Showing 84001 words to 87000 words out of 100561 words
tsaya daga yau! Ki tattara komai naki ki bar cikin gidan nan! Hukuncin zagin da ki ka yi mini kuma zai biyo baya dan tabbas sai na azabtar da ke fiye da zatonki, in sha Allahu.”
Murmushi Ladiyo ta yi sannan ta ce “idan ki ka ce in tattara komai nawa, to zan tattare jama’ata ne sannan zan tattare kuɗin asusun wannan ƙungiya da kuma wannan gidan da aka siya da kuɗin ko wacce ɗiya a cikinmu sabida a halin da ake ciki a yau da har gaban abada ni ce shugabaaaaa!”
Ɗifff!! Haka wajen ya kasance kamar an yi ruwa an ɗauke kafin Ladiyo ta ɗaura da cewa “dan haka da ni da ke za a ga mai barin gidan nan muddin ki ka matsaaaaa! Amma idan ki ka kwantar da kai to ba ni da plan ɗin korar kiiiiii…”
Hankalin Yagwalgwal a take ya soma tashi jin kowa ya yi ɗiff!!! Saɓanin in da ace da ne sai sun lakaɗawa Ladiyo dukan tsiya na rashin kunyar da ta yi mata….
Ta na wannan lissafin ta ji muryar wata a cikinsu ta yi gyaran murya babba ce sosai itama ana girmamata a gidan ta ce “Ammm…Yagwalgwal..”
Da masifar sauri Yagwalgwal ta juyo ta kalleta ta na mamakin yadda ta kira sunanta haka.
Sam Matar ba ta damu ba ta ɗaura da cewa “A gaskiya mun gaji da mulkinki! Saboda ba ki kaimu ga ci gaba sannan ba kya ɗaga darajarmu, tsoronki da gudun maganarki baya daga cikin ɗabi’un shugaba, Ga Ladiyo nan za ta jaa mu mu je gaba in sha Allahu, ba za ta dankwafar da mu ba….
Akwai abubuwa da yawa da ki ke yi waenda cutarwa ne a garemu, shiru kawai mu ke yi miki, amma saboda Allah ta ya za a ce mu na da ɗakunanmu amma mu dinga bi hotel hotel, wanda kuɗin hotel ɗin in an tattala mu ake bamawa….
Tunda ke ba za ki iya karawa da su Mai Unguwa ba! Ladiyo za ta iya dan haka ki haƙura ki koma gefe ki sha kallo kawai…..”
Har wani jiri-jiri da dishi-dishi Yagwalgwal ta ke gani tsabar tashin hankali, da kyar ta iya cewa “akwai mai jaa a maganar da Khairiyya ta gama yi yanzun?….”
Ɗifff!! Haka su ka yi kowa ya yi ƙasa da kanshi ya na guna-guni….Aimana ce kawai ta ɗaga hannu, ita ɗaya kwal! Wanda a tsari rabin mutanen wajen ne a bayan Ladiyo amma ganin da ragowar su ka yi Ladiyo ta fi power a wannan lokacin ya sanya su ka zaɓi suma su bi bayanta gudun kar ta yi winning ta haɗa da Yagwalgwal ɗin da su duk ta kora a cikin gidan, ko kuma a takura musu a mayar da su kamar bayi.
Cikin sauƙe numfashi Khairiyya ta ɗaura da cewa “kin gani ae da idanunki, kowa kara ce kawai ya ke yi miki amma ki na kwarar mu!
Ko baya ga haka ma a gaskiya ba zai yiu a ce kura da shan duka gardi da amsar kuɗi ba, tunda har ke kin yi retire daga buɗe ƙafa kamata ya yi a ce hatta kujerar ma kin yi retire a kanta.”
Duk jaraba da masifar Yagwalgwal yau ɗin sai ta gagara cewa komai, hankalinta bai ƙarasa tashi ba sai da amintacciyar Ladiyo ta ɗaga hannu sama ta soma cewa "Ladiyo! Ladiyo!! Ladiyo!!!" Ragowar jama'ar wajen har da ƙaton kwarton suma duk su ka ɗauka, kowa ya shiga cewa "Ladiyo" Da ƙarfi su na ɗaga hannu.
Jikinta Yagwalgwal har wani kalar karkarwa ya ke yi, ganin ana shirin yi mata juyin mulki a take a wajen ne ya sanya kawai ta juya da sauri ta bar wajen ta na ɗingishi.
Ta na shiga cikin ɗakinta ta mayar da ƙofar da sauri dan har an soma biyota, dan haka ta rufe ƙofar ruff sannan ta saka sakata kafin ta juya ta jingina da jikin ƙofar jikinta ya na karkarwa...
Sai kuma ta rushe da kuka sosai, ta na kukan ta zame ta zauna a wajen ta na haki.
Abun kamar a mafarki haka ta ke jin sa, wai yau ita Yagwalgwal ce aka yiwa haka akan Ladiyo? da me Ladiyo ta fi ta fisabilillahi..ta ya za ta bada kujerarta a ladiyo kujerar da ta ke ji da ita.
Kujerar da in har ta bada to fa ba ta da wani sauran gata a duniya, in ba nan ɗin ba ba ta da koina ba ta da wajen zuwa dan wallahi in aka kwace mata kujera sai dai ta bar gidan ba za ta zauna a ƙarƙashin Ladiyo ba ta san wahala za ta sha kwarai…
Kujerar da itace cin ta shan ta suturarta, apart from all this ma ae babbar faɗuwa a garesu bai wuce a ce ki na kan kujera wata ta sauƙe ki ta hau ba!
Shin da me Ladiyo ta fita?
Ta sake yiwa kanta tambayar ba tare da ta san waye zai bata amsar ba.
Kyakkyawar bafulatana kamar ita mai asalin kyawun fuska da sura sam! Bai kamata a ce ta bari Ladiyo ta wantsalar mata da mulkinta ba...ta san Likita ya ce mata ta dakata da buɗe ƙafa haka nan saboda ciwon ƙafarta amma gara ta mutu a matsayinta na sarauniyar wannan ƙungiya ta su mai daraja akan dai ta ci gaba da rayuwa a matsayin wadda Ladiyo ta yiwa juyin mallaka saboda ta gaza!...
Da wannan lissafin fa miƙe ta je ta zauna a kan katifarta ta na huci...
Tabbas ba su san wacece Yagwalgwal ba har yanzu! Za ta fito musu da asalin fuskarta ta yadda kaff ƴan ƙungiyar tasu da kuma jama'ar Unguwar Mariri sai sun yi dana sanin underestimating ɗinta da su ka yi, dama chan ruwa ne ya daki babban zakara amma wallahi yanzu ko Mariri za ta kama da wuta tabbas sai ta nuna musu she's the queen, leader and unstopabble.
Tabbas an kunto Kura!!!.
•••••••••••••
Wata kalar Halitta ce kamar dangin tsuntsaye…saboda tsabar yadda aka yi kacha-kacha da ita da tsafi da ƙazanta da ikon Allah sun gagara fahimtar mecece gaba ɗayansu, har Baba!.
Girmanta ya kusan kai Zakara ƙosashshe, haka tsayinta shima da yanayin kai da ƙafafuwanta, in ba ka lura sosai ba to ba za ka gane ba zakara bane ba.
Bayan furen da ta je masa da shi, har da layu da allurai duk an maƙala a jikin tsoka da ƙofofin halittar ko wanne ya samu wajensa….gashi tsokar jikin nata kamar an yi mata wanka da jini da gawayi…an goggoga a koina.
Abun dai ba kyan gani babu fasali sam!.
Da masifar ƙarfi Anne ta runtse idanunta, ranta in ya kai dubu to a yau ya yi ƙololuwar ɓaci! Tabbas yadda Baba ya tozartata wallahi itama sai ta tozartashi! Dukda ba ta ji ta tozarta ɗin ba dan ita abun kunya gaba ta bashi ba baya ba amma ta fahimci goal ɗinsa dan haka sai ta rama…
Gashi ya tarwatsa mata aiki dan haka in sha Allahu itama sai ta tarwatsa masa lissafi a yau ɗinnan…
Ta yi masifar kashe kuɗi akan aikin gashi a yanzu ta san ko
ɗura za ta yiwa Afra ba za ta taɓa yarda ta ci duk wani nama da zai fito daga hannunta ba. Ce mata aka yi ta tsunduma Halittar a yadda ta ke a cikin tukunya ta dafata luguff da kayan ƙamshi sosai saboda ƙarnin ya fita, in ta kammala tafasawa sai ta cire abubuwan jikin ta haɗa da gashi ko farcen Afra ta binne, shi kuma naman ta soya ta bata ta ci, bayan ita kowa ma zai iya ci wannan ba damuwa bane ba.
Yanzu kam a yadda ta gani ta san tata ta ƙare dan ba za ta taɓa ci ba….
Besides ma an ce mata in aka gani a haka a ɗanyenta aikin ko ta yi ba zai yi tasiri ba.
“Innalillahi wa inna ilaihirraji’un….”
Amal ta furta jikinta na wani kalar mahaukacin karkarwa.
Sai kuma ta juya ta wuce ɗakin Adda saboda dama chan ita ta na da tsoro sosai, Halittar kuwa kallonta kaɗai in ka yi duk jarumtarka sai ka taɓu dan ka na ganinta ka ga tsafi! Tsagwaronsa.
Salati Baba ya yi haka Adda itama yayinda Ya Amir ya yi saurin kawar da kansa gefe ya runtse idanunsa da masifar ƙarfi Ya Abba kuwa kafe abun ya yi da ido kawai ya na kallo, ransa na ƙarasa ɓaci! Ko a tarihi ba ya jin akwai azababbiyar uwa kamar Anne! Dan ko shakka babu ƴar cikinta ta shiryowa wannan ƙitimurmurar…yanzu da ace basu gani ba kenan wannan gagarumar wahalalliyar ƙazantar za ta ciyar da su, Allah kaɗai ma ya san me da me su ka saba ci…
Ya ƙarashe lissafin nasa tsanar Anne ya na sake dira masa a cikin zuciya, ba ya so ya tsani ɗan uwansa musulmi amma wallahi ya tsani matarnan kamar Mutuwarsa….
“menene wannan?”
Muryar Baba ta dira a dodon kunnuwanta, muryar har wani karkarwa ta ke yi tsabar baƙin ciki da ɓacin rai, ko shakka babu ba yau ta soma yi musu wannan ƙazantar a cikin gida ba!
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
Ya shiga nanatawa a cikin zuciyarsa.
A hankali Ya Amir ya buɗe idanunsa waenda su ka yi jaaa sosai ya ƙarasa wajen da abun ya ke ya yi addu’o’i sannan ya rarumo buhu da aka cusa a jikin windown ɗakin Ya Abba ya wareshi kafin ya nemo kara ya tura abun da ledar cikin buhu ya yi waje da karar da buhun da abun domin ya je ya jefa a kwata…
Dan masifa wajen da aka ɗauke abun a kai sai da ya chanja kala wala abubuwan da su ka gogawa Halittar ne ya gogu a wajen ko kuma dai tsabar kata’in da ya ke jikin Halittar ne ya sanya wajen ya sauya kala ya yi duhu sosai.
Juyawa ta yi za ta fita, Baba ya sake shan gabanta, sannan ya daka mata tsawa sosai kamar ba shi ba ya ce “na ce miki menene wannan abun? Sannan me za ki yi da shi?”
Wani maƙofcinsu da ya zo wucewa ne, ya leƙo ganinsu cirko-cirko kowa a fusace ya sa ya yi salati kafin ya ƙarasa shigowa ciki ya ce “subahanallah, Mallan a yi haƙurin dai da aka saba dan Allah….”
Shiruuu Baba ya yi ya gagara cewa komai, haka su Adda suma.
Ganin ta samu mafaka ya sa ta yi wani dogon tsaki ta zo za ta wuce, Baba bai san lokacin da ya saka hannu ya janyota ba sannan ya sake daka mata tsawar “ba za ki gaya min menene ki ka shigo mini da shi cikin gidan nan yau ba? Sannan da izinin wa ki ka fita da sassafe?”
Ganin yadda Baba ya gigice ya fita a haiyyacinsa ya sanya Afra da Adda su ka soma kuka! Duk haƙurin Baba duk kawaicinsa saboda Allah duba abunda Anne ta maida shi, gaba ɗaya ta gigitashi….
Shi kuwa Baba wannan karon da niyyar sakin Anne ya ke! Saboda ya gaji dan tabbas ta kaishi maƙura kuma babu wani alamun shiryuwa a tare da ita sai dai taɓarɓarewa! Afra dai ƴarta ce amma kalli tsafin da ta je ta ƙullo
ko lafiyar Yarinyar ba ta dubawa…kuma Allah kaɗai ya san sau nawa ta yi musu irin haka a cikin gida! Dama chan ya san ta na yi amma bai sake tabbatar da tsafi ne ta ke yi ba na gaske sai yau!
Sannan da ikon Allah nauyin da ya ke ji ya na dannesa kar ya rabu da ita yau kam babu shi, ƴaƴa in sha Allahu shi da Adda za su rainesu
Amma Anne kam ya gaji wallahi ya gaji!!!!
Ya aiyyana hakan a cikin ransa wata kwallar masifar baƙin ciki ta na ziraro masa…
A hankali ya Abba ya sunkuyar da kanshi ƙasa ya yi shiruuu kafin chan ya ɗago ya ɗan matso kusa da Baba sannan ya ce “Baba ka yi haƙuri dan Allah, mu bar maganar kawai ba yanzu ba…”
Dan zuwa wannan lokacin soron ya yi maƙil da makwabta da Abokan arziƙi. Ƙofar gidan kuwa kamar an zo ganin gomna.
Ko da Baba ya waiga ya kalli Ya Abba sai da ya ji kamar ya fashe da kuka shima, dan idanunsa tap! Su ke…cike da kwallah, ga shi sun yi jaa sosai.
Girgiza masa kai ya yi sai kuma ya ce “Abba na gajiii, sannan ba za ta wuce daga nan ba yau har sai ta gayawa mutane menene ta zo da shi! Sai ta ɗanɗani ɗacin maganinta a Bakinta yau ba zan barta ba.”
Tausayin Baba ne ya hana Ya Abba magana gashi yanayinsa ya sa ya kasa ci gaba da kallonsa dan haka ya yi saurin sunkuyar da kansa ƙasa. Sai kuma ya ɗago da sauri jin Anne ta na cewa “Me ka ke magana a kai? Me na shigo da shi? Abun na ka har da sharri kuma yau?”
Ran Adda a ɓace a ta ce “babu batun sharri fa Anne, ya ki ke nema ki juya magana ne? Kar ki yi halin Yara mana, duk ɗinmu nan har ke mun san kin shigo mana da abu cikin gidan nan dan haka ki faɗa, menene kuma a ina ki
ka samo….”
Murmushi Anne ta yi sannan ta ce “sannu baƙar munafuka! Ai kowa dama ya san duk kun tsaneni, dan haka dan kin ce hakan ba abun mamaki bane ba, kai
kuma”
Ta juya ta kalli Baba sannan ta ce “duk kalar ɗawainiyar da na ke yi da kai ba ka gani ba ko? Kullum ba ka da wani buri sai na ganin ka tozarta ni ko? To da Allah na dogara wallahi.”
Dai-dai nan Yadikko ta buɗe ƙofar ɗakinta ta fito ta na dogara sandarta ta ƙaraso wajen sannan ta ce “gafara dai!! Wayene ya ke yi mana hayaniya cikin daren nan?…”
Sai da Baba ya ɗan sunkuyar da kansa ƙasa kaɗan tukunna ya ɗago ya kalleta sannan ya ce “Yadikko Safiya dai ko…”
Wani ƙululun baƙin ciki ya na rufe shi, kallo ɗaya tak! Za ka yi mata ba ka buƙatar na biyu wajen fahimtar a make take maƙwal!!.
“Auho! Auho, eh safiya…
Su waye ne, mai ya faru?”
Ta faɗi hakan ta na mai tsayawa waje ɗaya da kyau a cikin soron sannan ta hau lalube.
Da sauri Anne ta matsa gareta ta riƙo hannunta sannan ta ce “Yadikko wae daga na fita amso sadaka a bayan layi shine su ka tisa ni gaba da tambayar ina na je…”
Da sauri Adda ta ce “wallahi ba sadaka ki ka je a amsa ba, a wajen sadakar ne ki ka amso
Kayan tsafi?”
Salati Anne ta yi sannan ta ɗaura da cewa “wae wanne kayan tsafi ku ke nufi ne? Ya na ina? Sharrri za ku yi mini ne ku haɗe mini kai? Zan sauya muku fa yanzunnan zan fito muku a Nuratu ta! Ba na ciki da **** **** uba…”
Dai-dai nan Ya Amir ya shigo cikin gidan, da sauri Ya Abba ya kallesa ya ce masa “a ina ka jefar da abun..”
“Kwatar bakin titi”
Ya bashi amsa ya na mai waigawa ya kalli
Mutanen da su ka yi
cirko-cirko a bayansa dan da kyar ma ya samu ya shigesu ya shigo cikin gidan, kamar ya san me ke shirin faruwa, ya ce “mun sallameku, ku je kawai ba komai za mu daidaita a tsakaninmu an gode.”
Kasancewar a cike ta ke kullum ya sa Ya Abba ya fahimci ko ya je ga kwatar ba zai samu abun ba ruwa ya riga ya tafi da shi, if not da sai ya ɗauko ya kawo ya nunawa mutane…in ta ga dama ta ci gaba da denying.
Ashar ɗin da Yadikko ta makawa Adda ne ya maida hankalin kowa garesu sannan ta ce “in na ƙara jin Bakinki sai na tsine miki tass!!”
Sai kuma ta ce “kai kuma Habu yanzu abun sadakar ne ba ka so a karɓo ko me?
To nima dan na makara inata lazimi ne tun Magariba, da tuni hadda ni za a je, sarai na san da batun kuma ba ka nan ne shiyasa ta tambayeni ni kuma na ce ta je…”
Girgiza kai Baba ya yi, sannan ya ce “ba komai Yadikko
Ki koma ciki shikenan komai ya wuce…”
Dan gaba ɗayanta a buge ta ke yanayin maganarta ma kamar wata ƴar daba gata dai tsohuwa tukuff da ita shiyasa abun duk sai ya zama wani very awkward.
Sosai Anne ta ji daɗin yadda Baba ya muzanta, dama tunda ya yaga ledar nan ta ci burin yau sai ta tozartashi wallahi, sai ta kunyata shi fiye da zatonsa a yau ɗinnan, na Yadikko somin taɓi kenan, sai ya san ya taɓota, sai ya kwashi kashinsa a hannu.
Nuratu ba ta barin ta kwana.
Ƴan Uwana maza da mata, ku tsaya in baku labarin amintaccen guri kuma muhalli na siyar da ingantattun *KAYAN YARA* na alfarma, siyayya cikin aminci, farashi na musamman da babu irinsa(mafi rahusa), kaya na kece raini da fita kunya sai a *H&A KIDDIES CLOTHING*
Domin samun su ku garzaya shafinsu na instagram mai suna *H&A_KIDDIES_CLOTHING*
Ko kuma ku nemesu a WhatsApp ta number waya kamar haka *08143828139*
Kar ku bari wannan damar ta wuce ku...Kaya na ƴan kwalisa sai a *H&A KIDDIES CLOTHING* ga kyau ga quality ga araha dai-dai kudinku tested and trusted.
Za ku iya samun kayan Yara na zuwa gurin biki, suna, birthday parties, kayan zaman gida da dai sauransu....
location:Kano
Delivery:NationWide.
kar ku bari a baku labari, sai kun zo🙏
SIYEN NA GARI, MAI DA KUƊI GIDA
BULAMA ✍️
0806 402 1951
0903 441 3252
[10/22, 8:25 AM] Maimoo 3: *BAƘAR TUKUNYA…*
*page 34*
….
Da kyar Anne ta tattaro nutsuwa ta nufi wajen Afra wadda tunda ta shiga ɗaki ta ke kuka, gaba ɗaya gidan ya burkice sai ka ce wajen zaman makoki.
Dama sallama baya daga cikin ɗabiunta ba kasafai ta fiye yi ba dan haka sai da ta kai ga shigowa har cikin ɗakin tukunna Afra ta lura da ita…
Da masifar sauri Afra ta miƙe tsaye sai kuma ta nuna mata hanya ta na kuka sosai kamar ranta zai fita ta ce “fita!!!
Dan girman Allah ki fita, ba na son ganinki.”
Matsowa Anne ta shiga yi Afra ta na jaa baya sai da ta kaita bango tukunna Annen ta saka hannu ta rungumeta, a take Afra ta sake rushewa da wani rikitaccen kuka dan gara a yi mata ƙawanya da ƙayoyi akan wannan rungumar da Annen ta yi mata! Ba wai.
Cikin kuka sosai numfashinta har ya na tsitstsinkewa ta ce “Anne ki cika