Showing 117001 words to 120000 words out of 202729 words

Chapter 40 - MAZAN KO MATAN HAUSA NOVEL

M SHAKUR   

17 Feb 2025

8947

tarnish his image because of stupid feminism mentality na we are equal nidashi, Baba wlh wlh Baba zaku rasani har lahira idan Nura bai komardani ba, Baba tsoron alhaki bazaima barni nayi wani aure ba dan kowa zan aura nasan sai Allah yasa ya gallazamini azaba wacce tafi wanda nabawa Nuri na sau dubu, Baba kaji tausayina cikin nan was the hope na zai komardani cus Nuri loves children but shima yafita, kai kadaine mahaifina hope dina Baba cus Nura najin maganan ka, yanajin kunyanka, kace ya aureni Baba, zuciyata zara tarwatse na rasa Nuri na, wayyooo Allah na ni Hadiza! Wayyyoo zuciyata na shiga uku, na bani, na lalace, na tagaiyare na ga ukuba, Baba dan kaunar dakakema Annabi Muhammadu SAW kasa Nura ya maidani” Tafashe da kuka majina shabe shabe for the first time Baba yasauke kai daga kallonta shima idanunshi sunyi jaaa but baiyi kukaba amman kowa na dakin harda Amadu tasa kuka.



Kuna ganin Baba yama Nura magana???

But then again! I feel bad and emotional for Hadiza, for ita da kanta ta zauna tai analysis na laifukanta haka dudda ance hali zanen dutse but ina ganin mu jira Muga new Hadiza ne ko Yaya??

Kuna ganin ta chanza ko a’a???
💫MATAN?? Ko MAZAN??💫


✍🏻M SHAKUR


EPISODE 3️⃣7️⃣

CHAPTER ONE IS COMING TO AN END😫 Labarin Nura da Hadiza yasoma karewa have you subscribe for chapter two?? Is just 1k, zamuyi magana akan Matan aure da Mazan aure masu biye biye, no judgement but I will teach you something you never knew about cheating and I will help you overcome it.
Kome kikeyi don’t miss this chapter 2!!
Chat me up today and make payment.
wa.me/+2347012181461

37
Juyoda kanshi Baba yayi a tsanake ya kalleta dudda ta bashi tausayi but ya danne, yakalli Mama yanda take kuka da Anty Jams dama Amadu ya nuna Hadiza yace “duk sabida yarinyar nan kuke kuka?” Saikuma yayi shiru dan yanda Hadiza tafadi abubuwan datayi da bakinta sai zuciyan Baba yasake sosuwa ya nuna Hadiza up and down da hannu yace “kin dauka wannan borin da hayagagan nan dakikeyi shine zaisa nakira Nura namai magana?” Baba yadanyi murmushi mai ciwo yace “Hadiza yanzu haka ki fadi awajen nan ki mutu ni nasan cewa lokacin ki ne yayi bawai damuwan Nura ko wani abu bane yakasheki ba, cuta ba shine mutuwa, shi mutuwa lokaci ne kinsan mutane nawa har wankan gawa aka musu daga baya suka farfado why? Because lokacinsu baiyiba, idan lokacin mu yayi, ko yanzu, ko anjima, ko gobe, ko jibi ko gata, ko citta ko badin badadan zamu mutu Hadiza” yanuna kanshi da hannu yace “kin ganni nan dattijon arziki ne sabida ke bazan zubar da kimata a idanun Nura ba, bazan taba mishi magana yakomar dake dakinki ba idan yanaso yayi yayi idan bayaso duka daya awajena abu daya zan fada miki ki kama Allah ki rike addu’a kuma, sannan ki nemi gafarar wayanda kuka kuntata mawa Allah yasa mudace tashi Amadu muje” tashi Adamu yayi suka fice Hadiza tai kuka tai kuka har saida Mama tai ihu tace “wai bazakima mutane shiru ba kashe kanki zakiyi da kuka, kima mutane shiru dalla” tashi Anty Jams tayi tawuce inda Hadiza take kama hannunta tayi tadagata tace “muje daki” da kyar Hadiza ta iya tabi Anty Jams daki.


Sunyi nisa sosai, Nura yana tuki yana kallon hanya ahankali Aman dake gefenshi yana kallonshi yace “Dady” dan juyowa Nura yayi yakalli yaron yace “yes Son menene?” Dan shiru Aman yayi sai chan yace “you don’t want to make Mommy come back home with us”? Dan kallon yaron Nura yayi sometimes tambayoyin Aman nabashi mamaki kaman wani babba, dan shiru yayi baice komiba ahankali Aman yace “Dady is it because Momy na zaginka”? Dasauri Nura ya kalli yaron kafin yace wani abu Amal ta taso da gudu tana leko da kanta ta wajen takalli Aman tana zaro idanu kaman wacce zatai gulma cikin whispering but kana iyajinta sarai tace “Ya Aman Momy use to call Dady munafuki…….” “Amal!” Nura yakira sunanta da tsawa saida yarinyar ta firgice tace “Dady sorryy ai bantaba fadi ba ko Ya Aman”? Gangarawa Nura yayi yay parking motan gefen hanya, yasan yaran sunsan suna fada but baitaba sani har zagin sun sani ba, dasauri yajuyo yakalli Amali daduk ta rude strictly yace “kika kara fadin something like this I will be very angry with you kinason Dadyn ki yayi fushi dake?” Girgiza mai kai tayi tafashe da kuka tace “Dady sorry” dan shiru yayi yana kallon yanda take kuka saikuma yace “come here” dasauri tazo hannunshi yasa ya share mata fuska yace “stop crying okay babu kyau yana suna sauraron fadan Momy and Dady is a bad habit” gyadamai kai tayi tace “sorry Dady” peck yamata a goshi yakalli Aman dake kallonshi yace “I dont want this discussion ever again am I clear”? Gyadamai kai yaron yayi yace “yes Dady” zaunar da Amali yayi, yatada motan tareda dan sauke ijiyan zuciya yawuce.

Ummi na zaune dakin Hajiya tana matsa mata kafa basu dade da dawowa daga kesson ba itada Meena taga yaran sun shigo da gudu abin ya bala’in bata mamaki da Nura yayi sallama yashigo falon sai mamakin ya idasa kasheta batasa ran ganinshi ba yau danta dauka awajen Anty zai kwana yau, gaisawa yayi da Hajiya Ummi ta kalleshi akunyace sabida Hajiya dake wajen tace “sannu da zuwa Baban Amali” dan kallonta yayi yasakin mata good smile yace “me kika dafamin am hungry?” Tashi tayi tawuce kitchen din Hajiya, Hajiya dake kallonshi tace “yamai jikin?” Ahankali yace “dasauki gobe zansa driver ki yakaisu suje su kwana jibi su dawo, gata dasafe zamu wuce Abuja dukanmu” gyadamaikai Hajiya tayi tace “Allah kaimu, shima yaron nan dake neman auren Meena ai katuna gobe zaizo yaganka ko”? Anatse yace “natuna Hajiya Allah kaimu” abinci Ummi takawomai yaci yayi damm sannan yawuce masallaci bai dawo gidanba sai around 9, dakin Hajiya yawuce yamata saida safe sannan yawuce side dinshi Ummi na zaune tana duba wasu books yashigo da sauri tasaki books din ta tashi dagudu tai wajenshi murmushi yayi yace “ammata na” ahankali tace “an samari na” murmushi yayi yadagata suka wuce kujera suka zube lamo tayi ajikinshi ahankali tace “na dauka awajen Anty zaka kwana”? Remote yadauka yashiga kunna tv irin wanda bayason maganan nan yace “anan zan kwana” lurada yanayinshi datayi yasa bata kara cewa komiba daura idanunshi yayi cikin nata yace “kallon fa wawatsula kikeso?” Wani irin murmushi Ummi tayi tun ranan data gayamai kalman yarike gam yake fadi, kannemai idanu tayi tana lashe baki ahankali tace “ni gwaguyanka nakeso nayi” ohhh shi baimasan yanda zai misalta abinba but kobaiso dazaran Ummi tamai batsa sai jikinshi yatashi bakinta ya shafa idanunshi na kankancewa yace “menene kuma gwaguya baby” sauka tayi daga kan jikinshi takai hannunta kan idanunshi tace “rufe idanunka kagani” kulle idanunshi yayi kawai tai kneeling agabanshi tasa hannunta ta daga riganshi sama tana kwance mazariyan wandon yadin jikinshi hmmmmm…
Saida Ummi takusan sakashi sakin mata fitsari abaki anan falo suka watsewan su.
**
Washe gari around 11 nasafe Nura yasa driver Hajiya yakai yaran gidansu Hadiza.
Jibin daya fadi jibin akaje daukosu suka dawo da tsaraba sosai washe gari suka wuce Abuja.
Ummi kusan mutuwan tsaye tayi ganin durmemen gidan dasuka koma manya manyan flat daban daban guda uku ne komi iri daya, saida yafara shiga da ita ko’ina sannan yakaita second flat din inda yazuba mata furnitures naban mamaki a akwati saiti 16 jere a tsakiyan babban falon sai kawai Ummi tahau kuka dasauri yaran sukahau tambayanta menene shima Nura ma haka dago rinanun idanunta tayi takalleshi tace “ko amafarki bantaba tunanin zanyi rayuwa a irin wannan gidanba, kamin komi kuma, ga akwatina kaman wata yar sarki” murmushi yamata yace “kına kuka agaban su Amali, Amalili look at Anty Ummi is crying let’s make her smile” sai kawai yama Ummi chakulkuli suma yaran sukahau mata tahau dariya sosai daganan suka wuce sama 4rooms ne asama ga masters bedroom nashi ga nata ga wasu dakuna biyu dayace anan su Amal zasu zauna daganan shida Aman suka wuce mosque dudda baya nuna mata komi but shigowanta gidan nan yakara tabbatar mata da Anty batanan duksai taji tadamu hankalinta yaki natsuwa sauka tayi itada Amali suka tafi kitchen kunga kitchen Ummi kawai tasaki baki suka kara fitowa waje wow gidan yahadu babban gaske yayi wani karamin kauye girma.


Damuwa tama Hadiza yawa taki kwaso kayanta daga Abuja tasake dagewa da addu’a da sallan dare, tanason taje tasami Hajiya but batasan taya zata mata magana ba yau ne the second time datake kara nadaman rashin shirinta da kannen mijinta, ijiyan zuciya ta sauke ta dauki wayanta tareda dialing number Ya Aisha amman harya katse bata daga ba sauran biyu takira basu dagaba, saikuma kaman bazata iyaba taciro number Meena tai dialing shima harya katse bata dagaba kawai saitaji hawaye sun zubomata dasauri ta sharesu ta ijiye wayan ta buga tagumi tai shiruuuu tafara tunani zaka iya kai downgrading yan uwan mijinka kana ganinsu kaman bakomi ba sabida mijinki na sonka but the truth is kowa nada rananshi arayuwan nan always respect kowa ijiyan zuciya ta sauke kafin ahankali ta kwanta akasa kaman marainiya Mama tadade tsaye agaban dakin tasaga labule tana kallonta amman bata sani ba, tsakanin uwa da d’a sai Allah, Uwace aduniyan nan duk lalacewan danta tanason abinta haka, tafi kowa tausayin Hadiza da damuwa da damuwanta, shigowa dakin tayi ahankali ta zauna gece ta hakan yasa Hadiza ta dan dago kanta saikuma ta tashi zaune da wuri takalli Mama, hannu Mama takai takama kuncinta tace “Hadiza na kin ganki kuwa? Kaman bake ba kashe kanki zakiyi ne dukkin rame saikace wacce kanjamau ki kama kinyi duhu, baki iyacin abinci, menene Hadiza? Ki hakura da Nura mana tunda shi ya hakura dake? Allah zai baki wani mijin daya fi zama miki Alkhairi” dan lumshe idanu Hadiza tayi cikin sansanyan murya tace “Mamaa” saikuma kawai tafashe da kuka Mama tadade tana kallonta kafin kawai ta mike hijabin Hadizan ta dauka da car key dinta da aka kawo mata daga abujan dan dama a plazan shagonta tai parking motan tadauki wayanta duka tamika mata dasauri Hadiza dake kallon Mama tana kuka tace “Mama mezanyi dasu?” Ahankali Mama tace “tashi kije wajen Hajiya go and amend mistakes naki Hadiza” Shiru Hadiza tayi tana kallon Mama saikuma cikin wani kalan muryan ban tausayi tace “idan takoreni fa” ahankali Mama tace “tashi kije kozata koreki bakomi ta isa ne but ki sauke nauyin dakikejin nan azuciyanki and asked her for sincere forgiveness ba irin wanda kikayi a asibiti ba, kinji don’t be scared tashi kije Allah zai dauraki akanta zan miki addu’a” Hadiza kaman tayi mutuwan zaune saikuma ta tashi ta karbi Hijabin tasaka ta karbi wayanta tawuce tafita.
Parking Hadiza tayi awajen gidan tadade zaune cikin mota sannan tabude kofa tafito jikinta duk yay sanyi kaman kankara dan batasan mezataje ta tarar ba tawuce tashiga gidan, matan datagani tsakar gida ta gaida tana tambayan ko Hajiya na nan aka cemata eh tawuce ciki sallama tayi agaban dakin daga ciki muryan wata mata ta amsa tace “shigo” ahankali Hadiza tacire takalmi tashiga ciki Hajiya tagani zaune kan kujera tareda wata mata wacce ita ta amsa sallaman tana nunama Hajiya wasu kaya da aka kawo ido cikin ido Hadiza tayi da Hajiya da sauri ta sauke kanta kasa matan tace “bismillah zoki zauna” wucewa Hadiza tayi tasami waje ta sauna akasa matan tace “bari naje Hajiya” Hajiya tace “to Salamatu ayi amfanida rabi kada ki manta” matan tace “to” tawuce tafita dakin yarage daga Hadiza sai Hajiya, ahankali Hadiza da kanta ke kasa tace “ina yini Hajiya” Kai tsaye Hajiya tace “lafiya lau Hadiza ya jikin naki? Naso zuwa dubaki amman kinsan kafan nawa maneji ne saisa, Allah yasa mai ceton ku ne sannu sannu”.

💫MATAN?? Ko MAZAN??💫


✍🏻M SHAKUR


EPISODE 3️⃣8️⃣

Why are you cheating on your husband?? “Sabida baya gamsar dani! Sabida yanada karamin gaba! Sabida he’s not romantic! Sabida baya bani kudi am suffering to feed our kids!”.

Why are you cheating on your wife?? “Sabida tabude dayawa! Sabida bata iya kwanciya agado ba! Sabida she’s local batasan wassup ba! Sabida bata gayu! Sabida auren hadi ne! Sabida bata daukan bukatu na!!!”
Kunsan this are the common reasons din da ma’aurata kebadawa na cheating???
Subscribe with 1k and read to learn chat me up now!!
wa.me/+2347012181461


38
Dan kallonta Hajiya tayi ganin yanda kanta ke kasa yasa tace “tashi ki dauko ruwa da drink a fridge ki debo duk abinda kikeso a kitchen ni kadaine Meena batanan” girgizama Hajiya kai Hadiza tayi baki tabude zatai magana saita kasa Hajiya duk tana lurada ita amman tai shiru ta maida kanta kan tv, cikin wata kalan murya dake breaking Hadiza tace “Hajiya bansan ta ina zan faraba, yau kalamai sunyi karanci abakina dazan hada nabaki hakuri bisa kuskuren danamiki abaya” yadanyi shiru sabida muryanta was shaking sosai tace “Hajiya nasan nayi abubuwa da dama dasukasa kika tsaneni harda su Ya Aisha ma I called all of them dan nabasu hakuri harda Meena babu wanda yadauki wayana I understand no one wants me, Hajiya dan girman Allah dan darajan Allah Hajiya kiyakuri ki yafemin kuyafemin dukanku gabaki daya Haji…….” Sai kawai kuka ya kufcemata Hajiya tai shiru tazuba mata idanu dukta lalace kaman ba Hadiza ba, tabama Hajiya tausayi dan she’s a mother babu abinda kecin mutum kaman guilt din yama wasu laifi basu yafemai ba dan gyaran murya tayi anatse dan ba kwana kwana tace “stop crying Hadiza ya isa Allah ya yafemana Hadiza gabaki daya wlh har raina nayafe miki, su Aisha baki musu komi ba wayan nan, Nura ma inamai tabbatar miki shima ya yafemiki” Hajiya tadanyi shiru tana kallonta har ranta din tayafemata tace “amman Hadiza bazan miki karyaba banma d’ana sha’awan aurenki har abada!” Dasauri Hadiza yadago rinannyn idanunta tana kallon Hajiya data gyadamata kai tace “Mun yafe miki kuma bamu rikeki araiba, an riga an zama daya yanzu Hadiza kin haifamana yara so har lahira ana tare, amman dai babu zancen aure tsakaninki da d’ana yanda kikeson Aman da Amal yanda kikasan darajan su ki kasan zafin haihuwansu haka nasan na nawa dan, koda kin chanza hali Hadiza wasu tabon basa goguwa dan haka kitashi kije amman idan zancen yafiyane wlh tallahi mun yafemiki, yaranki kuma idan sukai Hutu zaa dinga kawo miki su idan kinason ki gansu call me ko wani cikinmu za’a kawo miki su” hade hannayenta Hadiza tayi dagudu zuciyanta har mata yakeyi kaman zai katse tazo gaban Hajiya tana kuka sosai tace “Hajiya ki rufamin asiri, Hajiya Nura kadai nakeso arayuwana dashi kadai zan iya zaman aure” Dasauri Hajiya tace “d’ana yahakura dake Hadiza, please mubar maganan nan tashi kitafi akwai mutane a tsakar gidan nan kar aji muryanshi a shigo adauka wani abune tashi kitafi” Hajiya tai maganan tana dafa kujera tana yunkurin tashi kama kafan Hajiya Hadiza tayi tace “Hajiya kiji tausayina ki kalleni amatsayin yarki” Dasauri Hajiya ta nuna Hadiza da hannu tace “kul! Karki sake ki kwatanta yarana dake sabida nabasu tarbiyan da sunsan banbancin matsayin namiji da mace! Kap yarana mata mazajensu ne jagororin su! Yarana bazasu taba yima mazajensu kazafi ba har abada wlh inaaaa! Basasu taba yima masajensu tabon dahar abada bazai bar sunan su ba! You have no idea kotun da shairin dakikama Nura yayi affecting nashi da business nashi kinsan investors nawa ya rasa? Sakenmini kafa!” Hajiya tamata tsawa dan batason tuna abubuwan da Nura yagayamata ya sameshi daya koma Abuja kwanakin baya, ahankali Hadiza tasaki kadan Hajiya idanunta sunyi jazur Hajiya tace “wallahi na yafe miki Hadiza kinji namiki rantsuwa hakama Nura ai ko darajan yaranki yakai mu yafemiki amman I will tell you this to your face dan bazan miki karyaba ko in yaudareki ko amafarki, ko amafarki Hadiza banama d’ana kwadayin ki kuma, sai anjima” Hajiya tawuce dakinta ahankali tareda maido kofa tarufe.
Hadiza tai kuka tai kuka awajen na. Harta godema Allah takai almost 30min sannan ta tashi da kyar tawuce ta tafi bata damu da mutanen dake tsakar gidan ba haka tawuce, Hajiya tadade gaban dakin tanajin kukan Hadiza dake tabata kafin ahankali takoma bakin gado ta zauna tai shiru saida taji tafiyan Hadizan sannan tasauke ijiyan zuciya wayanta tadauka ahankali tai dialing number Nura.

Ringing daya ya katse yakirata back ya gaidata cikin tattausan muryan irin conversation na d’a da mahaifiyarsa Hajiya tace “yanzu Hadiza tabar gidan nan” dan shiru Nura yayi baice komiba, ahankali Hajiya tace “tazo tabani hakuri kan komi dayafaru tama kira su Aisha wai tabasu hakuri amman duk basu dauka ba, Nura duk ta lalace” “umm” was the only thing daya fito daga bakin Nura dan shiru Hajiya tayi sai chan tace “Son I know nidakai we had this conversation before, nasan abubuwan da Hadiza tamaka hurt me deeply, and I support you dakace bazaka kara zaman aure da ita ba but I looked into her eyes today Nura I saw sincere nadama, wlh danasani ne cike tap a idanunta, koda naji haushi ina fushi da ita the decision is still yours Nura, kanason Hadiza ko baka sonta yanzu tell me the truth Nurudeen” dan shiru Nura yayi tareda lumshe idanunshi ya jinginar da kanshi jikin kujeran office din, kaman bazaiyi magana ba ahankali yace “I will always love Hadiza Hajiya, but har cikin raina nahakura da ita kaman yanda na fadamiki ranan, nabude new chapter in my life, na yafemata, I’ve moved on, bazan iya cigaba da zama da itaba anytime na kalleta I will remember itane the first person data taba zagina kala kala aduniya, the first matan data chakumeni, tamin kazafi tamin kotu, akwai somethings aduniya dahar kamutu kanaso but u will never get them sabida wasu dalilai I think Hadiza is just one, Hajiya inason Hadiza sabida bani nadaurama kaina son ba Allah ne shi kadai zai iya cire mini, but nahakura da ita har abada, please Hajiya kada ki karamin maganan ta”
Ijiyan zuciya Hajiya tasauke tace “shikenan Nura, remember this kome kakeso I will always support you, all I want is inganka

25, August 2025
Saadatu Ali

Yes

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login