Showing 30001 words to 33000 words out of 110331 words
kansa yake qasa Koda wasa yaqi kallonta,cikin ranta tace Allah karimun waheedun yau nice nazama dodon Aryan,tun ranar da Mawahib takirata tana kuka Bata sakejin kansu ba kosun shirya kansu kokuma sunacan sunacin mutuncin juna oho musu,tace masa"Captain ya Abuja?"
Fuskarsa babu yabo babu fallasa yace"Alhamdulillah"
Daga nan baisake cewa uffan ba.
Ashraf yace"Anty Mamy kicewa mama Sadiya Wanda suka raka yarinyar Nan su zauna su kwana tareda ita,zan kwanta anan tareda Aryan"
Cikin fahimta Mamy tace"to shikkenan bari in kawo muku abincin saina wuce part dinta Infada mata"
Captain Aryan yana jinsu,yana ganin shigewarta kitchen yatashi tsaye yace"tashi mutafi"
Ashraf yayi murmushi yatashi suka futo,part din Hajiya kilishi suka nufa tundaga bakin qofar falo sukejin hayaniyar mutane, alamun akwai sauran Wanda basu kwanta ba, Hakan yasa suka juyo suka koma cikin dakinsu, suna zuwa Ashraf ya kwashe da dariya yana qoqarin cire babbar rigarsa,ya Kalli Captain Aryan cikin dariya yace"wai Kai kunyar Anty Mamy kakene?"
Captain Aryan ya yatsina fuska yace"kunya Kuma?"
Ashraf yace"ni zaka rainawa wayo? tunda mukaje kayi kidis dakai kamar wani baqo,saini kadai nake mata magana "
Cikin damuwa Captain Aryan yace"niba kunyar ta nakeji ba"
Ashraf yace"kunya kakeji mana,kazo gaban surukarka, tun yanzu kana irin wannan kunyar idan kunfara amarci gidan zaka daina shigowa Kenan?"
Captain Aryan yadaure fuskarsa tareda girgiza kai yawuce toilet domin watsa ruwa,bayajin har abada wannan abun da Ashraf yake fada zai faru tsakanin shida wannan yarinyar, yana shige wa toilet adede lokacin Mamy takawo musu abincin sannan tayiwa Ashraf saida safe tafice daga dakin.
Sama Sama sukaci abincin sannan Ashraf ya kalli Aryan yace"kaga saqon dana turawa Mama Sadiya yanzu"
Yafadi haka yana bawa Captain Aryan waya.
Captain Aryan ya kar6i wayar yafara karanta saqon a fili kamar haka "Mama nasan Nabiha batason auren nan,Nima kuma kinsan hakane,to tasanar dani akwai Wanda take jira,Ina miki alqawari babu abinda zai samu Nabiha,bazan ta6a miki yarki ba,yanda kuka kawota haka zata auri Wanda takeso, daga Ashraf"
Captain Aryan yana gama karantawa yace"eh tura mata,dansu tabbatar wannan aure auren dasuka qulla mana babu inda zaije, ko Nima in turawa Anty Ma-my irinsa?"
Ashraf yace"karka tura,gara nawa hadin da sauqi akan Naka, kaifa ta ko'ina adaure kake, baka Isa kasaki yarinyar Anty Mamy ba, nidin de daba dogon mutunci nakeyi da Nabihan ba to zan'iya tura musu, tashi muje wajan Momy"
Haka suka nufi part din Hajiya kilishi.
Alokacin da Mama Sadiya taga saqon saitayi murmushi ta nunawa Mamy, itama ta karanta, Mamy tayi dariya tace"to bari mugani ayi Zaman auren, tunda kikaga haka da Aryan din sukai wannan shawarar, bazai turo ba sai Aryan yasani, duk su biyun zamu gauraya ne, dani suke zancen"
shabiyu saura,suka qarasa part dinsu, Alqali yana zaune afalo yana duba hisnul Muslim yaga shigowar su, Kai tsaye wajan sa suka nufa tun a wajan daurin aure rabon su dashi, kasancewar ko acikin duhu suke zai banbance su shiyasa Kai tsaye ya Kalli Ashraf cikin rashin wasa yace"mekake baka tafi gidanka ba?"
Cikin ladabi Ashraf yace"Daddy dama Naga akwai baqi a gidan ne dangin mamanta,shine nace su kwana tare Nima zan kwanta anan tareda Aryan"
Jin wannan bayanin nasa yasa ya gamsu,baisake cemasa komai ba Yajuya wajan Aryan yace"yaka baro iyalin naka?"
Captain Aryan yace"Lafiya kalau Daddy"
Alqali yace"babu damuwa deko?"
Kai tsaye yace"babu komai"
Alqali ya jinjina kansa sannan yace"Kariqe yarinyar nan amana,nasan babu Wanda yakeson auren acikin ku,amma karka duba wannan,Koda yaushe karka manta mahaifiyar ta ta rungume ku a lokacin da bakwa tareda taku mahaifiyar,saboda haka ko bayan raina karka kuskura kasani hannunta"
Lokaci daya jikin Captain yayi mugun sanyi,cikin sanyin jiki yace"to Daddy"
Alqali yace"zaku Iya tafiya"
Cikin sanyin jiki suka nufi dakin Hajiya kilishi,tana zaune adakin ita kadai tagama saka turaren wuta adakin Kenan, kasancewar ba'a Dade da gyara mata dakinba sakamakon baqi dasuka wuni adakin.
Zama sukai agefen gadon sukai shiru,Hajiya kilishi ta Kalle su tace"Lafiya?"
Ashraf yace"Momy ashe fishi kikeyi da Aryan"
Tajuyo ta Kalli Ashraf tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi, sakoka yayi agaba Kenan kazo Kamin duka saboda Ina fishi dashi?"
Cikin sauri Ashraf yace"Momy bahaka bane bafa...,kiyi haquri dan Allah,Kinga fa duk ya rame wallahi,ni rakoshi nayi yabaki haquri"
ya qarasa maganar yana zungurin qafar Aryan
Cikin sauri Aryan da yaji abinda Ashraf yamasa ya kalleta yace"Momy kiyi haquri idan nayi miki laifi kiyafemin,banajin dadi idan banji muryar kiba,fishin ki zaiyi tasiri akaina har hakan yashafi aikina"
Cikin 6acin rai kilishi tace"au cewa kake idanma Kamin laifi? Saboda angama shanyeka ko Babana? bazan ta6a Jin sauqin zuciyata ba harsai karabu da yarinyar Maryam,har abada bana fatan ace jinina yana auren jinin Maryam,karka sake Kiran wayata inde kasan baka saki yarinyar nan saki uku ba,naji dadi da Allah yasa ba haihuwa zakayi ba bare harka hada jini da wannan yarinyar...."
jin kalaman nata sunyi tsauri dayawa yasa Ashraf yafara hawaye, cikin sauri yafice yabar dakin.
Captain Aryan idanunsa suka kada sukai jajir amma shi baiyi kukan ba, cikin ladabi yace"to Momy zanyi yanda kikace,amma kiyi haquri kiyafemin"
Yana fadar haka Yafuto daga dakin nata jikinsa a mutuqar sanyaye,Alqali baya falon,Kai tsaye saiya wuce dakinsu,yana zuwa yaga Ashraf har lokacin yana goge hawaye,zama yayi kusa dashi cikin dauriya yace"wai kukan menene Ashraf?"
Hawayen idonsa yagoge gaba daya sannan yace"toya zakayi? Ya sukeso kayi? shi Daddy yace karka saketa,ita tace saika saketa saki uku,yanzu saboda Mawahib har Momy zatayi alfahri da rashin haihuwar ka saboda karka hada jini da'ita? Ni bazan iyajin wannan fadan nataba,zuciyata saita buga"
Ya qarasa maganar wani Hawayen yana zubo masa,Captain Aryan ganin Ashraf da gaske de kukan yake hakan yasa yadaure yazo kusa dashi yafara cewa "kayi shiru mana,aini bana kukan,kamar mace kana kuka Ashraf to waye zai lallashi Amarya bayan sati daya?"(πππ)
Cikin sauri Ashraf yadauki fillo yadoka masa shikuma yana dariya,dahaka yayi nasarar lallashin Ashraf harsukai warware kamar babu abinda yafaru.
Washegari da yamma yayi shirin komawa Abuja,sunyi kyau sosai cikin baqin yadi Mai tsadar gaske,Sai hasken fatarsu yasake futowa sosai,kana ganinsu kaga angwaye,kafin yatafi sukaje wajan Hajiya kilishi,Ashraf Sai dauke Kai yake, suna gaisheta ya kawar da kansa gefe saboda abunda yafaru jiya da daddare.
Cikin sanyin jiki Captain yace"Momy zan wuce kimin Addu'ah"
Daqyar tabude baki kamar bataso tace"Allah ya tsare hanya"
Cikin sanyi jiki yace"Amin"
Yasaka hannu a aljihun rigarsa ajiye mata damin kudi guda biyu, sannan yasake bata haquri,suka futo daga dakin.
a gurguje Ashraf ya rakashi part din Mamy,ta dauko masa wata gumba dataji hadi irinna Yan maiduguri tasaka acikin baqar leda ta bashi tace yakaiwa Mawahib,cikin ladabi ya kar6a da hannu biyu,saida yaga tajuya sannan ya ajiye mata kudi dami daya akan kujera daga Nan suka futo.
abakin get ya hadu da iyayen nasa maza,yayi musu sallama, Alqali yasake jinjina masa akan ya riqe Mawahib da kyau, sannan suka shiga Mota da Ashraf yakaishi Airport shikuma yajuyo gida.
Sai qarfe shida na yamma yasauka a Abuja, suna Sauka Ana Kiran sallar magrib.
David yana ganin dawowar oga Captain yayi sauri yabude masa get cikin rawar sauri, saboda yasan yau bai kwana agidaba.
Matar gidan kuwa batasan baya nanba,idan yana nan dinma Sai suyi kwana da kwanaki basu haduba, shiyasa yanzun ma Batasan cewa yaje kano ya kwana ba,Kuma suma yan gidan babu Wanda yace mata Yaya Captain yazo gida.
Yana Bude falon nasu wani qamshi mai dadi na turaren wuta da air freshener yadaki hancinsa,qamshin yamasa dadi hakan yasa ya lumshe idonsa sannan yabude kai tsaye yahaye Sama ya shige dakinsa, zubewa yayi akan gadon sa yana maida gajiya,saida yahuta sosai sannan yakira Yan gida Yafada musu yasauka,fridge din dake cikin dakin yabude yadauki ruwa yasha sannan yaje yayi wanka yadauro alwala yazo yagabatar da sallah sannan ya zauna yana azkhar.
Yadade a zaune har wajan qarfe tara nadare sannan yatashi yacire farar jallabiyar jikinsa yasaka rigar bacci doguwa kalar dark blue,rigar iyakar tsawonta gwiwar sa,daga gaban rigar abude take kana Iya hango gashin dake kwance a faffadan qirjinsa.
Yana kwanciya akan gadon yaga ledar da Anty Mamy ta bashi yakaiwa Mawahib,dan qaramin tsaki yasaki yatashi ya dauko ledar batareda yadamu daganin menene aciki ba,Yafuto daga dakinsa yanufi dakinta
Adede lokacin tafuto daga wanka, kasancewar tasan baya ta6a shigowa dakinta hakan yasa taqi rufe dakin da key,ta tsaya a gaban mirror tana shafa humra ajikinta.
Sauke towel din dake jikinta tayi yayi qasa gaba dayansa,surar jikinta da dukkan dirin jikinta ya bayyana muraran batada komai ajikinta, ta dauki turare spray tana feshe duka jikinta dashi, adede lokacin yaturo qofar dakin zuciyarsa daya yashigo(ππ»ββοΈπ³π)
Idonsa bai sauka a ko'inaba Sai akanta,gabansa yayi wata irin faduwa,a zahiri, Kuma agabansa, bai ta6a ganin mace babu kaya ba Sai yau.
Idonsa qyam akan nashanunta Wanda suke atsaye cif,ya Kalli bajajjan hips dinta cikin ransa yace"yahaka?, dama natane? dama jikinta ne ba cuko ba?"
zai Iya cewa akaf tarihin rayuwarsa bai ta6a ganin yarinya me qananun shekaru dakyan jiki kamar taba.
Lokaci daya yaji wani abu zirrrr tundaga qwaqwalwar sa har zuwa tafin qafarsa,duk saiya nemi jarumtarsa yarasa, Sai jikinsa yafara rawa.
Mawahib tana dago kanta ta ganshi a tsaye,lokaci daya tasaki wani irin ihu ta tsugunna qasa tareda wawuro towel din data jefar aqasa tarufe jikinta dashi,tuni hawaye suka 6alle mata afuska,ta qudundune a waje daya tana raskar kuka.
Kukan tane yasa yagama dawowa hayyacinsa, cikin sauri ya ajiye mata ledar a wajan, Yajuya yafice daga dakin cikin sauri.
Yana zuwa dakinsa Yafada kan gado yana maida numfashi kamar Wanda yayi gudu.
Lumshe idonsa yayi tareda dora hannu akan sumar kansa yashafa sumar zuwa fuskarsa, haushin kansa yakeji meyakaishi? meya aikata haka? Wanne kallo yarinyar nan zata dinga masa?
Cikin sauri yaja bargo yarufe jikinsa dashi har kansa, ya Runtse idonsa tareda karanto addu'ar bacci,cikin ikon Allah bacci ya dauke shi,saide ko awa biyu cikakke baiyi ba yafara ganinta cikin baccinsa a'irin wannan yanayin daya ganta dazu.
Cikin taqaici yatashi yazauna tareda sakin wani irin dogon tsaki, afili yace"a a, waiya haka ne?"
Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
idona nahana bacci nacinye lokaci na narubutashi,bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqadππ»
Mrs Usmanβπ»
[7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: Mawahib littafin kudi ne,duk me buqata naira 500 ne kacal ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
bazanja Allah ya'isa ba,amma muddin kika karanta baki biyani haqqina ba nabarki keda mahaliccinki faqadππ»
Cikin kuka Mawahib tafara tirjewa tana kiran sunan Mamy, har zuwa wannan lokacin Mamy kanta yana dafe da hannunta, saide ruwan hawaye dayake gangarowa har zuwa tsintsiyar hannunta, tanan ne zaka fahimci kuka take,shikkenan komai yaqare, yau Mawahib dinta ce ta auri dan Yaya kilishi,Ma'aruf ya cuceta duniya da lahira, Abba yayi murmushi yazo saitin kunnanta yace"Maryan shikuma wannan ikon Allahn yaya zakiyi dashi kenan?"
bai jira amsar ta ba yajuya yabi bayan Mawahib da Captain Aryan,Captain dayake riqeda hannun Mawahib tana masa ihun kuka jiyaje kamar yadauketa da mari(ππ»ββοΈ)
Alhaji Isah yayi sauri ya tarar dasu,kai tsaye yabude musu mota yakira driver yace"zoka kaisu Airport"
Mawahib tanajin maganar Abban ta ta qwace hannunta daga cikin na Captain tatafi da gudu ta rungume Alhaji Isa cikin kuka tace"Abba banaso,dan Allah Abba karka bari yatafi dani,zan mutu Abba"
Alhaji Isah yayi murmushin qarfin hali yaja hannunta yasakata cikin mota, sannan yakama hannun Aryan da idanunsa sukai jajir shima yasaka shi a motar sannan ya rufe musu motar yajuya cikin gida yanajin zuciyarsa tana karyewa saboda kukan Mawahib din
Acan dakin Hajiya kilishi kuwa,Alhaji Ma'aruf yajuya ya kalli Mamy yace"Maryam meyake faruwa ne?"
Mamy batace dashi uffan ba tajuya tatafi part dinta idonnan nata yayi jajir saboda kuka.
Alqali ya kalli kilishi cikin daure fuska yace"wuce daki"
Haka ta wuce daki saikace mahaukaciya, tayaya ne tanaji tana gani za'a bawa Aryan Mawahib,Aryan din dataci buri akansa shine za'a hadashi da wannan tantiriyar yarinyar dabata da aiki Sai nunawa mutanan gari jikinta,inde tanada iko akan Aryan tosaiya saki wannan yarinyar.
Alqali yanemi waje ya zauna sannan ya kalli Alhaji Ma'aruf da Ashraf dasuke tsaye yace"duk ku zauna"
Bayan sun zauna ya kalli Alhaji Ma'aruf yace"Alhaji Maryam acikin gidannan take,sannan mutumin dakuke waya dashi akan maganar auren nan shine mijin ta,wato Alhaji bazamu kira abinda kayi amatsayin kuskure ba,abinda kayi ka kyauta, kuma muma kahutar damu, saboda mu a wajan mu da Ashraf da Aryan duk dayane,kaga wannan yaron dayake zaune?"
Yafadi hakan yana nuna Ashraf, Alhaji Ma'aruf yajuya ya kalli Ashraf sannan yace"naganshi Alhaji,amma yanaga haka? yanaga kamar wancen dayan? kode yanbiyu ne Alhaji?"
Alqali yace"yanbiyu ne,kuma dukansu 'ya'yanane, wannan shine Ashraf, shine babba,sai Captain Aryan shine qarami,yanzu haka zaman da kaga munyi anan da wannan goro dakake gani nasaka ranar Ashraf ne da Mawahib,Captain Aryan kuma muka yanke shawarar zamu hadashi da yar'uwarsa Asalamiyya,to shine shida dan'uwan nasa suka samemu da wannan maganar cewa kayi masa aure kaji dalilin dayasa muka kiraka domin musake tabbatar wa da abinda suka fada mana,tunda muke da Maryam bata ta6a nuna mana mahaifin Mawahib ba,tun bayanda yan tashin hankali suka faru abaya har Allah yasa aka samu saki a tsakanin ta da mijinta tabar gidannan tsawon wasu shekaru daga baya kuma Allah yayi zata dawo gidannan Isah yaje aka sake daura musu aure, sai muka ganta da wannan yarinya, muka kar6i yarinya muka riqeta da hannu bibbiyu,saboda mun yarda da Maryam mun tabbatar bazata haifi yarinya bata hanyar aure ba,ita bata kawo mana uban yarinya ba,muma Kuma bamu tambayeta ba,to abinda yake faruwa anan gidan shine iyayen yaran Nan mata basa jituwa,hakanne yasa muka dage kan hada auren Ashraf da Mawahib domin asamu sasanto a tsakanin su,to ashe Kai kariga kabata Captain Aryan,amma duk da hakan babu matsala,suje Allah yabasu zaman lafiya da zuri'ah tagari"
Gaba daya falon aka amsa da "Amin"
Alhaji Ma'aruf yace"ikon Allah,lalle ubangiji yayi hukuncin sa anan,to Allah yabasu Zaman lafiya,amma ni idan Naga wannan dinma ai Sai in dauka Captain Aryan dinne"
Ya qarasa maganar yana kallon Ashraf.
Alqali yayi murmushi yace"haka suke,tun suna yara ba'a cika banbance suba"
Alhaji sammani wakilin Asalamiyya yace"to yanzu Alhaji, Ina maganar saka ranar Asalamiyya da Aryan ta tsaya?"
Kai tsaye Alqali yace"Sammani tunda wannan abu yafaru, Ina ganin abar maganar Asalamiyya agefe, idan Captain ya zauna da matarsa sunga halin juna, yaji yanada ra'ayin qara aure,idan har Asalamiyya din tamasa saiyazo su daidai ta idan har zuwa lokacin batayi aure ba"
Alhaji Sammani yayi qasa da Kai cikin ladabi yace"to ai ranka yadade atawa shawarar Ina ganin mezai hana Ashraf yamaye gurbin dan'uwansa Captain Aryan,kamar yanda Shima Captain din qaddara tasa yamaye gurbin Ashraf?"
Alqali yace"da nayi wannan tunanin,to daga baya saina yanke shawarar Shima Ashraf din zan hadashi aure da qanwarsa NABIHA"
Jikin Alhaji sammani yayi sanyi, gashi babu damar dazai kushe Nabiha, kokuma yayi musu da Alqali tunda ga mahaifinta nan a zaune,cikin danne damuwar sa yace"eh hakane,hakanma ai yayi,to Allah yasanya Alkhairi,Allah yabasu Zaman lafiya gaba daya, mu bari muwuce"
Alqali yace"Allah ya maida ku gida lafiya"
Alqali dayake babban mutum ne Kuma Wanda yake mu'amula da mutane sarai yagane halinda Alhaji Sammani yake ciki,shikuma da hankalin sa bazai iyu yahada dansa aure dawani dangi na kilishi ba,shima kansa haquri yake da'ita tayaya zai sake qoqarin hada iri dasu?(π³πππ»ββοΈ)
abinda yasa ya amince mata da auren Asalamiyya afarko ma saboda tabar Ashraf ya zauna da Mawahib lafiya shiyasa Shima yace ya amince Aryan din ya auri Asalamiyya,amma yanzu tunda ubangiji yayi hukuncinsa yanda yakeso sai abar maganar Asalamiyya,Yara kuma suje gidajen su su qarata, acan saisu daidaita kansu.
Ashraf yanajin abinda Alqali yayanke yayi qasa da kansa yana tunani,shide Dama Mawahib yakeso, to Aryan ya aureta,maganar ta tariga ta wuce,amma Nabiha de baya sonta,tunda yake da'ita kallon qanwa yake mata, bai ta6a tunanin aurenta ba,Kuma yasan ta'inda zai 6ullo mata cikin ruwan sanyi zai sallameta.(ππ»ββοΈ)
Alqali ya Kalli maqocinsa daya zama mutum mutumi zaune, sannan ya Kalli amininsa yace"ga abun saka Rana nan, ga mahaifin Nabiha nan, kusaka musu ranar daya dace, tunda su wadancan mutum biyun anriga an daura"
Nan take sukai abinda zasuyi, aka tsaida ranar auren Ashraf da Nabiha,sati biyar Masu zuwa,Ashraf yanajin haka yatashi yafice yabar falon cikin rashin damuwa saboda yasan abinda yagama qullawa aransa.
Alhaji khaleed yakira Mama Sadiya yabata umarnin takawo musu abinci,Nan take tasaka hijabin ta takawo musu abinci,already Hajiya kilishi takawo musu lemuka da ruwa,zata juya tatafi Alqali yace"dauki wannan goron kije ki rabawa dangin ki da sauran yan'uwa, nasaka ranar Ashraf da Nabiha ne"
Mama Sadiya taji maganar banbarakwai,Ashraf ba Mawahib za'a bashi ba? ganin mutumin daya Bata umarnin bawanda zata tsaya jayaiya dashi bane, Hakan yasa ta dauki goron tareda cewa "Allah ya tabbatar da Alkhairi"
Bayan tafita Alhaji Bala abokin Alhaji Ma'aruf,shine Yazuba musu abinci, sukaci su kasha kowa yana farinciki, Alhaji Ma'aruf yasaka hannu a aljihunsa yadauko rafar kudi dami daya,wadda zata Kai kimanin dubu Dari, yabawa Alhaji khaleed yace"Kudin sadakin Ruqayya ne,Wanda abokina gashinan a zaune Alhaji Bala shine yabiyawa Aryan, amatsayin sa na waliyinsa"
Alhaji khaleed ya kar6i kudin tareda godia,Alhaji Ma'aruf ya Kalli Alqali yace"inaso zanyi magana da Maryam da mijinta kafin muwuce"
Alqali yadauki wayarsa yakira Abba yace"inason ganinka kaida maryam"
Bayan wasu min tuna suka shigo shida Mamy amma idonta yayi jajir har yanzun kuka take, zama sukayi, Alqali ya kalleta yace"Maryam kukan ne har yanzu?"
Cikin kuka Mamy tace"yaya wannan mutumin ya cutar dani,Kuma ya dauki yata yamata aure babu sanina, bayan baisan wahalar taba, baisan cintaba baisan shanta ba, baisan Yaya take rayuwa ba"
Alqali yayi murmushin manya yace"to ayi haquri mana,Maryam shekara da shekaru ai ya kamata ace kin yafe masa haka ko?"
Alhaji Ma'aruf da jikinsa yayi sanyi yace"hakane Alhaji, haqiqa nime laifi ne awajan ta,acikin Zamana da Maryam zan'iya cewa nine na cutar da'ita,ashekarun baya banida wata sana'ah data wuce fashi da makami,da'ita nake cinyarda Maryam da mahaifiyata wadda ta Ruqayya taci sunan ta, kafin Allah yamata rasuwa,har Allah yabawa Maryam ciki ta haihu na sakawa yarinyar sunan mahaifiyata,bayan haihuwar ne Maryam ta kamani Ina waya taji duka sirri na,munyi tashin hankali da'ita, tace na daina nace wannan sana'ar tawa babu fashi, wannan dalilin ne yasa tace tona zaba kode in daina sana'ah nadena ciyar dasu da haramun mu zauna nida ita da yarmu, kokuma na sauwaqe mata, alokacin idona ya rufe da kudi, hakan yasa nace na zabi sana'ar fashi akansu, daga ranar Maryam ta dauke Ruqayya, bansake sanin Ina sukeba, saide number ta itace de bata sauya ba,lokaci zuwa lokaci Ina kiranta amma bata taba dauka, haka na