Showing 81001 words to 84000 words out of 110331 words

Chapter 28 - MAWAHIB COMPLT HAUSA NOVEL

13 Sep 2024

19689

bata dauki wayarta ba saida ta'idar da sallah tayi azkar sannan tayiwa Mawahib Addu'ah, cikin sanyin jiki tatashi tafara ninke hijabin jikinta Zuciyarta fal da tunanin halin da Mawahib take ciki,wayarta ta dauka zata shiga kitchen tana duba wayar taga text din Captain,cikin sauri taduba time din daya turo taga tun kafin atada sallah a masallaci,tana gama karanta text din tazauna agado jagwab tafara Salati meyasa bata duba wayarta da wuri ba ga yarinyar ta can awani hali?
Cikin sauri tatashi tafuto daga part din tanufi dakinsu Captain, abakin qofa sukaci karo itada Hajiya kilishi data kasa runtsawa, Hajiya kilishi tace"Maryam kema kinji ihun nata ne?"

Cikin sanyin jiki Mamy ta 6oye damuwarta, saboda kar mutanan gidan suyi tunanin wani abu,tace"A a Yaya,Captain yamin text ne yace inzo indubata"

Cikin tsananin mamaki Hajiya da bata kalli inda wayarta take bama bare taga saqon da Captain yaturo mata na sallama tace"kamarya kizo? to ina yatafi?"

Mamy tace"anyi masa kiran gaggawa ne awajan aikin su"


Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"zancen banza zancen wofi,ya za'ai yatafi yabar yarinya tana wannan ihun kukan?"

Bata jira amsar Mamy ba tatura dakin suka shiga atare,tun kafin su qarasa gadon sukaci karo da wandonta daya cillar dashi qasa,ga rigarta daya yaga acan gefe kusa da bedsheet din daya cire,Mawahib tana ganin Mamy tasaki wani irin kuka.

Hajiya kilishi kuwa tana ganin bedsheet din dayake qasa duk gashinan jini ya 6ata shi, ga idanun Mawahib sunyi jajir saboda kuka,saita dora hannunta akanta tasaki kuka, Mamy ta kalleta tace"haba Yaya kidena kuka mana"

Cikin kuka Hajiya kilishi tace"dole nayi kuka Maryam,wannan rashin imanin har ina?"
Mamy ta qarasa wajan Mawahib ta zauna ta rungume ta tace" ya'isa, yi shiru, kukan ya'isa haka"

Cikin kuka tace"Mamy zan mutu,"

Wannan Kalmar da Mawahib tafada itace tasake sa Hajiya kilishi fashewa da kuka, sai jijjuya kai take cikeda tausayi, Mamy ta dagata zata kaita toilet,anan taga jallabiyar Captain dinma datake jininta itama jini ya6ata ta,cikin sauri Mamy ta runtse idonta, takama jallabiyar tacire,Hajiya kilishi tayi sauri tawuce toilet tahada mata ruwan zafi.

Mamy Kuma takamata tace"tashi muje kishiga cikin ruwan zafi"

Cikin hawaye tace"Mamy bazan Iya takawa ba"

Hajiya kilishi ta qaraso da sauri suka kamata su biyun, suka kaita toilet, sannan Mamy ta sakata cikin ruwan zafi, tana shiga cikin ruwan tasaki wata qara zata tashi, saboda wanda Yaya Captain yasakata bekai wannan zafi ba, Mamy ta maidata ta koma tazauna, Hajiya kilishi ta goge hawayen idonta tace"duk yanda akai Aryan bai sakata acikin ruwan dumi yanda ya kamata ba saboda shi dama baya son ruwan zafi, gani zaiyi itama zafin zai mata yawa"

Mamy tace"toya za'ai Yaya,ai sai haquri"

Saida suka sauya mata ruwa sau uku,sannan suka kamota suka futo,Hajiya kilishi ce ta riqeta Mamy Kuma tasake gyara gadon sannan suka kwantar da'ita daga gefe,ahankali Mamy ta tsugunna ta bude qafafun Mawahib taduba wajan sannan ta miqe tsaye tace"dole sainayi mata dinki Yaya"

Hajiya kilishi tace"dinki? innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, Ina ganin ikon Allah ni kilishi...."
saita saki kuka.

Mamy tace"Yaya kidena kukan nan kada mutanen gida suji"

Cikin kuka tace"ji na nawa Kuma Maryam? yanda ya haiqewa yarinyar nan waye acikin gidan nan zaice baiji ihun kukan taba? Aryan baya hayyacinsa,inajin maganin maza yasha"

Mamy tace"babu wani magani Yaya, tunda kikaga haka gardama ta masa,inda ta tsaya koda zataji ciwon bazai kai har hakaba,tayayane zata nunawa soja itama me qarfi ce?, bari inje daki in dawo"

Mawahib tanajin yanda suke tattauna wa,hawaye ne kawai yake zuba daga idonta.

cikin kuka Hajiya kilishi ma tafuto daga dakin tawuce part dinta, Mamy tabita da kallo kamar cewa akai Captain din yakashe Mawahib,ta girgiza kanta tatafi part dinta da sauri.

Hajiya kilishi tana zuwa falonta tazauna a kujera tadafe kanta tana share hawaye tareda ajiyar zuciya.


******


Abba daya dawo daga masallaci yanzu, ya Kalli Mamy ganin tana hada wata allura yace"meyake faruwa ne?"

Cikin damuwa tace"Alhaji yarinyar nan taji ciwo ne sosai,zanyi mata dinki"

Cikin sauri yace"subhanallah...kode zamu tafi asbiti ne?"

Tace"A a babu matsala zanyi mata komai, idan munje asbitin ma zasu dinga surutu ne suyi tunanin rape ne akayi mukuma muka 6oye"

Cikin sanyin jiki yace"yanzu tana wanne hali?"


******


Alqali da Ashraf suka nufo part dinsu, Alqali yana tambayar Ashraf "meyake faruwa kazo gida haka sassafe kabar iyalinka?"

Ashraf yace"naraka Aryan Airport ne"

Alqali ya kalleshi yace"eh naga yaturo min saqo dazu,yatafi Abuja,Allah yakaishi lafiya, shiyasa jikinka yayi sanyi kenan? Ashraf anya rayuwa zata iyu dahaka kuwa? inde dan'uwan ka zaiyi tafiya saika saka damuwa aranka? Ina Abuja Ina kano? idan kanason ganinsa basai kaje ba?"

Ashraf ya Kalli mahaifin nasu,shi kadai yasan inane Captain zai tafi,shi kadai yasan Ina aka tura qanin nasa.
Meyasa Aryan yabashi ruqon wannan babban alqawari?
tayaya zaiyi shiru da bakinsa shi kadai ba tareda iyayensu sun san cewa yaqi aka tura shi ba?
Dan Kar Daddyn nasu ya fahimci wani abu hakan yasa yasaki ajiyar zuciya yace"to Daddy insha Allah"

Alqali yace"yawwa kokaifa, Allah yayi muku albarka"

Kafin Ashraf ya amsa suka shigo dakin anan suka tarar da kilishi tana zaune tana share hawaye, gaban Ashraf yafadi kode taji labarin Ina Aryan yatafi ne?

Cikin sauri suka qarasa wajanta Alqali yace"Kilishi meyake faruwa?"

Cikin muryar kuka tace"Yakashe ta"

Ashraf yazaro idonsa waje(😳)
Yace"wa aka kashe?"

Tace"Mawahib,Aryan yayi mata kaca-kaca babu dadin gani,Ashraf Ina imanin dan'uwanka yatafi? yarinya qarama yakasa binta a sannu tun cikin dare muke jiyo ihun kukanta babu damar dauki,nabar su acan itada Maryam zata mata dinki bazan Iya ganin wannan a zabar ba"

Alqali ya zauna yace"dinki?"

Hajiya kilishi tace"dinki za'a mata,yarinyar duk ta rame dare daya abun tausayi ido duk ya kumbura"

Ashraf ya sunkuyar kansa qasa yana sosa qeyarsa,saboda maganar ta masa nauyi.

Alqali yace"amma yasan da wannan danyan aikin yatafi Abuja yabarta? Wanne irin aiki ne za'a yi da bazai jira gari yawaye yabawa yarinya kulawa ba kafin yatafi?"

Hajiya kilishi tace"ni ban yarda ma kiransa akai ba,nasan halinsa sarai kawai guduwa yayi saboda shi yasan abinda ya aikata"

Alqali ya girgiza kansa yace"Allah yarufa asiri,kitashi kihada mata tea saiki kai mata tasha"

Hajiya kilishi tatashi tsaye tanufi dining dinsu tana fadin"zaizo yasameni,wato shiga me qarfin doki"

Ashraf yasake yin qasa da kansa yana sosa kansa,yasan cewa yana magana zata rufeshi da fada tace ai tare suke qulla komai,bayan kuma hakanne tare suka qulla din. (πŸ˜‚)

******


Mamy da Mama Sadiya ne adakin wadda tazo yanzu saboda itama tun ihun farko tasan cewa gidan ba kalau ba, itace take miqowa Mamy abinda take buqata, ita
kuma Mamy tana mata dinkin,duk da Mamy tayi mata allura kafin afara dinkin hakan bai hanata jin zafi ba, saida mama Sadiya ta riqeta,Mamy tayi mata dinkin cikin nutsuwa.

Zuwa wannan lokacin Mawahib kasa kukan tayi, saide hawaye dayake zarya a'idonta,bayan angama Mama Sadiya tace"bari naje nahada breakfast sai akaiwa Abban Mawahib dinma tunda ke kina nan"

Mamy tace"to shikkenan,ai yau ba zanje asbitin bama,zanyi musu waya"

Mama Sadiya tace"ai abun da tausayi, bazai iyu abarta ita kadai ba"
tafadi hakan tana ficewa daga dakin.

Mamy ta Kalli Mawahib tace"kidena kukan mana"

Mawahib tana jinta tayi shiru,amma bata daina hawayen ba,saboda ita kadai tasan metake ji ajikinta.

Hajiya kilishi tashigo da tea a hannunta tace"kungama dinkin Maryam?"

"angama Yaya,gata nan kwance"

Tea tabata tace"toga tea me kauri nahado mata zataji dadin cikinta insha Allah"

Mamy ta kar6i tea din tace"to Yaya angode"

Hajiya kilishi ta Kalli Mawahib datake zubar da hawaye tace"sannu Mawahib,yarinyar nan kin adda azaba,kiyi haquri kidaina kuka,shima duk inda yaje zaizo yasameni"

Mamy ta Kalli Mawahib tace"kici gaba da kukan, idan ruwan hawayen naki yaqare sai naga da wanda zakici gaba da kukan,tun asuba kina kuka anyi lallashi anyi ban haquri kinqi kiyi haquri,kowa da haka yafara saide na wata yafi na wata, amma bazakiyi haquri ba kamar akanki aka fara kar6a budurci?"

Hajiya kilishi tace"um um Maryam...,kibarta tayi kukanta,irin wannan abun de, kuma acikin wannan gida,to akanta aka fara,saboda nima ko ubansa bai ganamin wannan azabar ba" (πŸ™Š)

Mamy tayi shiru ta dauki tea din tabata,a hankali ta kar6a tafara sha,kad'an tasha zata ajiye Mamy tasata ta shanye shi duka.

Ashraf ne Alqali yazo yaga jikin Mawahib din,dakin yaturo yashigo shida Ashraf, idon Ashraf yasauka akansu, yagansu sun sata atsakiya ga qafafun ta a bubbude ,kansa yadan sosa sannan ya sunkuyar da kansa yace"Anty Mamy Ina kwana"

"lafiya Ashraf,ya Nabiha?"

"tana nan kalau wallahi, yame jikin?"

Mamy ta Kalli Mawahib tace"gata nan sai langwai take jiki da sauqi,dauketa kakaimin ita dakina dan Allah,sai a rufe nan din"

Cikin sauri ya girgiza kansa yace"A a"

Hajiya kilishi ta kalleshi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi Mawahib dince bazaka dauka ba?"

Kansa ya shafa yaqi cewa komai,Hajiya kilishi tayi ajiyar zuciya tace"ai shikkenan"

Mamy tayi murmushi tace"to Ashraf Mawahib datana da aure dabata aure ai qanwar ka ce"

Abba ne yayi sallama yashigo dakin ya shirya tsaf zai fita aiki, yagaida Hajiya kilishi, Ashraf ma ya rissina ya gaishe shi.

ya Kalli Mawahib yace"sannu Ruqayya"

Daga masa kanta tayi alamun amsawa amma batace uffan ba.

Abba ya Kalli Mamy yace"zanfita aiki Maryam, saina dawo"

Tace"to Alhaji Allah Yakiyaye hanya, ko zaka dauki Mawahib mukoma can?,Ashraf yaqi daukarta"

Abba ya kalli Ashraf yayi murmushi ya qaraso ya dauketa cak, suka futo daga dakin,Mamy ta Kalli Mawahib datake goge hawaye tace"bazaki daina wannan qananun kukan ba? aida kinyi shiru ganin ubanki ne yasa zakici gaba da kukan"

Hajiya kilishi tace"kai Maryam sai fada kike yiwa yarinyar nan dame zataji ne?"
ta kalli Abba tace"isah kaimin ita dakina,zanyi jinyarta"

Abba de yana jinsu baice komai ba yayi murmushi yajuya yakai Mawahib har cikin dakin Hajiya kilishi, sannan suka futo daga dakin.

Mamy tawuce dakinta tayi breakfast sannan tawuce kitchen tadafa mata farfesun kifi,takai mata,alokacin tana kwance da apple a hannunta tana karya ahankali,farfesun tabata taci sosai, sannan ta kalleta tace"babu inda yake miki ciwo bayan wajan dinkin ko?"

Idontane yacika da qwalla amma taqi basu damar zubowa tace"bacci nakeji kuma nakasa yi"

Mamy ta jinjina kanta, sannan tafuto taje part dinta tahado allurar bacci tazo tayi mata, ko minti biyar bata sakeba, wani irin wahalallan bacci ya dauketa.

Ta dade tana bacci har azahar, Hajiya kilishi data idar da sallah adakin tajuya tana kallonta tana azkar,hannunta ta daga zata fara Addu'ah taji Mawahib tana cewa "Yaya Captain zan mutu....kayi haquri,wayyo!!..."

tafadi wayyo din da qarfi tareda firgita tabude idonta.

Cikin sauri Hajiya kilishi ta ajiye carbin hannunta sannan tafara yimata magana tace"Mawahib..,kin tashi ne?"

Cikin idonta dake cikeda da bacci tace"um...." tareda lumshe idonta taci gaba da baccin.

Hajiya kilishi tasaki ajiyar zuciya tana girgiza kanta, lalle yarinyar nan tasha wahala a hannun Aryan,har cikin bacci ma yarinya tana firgita wacce irin rayuwa Aryan ya daukar wa kansa?
Mutane suna cewa ko awajan aiki ana cewa danta Aryan jarumi ne, bata tabbatar da hakaba sai yanzu,haqiqa taga jarumi ganin idonta(πŸ˜‚)

Tsawon sati daya Mawahib ta dauka Hajiya kilishi tana bata kulawa,acikin kwana bakwai dinnan kullum saita shiga cikin ruwan dumi haka bata aikin komai Hajiya kilishi tahana,zuwa kwana bakwai dinnan tagama warkewa ras,babu abinda yake mata ciwo,saide duk lokacin data tuno irin gumurzun da sukai itada Yaya Captain saita ji tsoro yasake kamata,idan ta tuna yana Abuja har wani nishadi takeji.

Hajiya kilishi Kullum saita gwada kiran wayarsa, amma bata shiga wayar tana kashe,haka Alqali Shima yakira yakira yaji shiru.

A6angaren Ashraf kuwa yafi kowa shiga damuwa saboda rashin samun Aryan awaya,idan yazauna yayi shiru ko agida ko awajan aiki maganar Aryan dince take fadowa ransa lokacin dayake cewa zamu tunkaresu, komu kashe ko akashe mu,idan ya tuno wannan furucin nasa saiya ji qwalla tacika idonsa.

Har yanzu bai fadawa kowa ga inda Aryan yatafi ba.
Haka sukaci gaba da nemansa har tsawon sati biyu, amma babu labarin Captain Aryan.

Alokacin Mawahib takoma part din Mamy tana rayuwa acikin dakinta,tsawon sati biyun nan tayi tunanin Yaya Captain zai kirata yaji awanne hali take ciki, amma taga shiru bai kirata ba,tunani tafara Anya kuwa soyaiyar dayake kuka yake fada mata yana sonta Anya da gaske ne? yasanar da'ita zaiyi tafiya amma wacce irin tafiya ce zatasa yakasa kiranta!?

ta dauki wayarta ta kirashi akaro na biyu tun aurensu,saide tana kira taji wayar akashe.

Haka tayi haquri tabari har zuwa yamma tasake kira nanma taji waya akashe, mamaki ya kamata Anya Yaya Captain lafiya kuwa? tasan cewa baya kashe wayarsa,cikin damuwa tafuto daga dakinta takira Yaya Ashraf tace"Yaya Ashraf yau tun safe Ina kiran wayar Yaya Captain amma bana samunsa"

Ashraf yayi shiru yana tunani to Mawahib sai yau takira Captain kenan,gyara muryarsa yayi yace"may be baida caji ne,zan kirashi zuwa anjima idan munyi magana saina fada masa ya kiraki"

Tace"to shikkenan"

Ta ajiye wayar jikinta yadan fara sanyi.


Hajiya kilishi kuwa ganin sati biyu shiru Aryan bai kirasu ba,kuma idan sun kirashi basa samunsa,hakan yasa hankalinta yatashi,da farko tayi tunanin saboda abinda yayiwa Mawahib ne yasa yakashe wayar yaqi kunnawa harsai sun huce,daga baya kuma dataga shirun yayi yawa daga nan tasan cewa akwai matsala.

Da daddare suna zaune da Alqali ta kalleshi tace"nikam Alhaji shirun Yaron nanfa yayi yawa babu waya babu wata magana qwaqwqwara akan ahaka"

Alqali yace"nikaina abun yafara damuna, yau satinsa biyu kenan, dazu munyi magana da khaleed da Isah, Isah yace zaije Abujan yagano to nahanashi zuwa saboda yanayin aikinsa, sai muka yanke zamu tura Ashraf yaje yagano mana ko lafiya.

Hajiya kilishi tasaki ajiyar zuciya yace"yawwa,amma shirun ai ya'isa haka,ko a wayar wani ai yakamata yakira mu idan tasa wayar ce bazai budeba"


Bayan kwana biyu Mawahib tana kwance a dakinta sai juyi take tana so tayi bacci amma kuma takasa, ko Yaya ta lumshe idonta shi take gani, kuma tasan rashin baccin nata baya rasa nasaba da yanda Yaya Captain din yasabar mata da kwanciya a jikinsa, wayarta tadauka tasake gwada kiran wayar Captain Aryan,taji waya a kashe,mamaki yasake kamata, shekaran jiya Yaya Ashraf yace zai masa magana, jiya ta wuni tana kira wayar a kashe,yauma haka.

Tashi tayi tanufi dakin Mamy tana zuwa tazauna jagwab akusa da'ita, Mamy ta kalleta tace"kekuma lafiya kikazo zaki sani agaba kifara min wannan jarababban kukan naki?"

Cikin damuwa tace" Mamy ba kuka zanyi ba, Kingani kullum idan nakira wayar Yaya Captain bata shiga,shekaran jiya nakira shi, jiyama, yauma haka,Mamy ke kunyi waya ne?"

Jikin Mamy yayi sanyi tace"Mawahib ai Captain yau sati biyu da kwana biyu kenan wayarsa a kashe,nikaina tun ranar daya tafi nake kiransa amma bana samunsa,babu ranar da zatazo tawuce ban kira Captain ba,tun tafiyar sa da kwana biyar danaji wayarsa a kashe jikina yabani ba lafiya ba,to babu wanda nafadawa saboda kada na tada hankalin iyayensa"

bakinta tabude cikeda damuwa sannan tasaki wani irin numfashi tatashi tafuto daga dakin kamar an tsikare ta, Mamy tabita da kallo cikin tausayawa dan da alama tunda Mawahib tafara nuna damuwa akan Captain haqiqa tafara sonsa ne.


Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan
adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal

sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kankiπŸ’ƒπŸΌ


Mawahib tana barin dakin Momy takoma dakinta tazauna a gadon tafara tura masa saqo Kala Kala,sannan taci gaba da kiran wayarsa, takira wayar har babu adadi, amma bata sameshi ba.

Har yamma tana kiran wayarsa amma shiru,daganan kuma jikinta yayi sanyi, gabanta yafara faduwa, tatuna lokacin dazai tafi, tatuna kalaman sa a gareta lokacin dayake fada mata cewa zanyi tafiya me nisa,bansan yaushe zan dawo ba, bansani ba zan dawo dinma kokuma bazan dawo ba, amma inaso kisani Ina sonki...
duk abinda kike buqata karki tambayi kowa ki tambayi Ashraf,koda bana raye ki kalleshi, kisa aranki kamar ni kike kallo ki yafemin....


tana gama wannan tunanin gabanta yayanke yayi wata irin faduwa,jikinta yafara karkarwa,a fili ta furta "Ina yatafi?"

Cikin sauri ta dauki wayarta takira Nusaiba matar Captain Habib abokinsa wanda sukaje gidansu suka kaimusu ziyara.

Tana dauka cikin tashin hankali ko tsayawa batayi sun gaisa da'ita ba tace"Aunty Nusaiba,dan Allah inaso ki turomin number Abban mufid zan tambayeshi naji Yaya Aryan ko lafiya muna kiran wayarsa bata shiga, koda yaushe a kashe"

Cikin mamaki Nusaiba tace"kamarya? Mawahib wai bakisan antura Captain Aryan wani daji zasuyi yaqi ba?"(πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ)

tanajin haka taqame a zaune tareda sakin wayar tata tafadi qasa,gabanta yayanke yafadi,hawaye yafara zuba daga idonta, tadora hannunta aka tasaki wani irin ihun kuka tace"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...."

Mamy datake kallo afalo, cikin sauri ta miqe tsaye tace"yau naga takaina yarinyar nan kode tahadu da matsalar aljannu ne?"

tatashi da sauri zata nufi dakin Mawahib Hajiya kilishi da mama Sadiya dasuka jiyo ihun nata suka fado cikin falon cikin sauri,Hajiya kilishi tace"Maryam Mawahib qonewa tayi ne da ruwan zafi?" (πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ)

Mamy tace"tana dakinta,nima Ina nan najiyo ihun nata"

gaba dayansu suka saka kai cikin dakin Mawahib,har yanzu hannunta yana kanta tayi baza-baza da gashinta tana kuka kamar mahaukaciya.

Mamy tace"Mawahib menene?, me aka miki?"

Cikin kuka tace"yaya Captain ne..."

Cikin sauri Hajiya kilishi tace"yakiraki ne? meyace miki?"

Cikin kuka tace"wai antura shi yaqi...,dama yacemin qila bazai dawo ba yatafi kenan...,Mamy dan Allah kice masa yadawo wallahi yanzu inason mijina zanyi masa duk abinda yakeso"(😭)


Hajiya kilishi tanajin haka ta jingina da bango tafara silalewa qasa zata zauna.

Cikin tashin hankali Mamy tace"yaqi kuma?"





(Sorry Mawahib πŸ˜₯πŸ™πŸ»)
Mutara zuwa yammahπŸ™πŸ»



Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034

muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki





Amnah El Yaqoub✍🏻
[7/15, 4:20 PM] AMINA KABIR CAPS: MAWAHIB



*13&14*




Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034

muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki



Mama Sadiya tace"ai bamuga ta zamaba kamata yayi a fadawa su Alhaji atashi tsaye da Addu'ah in saukar Alqur'ani za'a masa ma sai ayi, ko kwanakin baya dasuka tura shi ai yana Samun damar kiran waya kota minti daya ce"

Hajiya kilishi data silale awajan ta zauna tayi shiru kamar bata cikin hayyacinta, duk maganar da Mama Sadiya tayi kokadan bata jitaba, Mamy tacewa Mawahib "to ai Addu'ah zaki masa yanzu tunda de har anji inda yatafi"

tajuya ta kalli hajiya kilishi "Yaya kiyi haqiru,in Allah yayarda Captain yana cikin qoshin lafiya"

Cikin sanyin jiki Hajiya kilishi tace"rannan yacemin ankashe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login