Showing 66001 words to 69000 words out of 110331 words
abinci?
ko natane bashida dadi?
gaba daya mamakin sa yagama kashe ta,gaba daya gani take kamar an sauya mata shi.
Sun dade dagama cin abincin harta yi tunanin ko wani yake jira,saita ga yatashi yadawo kusada ita ya zauna,cikin sauri ta kalleshi,bai damu da kallon nataba yakama hannayenta duka biyun yariqe, sannan ya Kalli qwayar idonta yace" I'm sorry"
Cikin mamaki Mawahib ta kalleshi sai rarraba idanuwa take,cikin rawar murya tace"for what...?"
Yakalli qwayar idonta sannan ya sassauta murya tace"for everything...,kiyafemin,nasan nayi miki laifi abaya,ba daya ba, ba biyu ba,kuma kina kallo na da wannan abun aranki, amma na kar6i laifi na,na kar6i kuskure na,inaso kiyafemin please..."
Jikin Mawahib yayi wani irin sanyi,meyasa Yaya Captain yake mata wannan abubuwan ne?
waye ya sauya shi?
bazata Iya qin yafe masaba,duk da ba soyayya ce a tsakanin suba yanzu zaman nasu yafi na baya,yana kokarin kyautata mata,kallonsa tayi, cikin sanyin jiki tace"nayafe ma Yaya Captain"
Cikin sauri yace"are you sure?"
Murmushi tasaki tace"very sure"
Idonsa ya lumshe yana hamdala aransa,saura Kuma batun soyaiya,but kar tayi tunanin saboda soyayyar sane yasa yanemi yafiyar ta,yanemi yafiyar tane saboda yafara wanke kansa a wajanta,hakan yasa ya haqura bai fada mata cewa yana sonta ba,Mawahib ta Kalli idonsa taga bakinsa yana motsi kamar yanason yafadi wani abu, har lokacin hannunta yana cikin nasa hannun,yadago kansa ya kalleta yace"muje gida?"
Cikin sauri ta daga masa kanta,dama atakure take awajan,takasa sakewa har yanzu, tarasa dalilin sa na neman wannan yafiyar, amma dole zata tambayi Nabiha.
Hannunta cikin nasa suka futo daga wajan,yabude mata mota tashiga sannan yashiga yaja suka dauki hanyar gida.
basu qarasa gida ba sai qarfe hudu da kwata, hakan yasa yana ajiyeta yajuya yatafi masallaci,itama sallah tayi, tacire laffayar jikinta ta watsa ruwa, sannan tasaka yar qaramar riga tafuto falon qasa,saitake jin ranta fes, kamar ansauke mata wani abu data dade yana damunta, hakan yasa tashiga kitchen ta dauko robar ice-cream guda daya tayi zamanta afalon tafara Sha,Yaya Captain bai dawo ba sai wajan qarfe biyar,yana zuwa yaganta afalon tabaje tana shan ice-cream yayi murmushi yawuce sama, ko banza tunda yanemi yafiyar ta yasan hakan yayi tasiri sosai tunda gashi harta Iya fara zama afalon duk da tasan yana gida zai Iya shigowa kowanne lokaci,amma ahakan tazauna bata gudu daki ta kulle kanta ba, hakan ya nuna tafara dan sakewa dashi.
Qananun kaya yasaka yafice motsa jiki,bata bar falon ba saida taji anfara kiran sallar magrib, tatashi tayi sama,ta gabatar da sallah sannan tabude qur'ani tana karantawa har zuwa lokacin sallar isha'i.
Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan
adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal
sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki๐๐ผ
Bayan ta idar da sallah tasauko tayi masa abinci marar nauyi dan kadan dede cikinsa,sannan takoma dakinta,Captain Aryan kuwa yana dawowa daga masallaci yaci abincin sa, ya kunna kallo sannan yasaka computer sa agaba yana aiki saboda yau bai fita aikin ba, bai tashi daga wajan ba sai qarfe goma da rabi,da computer yawuce sama ya ajiyeta, sannan yacire jallabiyar jikinsa yashiga wanka.
Mawahib kuwa ta dade a kwance a gadonta tana chatting,tayi luf cikin bargo,wayarta ce tafara vibration,cikin mamaki taga sister Saudat qawar Mamy data kawo mata ziyara itace take kira,dauka tayi tareda sallama, Sister Saudat tace"kuna lafiya deko?"
Mawahib tace"lafiya kalau Anty,harna kwanta bacci ma naga kiranki nayi tunanin koba lafiya ba"
Sister Saudat tace"harkin kwanta bacci kamar Yaya? kin kwanta bacci kokuma kun kwanta bacci?"
Tace"na kwanta Anty"
Cikin sauri sister Saudat tace"Mawahib meyasa bakya jin magana ne? na hanaki kwana ke kadai saida mijinki bahaka Nafada miki ba?"
Cikin sauri tace" Hakane Anty but..."
"but what Mawahib? banason jin shirman komai kitashi kisaka kayan dana kawo miki kitafi dakin mijinki yanzu yanzun nan kokuma nakira Mamyn ki nafada mata"
Cikin 6acin rai tace"to Aunty"
ita tarasa meyasa matar nan takeson turata awajan Yaya Captain bayan ba saba zuwa tayi ba,fisabilillah taje wajansa tace masa me?
duk ranta babu dadi tatashi tana tura bakinta gaba tabude jakar kayan taga duka babu na arziqi,gaba dayansu idan tasaka sai anga komai nata, hakan yasa taduba wata qwaya daya medan dama dama data gani me dogon hannu,tanada dan fadi rigar,amma tsawonta Iya duwawunta ya tsaya,sai wandon rigar shima dan qarami ne gaba dayansa Iya tsawon rigar ya tsaya shima,duka cinyoyinta a waje suke, daga gaban rigar akwai botir daga sama har qasa, amma botir guda biyar na sama anciresu, tundaga wuyanta har breziyar ta gaba daya yana waje, daga qasan breziyar ne akabar botiran rigar har qasanta, ta dauki turaren da Mamy ta bata wanda tace idan zata kwanta ta dinga shafawa ta shafashi sosai, ta kalli kanta a madubi taga yanda gaba daya fararen cinyoyinta suka bayyana,a fili tace"anya kuwa?, tayaya zanje wajansa ahaka? Ahakan ma shine me dan sauqi sauqi ita Ina tasamo wannan kayan ne?"
tasake kallon gaban rigar taga inda babu botir din gaba daya kana ganin na shanunta dasuka cika madedeciyar breziyar har suna futowa ta waje,girgiza kanta tayi,bazai iyu taje wajansa hakaba,tasaka hannunta tacire ribon din dake kanta, dogon gashinta ya sauko,ta tattare gashin gaba daya ta dawo dashi gefen kafadarta na dama,hakan yasa yadan 6oye qirjin nata,sannan tafuto kai tsaye ta nufi dakinsa amma kana ganin fuskarta zakasan cewa dole aka mata,kana gani kasan cewa ranta a6ace yake, Ahankali tatura qofar dakin tashiga, wani irin qamshi yabugeta, ga sanyin esi yana ratsa jikinta,wutar dakin a kunne take,amma baya cikin dakin da alama wanka yake, ga computer sa nan agefe,cikin sauri ta nufi gadon zata kwanta tashige bargo dan karya ganta da wannan sallamanmu kayan, saide tana dora hannunta a gadon da niyyar kwanciya,sai wayarsa tafara qara,idonta ya sauka akan sunan me kiran taga Asalamiyya (๐)
batasan dalili ba haka kawai taji ranta yayi wani irin mugun 6aci, dama tashigo da nata 6acin ran,saita fasa kwanciya tatashi ta Kalli agogon dakin taga qarfe goma shadaya nadare,kar kuma abun nasu yazama da rainin hankali,tabarshi yana mu'amula da'ita, tabarshi yana waya da'ita acikin gida duk da shawarar da Nabiha ta bata, rannan suna breakfast ta kirashi,da rana tana kiransa, yanzu ma da dare saita kira shi?
Karfa ace Momy kilishi ce take turowa Yaya Captain wannan Asalamiyyan,tayaya harta bari tayi sakacin da wata zata kira mijin ta qarfe goma shadaya na dare? duk da bata sonsa bazai ta6a iyuwa ayi mata wannan cin kashin ba,idan auren ta zaiyi yaje ya aure ta inyaso Momy kilishi tasashi yasaketa (๐๐ปโโ๏ธ)
Tana gama wannan tunanin wayar tasake ringing akaro na biyu, cikin sauri ta dauka tace"wai ke bakisan lokacin dazaki dinga kiran mutum me iyali bane?"
Asalamiyya tasaki dariya tace"ina ruwan masu iyali,ke harkin samu damar da bakinki yabude dahar zaki hanani kiran dan'uwana? kokin manta matsayin mahaifiyar sa awajena? yaushe aka haifeki? yaushe ki kasan dad'in mijin dahar zaki min shamaki da kiransa? yanzu nafara kiran Yaya Aryan kuma bazan daina ba sainaga ganni acikin gidansa amatsayin matarsa,matsayin uwar yayansa,kibari idan kuka samu yancin kanku keda mahaifiyar ki saiki fara iko da mijin"
Mawahib ta jinjina kanta, lalle ta riga tayi sake, cikin 6acin rai tace"ko? to saiki bari idan ya futo daga wankan Sunnah saiya kiraki"(๐๐)
Tana fadin haka takashe wayar tayi wulli da'ita kan gado,Captain Aryan daya mace atsaye yana kallon surar jikinta, cikin jin dadi yasaki wani irin murmushi,meyake gani a fuskarta kamar fa kishin sa take, idan kishin sa take hakan yana nufin tafara sonshi ne? wani irin dadi ya kamashi,tun lokacin data daga wayar yafuto daga toilet yanajin su,yanda take nuna cewa shidin mijin ta ne hakan ba qaramin dadi yayi masa ba,sosai ta birgeshi,saide furucinta na qarshe yabashi dariya,shida zai samu ma ta bashi hadin kai yayi wankan Sunnar aida tagama masa komai (๐)
Mawahib data dafe kanta da hannunta cikin 6acin rai tanufi hanyar barin dakin,tun farko ita taqi shawarar Nabiha, da tun lokacin da Asalamiyya tafara kiransa tayi maganin abun da abun bekai hartazo tana fadawa Mamyn ta magana ba.
cikin sauri Captain Aryan yajefar da dan qaramin towel din dayake goge fuskarsa ya nufeta tareda ruqo hannunta,yanda ya matso jikinta hakan yasa turaren data shafa wanda Mamy tabata yafara fizgarsa,cikin laushin murya yace"Ina zaki?"
Hannayen ta taharde a qirjinta ba tareda tajuyo ta kalleshi ba tace"dakina"
Kasancewar ta bashi baya hakan yasa cikin sauri ya rungumota tabaya,har tanajin yanda danshin ruwan dake qirjin sa yake ratsata, fuskarsa ya matso dab da tata fuskar, tanajin yanda numfashin sa yake sauka akan fuskarta,yanda tayi furucin tace zata tafi dakinta cikin fishi hakan yasa gaba daya ya rikice,yasaka hannunsa duka biyun yariqe fuskarta cikin sigar lallashi yace"meyafaru zaki tafi? fadamin me kikeso?,nine na 6ata miki rai?"
Cikin sauri ta girgiza kanta alamun a a
Cikin damuwa yasake yin qasa da muryarsa yace"bakinyi mata warning ba? bazata sake kiraba, shikkenan?"
Yanzun ma batace masa komai ba, kawai de ta daga masa kanta alamun amsawa, sannan tasaka hannu tacire hannunsa daya riqe mata fuska sannan takama handle din dakin zata fice, cikin sauri yasake fuzgota tadawo jikinsa, kamar wani sakarai ya kalleta yace"nabaki haquri fa"
Batare data Kalli inda yake ba tace"aina haqura"
Fuskarta yasake riqewa ya kalli qwayar idonta, cikin muryar rad'a yace"to meyasa zaki tafi?,kina fishi danine?"
ganin yanda ya rikice yake jero mata tambayoyi,hakan yasa takasa kallonsa,tayi sauri ta lumshe idonta,gaba daya ranta a6ace yake da wayar datayi da Asalamiyya, Yaya Captain din de mijinta ne, amma har ita Asalamiyya zata kira tana fada mata baqar magana haka kawai saboda tana taqama da Momy kilishi, wani irin hawaye suka silalo daga idanunta,yana ganin haka baiyi wata-wata ba, ya lumshe idonsa sannan yadora harshan sa akan fuskarta yafara shanye hawayen.
Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqad๐๐ป
Amnah El Yaqoubโ๐ป
[7/13, 6:16 PM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki
tanajin yanda yake lashe mata fuska jikinsa har wata rawa yake kamar wanda baya hayyacinsa,kwata kwata ranta baya mata dadi,jitake ta tsani komai dama batazo dakinba,hakan yasa gudun hawayen nata yasake qaruwa,ahankali yasaka hannunsa yafuzgota ya rungume ta tsam a jikinsa,kanta yanakan faffadan qirjinsa tanajin yanda bugun zuciyarsa yake bugawa cikin sauri, yasaka hannunsa yakashe wutar dakin,sannan yadauketa cak yanufi gadonsa da'ita,bai damu da towel din dayake jikinsa ba,kuma bai nemi riga yasaka ba,ya kwantar da'ita a gadon sannan ya kwanta yasakata cikin jikinsa,qamshin turaren data saka ne yake fuzgarsa hakan yasa yadora hancinsa akan wuyanta yana shaqar qamshin,cikin wata irin muryar rada yace" I'm sorry please stop crying"
Yana fadin haka ya lumshe idonsa yayinda hancinsa yake yawo a'iya wuyanta yana shaqar qamshin jikinta, d'is....yaji hawayenta ya d'iso akan fuskarsa, ahankali yasaka hannunsa ya goge mata hawayen, sannan ya laluba yadauko wayarsa, yacire security din sannan yace mata "kallah..."
Ahankali yafara bude idonta harta gama budeshi fes akan screen din wayarsa,akan idonta yakamo number Asalamiyya yayi blocking dinta, sannan ya kalleta da idanunsa dasuka gama qanqancewa yace"shikkkenan?"
Cikin sauri ta gyad'a masa kanta, yace"toki daina kukan"
Cikin sauri tasaka bayan hannunta ta goge duk wani hawaye dayake fuskarta,wata irin wawiyar ajiyar zuciya yasaki sannan yamaida kansa cikin wuyanta yana cigaba da shaqar qamshin turarenta, kasancewar tayi kuka hakan yasa tafara jan zuciya alamun tagama kukan, cikin wata irin muryar fitar hayyaci yace mata"nine nasaki kuka ko?"
Gyada masa kanta tayi batare da tayi magana ba.
Cikin shagwa6a yace" bazan sakeba kinji? "
Yanayin yanda yayi shagwa6ar yasa taji wani irin yanayin shauqi yana Neman kamata, bata Iya bashi amsa ba sai kanta data sake gyada masa.
Hancinsa ya gangaro zuwa qirjinta yaji inda qamshin yafi yawa, yashaqa yace" waye yabaki wannan turaren?"
Cikin rawar murya tace" Mamy ce"
Daga nan bai sake cemata komai ba, cikin jin dadi yamaida hancinsa zuwa cikin jikinta yana shaqar lungu da saqo najikinta, Mawahib tana jinsa tayi shiru tunanin ta ya tsaya cak! saide gabanta faduwa yake,tanajin yanda yake hade qafafunsa gaba daya yakasa nutsuwa yadena motsi, hancinsa yana cikin wuyanta, ahaka wani irin bacci me dadi ya dauke shi,tanajin yanda ya qanqameta ko motsin kirki takasa yi,gaba daya saita nemi baccin idonta tarasa,tayaya zata iya bacci ya qanqameta haka? badan gidansu daya da Yaya Captain ba, babu makawa yau datace shi maye ne,bata ta6a sanin anashan hawaye ba sai yau.
Motsi tayi zata juya tafara bacci amma cikin sauri yasake ruqota, hakan yasa tahaqura,batasan lokacin da bacci ya dauketa ba.
Sunyi wani irin bacci me dadi wanda su kansu basusan tsawon lokacin da suka dauka suna baccin ba,koda wasa basuji kiran sallar farko ba,haka lokacin da aka shiga sallah a masallatai ma basujiba,aka idar basu jiba,saida gari yayi haske sannan Mawahib tafarka,ahankali tafara bude idonta harta budeshi gaba daya tas a fuskarshi,baccinsa yake hankali kwance har lokacin,ahankali tafara qoqarin tashi ganin gari har yayi haske,motsin tane yasa shima yafarka, yana bude idonsa yasauke shi akanta,ahankali yasaka hannunsa yashafa gashinta,idonsa yana kanta sannan yashafa fuskarta yace"jiya kinyi kuka,kanki yana miki ciwone muje asbiti?"
Ahankali ta girgiza kanta Sannan tayi qasa da idonta,ta yunqura zata tashi yasaka hannunsa ya riqeta baice da'ita komai ba kawai kallonta yake,kasa kallonsa tayi, ahankali tace"lokacin sallah yawuce fa"
Agogon dakin ya kallah sannan yatashi, itama tatashi tana gyara gaban rigar ta,Sannan tasake gyara gashinta daya barbazu, duk yana kallonta, saida yasake qarewa shigar tata kallo, cikin ransa yana fadin fine girl, sannan yasauko daga gadon ya shige toilet.
Cikin sauri itama tafice daga dakin takoma dakinta.
Bayan ta idar da sallah babu abinda tayi, kawai saukowa tayi tafara qoqarin hada masa abinda zaici kafin yafita aiki.
saboda tasan ya makara wajan fita aiki saita hada masa iya tea da bread sai wainar qwai,taqara dafa jallop din soyaiyar taliya 'yar kad'an tadora masa da soyaiyan naman kaza agefe,tana jera abincin a dining yafuto cikin uniform dinsu yana tafiya yana kallon agogon hannunsa, baiyi tunanin harta gama abinci ba adan qaramin lokaci haka,kai tsaye wajanta ya qarasa yadora hannunsa akan kujerar dining din cikin girmamawa yace mata "Ina kwana?"
Kallonsa tayi cikin mamaki,Allah yaso ba'acikin mutane yake mata wannan gaisuwar ba,sai mutane suyi tunanin wani abun take masa,babba dashi amma shine yake fara gaishe ta,cikin kulawa ta amsa masa, sannan tazuba masa jallop din taliya wadda taji kayan ganye dasu carrot tatura masa gabansa,ya Kalli taliyar yahadiye wani irin saliva,sannan yaja kujerar baya yazauna yasaka fork yafara ci yana lumshe idonsa,tana daga tsayen tana satar kallonsa yanda yake lumshe ido, da alama abincin yayi masa dadi amma miskilanci bazai barshi yayaba mata ba,wainar qwan tasake tura masa gabansa, tabude bread ta dauko slide hudu ta ajiye, sannan tabude flasks tazuba shayi tahada masa shi yayi kauri, sannan tabar wajan takoma kitchen,gyara kitchen din tayi, tafuto cikin sauri zata fara gyaran falon yataso daga dining din, taku uku yayi zuwa hudu yasaka hannunsa ya fuzgota tafada jikinsa,baice da'ita komai ba yadauketa cak yawuce dining din, bai mata mazauni a ko'inaba sai akan cinyarsa,cikin sauri ta kalleshi tace"yaya Captain zan gyara kitchen..."
Cikin sauri yagirgiza mata kai yace"bakya gajiya ne?kici abinci first"
Kafin tayi wata maganar yafara bata abincin a bakinta,ya 6ata lokaci sosai wajan bata abincin,yana bata tea wayarsa tafara ringing,dauka yayi batare da yayi magana ba, daga dayan 6angaren akace"Captain Aryan lafiya jiya baka shigo office ba, yauma shiru"
Saida yabata tea din sannan ya Kalli wayar yace"Captain Habib Ina hanya"
Captain Habib yayi murmushi yakashe wayar.
Saida ya tabbatar ta qoshi,sannan yadauki tissue yana goge mata bakinta, Mawahib tayi zugud'um tana kallon ikon Allah,gaba daya al'amarin yaya Captain daure mata kai yake,yakamata tayi waya da Nabiha,saboda abun nasa yawuce tunanin ta,tana cikin wannan tunanin taji yasakar mata kiss a wuyanta,cikin sigar rada yace"kiyi haquri akan abinda yafaru jiya,zan fita,ki kulamin da kanki...."
Gabanta ne yayi wata irin faduwa rasss!
lokaci daya Yaya Nabil yafado mata,shine yake fada mata wannan kalaman,tasan cewa shikuma soyaiya suke, amma Yaya Captain fa?
Kanta ne ya daure,harya ajiyeta zai fita jikinta a Sanyaye yake,tasan de yayi mata magana, amma batasan meyace ba harya fita,yana fita ta zauna jagwab a kujera tareda dafe kanta.
Bayan yarage ayyukan office yadauki wayarsa yakira Hajiya kilishi,saida yayi mata 5 missed call bata dauka ba, ya lumshe idonsa tareda ajiye wayar, akwai babban qalubale acikin rayuwar aurensa, yarasa tayaya zai warware wannan matsalar, sai yaushe ne Momy zata sauko tadaina fishi dashi?
Yaya zaiyi da ransa? Ashe haka Ashraf yaji lokacin dayake qoqarin fahimtar dashi irin soyaiyar dayake yiwa Mawahib?
haqiqa soyaiyar Mawahib kamar jarabawa ce da ubangiji yayi masa, Koda wasa bai ta6a tunanin cewa shi Aryan zai so Mawahib ba, soyaiya ma mai tsanani kamar wannan,baya tunanin akwai wani abu wanda bazai Iya sadaukar mata dashiba, ciki harda ransa,agefe guda ga Momy tanaso yasake ta, idan yasake ta Yaya zaiyi da soyayyar ta?
wayarsa yadauka yakira Ashraf,bayan yadauka cikin damuwa yace"Ashraf yaya zanyi da matsalar Momy ne?,bata daukan wayata, dama ranta ya6aci,kuma zuwanmu gida bayan umarnin data bani hakan yasa tasake yin fishi dani,narasa yanda zanyi da raina,idan nasaketa yaya zanyi da soyayyar ta Ash? tayaya zan fadawa Momy soyaiyar yarinyar nan tasa bana gane komai?"
Ashraf yayi murmushi yace"dan soyaiya,ya'isa haka"
"Ashraf bazaka ganeba,idan Ina tareda ita manta komai nake wallahi,ciki harda kaina, ina mantawa dani ko waye gaba daya sai inzama kamar yaro sai yanda tayi dani"
Ashraf yace"ka kwantar da hankalin ka,Momy fa tana sonmu,zata huce,amma wai ya ake ciki ne? kafada mata kana sonta kuwa?"
Dan qaramin tsaki yasaki"nakasa fada mata,bazan iyaba,koda nayi niyar fada mata saitamin kwarjini,bansan Yaya zanyi ba"
Ashraf ya kwashe da dariya yace"serious.... Aryan, wai kaine kake tsoron mace? kaga karka bani kunya,qanina yafi qarfin kowacce irin mace,kayimin alqawari yau zaka fada mata"
Cikin sauri yace"amma Ash..."
Dasauri Shima Ashraf din ya dakatar dashi yace" no,banason jin komai,kafada mata,na tabbatar