Showing 42001 words to 45000 words out of 160450 words

Chapter 15 - LOKACI BAI KURE BA COMPLETE

M SHAKUR   

01 Oct 2025

95

yabude motan yashiga yazauna, wajen window sa taje tasa hannu tai knocking, sauke glass kasa yayi kadan yamata wani kallo yace  get in bana magana da mutane awaje yaja glass din sama abinsa bata ganin komi kuma, dan jim tayi sai kuma tajuya tazagayo ahankali tabude motan batare data kalleshi ba tashigo tazauna taja kofan tarufe, tasauke kanta kasa tashiga wasa da yatsunta ahankali, motan yayi shiru, chan tadago kanta tadan kalleshi ganin ita yake kallo da sauri tamaida kanta kasa kirjinta na dukan uku uku tacigaba da wasa da yatsunta murya chan kasa tace  thank you for everything tayi shiru murya kasa kasa tace  Allah saka da alkhairi, Allah kara budi da matsayi da daukaka, thank you dan lumshe idanu Salim yayi yabude har cikin ransa yaji dadi but yayi shiru, dan shiru tayi tanaso tayi magana but tana tsoro sannan she feels idan batayi ba kaman she s taking advantage of him ne azamanin nan waye zai kashe maka kudi haka, ba a tambayi Mama ko kwandala in this big hospital ba only mean yabiya komi, dan dago kai tayi ta kalleshi hada ido sukayi da sauri tamaida kanta kasa su wai sojoji haka sukeda kallo, tana wasa da yatsunta maganan na mugun mata wuyan fita tana kuma fargaban fadamai but haka tadaure amman tai kasa chan da muryanta sabida tsoro da shakkan sa tace  nawa ka kashe mana ni da Waleed dakuma kudin asibitin Baba? In sha Allah I will work hard and pay you koda kadan kadan ne, uhmmm nawa ka kashe? Tai maganan ciki ciki wlh kalaman ma basu fito da kyau ba tsabagen tsoro dakuma fargaba, kusan two minutes taji shiru hakan yasa tadan dago kanta kadan faduwa gabanta yayi ganin wani mugun kallon dayake mata dayasa taji hanjin cikinta ya kada tamaida kanta kasa tawani yunkura dasauri takai hannu da gudu zata bude kofa ya danna lock wlh batasan sanda tace  kay& & .kaya kuri idan maganata ta bata maka rai dan daidaita muryansa yayi dan maganan datamai yabatamai rai yace  I will be back anjima da daddare for an answer game da maganan dana miki! Gyadamai kai tayi not herself why is he insisting about auren nan ita she hates aure, kai tsaye yace  get out! batasan sanda tabude motan da sauri ba har saida kofan yadaki next car dake wajen tafito da sauri tamaida kofan ta rufe, reverse yayi dasauri yabar wajen tabi motan da kallo idanunta sunyi ja sannan tawuce takoma cikin asibitin takoma tashiga dakin nurse tazo da takarda tabata tai signing tafice Mama ta kalleta sosai tace  meya ce? Faduwa gabanta yayi jin tambayan da Mama tamata sai lips dinta yahau rawa Mama ta tsareta da idanu ahankali tace  cewa yayi wai bayan an sallamemu mu koma gidansa daya kaini nida Waleed jiya dukanmu muyi zaman mu wai yabani gidan shine nacemai a a banso tai shiru Mama dake kallonta tace  sai yace mene? Kallon Mama tayi batasan mesa gabanta ke faduwa ba murya chan kasa tace  yace tunda inada girman kai bazan amshi kyautansa ba wai zai aureki yabani gidan a matsayin sadaki yabani zuwa dare nayi tunani Mama na kallonta tace  wani shawara kika yanke Safeerah? Dasauri takalli Mama tace  Mama mesa kike min tambaya haka? Mama na kallonta tace  aure nabiyu ne wannan kinada yancin zaban miji dakanki bata fuska tayi tace  Mama ni bazan kara aure ba harna mutu zanyi tunani nasan inda zamuje idan an sallami Baba Mama tadade tana kallonta sai bata kara cewa komiba.
EPISODE 2?? 4??





Waleed shima bacci yayi dan yayi ciye ciyen nan Mama ta kwantar dashi kan lafiyayyen couch na dakin.
Motsi Baba yayi hakan yasa daga Safeerah har Mama suka taso da sauri Safeerah tai wajen muryanta yayi rauni sosai tace  Baba Baba kanajina gani nan bude idanunsa Baba yayi ahankali yadan gani dishi dishi but he was able to know Safeerah ce murya chan kasa yace  Mamana kin dawo? Ina Waleed? Fashewa da kuka Safeerah tayi kawai ta rungume Baba sosai tace  Baba kayakuri dan Allah, Baba baran karaba kayakuri I m sorry kaji Baba, sabida nine rashin lafiyanka yatashi ko, baram kara tadamaka da hankaliba kaji Baba hannunsa yadaga ahankali taredayin murmushi dan gaskiya yasami sauki yace  ai kaganta ga kiriniya ga iya kuwa, Feerah rigima, ya isa toh bar kukan haka ya shafa bayanta Mama ta tsaya tana kallonsu kai Baba na son Safeerah bana wasaba to ko don ita kadaice yarsa oho amman baya wasa da Safeerah dagosa Safeerah tayi tana dago gadon ya zauna tace  meke maka ciwo yanzu Baba? Girgiza kai yayi yace  ba abinda ke min ciwo Alhamdulillah inama dan gani baga Waleed chan ga kujera ba yanuna Waleed dake bacci, Mama ya kalla yace  waya kawoni asibiti ? Yayi tambayan sabida yasan ba Mama Kubra bace wannan dake fushi dasu ahankali tace  Salim ne yakawo ka shiru Baba yayi yana tunani yatuna sanda yazo yana masa maganan Safeerah daidai nan Dr Isa yazo Baba yaduba tsaf sannan yayi murmushi yace  bansan ko Major Salim ya gayamuku ba, inhar kanaso zaka bamu yardan ka muna kyautata zato zamu iya maka aiki a idanunka da sababbin technology mu dasuka shigo tsaf zaka iya gani, Major Salim yariga yabiya kudin aikin consent naka kawai mukeso dazaran BP ka yasauka sai ayi fixing time ashiga surgery Baba tunda Dr Isa yafara magana kowa na dakin kallonsa yake especially Safeerah da kirjinta yahau bugawa batada burin da ganin Baba ya dawo, wayan nan idanuwan sune suka tankwafar da Baba yakasa samin sana a muguwar yayarsa na yanda taga dama dashi, Baba yaje school yayi FCE he s such a good teacher idanunsa suka dawo he can look for teaching job again har ranta taji dadi, Baba yadan kalli Mama sabida shi kudin ne aransa sai cin kudin Ogan yarsa suke but saiyaga Mama ta gyadamasa kai hakan yasa yace  to likita kunada consent dina a ina zanyi signing? Wata takarda yasan karba daga hannun nurse ya matso yasa a hannun Baba yasamasa biro Baba yayi signing, Dr Isa ya karba yace  I will monitor you zuwa gobe idan BP ka yazama stable za asa lokaci na aikin gyadamai kai yayi yace  an gode likita, Allah saka da alkhairi juyawa yayi yafice, Mama takalli Safeerah tace  kinyi salla wai ke yarinyar nan girgizama Mama kai tayi, Mama tace  tashi kitafi masallaci kiyi salla tashi tayi ba musu tawuce tabude kofa tafita ta rufo zata wuce saitaki ta tsaya dan yanda Mama ta korata when she can simply pray adaki is somehow kunnenta tasa jikin kofan muryan Mama taji cikeda damuwa tace  Yayarka nata kiran wayanka Malam nasaka wayan silent banso yarka maraji tagane, sakon ta ya shigo ta aiko maka da sako a message wayan Baba ya kalla cikeda damuwa yace  mita fada a sakon? Shiru Safeerah taji Mama tayi sai chan tace  waya baka izinin shigomin dawani kato gida? Gidanka ne ko gidan ubanka ne? Gidana ake shigomin da wasu batare da izinina ba to bari kaji zumunci yaci uwarsa da ubansa tunda baku da godiyan Allah dakai da matarka kuma ku kama sahu kubi yarku ko kofar gidana kada ka kara zuwa inba hakaba saina maka wulakanci wanda harka mutu bazaka mantaba munafuki shashasha Mama ta sauke ijiyan zuciya ta kalli Baba tace  yanzu ina zamu Malam? Ta ina zamu fara gamu da y a, gamu da jika? Kano zamu koma da ake nemanmu akashe? Inamu ina zaman Abuja? Ko an maka aikin ma a ido kafin kasami aiki it takes time a zamanin nan damuke, bazan maka karyaba nadamu Malam murmushi Baba yayi saiya rungumo Mama yanada danne damuwa yace  kidena damuwa ni nasan Allah bazai barmu ahaka ba, ya isa dan Allah karki kuka yarinyar nan tazo ta gane wani kalan nauyi Safeerah taji zuciyanta yamata sai kawai ta tashi wajen kofan tawuce masallaci salla tayi tasa goshinta akasa takuma yi shiru kunya takeji tamayima kanta maganan aure after abinda tagani a auren, saita kasa rokon Allah komi ta taso kawai ta zauna har akai asir tayi sannan tadawo, tana bude dakin taga wani soja aciki yakawo basket dake dauke da manya manyan kulan abinci ga gwangwanin cerelac da madara a gefe aikin Salim ne, why is he so good to her? Meya yakemata alkhairi haka for mutumin da sau biyu sika hadu on Monday and Tuesday what is happening? Godiya Mama tama sojan yajuya yafita tabude kulan dan wlh yunwa takeji, tuwon shinkafa ne da miyan kuka mai kifi da kaza da man shanu, sai jellof rice da chicken tace  mezan sama ka Malam ahankali Baba yace  tuwon yabani sha awa samai tayi ya karba yafara ci sai kallonsa Safeerah take Mama ta kalleta tace  ke bazaki ci ba ahankali tace  anjima zanci duk son abincinta dakuwa yamata yawa she loose apatite.
EPISODE 2?? 5??






Shi daman iyayensa sun sani ko yana gari baiwani cika zama gidansu ba sai idan yaga dama ko Ammi na kewansa he s always fighting da Daddy so he s avoiding him, gidansa na barrack yawuce bayan yatashi daga office, wanka yayi yasaka simple yadi brown jumper ce dinkin, Hermes slippers yasaka na maza yafito yana zuba uban kamshi, wata envelope dake kan table na falon yadauka yabude yaciro takardan yakalla sai kawai yamaida cikin envelope din yarike yafito yashiga mota, super market yabiya yayi sayyaya mostly for Waleed ne da irin kayan tea yasaka a booth yakoma gaba yawuce hospital wasu soja yabama kayan akai dakin ya tsaya yayi isha i a mosque yayi magana da Dr Isa yana basa update kan lafiyan Baba.

Duk suna dakin Mama na goye da Waleed da akeso yayi bacci dan rigima yake saiya fita waje wasa yamafara gyangyadi while Safeerah na magana da Baba akai knocking Mama tawuce tabude kofa soja ne yashigo da uniform da leda yace  good evening Oga yace na kawo he s coming ya ijiye yajuya yafita Safeerah tai shiru tana kallon kayan kaman yanda su Baba keyi tace  zan maidamai abun yayi yawa Baba ahankali yace  ke kul babu kyau maida kyauta bata sake magana ba almost 20mins akai knocking tareda sallama gabanta kawai yafadi jin muryansa, Mama tace  shigo Salim bude kofan yayi yashigo Safeerah takasa kallonsa ya gaisa da Mama yama Baba yajiki, Baba yace  Salim dawainiyan nan batai yawa ba? Toh mungode Allah amfana, nagode kwarai Allah ya saka da mafificin alkhairi kansa yasauke kasa yace  Allah kara lafiya Baba, kadinga cin abinci akai akai sannan karage damuwa Baba, duk batada amfani Baba kadakai yana yabawa da natsuwan Salim da hankalinsa yace  ba shakka haka maganan ka take Salim, Allah yayi albarka anatse Salim yace  tom Allah saida safen ku Allah baka lafiya Baba sosai Baba yaji dadin addu an yace  Ameen Ameen Salim nagode sosai juyawa yayi yasaci kallon Waleed dake bayan Mama karaf Mama ta lura murmushi tayi tace  abokinka yayi bacci da yanzu yafara binka sunnar dakai kasa yayi yace  saida safen Mama, zanzo gobe da yamman In sha Allah Mama da Baba sukamai godiya, Baba shi kawai yanason yaron wlh hakan yasa yakalli Safeerah yace  baki iya gaisuwa bako, anyways ke jeki masa godiya ita sai yanzu tasan bamatayi gaisuwa ba, mikewa tayi tawuce tana bude kofan tagansa tsaye gefen kofan saida gabanta yafadi, kaman daman ita yake jira yayi gaba abinsa tabisa abaya dudda bataso taje har waje ya shige mota kin shiga motan tayi hakan yasa yasauke glass yamata wani kallo dasauri tashigo tamaida kofan tarufe, Envelope yadauka yamika mata yace  take this dago kanta tayi takalli abinda yake bata but kallon dayake mata yasa tasaka hannu ta amsa ahankali gabanta na faduwa yadauke kansa yakalli kofa yace  that is the house papers! Dasauri ta kalleshi shima juyowa ya kalleta da kyau wani irin kwarjini yamata dasauri ta sauke kanta kasa chan yace  remember i made this offer since naga baki son kyauta it hurts your ego yasake shiru chan for the second time today yace  marry me Safeerah! Wlh gabanta faduwa yayi da karfi akwai yanda kalman ke fita daga bakinsa yake shiga kunnenta, why is he so adamant about ya aureta, yanda kirjinta ke bugawa saitaji gumi yasoma keto mata, he sees and noticed yanda take tsoronsa if he wants zai iya tsoratata now and hear ta yarda da zancen auren but baison haka, shi ko bata auresa ba yariga yabata gidan har ransa, he s just using the gidan ne as excuse he really wants to marry her, dudda baida tsoro but deep deep chan chan kasan zuciyansa baisan mesa ba he s scared kartace bazata auresa ba, kotace ta yarda ta karbi kyauta basai sunyi aure ba, he s just praying kar her little brain dinta yayi wayon gayamai haka, shi kansa baisan mesa he just wanna make her his ba, baitaba feeling haka for Nana ba, but look at the way yakeso wata tace ta yarda zata auresa.
Calmly yace  I told you nabaki zuwa dare for final decision naki, here are the papers kirike gidan nan amatsayin sadakin ki dasauri tadago kanta takalleshi gabanta na faduwa batason aure, dan rage muryansa yayi yace  a musulunci mace can decide to collect anything as sadaki, zaman1n Annabi akwai wacce aka bawa takalmi a matsayin sadaki, akwai wacce aka koyama suratul Fatiha a matsayin sadakinta! Baki Safeerah tabude dake rawa sosai zatai magana hannu yadaga mata hakan yasa maganan ta makale a wuyanta yace  I am not forcing you, aurena is your decision! I just wants to help you! I don t need anything from you kome azuciyanki, kome kike tunani cus nasan kin taba aure, all of that bana bukatan komi, I just simply wanna help, and it all depends on how far you can go for parents naki! And Waleed sosai gabanta ke faduwa, everything nadawo mata especially messege da Momma ta turo dasuka boye mata basu fadamata ba, rashin hankalinta da haukanta yasa all this yafaru dasu su Baba yanzu suma are stranded like her, byro dake gefen wajen ta tsare da idanu kafin ahankali tamika hannunta dake rawa sosai tadauka wani irin boyayyen ijiyan zuciya Salim yasauke daya rasa ta mecece, envelope din tabude tajawo papers din tafito dashi murya chan ciki that sounds kaman tana kuka tace  bana gani kunna mata wutan motan yayi ta kalli papers din saikuma ga agreement da aka rubuta sadakin Safeerah ga signing dinsa yayi saura nata, hawaye ne yadauko daga idanunta ya sauka kan papers din ya tsareta da idanu he knows she is scared, she s troubled, tana cikin tsoro what if abinda yasameta ada yakara samunta a aurensa yasan she is signing this papers sabida babu yanda zatayi ne sabida her parents needs it so somehow zamata iya ji kaman he is taking advantage of condition nata ne, but is not like that, he wants to protect her with everything and anything in him, he wanna become her shield and make her untouchable, he wants to give her everything and anything she ever wanted in her life, he will bring back that happy Safeerah ta 5yrs back and remove this sadness and pain daga zuciyanta.

Karasa signing tayi saita ijiye papers din ahankali da pen din kan cinyanta, takai hannu ta goge fuskanta tass sannan batare data kalleshi ba tadauki papers din ta mikamai ahankali tace  na yarda zan aureka hannunsa yasa ya karbi takardun yace  ok sannan yazare aggreement din yamaida takardun gidan envelop yadauki key gidan yasa acikin envelop din yace  your house papers and key Madam Salim! Kaman jira take rushewa da kuka tayi kaman yar yarinya tasa hannu ta karbi papers din tajuya tabude kofan motan dasauri tafita ta maida kofan tarufe ta wuce ciki tana share fuska ya tsaya yabita da kallo harta shiga kafin ya sauke ijiyan zuciya ahankali ya kunna motan yayi reverse yafita daga hospital din tadade a lobby asibitin saida fuskanta ya washe sannan tawuce dakinsu tabude kofa ahankali Baba yayi bacci sabida alluran dayake kai ga Waleed kwance gadon kusada Baba yana bacci, Mama na zaune kan kujera tana jiranta file din ta ijiye kan drawer tazo kusada Mama tazauna jikinta duk yayi sanyi, Mama tace  menene a file din? Kasa dagokai tayi ta kalli Mama, anatse Mama tace  Safeerah! Dago kanta tayi idanunta sun cika da hawaye Mama tace  nace menene an envelope din chan? Hawaye ne ya sauko daga kan idanunta tace  takardun gidan na amso, zan auri Salim Mama!
EPISODE 2?? 6??



Yau duk wani schedule nasa he cancelled it inda ma ake bukatan sa he makes sure yayi assigning soldiers dazasuyi representing nasa, kwata kwata baya so yama Dad maganan nan agida dan shi wani irin mutum ne da yanada principles, ya tsani yana magana da wani another person from nowhere yashiga maganan, baison ya tunkari Dad da maganan yazama case, ko Ammin sa ko kannensa su jiyo su shigo zancen cus Dad can shout, so he decided to meet mahaifinshi a kampaninsa, Maradi Private Jet and Co.
Yau wata benz yadauka fara yayi parking kusada inda motar mahaifinsa yake a special parking space nasu yana sanye da very simple yadi mai bala in tsada off white, ba hula akansa saidai yasaka dark shade yawuce ciki sai gaidasa ake, maybe throughout this year this is the second time yake zuwa kampanin nan, direct elevator yashiga yayi sama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login