Showing 84001 words to 87000 words out of 135555 words

Chapter 29 - AKIDATA book 1 HAUSA NOVEL

17 Jan 2026

647

gama ganin likitan, ranar da zata bar ?asar nan dan Allah ka tabattar jirgunta ya tashi, da ni naso in kaita da kaina, amma akwai taron kasuwanci na shekara da nake halarta, idan har ban halarta ba akwai matsala ga dukiyata, wadda take gauraye data al'umma"

Yusuf yace "dukiyar ka data al'umma kuma?"

Alhaji Nasir yace "Eh mana, akwai hannun jarin mutane a cikin kasuwanci na, wanda ciki harda masu ?aramin ?arfi idan har ban halarci taron nan ba to tabbas dukiyoyin wasu zasu halaka"

"Amma meyasa dukiyar wasu zasu halaka, dan baka halarci taron ba? '

Alhaji Nasir yayi murmushi yace
" karka damu, idan Allah yasa kuka dawo zan gaya maka yanzu dare ya fara yi "

Yusuf a ransa yace" to ko dai Alhaji Nasir yasan ma?iyansa ne? "

A fili kuma yace "Amma yallaSai kana ganin za' a samu Nasara idan taga wannan likitan?"

"To abun duk lalabune a duhu Yusuf, bamu san inda zamu dace ba"

Suna cikin maganar sa?o ya shigo wayar Alhaji Nasir, ya Wakko wayar ya duba
Jikin Alhaji Nasir ne ya kama rawa, a Wan gigice yace
"Amm.. Ammm Yusuf jeka ka kwanta dare yayi, saboda ku samu ku fita da wuri gobe in Allah ya kaimu, kabi wannan varrender akwai Waki yana kallonka acan zaka kwanta"

Yana gama faWin haka ya shige wani Waki ya rufe ?ofa, mamaki ne yakama Yusuf ya mi?e ya nufi inda Alhaji Nasir ya kwatanta masa ya shiga.

Masha Allah, Wakine tangameme babu abunda babu na jin daWin rayuwa a ciki, gadon kansa abun kallo ne kamar ka sace ka gudu, hotunan Widad ne ko ina a Wakin, Yusuf ya dinga ?are musu kallo, idonsa ya sauke akan haWaWWen hoton Widad.

Tayi kyau sosai tayi murmushi cikin wata jar doguwar riga, ta baje gashin kanta kamar ba ita ba.
Ya daWe yana kallon hotunan dake jikin bango, sannan ya ajiye jakarsa, yana sake ?arewa Wakin kallo.

Ya shiga banWakin yayi alwala ya dawo yayi nafilfili yayi karatun Al'qur'ani da addu'oi sannan ya nemi guri ya kwanta.

Wajen ?arfe biyu na dare cikin bacci Yusuf yaji muryar Alhaji Nasir na rawa yana kiran sunan Yusuf, a gigice Yusuf ya farka ya tashi zaune.

Alhaji Nasir ya kamo hannun Yusuf yace "taso Yusuf akwai matsala"

"matsalar me Alhaji?"

"Yusuf rayuwar Widad, ni idan tawa ta salwanta bakomai, bana son Widad ta rasa Ranta"

Cike da mamaki haka Yusuf ya biyo bayan Alhaji Nasir,? suka tarar Widad na tsaye a falo tana kuka, gaba Waya Yusuf ya rikice yace

"Alhaji meke faruwa ne"

Jiki na tsuma Alhaji Nasir ya mi?awa Yusuf wayarsa

"RANA BA TA ?ARYA SEDAI UWAR ?IYA TAJI KUNYA, YAU ZAMU KAWO ?ARSHEN WASAN KURAR DA MUKE, KODAI KA YADDA KA BAMU ABUNDA MUKE BU?ATA KA HALARCI TARON KASUWANCI, KO KUMA KA HANAMU KA RASA RANKA DA NA 'YARKA, KOMU KASHE TA AGABANKA MU BAR MAKA MUGUN TABO, WATA?ILA HAKAN YASA KA BAMU ABUNDA MUKESO"

Yusuf yace "to koma mene ka basu mana, saboda rayuwar ka da tata su tsira"

"Yusuf ni kaina abunda suke so in basu ba nawa bane, nayiwa kaina Al?awarin bawa meshi abunsa, dan haka bazan basau ba"

Yusuf yace? "to ko ka kira jami'an tsaro"

"A' a Yusuf hakanma matsala ne, dan Allah ka Wau Widad ku tafi maza ku tafi yanzu"

Fashewa da kuka Widad tayi tace? "Ni bazan tafi na barka ba Daddy, bana son wani abu ya same ka, Daddy bana son tafiya kai kaWai ka ragemin"

Dattijon yana zubar da hawaye yace

"Widad bana son rayuwarki ta salwanta, nima ke kaWaice dani, idan suka kama ki komai ya Saci, ki tabbatar kin mi?a amanar nan ga masu ita, karki yards ta salwanta ko a karon banza wasu su karSa, maza ku tafi"

?an?ame mahaifinta tayi tana kuka tace "Daddy ba inda zanje, kome ze faru ya faru muna tare"

Daddy da kansa yaja hannun Widad ya kaita mota, ya kalli Yusuf yace "Allah ya kiyaye ku Yusufa, na yarda da kai ka kularmin da Amana
ta, ka kula da Widad kayi ha?uri da ita, karku sake ku dawo idan bani na kira ku ba, zaman Widad anan tana cikin hatsari mutanen nan dagaske suke"

Haka Yusuf ya shiga motar yaja, Widad tana wani irin kuka me ban tausayi.

Su kansu ma'aikatan sunyi mamakin fitar su Yusuf a wannan daren.

Saleh ne ya samu Alhaji Nasir yace? "Alhaji lafiya kuwa? Meke faruwane haka?"

Daula yace? "Wata 'yar ?aramae matsala ce, Amma komai ze daidaita insha Allah"

Alhaji Nasir ya koma cikin gidan yana safa da marwa ya rasa abunyi, wayarsa ya Wakko ya kira Bulama a waya ya sanar dashi halin da yake ciki.

Yusuf kam a besan inda ze nufa ba a wannan tsohon daren, gaba Waya sahu ya Wauke se abunda ba'a rasa ba,gudu yake yana ratsa tituna ba tare da yasan inda ze dosa ba.

Befi mintuna talatin ba sega Bulama yazo gidan a sukwane, suka haWu da Alhaji Nasir a harabar gidan, Bulama a gigice yace "Daula ina Widad Win take yanzu?"

A kiWime Daddyn Widad yace "na haWata da direbanta nace su tafi"

"su tafi suje ina?"

'Bulama na rasa yadda zanyi ne, ina tsoron rayuwar Widad ta taSu, nasan yaron baze cutar da ita ba"

A fusace Bulama yace? "kayi hauka ne Nasiru, kamar ya ka haWata da direba? Kasan daga ina yake ko kuma ina ze kaita, memakon ka kira' yan sanda kawai seka haWata da direba idan kuma bakinsa Waya da mutanen fa"

Girgiza kai Alhaji Nasir yayi yace? "bana tunanin haka Bulama kaina ya gana kullewa ne"

Alhaji Bulama ya Wau waya ya fara kiran 'yan sanda.

Sosai Yusuf yake gudu akan titi, yayin da Widad ta dun?ule tana aikin kuka, Yusuf ya kasa cewa komai se tunanin ya zasu tsira, sedai babu zato yaci karo da wata mota anyi parking Winta a tsakiyar titi, wani irin parking na rashin mutunci yanda babu damar Yusuf ya iya wucewa, ga gefe jeji ne, yayi reverse ze juya kan motar wata motar tazo ta ?ara rufe bayan tasu Yusuf aka sasu a tsakiya.

Wasu irin ?arti ne suka fito daga motocin suka kewaye su Motarsu Widad, gaba Waya Widad ta rikice ganin suna tunkaro su, suna zuwa suka buWe ?ofofin motar, suka sawa Yusuf bindinga aka suka ce Widad ta fito.

Ko motsi ba tayi ba balle ta Waga kai ta kalle su, cikin tsawa Waya yace? "ba magana ake miki ba"

Sunkuyar da kai tayi ta?i motsawa, Waya yasa hannu ze fizgota aikuwa ta ri?e Yusuf gam tana kurma ihu

"Yoseef karka bari su tafi dani"

Yusuf ya ri?e hannun ta yace? "me mu kayi muku kuke ?o?arin cin zarafin mu akan titi haka"

"zaka rufe mana baki ko semun fasa kanka da bindiga, dalla ku fizgota ta ?arfin tsiya suna Sata mana lokaci"

Ai Widad sekace Mayya ko ?arfe ta ri?e Yusuf gam, wani gigitaccen mari Wayan ya kwaWawa Widad yana ?o?arin janyo ta, sedai ga mamakin Yusuf mutumin yana sauke hannun sa Widad ta rama marin, dukda a gigice take tace?? "karka ?ara gangancin marina, wallahi ka kuma dukana sena rama"

"Ashar ya saki yace lallai wannan yarinyar akwai ?arfin hali, yau zamuyi maganinki"

Hannu ya kai ze sha?ota, amma Yusuf ya ri?e hannun mutumin yace? "karka kuskura ka sake marinta"

"Idan aka sake marinta me zakayi? Dan Allah oga ka bani dama in fasa kan gayen nan da bindiga"

Shugabansu yace "babu kisan kai a wannan deal Win, ban sani ba ko zuwa gaba"

Suka cigaba da jan Widad, Yusuf ya?i sakin ta, baya son ya zafafa suyi mata illa gashi babu makami a jikinsa.

Yace "idan kunga kun tafi da Widad to tabbas kun kasheni ne, amma ba inda zaku da ita"

Ganin Yusuf na Sata musu lokaci ga Widad na nema tasa asrinsu ya tonu, bakinta ya?i rufuwa sunan Yusuf kawai take kira, haka suka haWa da Yusuf suka sasu a tasu motar.

Suka ?ulle hannayensu, sukayi daji dasu, ihu Widad ta cigaba dayi, gaba Waya ta manne a jikin Yusuf sosai tana cewa
"ni ku ?yalemu, besan komai akai ba, direba nane kawai ku ?yalemu mu tafi"

Yusuf yace? "kiyi shiru karsu illataki"

Ai be gama rufe bakinsa ba, suka sa ?yalle suka rufe musu ido.

Widad tasa ha?oranta ta ri?e rigar Yusuf, duk dan kar su raba ta da Yusuf, se haki take tana jin yadda zuciyar Yusuf ke bugawa, Yusuf kam ya yabawa jarumtar Widad yau.

Shikansa Saleh da'aka haWa baki dashi akayi aikin, ya rikice gaba Waya ya shiga damuwa mussman yadda yaga Alhaji Nasir na zubda Hawaye yana kaiwa yana komowa a harabar gidan, Alhaji Bulama nata rarrashinsa amma se kuka yake kamar ?aramin yaro, zuwan 'yan sanda yayi dai dai da shigowar wani sa?on wayar Alhaji Nasir.

"A ZATONKA KA FIMU WAYO NE, MUN KAMA' YARKA DA DIREBANKA SUNA HANNUNMU, SHAWARA TA RAGE NAKA, ZAMU CIGABA DA AZABTAR DASU, DAN HAKA SEKA KA ZA?A KO RANSU KOKUMA ABUNDA MUKA NEMA A HANNUNKA"

Yana gama karanta sa?on ya yanke jiki ya faWi a gurin

In an karanta ayi share please
=?O? =?O? =?O?

Gyara, sharhi ko shawara
Ayshercool
07063065680

_*A?IDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*A?IDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Ha??in Mallaka ?& : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ?unsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani Sangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 24_25



Gaba Waya ma'aikatan gidan su kayo kan Alhaji Nasir, sedai jikinsa kamar babu rai, 'yan sanda suka ?araso cikin gidan aka kwashi Alhaji Nasir a daren zuwa Asibiti.

Widad kam gajiya tayi da zaman motar, saboda tafiya suke bata wasa ba cikin wani irin azababben gudu, jin tafiyar ta?i ?arewa ne yasa Widad fara mustu mutsu, tun tana mutsu mutsun har bacci ya kwashe ta, a firgice ta farka ta kurma wani uban ihu tana kiran
"wayyo Allah na Yoseef, karka tafi ka barni"

Yusuf yace "Widad ina nan, muna tare har yanzu Allah ze fitarmu insha Allah, ki dena shouting karsu miki wani abun"

Me tu?a motar yace gara dai kaja mata kunnen.

Memakon tayi shiru ta cigaba da ihu tana "ku ?yalemu mu tafi, yoseef na gaji da zaman nan hannuna igiyar nan ta dameni, bayana ciwo na gaji bayana ze karye"

Wata hoda su watsawa Widad, wanda hakan yasa ta baccin dole, ba Widad ba har Yusuf gaba Waya bacci ya kwashe su.

Ana kai Alhaji Nasir Asibiti, aka kwantar da shi aka dinga masa allurai da ?arin ruwa, ga oxygen ansa masa domin temakawa numfashinsa dake barazanar Waukewa.

Likitoci suka du?ufa akansa, suna bashi dukkanin taimakon da zasu iya, ga jininsa ya hau fiye da kima suna ta ?o?ari jininsa ya sauka.


Yusuf ne ya fara farkawa jin motar ta tsaya, aka buWe motar suka kwance musu ido, mamakine ya kama Yusuf, tun cikin dare suke tafiyar nan amma da'aka kwance musu ido yaga yanayin garin kamar Azahar ta gota, daji ne sosai ciyayi sun lulluSe ko ina, gaba Waya Yusuf baya gane inane gabas ko yamma ya kasa gane ta ina suka zo nan gurin.

Widad kam sam bata hayyacinta, ta farka amma se tangaWi take haka suka sasu a gaba zuwa wani gini.

Yusuf yayi mamakin yadda aka shigo cikin wannan uban dajin akayi ginin gida, suka buWe gidan suka shiga dasu Yusuf.

Gaba Waya gurin kango ne, kuma ga dukkanin alamu an samar dashi ne mussman saboda wannan aikin, saboda gurin sabon gini ne harda ragowar kayan aikin ginin.

Wani Waki suka kai su Widad suka ajiye, akan tsurar tabarma suka kawo musu ruwan pure water guda biyu suka ajiye musu suka maida ?ofa suka rufesu a ciki.

Yusuf ya Wau ruwa Waya ya fasa ya bawa Widad, aikuwa nan da na ta zu?eshi da alama tana jin ?ishirwar sosai, ga ko salla ba suyi ba haka ya zuba mata ruwa tayi alwala, Wan ragowar shima yayi ba tare da sun san inane gabas ba haka suka gabatar da salla.

Shiru Widad tayi, gaba Waya jikinta ciwo yake ga wata uwar yunwa da take ji, gashi har yanzu jikinta babu ?wari saboda hodar da suka watsa mata.

Ta kalli Yusuf da yayi shiru ya sunkuyar da kai, gaba Waya tausayinsa yakamata duk a dalilin ta wannan masifar ta faWa masa.

Kifewa tayi a gurin, hakan yasa Yusuf Wagowa da sauri yana kiran sunan ta, cikin kasala tace "Yunwa nake ji"

A hankali yace "kiyi ha?uri kinji, Insha Allah zamu bar gurin nan, kuma zaki ci Abinci"

Ba tace komai ba ta maida kanta ta kwanta, wani irin sanyi na ratsa ta, mi?ewa Yusuf yayi yana zagaye Wakin harda ban Waki sedai an rufe ko ina babu hanyar tsira.

Zagaye Wakin ya shiga yi yana sake tunanin menene mafita, ya kalli inda Widad ke kwancw ta takure sosai gwanin ban tausayi.

Haka suka wanzu babu me cewa komai tsawon wasu awanni, suka ri?e alwalarsu in sun kintaci lokacin salla se suyi.



Alhaji Bulama ya samu ya koma gida, dan Alhaji Nasir ya farfaWo ya samu bacci, yana zuwa Matarsa tace "kaikam ina ka tafi haka, na farka na nemeka na rasa na dinga kiran wayarka ka?i Wagawa, duk ka Waga mana hankali"

"Daula ne babu lafiya" ya bata amsa

Sekuma jikinta yayi sanyi tace "meya same shi?"

"An sace 'yarsa da direbanta, shi kuma ya yanke jiki ya faWi"

Dafe ?irji Hajiya Sarah tayi tace "Kamar ya an sace su sekace kaji? Yaza' ayi ace 'ya kamar ta Alhaji Nasir an saceta, suwaye suka sace ta?"

"Mutanen da suke bibiyar sa ne, ni nafi kyautata zaton harda haWin bakin direban nata"

Sarah ta girgiza kai tace "Amma Alhaji wannan yaron sam neyi zubin Azzalumai ba"

"ke bari, duniyar nan babu gaskiya shi mugu ai bashi da kama"

"Hakane, Allah ya fidda su lafiya, amma an sanarwa jami'am tsaro?"

Bulama yace "eh na sanar musu an fara bincike ma"

Gaba Waya Hajiya Sarah ta shiga damuwa, dukda yadda take jin haushin Widad, su Ramadan ma da Iman sin shiga damuwa sosai da jin labarin.



Isa megadi ne ya shigo falon gidan a gigice yana kiran Hajiya.
A fusace Hajiya Halima tace "lafiya kake min wannan kiran kamar wata 'yarka"

"Hajiya babu lafiya fa, muna nan zaune gaho an sace Autar daula da direbanta, shi kuma Alhaji yana kwance a Asibiti"

"to shine me zaka zo kanamin wannan kiran, aita sace tan mana ai hakane ya dace da ita, Allah yasa daga na su kashe ta ma kowa ya huta, fita ka ban guri ka koma kan aikin ka"

Galala Isa ya bita da kallo, "bazaka fita ba sena zo na kwasheka da mari"

Jiki a sanyaye yayi waje yana tunanin, to idan ma bata tausayawa Widad ba saboda tana musu wula?anci to Alhajin fa, wanda duk wani gata da jin daWi a dalilinsa suka same shi.
Yana wannan tunanin yayi karo da Anwar ba tare da ya sani ba.

Anwar yace " lafiya kuwa? Kana tafe baka ganin gabanka"

A firgice Isa ya labarta masa abunda ke faruwa, wata mummunar faWuwar gabace ta kama Anwar yace "garin yaya Isa? Ina Alhajin yake?"

Isa yace "Ance yana Asibiti, amma bam san wane Asibitin bane, sedai a tambayi Alhaji Bulama"

Anwar yace "shikenan nagode"

Ya nufi cikin gida da hanzari, ya tarar mahaifiyarsa da Ramlah suna ta hirarsu.

Anwar hankali a tashe yace "Mummy kin san meke faruwa kuwa, Daddy yana kwance ba lafiya sannan an sace little"

Cike da salo da iya rainin hankali Hajiya Halima ta mi?e tayi gigicewar ?arya tace "haba dai waye ya gaya maka, bana son wasa fa"

Anwar yace "ba wasa bane Mummy, ki kwantar da hankalinki, zanje gidan su Fahad inji komai, se inzo muje Asibitin".

"shikenan hanzarta Anwar, innalillahi wa inna ialaihi raji'un Allah yasa ba gaske bane"

Anwar yace "Mummy ki kwantar da hankalinki, ina dawowa" yayi waje da sauri ko ganin gabansa ba yayi saboda tashin hankali.



Duhu ya fara yi sosai, ba wanda yasa wani abu a cikinsa tsakanin Widad da Yusuf, can sukaji hayaniyar mutanen da suka sace su sun shigo, Widad tayi zumbur ta tashi zaune, suka saka mukulli suka kwance sar?ar da suka kulle ?ofar da ita da kuma kwaWon sannan suka shigo.

Manyan torchlight suka kunna suna haske su Yusuf, suka shigo hannunsu Wauke da mugayen makamai, da manyan bindigogi.

Babban ya haske Widad da fitila, ta sunkuyar da kai ta?i Wagowa yace "shegiya kalleta kamar ta Allah, zamu kawo ?arshen wannan izzar da gadarar taki uwar taurin kai"

Yai maganar tare da ajiye mata takeaway a gaban ta, wata bushashiyar shinkafa ce a ciki sekace ?anzo gefen shinkafar duk ?onanniya.

"ki tashi kici Abinci Malama, sedai ba irin na gidan shashsashan ubanki bane daya sangartaki"

?afarta ta saka tayi Ball da takeaway Win shinkafar ta watse a gurin.

Aikuwa ya harzu?a ya sha?eta yana faWin "nan ba gidan ubanki bane da zaki mana gadara, zakiga yadda zamu lallasa ki sekin sauke wannan izzar taki"

A gigice Yusuf yazo ya ri?e hannun sa yace "dan girman Allah kayi ha?uri ka ?yaleta, a galabaice take zata iya mutuwa inka cigaba da sha?eta"

Yayi jifa da ita ta faWi jiki ba ?wari tana kakari, ya kalli Yusuf yace "banza Wan shishshigi ga abunda shishshigi yaja maka nan, aka dinga ja maka kunne akanta amma ka?i ji, ga shi nan koba komai kaima ka shiga wahala"

Yusuf bece komai ba yayi kan Widad yana Wagota, da ?yar take numfashi.
Yusuf yace "Uwar Wakina, ki dena musu gardama ko so kike su kashe ki a gurin nan?"

Lumshe ido kawai tayi tana sauke numfashi da ?yar.



Hadda Saleh aka tafi Asibiti gurin Alhaji Nasir, an samu ya farfaWo har ya zauna sedai yayi shiru baya magana.

Saleh yace "sannu ranka ya daWe"

Daula ya jinjina kai, ya kamo hannun Saleh yana ta haki yace "Saleh 'yata, an sacemin Widad da Yusuf nayi dana sanin saka Yusuf a harkar tafiyar nan, gashi ya shiga matsala a dalilina"

Saleh yayi shiru sannan yace "kayi ha?uri ka kwantar da hankalinka Alhajin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login