Showing 75001 words to 78000 words out of 122205 words
sake cewa.
Sai dai ta yi shiru ba ta kuma magana ba, su kuma suka hau mamakin irin amsar da Nana ta bata, kuma ba ta iya ce mata komai ba.
Gaba ɗaya Nana hankalinta ya koma kan sauran kwanaki nawa ta koma gida, duk da kullum sai ta yi waya da Nene. Amma ta ga kamar kwanakin ba sa matsawa sam.
****
Hajiya Amina revers ta yi, ta dawo gida Nigeria, saboda kiɗima da tashin hankali da take ciki, ta rasa wanda za ta fara tunkara da maganar. Ta so samun mijin Alhaji Zailani a waya, ta fara yi masa bayani, amma ba ta same shi a waya ba. Ta koma gida a kiɗime, amma ta tarar da saƙon ya yi balaguro zuwa Abuja.
Jikinta na rawa ta kira Doctor Sharif, ya ɗaga yana faɗin "Hajjaju barka da yamma"
"Sharif abu zan tambaye ka dan Allah"
Gabansa ya faɗi, saboda yadda ya ji muryarta cike da tsoro da kuma damuwa.
"Hajiya lafiya dai?"
"Lafiya ƙalau, tambaya zan yi maka dan Allah"
"To Allah ya sa na sani"
"Dan Allah Sharif ana iya samun matar da ba ta da mahaifa dama?"
Ya yi shiru sanann ya ce "Me yasa ki ka tamabaya?"
"Ka bani amsa kawai"
Nutsuwa ya yi ya tattara hankalinsa, kar ya ba ta amsar da zai fallasa wani ɓoyayyen abin da bai kamata ba.
Duk da bai san dalilin da ya sanya ta yi tambayar ba.
"Eh ana samu Hajiya, sosai ana samu wani abu ne ya faru?"
"A'a shikenan na gode sosai" ta kashe wayar, sai a lokacin hawaye ya fara gangaro mata, da ta ƙara tabattar da har abada ba za ta samu haihuwa ba.
"Amina butulci za ki yi wa Ubangiji? Sauran ni'imomin da ya yi miki fa?" Wata zuciyar ta tunatar da ita. Sai dai kasancewarta biladama mai ɗauke da zuciya irin ta ɗan adam, sai ta kasa jurewa ta bi nasihar da zuciyarta take yi mata, ta fashe da matsanancin kuka mai taɓa zuciya. Duk da ta daɗe tana yin sa a ɓoye, amma ba ta yanke tsammani ba ta ci gaba da addu'a, amma a wannan karon da ta san ba ta da rabo baki ɗaya, sai ta sare.
*****
Shirye-shiryen bikin Abba yayi nisa, dan bai fi saura sati biyu bikin ba, ta ƙara saka masa ido da shi da Jamila. Jamila sam ba ta nuna mata cewar ta san abin da take yi ba, ta rabu da ita.
Ya kasance taronsu na ƙungiya lokaci yayi, dan haka suka shirya tafiya a wannan karon har da maman Khairat.
Da suka je masaukinsu ma a garin Abuja, Jamila ba ta shiga sabgarsu ba, harkokinta kawai take yi.
Maman Khairat ta ce "Wai Jamsy ya ne? Duk kin zama so silenta, babu wannan rawar kan"
Jamila ta ɗan taɓe baki kawai.
Hajiya Sa'a ta ce "Jamila haushina take ji, ban san me na yi mata ba"
Jamila ta ce "Mummy kenan"
"A'a ba wani Mummy kenan, magana za ki yi"
"To Mummy, ki na ta daughter daughter, amma ƙarara ki ka nuna ba kya ƙaunata, daga ganina tare da Abba, ki ka haɗe rai ki ka yi kicin-kicin, ki ka tashi nema masa aure. Abin ya bani mamaki"
Hajiya Sa'a suka haɗa idi da maman Khairat, ta ce "Haba daughter, ya za a yi na ƙi ki da Abba, ke me ma za ki yi da aure? Na daɗe ina gaya miki za ki iya rayuwa ki da kuɗinki, ba tare da kin yi aure ba. Za ki huta ki yi duk abin da ki ke so."
"Amma Abba ma ai yana da kuɗi, shi me yasa ba ki ce ya yi rayuwa da kuɗi kawai ba, ki ke shirin yi masa aure? Duk wata ƙasaita, kuɗi da wadatar mace, inuwar aure ginshiƙi ce kuma sutura ce ga 'ya mace.
Amma na san saboda ni rayuwata ta gama lalacewa, ke kuma kina son ɗan ki ya yi kyakykywar rayuwa, ki ka yi ƙoƙarin raba ni da shi. Sai dai tun ran gini tun ran zane. Ban ji haushinki ba ko kaɗan Mummy, abin da ki ka yi shi kowacce uwa za ta yi. Ina yi mana fatan dacewa da ƙarshe mai kyau" Tana gama maganar ta yinƙura ta tashi, ta bar ɗakin.
Safiyya ta ce "Kin ga Hajiya, ki bi yarinyar nan a hankali, alamu sun nuna hankali ya fara shigarta, ta san ciwon kanta, kuma abin da aka yi mata duk da ta samu kuɗi ya yi mata ciwo. Kar ki bi ta da ƙarfin tsiya ta yi tawaye"
Hajiya Sa'a ta numfasa ta ce "Na ga alama, amma ba zan taɓa rainon ɗan kwiykwiyo, ya girma ya fara yi mini haushi ba. Ina son samun jinin 'yar uwatta na riga Zailani samu ko ta halin ƙaƙa, daga nan zan yi maganinta"
Safiyya ta jinjina kai.
Doctor Sharif ya din ga kiran Alhaji Zailani, ya sanar da shi kiran da Hajiya Amina ta yi masa, amma ya kasa samunsa a waya, saboda su shinga taron manyan ƙungiya da suke yi, wanda sai sun kwana uku suke fitowa, sannan ayi babban taro na kowa da kowa da ke cikin ƙungiya.
Ganin kiran Hajiya Amina ya bawa Shukura mamaki, dan idan tana Saudiyya sai dai su yi video call.
Ta ɗaga ta ce "Mami, yaya ba ki samu tafiyar ba ne?"
"Shukura za ki iya zuwa gida, ban takura miki ba"
Cikin tashin hankali Shukura ta ce "Lafiya kuwa, ya na ji muryarki a haka?"
"Dan Allah idan da hali ki zo gida"
"Shikenan, gani nan zan kira baban Haidar na gaya masa, gani nan Allah ya sa lafiya"
Hankali a tashe, ga tsohon ciki haka ta ɗauki mota ta tafi gida. Tana matuƙar jin Hajiya Amina a zuciyarta, saboda bayan rasuwar mahaifiyarsu, tun su na ƙanana babu yadda ba ta so cuzguna mata ba, amma Hajiya Amina babu ruwanta. Ba ta damu da abin da mutane za su ce ba, ta riƙe ta da halin ta, sai da ta ƙara wayo sannan ta gane ba ta da wata uwa da ta wuce ta. Shi yasa take matuƙar jin damuwarta a ranta tamkar uwar da ta haife ta.
A bedroom ta tarar da ita, idanunta jawur sun kumbura. Cikin tashin hankali ta ƙarasa ta zauna ta ce "Lafiya kuwa? Ko ba ki da lafiya ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Yi haƙuri Shukura, na taso ki ga tsohon ciki, na rasa da wanda zan yi zancen nan na ji daɗi a raina."
Cikin damuwa ta ce "To meyafaru?"
"Shukura wai ba ni da mahaifa"
Shukura ta yi saroro, ta ce "Kamar yaya?"
Ta share hawayenta ta gaya mata duk abin da ya faru. A ƙarshe ta ce "Na kira Doctor Sharif ya ce mini eh ana iya samun mata da basu da mahaifa, amma na yi mamakin yadda duk yawon Asibiti da na yi a nan, ba a taɓa gaya mini ba"
Shukura ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Anya kuwa? Kin san fa kin daɗe da daina zuwa Asibiti a kan matsalar nan, Daddy ba ya so. Sannan ku ne ku ke yarda da maganar Sharif ɗin nan, ki rabu da shi mu je wani Asibitin daban, a sake duba ki a tabattar da abin da yake faruwa. Duk da ba na tunanin za a samu matsala a abin da can Egypt ɗin suka gaya miki."
Ta girgiza kai ta ce "A'a Shukura, babu inda zan sake zuwa, na yi maganar ne da ke dama na samu sanyi a raina, na kira babanki ba ta shiga"
Shukura ta yi shiru, kawai dai ta ji ita abin kamar akwai lauje cikin naɗi.
*****
Nana ta shafe sati na biyu, tana aiki a wannan gidan Abinci. Sai dai ita kanta tana mamakin irin yadda Al Hussain yake kyautata mata. Hakan ya sanya gaba ɗaya suka ƙara saka mata ido suka tsangwame ta, mussaman Adama da 'yar ta Raliya, da alamu suka nuna Al Hussain take so.
Idan aiki ya ɗan yi sauƙi, Nana kan fita ta shiga cikin gurin cin abincin, ta zagaya ko za ta ga ko mai da Sayyid ne, amma ba ta ga kowa ba. Sai dai gabanta ya kan faɗi a duk lokacin da ta ga masu rawani sun zo gurin cin abinci, sai ta ga kamar za ta gan shi a cikin su.
Ta gama zagayenta, ta koma cikin gurin girkin, Adama ta kalle ta ta tsuke fuska ta ce "Daga ina ki ke, ana tsaka da aiki?"
"Na ɗan je wani uzuri ne"
"Na me, kuma a ina?"
Nana ta ce "Uzuri dai na ɗan Adam, na yau da gobe, ai rayuwa na buƙatar sirri ko?"
"Ni fa na fuskanci take-takenki na rashin kunya baki da kunya ko kaɗan, saboda kin ga Al Hussain yana tsaya miki, wallahi idan ba ki yi wasa ba sai na kawo ƙarshen aikinki a nan, sai na saka an kore ki daga gurin nan"
Kallonta kawai Nana ta yi ta kawar da kai, ta ci gaba da abin da take yi. Har ta gama bala'inta, 'yan korenta suka taya ta, Nana ba ta tanka mata ba.
Washegari da sassafe, Nana ta baro ɗakinsu, ta tafi kitchen ta fara aikinta, duk da wasu lokutan suna yi mata mugunta, su din ga sakar mata aiki.
"Ina sauran ma'aikatan gurin nan?" Ta ji wata murya ta daki kunnenta, da ba ta san mai ita ba.
Ta ɗaga kai ta kalli matashiyar matar, doguwa fara jawur, mai kama da Al Hussain.
Kawai ta mayar da kanta ta ci gaba da aikin gabanta.
"Ke ba kya ji ina magana ne?"
Nana ta ɗago kai ta ce "Su na zuwa"
Nana na rufe bakinta, sai ga Adama ta shigo, ita da sauran ma'aikatan.
Wata irin rikicewa suka yi, suka hau tsuma su na gaida matar.
"Wace ce wannan? Da ba ta da mutunci ba ta da ɗa'a, nake magana tana bani amsa a wulaƙance" ta yi maganar tana nuna Nana.
Nana a ranta ta hau mamakin wane wulaƙancin ta yi mata, ita da ta zo guri babu sallama babu gabatar da kai, koma wace ce ba zai wuce ita ce mai gurin da ake faɗa ba. Nana a ranta ta ce "Koma wace ce ke, Allah ya fi ki" sai dai ba ta sake ɗaga kai ta kalle su ba, ta ci gaba da yankan kabejin hannunta.
Ayshercool
08081012143.
69
Adama ta risunar da kai ta ce "Ki yi haƙuri ranki ya daɗe, mu ma haka muke ta fama da ita mu ma, amma ki yi haƙuri baƙuwa ce"
"Baƙuwa kuma ba ta iya magana ba, baƙuwa daga ina?"
Raliya ta ce "'yar Nigeria ce"
" 'yar Nigeria, waye ya saka Al-Husssain ɗaukar wata 'yar Nigeria, dama haka 'yan Nigerian ku ke, ba ku da mutunci ba ku san me ku ke yi ba?" Maganganun matar sun soki zuciyar Nana, tamkar ta mayar mata da martani ta ce "Ku a Nijar ba ku san muhimmancin sallama, da girmama na ƙasa da kai ba" Sai dai ta yi shiru ta ci gaba da aikin gabanta. Haka ya ƙara tunzura matar ta fita fuuuu tana bala'i tana sai Nana ta bar aiki a gurin.
Matar na barin gurin Raliya ta kalli Nana ta ce "Allah ya ƙara, idan kina cin ƙasa ai ki kiyayi ta shuri, yau kin taɓo abin da ya fi ƙarfinki, kin yi a bakin aikinki"
Babban abin da ya ɗaure musu kai, bai wuce yadda Nana ta ƙara yin burus, ta ci gaba da aikin gabanta.
Adama ta ce "Anya yarinyar nan ba mahaukaciya ba ce kuwa?"
Ɗayar ta ce "Ko ta mayar da mu mahaukata ba. Amma idan haukan take ji, ai Hasna babarta ce"
Wata matashiyar mata ce ta shigo, sanye da uniform a jikinta. Ta yi sallama suka amsa.
Ta ce "Ina Nana?"
Nana ta ce "Ga ni"
"Ki zo ana neman ki a ofishin Al Hussain"
Ta ce "To gani nan" ta yi maganar tana ajiye wuƙar hannunta, ta wanke hannunta ta bi bayan matar.
Sai dai har matar ta yi gaba ta bar Nana, da ƙyar Nana take iya ɗaga ƙafafuwanta, saboda matsanancin nauyin da ta ji sun yi mata, ga sanyi da ya fara ratsa ta ta ko ina.
"Ya hayyu ya ƙayyum. Allah ka taimake ni, Ƙaisar kar ka yi mini haka mana" Ta furta a hankali zuciyarta na bugawa.
Ta saka hannu ta tura ƙofar ofishin. A tsaye ta tarar da matar ɗazu, tana zazzaga masifa, Al Hussain yana zaune yana kallon ta.
Sai dai Nana ta yi turus, ganin Ƙaisar a zaune a jikin na'urar sanyaya guri, da ke cikin ɗakin.
"Nana ƙaraso mana" muryarsa ta dawo da Nana hayyacinta. A hankali ta ƙarasa ya ce ta zauna a kan kujera.
"Al Hussain ka na da lafiya kuwa? Yarinyar ta yi mini rashin mutunci, ka ce ta zauna a kan kujera?"
Ya ce "A'a Hasna, na fa san halinki, kuma a aikin da Nana ta yi da mu na ɗan lokaci, ba ta da matsala sam. Nana meyafaru ne?"
Nana ta buɗe baki za ta yi magana, Hasna ta tari numfashinta ta ci gaba da masifa.
Al-Husssain ya daki tebur ya kalli Hasna, hakan ya sanya ta yin shiru tana harar Nana.
Nana ta ce "Ban san wace ce ba ne, ta yi haƙuri"
Hasna ta daki tebur ta ce "Ka gani ko, garin kwashe-kwashe ka kwaso mara mutunci, to wallahi sai ta bar gurin nan, tun da ba na ubanta ba ne"
Al-Husssain ya ce "Tsakani da Allah, Nana mutuniyar kirki ce mai girmama mutane, ba na tunanin za ta yi miki wani abu na rashin mutunci. Nana ki je ki ci gaba da aikinki" Ta jinjina masa ta kalli Hasna ta ce "Ki yi haƙuri, ban san wace ce ke ba, ba ki gaya mini ba, na zata a cikin abokan aikina ne kaw...
"Ke, na yi miki kama da wadda za ta zama abokiyar aikinki?. Za ta ci gaba da magana Nana ta tsare ta da ido, sai ta rikice gaba ɗaya ta rasa abin da za ta ce.
Al-Husssain ya ce "Maza jeki ki ci gaba da aikinki"
Nana ta miƙe tsaye, kawai ta ji jiri ya ɗebe ta, ta yi saurin riƙe kujerar. Al Hussain ya miƙe da sauri ya ce "Ba ki da lafiya ne?"
A sanyaye ta ce "A'a jiri nake ji ne"
"Idan ba za ki iya aikin ba, ki je ki kwanta ki samu hutu"
Nana ta ce "A'a zan iya ma, in sha Allah"
Ta lallaɓa ta fita daga ofishin, sai dai tana jiyo Al Hussain yana ce mata, ki yi a hankali kin san mu na da baƙi, idan kuma ki ka ci gaba da hayayaga mutuncinki ne zai zube, wannan halin naki babu abin da zai janyo miki sai raini.
Gaba Nana ta yi, tana bin bango, sai dai sosai ta ji Duniyar na juya mata.
Ta lallaɓa ta koma ɗakinsu da ƙyar, sai dai a ɗakin ta din ga jin wani irin sauti mara daɗi, ga sanyi tana ji amma numfashinta tamkar zai ɗauke.
Ta buɗe tagogin ɗakin, kasancewar saman bene ne, ta hango wasu irin manyan motoci a harabar gurin. Naɗin kan mutanen ya sanya ta tabattar da Buzaye ne, sai dai suna sanye cikin kaya na alfarma.
Nana ta zuba musu ido, tana son ganin fuskar ɗaya daga cikin mutanen da aka buɗewa wata danƙareriyar mota. Wanda haka kurum ta din ga jin kamar akwai wani abu mai matuƙar muhimmanci da yakamata ta sani game da mutumin, da ba ta san ko wane ne ba, duk da yanayin ƙirar jikinsa ba irin na Sayyid ba ne. Wata irin ƙara ta din ga ji cika mata kunne. Ta dafe kunnenta, ta durƙusa hawaye na bin fuskarta. Yanayin gaba ɗaya mara daɗi ne, rashin daɗin da ba za ta iya misaltawa ba sam.
Dariyar Giyaz ta din ga ji sama-sama, a hankali dariyar ta cika ilahirin ɗakin.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil, wa hifzan min kulli shaiɗanin marid" shi ne abin da ta furta a hankali.
"Asmy" ta ji muryarsa cikin karkarwa, yayin da ƙarar iskar sahara take kaɗawa.
A galabaice ta ce "Sayyid"
"Ma vie"
Ta sake cewa "Na'am Sayyid, na fara sarewa, ina jin kamar ba zan yi nasara ba, ba zan ganka ba, na fara karaya." Ta yi maganar tana kuka.
"A'a kar ki karaya, kar ki yi mini haka, ina buƙatar ki dan Allah"
A hankali take sauke numfashi, idanunta a lumshe ƙirjinta ya yi nauyi kamar numfasihinta zai ɗauke.
*****
Daren da Jamila ba za ta taɓa mantawa da shi ba, ya sake maimaita kansa.
Daren da ta zama ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar asiri, daren da aka lalata rayuwarta a matsayin maraba da shiga ƙungiyar.
Kamar yadda yake ɗabi'ar ƙungiyar, suna sanye da jajayen kaya. Sai dai a wannan karon Jamila ta gusa daga matakin farko na shiga ƙungiyar.
Babban abin da ya bawa Jamila mamaki, bai wuce yadda aka fesa wani abu a gurin, sai ganinsu ta yi a dokar daji ba.
Wani irin daji mai ban tsoro, mai ɗauke da manyan dogwayen bishiyu, ga shi baƙiƙirin ɗauke da duhu.
A wani fili suke a gaban wani dutse, babu tsammanni ta ga wuta takama a tsakiya tana ci bal-bal.
Daga bisani dajin ya din ga amsa kuwwa da wata irin ƙara mara daɗin ji.
Aka din ga karanto abubuwan da Jamila ba ta iya fahimta.
Aka jefowa kowa ƙyalle da abin da zai sadaukar na shekara, kafin zagayowar wani taron.
Jamila ta kalli ƙyallen da yake gabanta, jawur da shi.
Hannunta na rawa ta ɗauka ta fara ƙoƙarin warwarewa. Da hasken da wutar ta bayar Jamila ta karanta abin da yake rubuce a jiki, da aka rubuta da jini.
Ta din ga kallon ƙyallen tare da rubutun. Ta duƙunƙune ƙyallen ta jefa a wuta, kamar yadda kowa ya yi.
Sai dai jikinta a sanyaye, gabanta kuma ya tsananta faɗuwa. A wannan karon har da wasu irin dogayen mutane, da ta kasa gane mutanen ne ko kuwa wani jinsin ne, saboda yadda suka shallake kowa tsawo a gurin kuma suna sanye da baƙaƙen kaya har kansu a rufe yake.
A wannan karon abubuwan da Jamila ta gani sai da ta tsorata, ashe wancan karon babu abin da ta gani. Ƙungiyar mataki-mataki ce.
Su matakin su Alhaji Zailani ma, kowannensu yana da aljanin da kusan bauta masa yake yi. Sun ba wa aljanun jini babu adadi, na makusantansu, da wanda ma ba makusnatansu ba. Aljanun na iya shiga kowane irin hatsari, dan ganin buƙatar irin su ta biya komai wahalarta.
Haka suma su Alhaji Zailani, duk abin da Aljanun suka buƙata suna yi musu, domin ɗorewar biyan buƙatunsu. Alhaji Zailani ya kan karɓi saƙonnin nasa Aljanin ta hannun Malam Gambo, wanda su ne manyan malaman da suke gudanar da sihiri a cikin ƙungiyar bayan ɓangaren neman Duniya da samun kuɗi