Showing 6001 words to 9000 words out of 225093 words
asiri..
Ahumaggan nan zai fada ma aljanun su cewa yayi fyade ma budurwa,a gidan sarki kuma
zasu jira mu har kwana uku idan bamu kai kanmu ba kinsan zaki iya mutuwa ko?
Da sauri Tace eh..nasani
Anma ai basu sanin ko wacece akayi ma fyaden ba har sai takai kanta ko?
Ba tare da wani shakka ba Nace eh
Wani ajiyan ziciya Junnut ta sauke cikin sanyin tace "bahiyyah,Shiyasa nake so ki taimakeni...sai kuma tayi shiru alaman kalman ya mata nauyi abaki
Nace inajin ki junnut.. Nan ma sai ta kafe ni da ido tayi shiru abun ta
Da kyar sanda na dinga takura ta da cewa dare na dada yi mana ajejin,gashi tashin hankali ya gama mamaye zuciyar mu kafin ta shirya furta min.
Anan junnut ta nemi alfarma ta tana cewa
"Domin cikar burin rayuwa na
nake rokon ki da ki sadaukar min da darajar ki wajen sarki
Cikin kukan da bansan dashi ba Ta dada ruko hannu na tace
"Ina nufin kice masa kece akayi miki fyaden bani ba..
Zu je tare amma ke zaki dauki laifin
Inyaso koda an wanzar da hukunci akanki sai mu hada hannu mu dauko abbu mu kaishi chan inda ummah surbajo zata koma kasar nigeria sai ayi jinyar sa da dukiyata.
Cike da mamaki Nace junnut?kinsan me kike cewa kuwa
Tsaye ta mike tana dingishi,dan tun kafin na kawo korafi na tace toh nidai wallahy zan kashe kaina,daga yau muyi bankwanan a duniya bahiyya...kinsani
Idan bazan cika buri na ba gwara na mutu.
Nima tashi nayi a rikice nakai mata dan karamin mari a fuska,a zuciye nace zaki kashe kanki baki da hankali ne...
Cikin kukan bakim ciki ta sulale ta tsuguna gaba na tana mai tana kafafu na a kaskance tace bahiyya dan Allah ki taimake ni,wallhy nayi miki Alkawari zan dawo miki bazan rabu dake ba
...zamu yi rayuwar mu mai tsafta ni dake har abada..Alkawari ne.
Wani irin Tausayin ta ne naji ya shige ni sosai domin Wani Kuka mai shiga rai takeyi ayayin da nima na fashe da kukan na tsuguna na rungumo ta jiki na muka dunkule munayo tare..
Cikin tsananin son naga na yaye mata damuwar ta nace mata na Amince zan dauki alhakin yin mata haka..
Sai dai sharadi na shine wannan maganan ya kasance wata babban SIRRI l mai girma a tsakanin mu wanda ko abbu bana son yasan dashi.
Junnut ta dada rungume ni tana kuka tana min godiya
Tare da min Alkwarin duk dukiyar ta na wajen ummah surbajo zai dawo na jinyar abbu na.
Haka na dauka wannan kayan alkwarin makaina
Ni sam Bandamu da wani curses din da za'ayi min gobe agidan sarki ba.
Sannan a tunanina na yaranta na bana kawo cewa akwai abunda zai tsare ni wajen nema mahaifina gamsashen lapya,wani tsafi da aljanu duk gani nake sun yi kadan su kara da ikon Allah..
Iya kaci ne ace inhar da ummah surbajo zamu zauna a inda zata koma gobe a birni to zan iya rabuwa da abbu na. Toh Wannan shine kadai babban abun daya yake damu na yanzu..
Ta ya zan fara ma abbu bayanin haka?gashi Bantaba boye mishi komai ba sai yau da nake shirin zan boye mishi sirri na da kawata junnut..
Shin ko akwai abun da ya fi dadi a duniya kamar kasan kana da iyayen ka a raye koda kuwa baku tare?.
Follow @surayyahms
_toh Fans ina jiran amsa🤚🏻_
First page Dedicated to members of bwa
TOH YA KUKA GANI?ACIGABA?LET UR COMENTS SPEAK OUT FOR NEXT POST.
#SURAYYAHMS
[9/29, 2:42 PM] 0mer Farouk: _*♡AHUMAGGAH🌺*_
_A nigerian historical fiction_ _*WATTPAD SURAYYAHMS*_
_Brilliant writers association_
_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_
_2⃣-the cross roads♡_
Cikin daren A daddafe muka iso gida,samu mukayi abbu ya riga ya dauke motsi amma kuma numfashin sa bai dauke ba.
A gefe na ajiye maganin sa duka muka zube gwiwar mu agaban sa muna jimanta yanayin sa he is kind of stable now
nan na fita na shiga hade ruwan magani tare da ruwan zafin da junnut zata dan tsaftace jikin ta ita kuma tana dakin tare da abbu tana tallafa masa.
Babu abunda junnut take yi sai hawaye.
Abbu yayi luiii da shike ma bayada karfin magana sai ido yake binmu da shi har muka gama duk abunda zamuyi.
Anan Bamu kama hanyar gari ba sai da na tabbata junnut tayi wanka ta dan kimtsa kanta kafin na gyara na abbu kwanciya na fito na rakata har layin gidan su sannan na dawo.
Cikin wani irin yanayin tunani nake tafiya,babu abunda nake tunowa sai alkawarin mu da junnut da yadda komai zai zamto min daga gobe..
Shekara ta goma sha hudu ne kawai a duniya dan haka bansan ko hukuncin dana yanke dai dai bane ko ba dai dai ba.
Washe gari Da safe Bayan na hada ma abbu na maganin sa na bashi ya sha,sai nayi zamana gaban sa na tsura masa idanu na bance uffan ba...,na dade a haka ina tunani dan a daren jiya ma ko tunanin kiftawa baizo min ba,yanzu ma kallon shi kawai nake ina tuno irin rayuwar farin cikin dasuka bani shida ammuh a lokacin da bankai haka ba
Tabbas ummah surbajo tana da ilimin da zata sama min mafita game da rashin lpyar Abbu..
So nake abbu na ya warke sosai ya rayu koda babu ni atare dashi...
Sanyin safiya na kan busowa na fito nayi alwala nazo kan abbu nayi masa karatun qur'ani dai dai inda na kama..
Chan naga Abbun Ya farka ya bude idanun sa amma ko tashi da kyau bazai iyayi ba.
A Yadda na saba wanke shi nayi masa alwala haka nayi ta taimaka masa har yayi sallah...
Dan kadan ya sake shan maganin sannan ya kwanta yana kallo na,sosai yanayin sa ya dada rikita ni..
Gani nake idan ya kwanta baccin hala bazaima tashi ba tsaban wahalar dayake sha da jikin nasa.
Dana ga kallon
nasa yayi yawa
Chan sai abun ya fara bani a kwakwalwata ko dai wani abun yake bukata ne?sai nima bance komai ba,inda yabi da ido nake bi sai banga me yake kallo ba face ni,sai na tashi tsaye Ina dan dube dube ko zanga ya min alama..
Murmushi kawai yaso yayi amma Wani tari sai ya shake shi,karasowa jikin sa nayi a dame nace sannu abbuh...
Tarin bai tsagaita ba sai naga abbu ya ruko duka hannaye na
Yace bahiyyah,jiya a ina kikaje kika samu magani?
KAllon sa nayi A hankali na furta "jeji",wani runtse ido naga yayi alaman baiso yaji hakan ba amma baya da karfin da zai yi scolding dina..
Yace ke da junnut kuka je ko?
Toh meya faru da ku naga jini a rigar ta,ke kuma har yau idanun ki basu washe ba..shin bazaki fada ma mahaifinki damuwar ki ba bahiyyah?
Yadda yayi maganan sautin muryansa na karkarwa yasa Sai nayi shiruuu tsawon lokaci kaina a kasa bance komai ba.
Muna cikin haka aka yi sallamah agidan mikewa nayi na fita abbu na bina da kallo mai dauke da alaman tambaya.
Dogaren sarki nagani,yace Aika ne daga gidan sarki modibbo akan cewa naje cikin gaggawa
Abbu dai bai sake tanka ni ba Nan na shirya kaina na nufi gidan su junnut.
Junnut ce take gayamin cewa a jiya data shigo gida cikin dare ta cikaro da tashin hankalin ummah surbajo sai ta tutsiye ta da fada har da mari har sai da tayi mata karya akan abunda ya faru sai dai ta juya kan labari ya koma kaina kamar yadda muka shirya.
Kenan ummah surbajo ta rike cewa nice akayi wa fyade ba junnut ba, kwata kwata batason abunda zai shiga rayuwar junnut anan gaba dan haka ta sata agaba akan maganar.
Dan akan junnut umma surbajo bata da sani bata da sabo.
ummah surbajo gani take idan ta kyale maganan har ta bada junnut goyon baya ta boye ma sarki,toh hala wani abu zai iya biyo baya.
junnut tace min yau din ma ita tasaka ta agaba akan dole sai taje ta fada a gaban sarki modibbo,da taki data so haka har magana yaje gaban sarki shine aka aiko a dauko ni.
Daga nan Bamu wani bata lokaci ba muka kai kanmu gidan sarki modibbo muka aiwatar da plan din mu na cewa ni Bahiyya nice Ahummaga suke riske ni ba junnut ba..
Sai muka juya kan labari muka shirya duk yadda zamu samu hadin kansu.
Toh Kamar yadda aka saba jama'a sun taru sarkin matsafan da aljanun sa duk sun hallara za'ayi min hukunci.
Ganin mun yi tsuru tsuru muna rarraba idanu salon marasa gaskiya ga idanun mu kuma cike suke da hawayen tsoro sai yasa basu kulaba,tashin hanklin mu yasha masu sarki modibbo kai har yasa ba a bata lokaci wajen zurfafa bincike akan lamarin ba aka yanke hukunci.
A wannan lokaci koni bana kuka da jimamin da kawata junnut keyi,Abbu na chan gida bai ma sanda haka ba.
Anan fada kuma Sabida babu mahaifina awajen sai aka bani sharadin awowi biyu da cewa na tattara kaya na na bar garin an shafe ni a zuriar su,sannan ina gani boka da aljanun sa suka gama tsubuce tsubacen su akaina ina jin su bance uffan ba.
A Duk ilahirin jinsin zuriar fulani dake fadin jejin Nan basu kai kimanin dubu daya da dan dori ba dan haka kusan kowa yaji abunda ya faru dani
Wasu sunji bakin ciki sosai,wasu kuma Sunyi murna musamman yan mata sa'oin mu da suke ganin nice matoshiyar sa'ar su wajen samun mijin aure.
Junnut kam gaba daya sai ta birkice,itakadai ke rike dani tana jimami har muka kai kofar gidan su.
Muna Isa kuwa na samu har bakin nasu sun zo wanda zasu tafi da ita chan birni..
Dana shigo gidan ma,sanda
Ummah surbajo tayi min fada sosai akan abun da ya faru damu jiya nida junnut din
Tace duk gangancin mu ne ya jawo mana.
Don junnut bata manta marin da ta karba ajiyan data dawo cikin dare jikin ta duk wani iri ba...sai nayi tunani wai don ma junnut batace ma ita akayi ma fyaden ajiyan ba kenan?ashe kuwa da ta fada gaskiya hala ummah surbajo ma kawai zata iya kashe ta har lahira da fada.
Haka mukayi tsuru tsuru muna bata hakuri,da shike ma ummah surbajo tana da ilimin bature da yelwatan tunani Daga baya Sai ta shiga tausaya mana gaba dayan mu.
Dataga inata kuka sai da tayi kusan sani zazzabi da nasihan ta,aganin ta duk tsumayin rabuwa da aminiyata ne ya kawo ni gidan nasu a yanzu da bani da wata rayuwa mai daraja a idon kowa agarin.
Hakuri ta bani sosai tana cemin
Allah ya qaddara nan ne karshen gabar kawancen ki da junnut.
Kema yau zaki bar cikin wannan jinsin ga Junnut itama zataje chan nahiyar da ta dubi kudu wato chan persian empire asalin cikin kasar iran wajen dangin mahaifiyar ta.
A Cewar ummah surbajo,asalin mahaifiyar junnut jinin sarauta ce ta wani babban daula zuriar sarauniya DAWLAT KHATOON dan haka su kayi alkawari zasu rike rayuwar junnut a matsayin yarsu ta har abada gashi kuma yau sunzo cika alkwarin su.
Ita kuma ummah surbajon zata koma da zama na dindin a kasar nigeria chan cikin jahar kaduna.
Muna cikin saurarar ummah sai ga umaru dan mashayin garim ya taho gigice ya zube gaba na.
Yace baahi,ki taho,baba ahmadu mai magani...yana magana yana hako yana nuna hanya
A take naji yawu na ya dauke chak kaina yana wani iri bugu...
Nace mene ne,ina abbuh?
Su umma da junnut duk sukayi tsaye suna kallon shi da fuskan razana kamar yadda na ke binshi da kallon nima
Nan umaru ya sanar dani cewa ai yana tahowa ne yaga abbu na akasa kan hanya yana ta aman jini
Runtse idanu na nayi,dama saida jiki na ya bani cewa abbu zai iya cewa zai biyo ni yaga me na ke cikii
Ban tsaya sauraran komai ba,na sa gudu na fita agidan junnut zata bi baya nah ummah surbajo tayi sauri ta finciko ta tana cewa ke wai ina zakije? Bakijin magana ko
Maza wuce kije ki shirya yanzu zaki tafi, tace ummah zanbi bahiyya ne,sai bata kulata ba kuka junnut ta fashe da shi tace ummah Abbu baida lpya sosai dan Allah ki barni naje amma haka ummah surbajo taki sam tayi mata shiru junnut kuwa ta cigaba da kuka har saida ummah surbajo dan kanta ta gaji tace toh taje ciki tayi shirin ita zata bi bayana taga meke gudana kafin nan junnut ta amince ta motsa.
Nikuwa ina isa na haura kan abbu duk yayi wani iri,ga datti da kuran kan hanya ya shafu akan rigar sa yana ta habon jini.
Umaru ne ya taimake ni muka koma da abbu na gida,shima bai wani tsaya ba yayi tafiyar sa ya barni da Abbun a hannu a tsakar gida.
Zama nayi a gabansa shi yana daga kwance,har ya dan dawo hayyacin sa ya bude idanun sa ya kalle ni..,nan ya shiga yana tanbayata meya kaini gidan sarki.
Nikuwa a Duk tunani na nabari cewa yau komai yazo mana karshe tun da zan damka shi a hannun ummah surbajo akaishi birni ayi masa jinya,hakan yasa kawai na cije na fada masa abunda ya faru batare da yasan gaskiyan sirrina da junnut ba
Sai dai Har nagama nayi shiru banji ya ce uffan ba,hasali ma Idan ina maganan abbu kallo na kawai yake yana kada kan sa slowly nikaina bansan meyake tunani ba.
Sai chan naji Abbun Ya sake nanata min tambayar sa yana cewa bahiyyah Ahumaggahn ne suke riske adaren jiya?
Cikin dauriya da fargaba nace mashi eh..
Juya kanshi gefe yayi,ya barni cikin zullumi na tsawon mintuna ashirin
Chan Yace min yata bahiyya!
...kiyi hakuri da rayuwar duniya ki zama macen kan ki...,kar ki taba zubda kimar ki da darajar ki,sannan kar ki ci amanan kowa.
Mamakin kansa yasa na dago kaina na dube shi sai naga bama kallo na yake yi ba
Yace
Ni ahmadu yau naso ace qaddarar mu ta saba haka don kuwa har cikin raina nake jin ke din wata ce a duniyan nan kuna bazan taba yarda da sabanin haka ba.
Da Ahumuggah, sarki modibbo da aljanun sa duk sunyi karya su salwanta ikon ubangiji acikin rayuwar ki.
Kije inda zakije aduniyan na kuna kiyi aikin ki na kwarai,halal dinki kawai zaki nema bahiyyah,duk abinda ya saba haka kibar shi har abada..
Wani fat fat Zuciya ke bugu dan Dagowa nayi na kalle shi cikin sanyin jiki nace toh abbuh ...
"Kallo na shima yake yayi sai TAri ya dan turke shi duk da haka bai fasa ba yace
Kinji abunda na fada miki ko?
Nace ehhh naji Abbu,mikewa tsaye nayi da sauri ina shiri shiga daki zan dauko masa magani..
Sai naga ya ware Hannun sa ya mika min,sai nima na riko shi tarin na dada hauhawan sa a hankali...sai naji ya dada rike ni dam dam duk yunkuri da zaiyii kuma tarin sai ya kara karfi kamar yadda ya ke kara karfin riko ni.
Idanun mu a take suke rine ni dashi sukayi jajir muna kallon juna anan abbu Yace min bahiyyah,muryana na rawa sosai nace naam abbuh ...yace baki taba min komai na bacin rai ba a duniya
,shin haka zamu rabu bazaki fada min gaskiyar lamarin ki ba?...murya na na dada rawa na firgita kadan sai
Nace abbu?man take ya lura da cewa maganan ne yayi min nauyi abaki
Sai Yace toh shikenan bahiyyah ta
Na hakura Allah ya miki albarka daga nan,..bai sake kallo na ba ba sai aman jini daya shiga yi.
Kuka mai sanyi na fashe dashi,nikadai ina kanyi kamar wacce aka ma bishira da mutuwa,abbu sai ya kau da kansa bai ce dani uffan ba
Sai chan danayi zuciya ta tayi sanyi sai naga kamar bazan iya ba kawai sai na fara bashi asalin labarin abunda ya faru tsakani na da junnut ajiya cikin dare
Tun da na fara abbu yake wasu irin silent hawaye sai yayi shiru ya tsura min idanun shi labbansa dauke da karamin murmushi..
Hannun shi daya ya saka ya a shafo kaina dik jikin sa na rawa sosai
Yace ai dama nasani, Allah bazai taba bani kunya ba domin kuwa Allah baya tozarta bawar shi mai masa biyayya bahiyyah.
Da ace Jiki na ya bani cewa dagske Ahumaggah sun salwantar da rayuwar ki sabida ni da tun bayau ba na bar duniya nan..
Hakan bai faru ba shi yasa najira naji gaskiyan lamarin ki daga bakinki ki.
Abbu yace"Kinyi sadaukarwa mai girma bahiyyah ta"
Junnut ma yata ce bazan so ace hakan ya same ta ba,kuma naji dadi daya kasance babban burin ki ne masamu lpya na rayu awani wajen koda baki tare dani.
,...Allah ya sa sadaukarwan ki ya zamto sanadiyar wanke hakkin junnut akaina wanda halin rashin lpyata ne ya jawo mata wannan mummunan qaddarar a cikin rayuwar ta.
Allah ya bata abunda za taje nema..
Nikam babu abunda nakeyi sai kuka,zuciya cike da kaunar mahaifi na da kyar na iya tsagaitawa har nace ameen.!
Yau Ji nake kamar nafi kowa sa'ar uba a duniya , dan kuwa abbu is the most simple and most understanding father a duniyn nan..Duk da haka hakuri na shiga bashi ,amma sai ya jawo ni jikin shi ya rungume ni
Sosai.
Tarin ne ya sake
Addaban sa amma bai sake ni ba.
Yace na barki da duniya bahiyyah ta amanan kanki yana hannun ubangiji na
Albarka ta na tare dake Kar ki manta da wannan
"Kar ki ci amanan kowa don nasan da tarbiyan dana baki zaki iya zama da kowa..!
ke da junnut tamkar wani haske ne,dan haka kar ki sake ki bada fili ma shaidan har babban aminiyar ki ta dawo abokiyar gaban ki"..
Karshen maganan abbu na kenan sai yayi kalman shahadar sa ya bar duniyan mai gaba dayan ta..
Naji bakin ciki marar misaltuwa sai dai Ban iyayin wani kuka ba sai hawaye da dan addu'oin dana koya a chan islamiyar su ummah surbajo
Rabuwa da mahaifi irin nawa da zafi,anma Hakuri da juriya na wajen Allah na mika gaba daya,na kuma roke shi sai na samu sauki.
A daddafe naje na fada aka zo aka suturta abbu aka kaishi gidan sa gaskiya.mafi akasari daga mutanen garin mu sun dada jin tausayi na aransu
Tsegerun jiki kowa sai cewa sukeyi nayi na bar garin,acewar su tsinuwar aljanu dake kaina shiya kashe abbu na.
Ina daga tsakar gidan su junnut na rafka uban tagumi ina hawaye,sai naga an shiga daki da ita,anan suka gama duk wani maganan su