta zo gabansa ta zauna. Ya ɗaukko sauran kuɗin nan, ya ajiye a gaban ta.

Ta kalle shi ta ce "A ina ka ɓoye ne, ban gan su ba?"

Ya yi murmushi ya ce "Su na cikin kayana fa, ba ki duba bane ba. A cikin leda suke. Kuma da sun fi haka yawa, Habu ne ya karɓa".

Nana ta duba kuɗin, sai tarin kuɗin nijar, na Nigeria ba su dubu ɗari da goma ba.

Ta ce "Sayyid, idan ka ɗan ƙara hutawa, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ne, za mu koma Asibiti a sake duba ka. Da za su kai da na haɗa da sauran na guri na, a fara yi maka allurar nan ko guda ɗaya ce"

"A'a, kin manta yanzu mu zamu din ga sayen Abinci. Idan su ka ƙare ba mu da hanyar samun kuɗi. Kuma da akwai isassun kuɗi, gara mu bar gidan nan, da a yi mini magani"

"Ni kaina Sayyid ba na son gidan nan. Mama za ta aiko mini buhun barkono, idan aka kawo, na ga ana ciniki, sai mu ci gaba da sayarwa".

Ya jinjina kai ya ce "To, in anjima ki raka ni masallaci" Ta kalle shi ta ce "Da gaske masallaci za ka je?"

"Eh, ina son zuwa masallaci. Idan ki ka raka ni, sai ki dawo"

Ta yi murmushi ta ce "To shikenan, Alhamdillah sauƙi yana samuwa. In sha Allah zan kai ka. Bari na ajiye kuɗin nan, idan na raka ka ma, dan Allah zan je gidan Ummi" ya jinjina kai. Har za ta tashi ya riƙo ta, ya cire hijjabin da yake jikinta.

Ƙonuwar da take wuyanta ya gani, ya ƙura wa gurin ido sosai sannna ya ce "Mene ne wannan?"

Ta ɗan basar ta ce "Ba komai fa, ɗan ƙonewa ne kawai na yi"

"Ba ɗa ba ne ba, me ya kai ruwan zafi wuyan ki? Waye ya zuba miki?"

"Ba wanda ya zuba mini, sha nake yi ya zube" kawai ya rabu da ita, ba dan ya gamsu da amsar da ta ba shi ba.

Ta tattare kuɗin nan, na Nijar ta zuba su a cikin jakar gidan Sarkin Baka. Na Nigeria kuma ta haɗe su, ta saka a cikin kayan ta. Ana kiran salla, ya yi alwala, Nana ta ba shi mayafin rawaninsa, ya yafa a kan sa.
Nana ce ta fito tsakar gida. Barira ta gani, tana girki sanye da wata 'yar riga, milik ce amma ta yi baƙi saboda dauɗa, ko brezia babu a jikinta. Ga gashin hammata ya fito zaro-zaro idan ta ɗaga hannunta. Zanin jikinta ma baƙi ƙirin, tamkar an yi matsar man ƙuli da shi, sai annakiya take yi.

Nana ta ce "Barira, dan Allah ko za ki gyara, zamu wuce"

Barira ta ce "Bismillah ki wuce mana"

"A'a ai ni da mijina ne"

"Ku wuce ba wani abu ai" Nana ta yi shiru tana jinjina tumasanci da rashin sanin ciwon kai, na mutanen gidan. Babu yadda ta iya, haka ta kammo hannun Sayyid, ya fito ta rufe ɗakin. Ya ja mayafin ya rufe fuskarsa da rawanin, saboda yanzu ba ya iya naɗa shi, saboda numfashinsa.
Tun da ya fito Barira take kallon sa, ta na son ganin ainihin fuskarsa, amma ya sunkuyar da kai, kuma ya rufe fuskar sa suka fice.

Su na tafe Yana hutawa, saboda haki, a hankali har suka isa masallacin. Ta ce "Za ka jira ni na je gidan Ummin na dawo?"

"Zan koma gida da kaina"

"Har ka gane hanya?"

Ya ce "Eh ki gaishe ta"

Nana ta ce "Ai ba daɗewa zan yi ba ma"

Ya shiga Masallaci Nana kuma ta tafi gidan Ummi.

Su Nana na fita, Barira ta buga banɗakin tsakar gida ta ce "Ke Sajida kashin danƙo ki ke yi ne? Ki na manne a banɗaki yau mijin 'yar rainin hankalin nan dai ya fito. Ashe dole ta ɓoye shi, fari ne tas wannan gashin da na gani, da gaske nasa ne."

Sajida ta fito da buta a hannunta ta ce "Kai haba, ban gama ba ne shi yasa ban fito ba, zogala na ci da ƙuli ya ruɗa mini ciki"

"Aikuwa kin rasa, ba ki gan shi ba. Sai na ga kamar mata na rako, da na tuna Gali, ga baƙi ga ƙeya"

Sajida ta ce "Ba gara Gali ba da nawa mijin? Ke Gali na da tsawo, ni nawa ga gajarta ga muni"

"Gaskiya Sajida mijinki akwai muni kam, dogon baki kamar dangin burrai"

Sajida ta tsuke fuska ta ce "Ba na son iskanci kuma. Gara shi dai a kan Galin, da ki ka ce ba ya iya tsinana miki komai a shimfiɗa. Kalarsa kalar... Kafin ta ƙarasa Barira ta ƙunduma mata Ashariya, take faɗa ya kaure, suka ci wa junan su mutunci tsaf, suka tona wa kan su Asiri. Suka gaji dan kan su, suka haƙura.

****
Nana ta bawa Ummi labarin barkono da za a kawo mata.
Ta ce "Amma Ummi sai dai a kawo miki nan, can ɗakinmu babu gurin da zan ajiye a can"

"Bakomai a kawo, kuma nan da nan za ki ga an saye shi ba, ai unguwar nan fuskar jama'a ce, idan ka kasa kaya za ka samu alkhairi"

Su na tsaka da hira, babu zato babu tsammani sai ga Saleh ya afko cikin gidan. Wata irin mummunar faɗuwar gaba ta ziyarci Nana, bayan da ta gan shi babu tsammani. Duk ya ƙara lalacewa.

Turus ya yi yana kallon Nana, cikin mamaki ya ce "Nana, dama kina nan?"

"Eh" ta amsa a taƙaice.

"Nana da yanzu nine mijinki, amma ki ka guje ni"

Ummi ta haɗe rai ta ce "Saleh Nana fa matar aure ce, dan haka babu ruwan ka da ita dan Allah"

Saleh ya ce "Dan matar aure ce, kuma shikenan ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login