Showing 21001 words to 24000 words out of 135555 words

Chapter 8 - AKIDATA book 1 HAUSA NOVEL

17 Jan 2026

680

ne?

**********************

Manyan Mutane maza su uku, zaune a wani ?aton falo, da ganinsu kasan suna da kuWi saboda yanayin suturar jikin su, zaune suke suna tattaunawa fuskarsu Wauke da damuwa
?aya yace "nifa Al'amarin nan ya fara isa ta, tsawon shekaru muna fama akan abu Waya, amma abu ya?i ci ya?i cinyewa nifa na fara karaya"

"haba Alhaji Haruna, akan me zaka karaya haka? Ai ba gudu ba ja da baya, se burinmu ya cika se mun samu abunda muke nema, abun ba?in cikin yarinyar nan muguwar gaddamammiya ce, wani irin mugun A?ida ne da ita tamkar tasan abunda muke nema, sam bata da wani mutum data aminta da shi ya shiga jikin ta balle mu samu abunda muke so"

Alhaji Haruna yace "kai bari kawai Alhaji Musa, Yarinya kaman ba jinsin mutane ba, duk na kusa da ita ba wanda bamu bi ba amma bamu samu abunda muke bu?ata ba, Kalli yadda shirin mu na jiya ya wargaje.

"Hmmm bari kawai kaga jiya yadda ta wulakanta Jamil a harabar Store Win nan, ina zaune a mota na Wauka zeyi ?o?ari ta bashi lambar wayarta amma ta fasa wayar ta ?are masa zagi a gaban mutane"

Alhaji Haruna ya girgiza kai "yanzu meye abunyi ko mu kashe yarinyar nan mu huta mu kama Nasir daula ta ?arfin tsiya mu samu abun nan"

Alhaji Munir yace "kul Haruna, in baka iya kama Sarawo ba shi seya kama ka, wannan ai wauta ne, kasan yarinyar nan a gurin sa ta gaji wannan taurin kan, idan muka kashe ta tamkar mun kashe Nasiru Daula ne, kuma kasan akwai hatsari sace shahararren mutum kaman Nasiru a ?asar nan, dan haka ita yarinyar ya kamata mu ci gaba da farauta "

Alhaji Musa yace " to sace ta zamuyi ko yaya? Duk hanyoyin da ya kamata mubi munbi amma abu ya gagara, idan muka bari ta koma ?asar waje aikin mu ze kuma komawa baya ne"

"to sace ta zamuyi ko kuwa?"

Alhaji Munir yace? "A'a a yanzu ba sace ta ya kamata mu yi ba, zamu ci gaba da bin diddigin ta, kun san sace wannan yarinyar se anyi kyakykyawan shiri"

Alhaji Musa yace "Anya Alhaji Bulama be san komai akan abun nan ba? naga amintaccen Nasiru Daula ne ko zamu gayyato shi cikin mu?"

"TaSWijan ashe tamkar mu fita mu
tonawa kanmu asiri ne, kome zamuyi kar mu shigo da bare cikin mu, zamu ci gaba da yin zagon ?asa ne a sirri har mu samu abunda muke so"

Haka suka ci gaba da tattauna wa a tsakanin su.

**********************

Yusuf na bakin gate ya bada hankalin sa akan wayar sa, Amal ta fito yana ganin ta yai murmushi tace "Sannu da hutawa"

"Yawwa ranki ya daWe ya gidan?"

"lafiya ?alau, Widad na nemanka"

"to shikenan muje" ya tashi ya bita har part Win Widad, suna shiga Widad ta tsira musu ido, ta sauke idon ta akan Amal ta ?ura mata ido ko ?yaftawa ba tayi, Sum sum Amal ta fita ta basu guri, zuciyar ta Wauke da zazzafan kishin barin Yusuf daga shi se Widad a Waki.

Widad ta ?are Yusuf kallo kaman bata sanshi ba kallo Waya yayi mata ya Wauke kai, dogon wando ne a jikin ta da vest ko kunya ba taji a irin shigar data keyi Widad tace "zan fita anjima ?arfe huWu? zanje gurin birthday, ?arfe huWu, in kaga dama ka tafi yawon ka"

Ya jinjina mata kai yace
"Insha Allah zan kiyaye lokacin" daga nan ya fice.

?arfe huWu saura kwata akayi sallar la'asar, Yusuf ya gabatar da sallar la'asar, sannan ya shiga cikin gidan.

Yana zuwa ya tarar da Alhaji Nasir da iyalan gidan, gefen sa ga trolley alamun tafiya zeyi.

Yusuf yace "barka da rana YallaSai"

Alhaji Nasir yace "Yawwa Yusuf ya aikin, ya ha?uri da Daughter"?

Murmushi Yusuf yayi yace "ai mune take ha?uri damu, Aiki kuma Alhamdilillah, mungode Allah"

Alhaji Nasir ya jinjina kai yace "tafiya ta kamani zani Paris, se shagwaba take wai bazan tafi ba, Yusuf ga amana ta nan, na bar amanar daughter na a hannun ka, har inje in dawo kar a bari tayi kuka, idan tana bu?atar wani abun akula ayi mata dan Allah"

Widad da sauri ta kalli mahaifin ta sannan ta kalli Yusuf a wula?ance tace
"Allah ya kiyaye Ina da komai da nake bu?ata, dan haka bana bu?atar taimako daga gurin kowa balle talaka kaman direba na"

Gaba Waya suka Wauke wuta, shi kansa Alhaji beji daWin abunda Widad Win ta faWa ba.
Yusuf kuwa yai murmushi yace "indai wannan Amanar ce Alhaji na yadda na karSa, Insha Allah zaka je lafiya ka dawo ka tarar da ita, Allah ya bani ikon kula da ita"

Alhaji Nasir yace "Ai dama nasani duk me sunan Yaya na mutumin kirki ne, ban taSa ganin Yusuf wanda ba shi da kirki ba, Allah yayi wa Rayuwar ka Albarka"

Yusuf ya amsa da Ameen

Ita kuwa Maman su Ramla tamkar ta haWiye zuciya, wai direba ake bawa amanar 'yar masu gida, tunda ita cinye ta zata yi ai dole a ce direba ya kula da ita, shikenan direba ya kula da ita in yasan wata ai be san wata ba.
Ba ?aramin haushi take ji yadda Alhaji Nasir ke nuna wa Yusuf kulawa ba.

Yusuf ya Waukar wa Alhaji Nasir trolley Win sa suka fito harabar gidan, Nura ya taho jiki na rawa ya buWewa Alhaji Nasir bayan mota ya shiga.

Ramlah ce ta taho da nufin itama ta shiga motar ayi rakiyar Alhaji Nasir da ita.

Widad ta kalli Ramlah tace "ba gurin ki a motar nan, dan bama bu?atar rakiyar ki"? ta kalli Yusuf tace "shiga gaban motar" .

Nura ya tsaya ya kalli Widad ya kalli Yusuf, Yusuf ma saroro yayi yana kallon Widad, Waidad tace
"ba kaji ba? ko sena maimaita"
Yusuf? ya buWe gaban mota ya zauna, yayin da ita da mahaifin ta suka shiga baya suka zauna.

Nura ya ja mota suka tafi, Ramlah ta rasa me zata yi ne, Mummy tace
"yi ha?uri ?yalesu, in sun san wata basu san wata ba"
Haka ta rarrashi Ramlah suka wuce cikin gida.

Jefi2 Alhaji Nasir da Widad suke hira, yayin da Yusuf da Nura suka yi shiru kowa da abunda yake sa?awa a ransa

Suna cikin tafiyar ne, Alhaji Nasir yace "daughter na dan Allah ina sake ro?on ki, karki watsamin ?asa a ido, idan fahad ya dawo ku daidaita, ina son ganin ki cikin farin ciki ne daughter bana son irin wannan rayuwar takura kan da kike yi"

Banza tayi da Daddyn, seda aka ja lokaci sannan tace? "Daddy na fara tunanin ka dena sona, idan har kana tunanin yi mun aure ne ze sani farinciki, to tabbas zaka sake jefani ne cikin wata damuwar, kafi kowa sanin meye buri na, Aure ze zama tamkar barrier ne a cimma buri na"

"Daughter yanzu abun nan baze wuce a gurin ki ba? Ba zamuyi ha?uri ba mu barwa Allah, ba zamu yadda komai ya faru damu mu?addari ne daga Allah ba?"

"Daddy bazan taSa mantawa ba, kuma bazan yafe ba sena cika buri na, kuma ka dena min batun Auren nan bana so, bazan iya zama a ?ar?ashin wani ba inyi masa biyayya ko waye shi, ku ?yaleni da zancen Auren nan please bana so"

Ta mirror Yusuf yake ganin Widad yadda Hawaye ya wanke mata fuska, ta rintse ido tana magana cikin kuka.

Alhaji Nasir ya rungume ta a jikin, sa cikin sigar rarrashi yace

"Am sorry my dear, i don't mean to hurt you, nasan tamkar na fama miki wani ciwo ne dake cin zuciyar ki, amma kiyi ha?uri ina ?o?arin wanke miki wannan damuwar ne, ina son komai ya wuce kema ki fuskanci rayuwar ki"

"No Daddy i can't, ta yaya zan manta da abunda ya faru, Daddy bazan ?ara yadda da kowa ba, yin aure na tamkar ?ara kusanto da ma?iya jikin mune, ni bazan yadda da kowa ba balle a sake cutar dani a karo na biyu ba, Daddy i repeat my self bana son kowa a kusa dani, bana so" sosai kukan nata yake ?ara ?arfi harda sheshshe?a.

"yi ha?uri daughter na, Amma ina sa ran Insha Allah zakiyi alfahari da auren fahad, yana da kirki sosai Wan uwanki ne, tunda jinin Alhaji Bulama ne, bana tunanin akwai wata cutarwa da Alhaji Bulama ze mana"

Haka nan Yusuf yaji ta bashi tausayi, duk abunda zesa Widad ta sauke wannan izzarta ta, ta dinga irin wannan kukan lallai ba abune ?arami ba.

Har suka je airport Widad kuka take, har kyawawan idanuwan ta sunyi ja, haka suka yi Sallama da mahaifin ta.
Alhaji Nasir ya dubi Yusuf yace "Yaya na a kulamin da amana ta"

A fusace Widad tace "Daddy karka ?ara cewa ka bar amana ta a hannun wani , ka barni a hannun Allah zaka je ka dawo ka tarar dani lafiya Insha Allah, amma zuwa yanzu yaci ace kayi darasin da bazaka ?ara bawa mutum yadda da Amana ba, narasa me yasa Daddy ka kasa fahimta ta"

Alhaji Nasir yai murmushi ya ri?o hannayen ta yai mata raWa a kunnen ta, sannan a fili yace? "ina da surprise a gare ki idan na dawo, ku koma karku yi dare my lovely"

Haka Widad suka juya zuwa mota, yanzu ma Nura ne ke jan Motar

Widad tace "yi parking anan" Nura ya tsaida motar, tace masa

"gaya masa? inda farm house yake"

Nura ya gane abunda take nufi, dan haka yaiwa Yusuf kwatancen inda tace.

Daga nan ta Waga idon ta wanda suka ji?e da hawaye tacewa Nura

"fita ka bar motar nan ka hau ta haya ka koma gida, Kaikuma ka karSi tu?in mu tafi"

Nura yace "Amma ranki ya daWe motar Alhaji ce kuma....

"motar Alhaji ta ubanka ce? Ko ta Ubana?" ta jefo masa tambayar

"A'a amma ban fito da kuWi ba"

"Idan ka bari na sake magana, zan Sata maka rai fiye da tunanin ka, fita daga motar nan nace, idan ba tare muka haWa kuWi muka siya ba"

Haka Nura ya fice daga motar, Yusuf ya karSi tu?in.

Yusuf ya dinga bin kwatancen da Nura yayi masa, har sukaje gidan gonar Widad bata dena kuka ba, Sam Yusuf yaji beji daWin yadda take kukan ba, gashi ita ba'a iya mata balle ya rarrashe ta
Wani irin tangamemen gida ne har yaso yafi gidan da su Widad ke Rayuwa a ciki girma, Yusuf ya fara tunanin anya wannan gidan gona ne? Horn Yayi aka buWe masa wani jibgegen gate me matu?ar nauyi ya shiga da Motar cikin gidan.

Ma'aikatan gidan ne suka dinga tahowa cikin matu?ar sauri inda motar su Widad take, Kallon gurin Yusuf yake yi, dabbobi kala kala a Sangarori daban daban wanda idon sa yake iya gani, gefe kuma gida ne sosai ginanne a ciki, cikin zafin Nama ta fito daga motar tana ta Hawaye, cikin girmamawa ma'aikatan ke zubewa suna gaishe ta, babu wanda ya samu Arzi?in kallo balle ta kula shi.

Cikin matu?ar sauri ta nufi Sangaren da yake gida ne a cikin gurin, Yusuf ya bita shima cikin sauri, binsu ma'aikatan suka yi da kallo mussman Yusuf, Wani irin murgujejen kare ne fari da ba?i a jikin sa ya nufo inda Widad take yana wani irin gurnani gami da sufa.

Dur?usawa tayi ?asa Karen yazo yana zagaye Widad yana shanshana jikin ta, shafa gashin karen tayi tana kuka tace "I miss you Miz"
Karen ya kwantar da kansa a jikin Widad yana zaro harshe, ko tsoron sa bataji balle ?yama.

Haka karen yai lamo a jikin ta tareda ?urawa Yusuf ido, ita kuma tana cigaba da kuka, can kuma ta shafa kan karen tace
"Excuse me Miz, I will see you later"

Ta mi?e zata yi gaba Yusuf ya bita, Karen nan ya bishi yana masa wani irin haushi da gurnani yana zubar da yawu, Yusuf a ransa yace
"Wane irin jarababben kare ne wannan se kace zaki?"

Widad ta juyo ta kalli karen tace
"don't Worry, I trust him Miz"

Daga nan ta mi?e ta ci gaba da tafiya, Aikuwa tana faWar hakan karen ya dena bin Yusuf.

Sunyi doguwar tafiya sosai a cikin gidan, dabbobi daban daban wasu daka gansu kasan sun sha banban da kalar namu na Nigeria.

Gida ne sosai a ciki ginanne me matukar kyau, ya tsaru sosai sedai da alama babu mutane a ciki.

Wani Waki Widad ta nufa ya bita, suna shiga Wakin Widad ta ?ara sautin Kukan ta, wani katafaren gado ta nufa ta zube a gaban gadon ta ci gaba da rera kukan ta, daga jin yadda take fidda sautin kukan kasan kuka ne me taSa zuciya.

Yusuf se binta yake da ido cikin tausayawa halin da take ciki, amma bashi da damar yayi mata magana ko ya rarrashe ta dan bata son shisshigi, yanzu zata masa rashin mutunci.

Ba tare da ta kalli Yusuf ba, a hankali tace "Excuse me please" Yusuf ya jinjina kai ya fice ya tsaya a wajen Wakin, kusan mintuna talatin yana tsaye yana jiran ta.

Fitowa tayi Wauke da wata shigar ta daban, kamar ba ita ba, shigar jikin ta ba kace musulma ce ba.

Kallon ta Yusuf ya tsaya yanayi duk wani ilahirin surar jikin ta seda ta bayyana, Farar fatar ta se Waukar ido take.

"let's go" shine abunda ta cewa Yusuf, haka yabi bayan ta zuwa inda motar su take, nan ma ma'aikatan ne suka kuma biyo ta suna mata Fatan Alkhairi, gaban motar ta buWe ta Webo kuWi bandir bandir ta basu, ta shige motar Yusuf yaja motar.

Wani ?aramin kati ta mi?awa Yusuf, kwatancen inda gurin partyn yake ne, shi sam ya manta tace ze kai ta gurin birthday ne, ga yamma tayi sosai, se dai bashi da ikon magana haka ya bi kwatancen.


"Hello ranka ya daWe, bayan tsawon shekaru yaufa tazo gidan gona"

"Me tazo tayi?"

"Nima ban sani ba YallaSai"

"ta fita da wani abu daga gidan ne?"

"A'a bata fita da komai ba, kaya kawai ta canza sannan ita da wani matashi suka zo yana tu?ota"

"Direban tane kokuma waye?"

"Gaskiya ina tunanin ba direban tane ba kawai, dan a biye yake da ita, har cikin gida duk inda ta shiga yana binta"

"Good, ina so aje anemo min waye wannan matashin, me yake yi a tare da ita, Akwai yuwuwar ze mana Amfani"

"shikenan Oga an gama"

*******************

Koda sukaje gurin birthday Win a harabar wani katafaren gida, da ganin yaran da suke shiga suna fita a harabar gurin kasan sun ji?u da kuWi, fitowa Widad tayi daga motar, Yusuf ma ya fito ya kulle motar.

Wata 'yar siriryar Murya suka ji tace "hey beb you are here?"

Da sauri Widad ta juya suka rungume juna da matashiyar Yarinyar da zata yi sa' ar Widad, suna murmushi

Widad tace "Happy born day baby"

"Thank you sweetheart"

Wani matashi ne ya biyo bayan Yarinyar ya kalle ta yace
"Sweetheart who is this beb?"

"She's My best friend in UK, we take part in the same school, She's Alhaji Nasir daula's daughter"

Ta kalli Widad tace "Baby wannan cousin Wina ne"

Matashin yai murmushi yace "wow Nice to meet you baby"

Ya mi?a mata hannu da nufin su gaisa, Amma cikin zafin nama Yusuf ya saka hannun sa a na Matashin wanda hakan ya hana Widad gaisawa da Matashin.

Kallon sa sukayi gaba Waya da mamaki, Widad kam mazewa tayi kamar ba taga Abunda Yusuf yayi ba, suka nufi gurin da ake Shagalin birthday Win.

Yusuf bin bayan su yayi, Nurat ta kalli Widad tace

"Beb waye wannan ne wai?"

"Why are you asking?" Widad ta tambaye ta

"Abunne ya bani mamaki, nasan baki da brother, Amma me yasa ze miki haka? Lallai kinyi sanyi ko kin fara sauka daga kan A?IDAR taki ne?"

Widad ta girgiza kai tace "babu abunda ya canza, sedai kin san komai na Widad a lissafe yake"

Jinjina kai Nurat tayi tace

"Wannan ma cikin lissafin ne kenan?"

Widad tace? "Maybe"

Nurat tayi murmushi tace "You are wonder lady"

Sukayi Murmushi suka nufi kan stage Win, Widad na Hawa kan stage Win tare da Nurat aka Wauki tafi ana shewa.

Cake Nurat ta yanka, aka dinga tafi ana ihu, tare da wa?o?in birthday.
Kyautar Mota Widad tayi wa Nurat, a matsayin birthday gift, gurin ya hagirtse da shewa anawa Widad kirari, suka shiga cashewa a stage din nan kaman ba yaran musulmi ba.

Kiran Yusuf akayi a waya, ya fita waje domin amsa Wayar saboda hayaniyar da take tashi a gurin.

Yana Waga wayar yasa a kunnen sa tare da yin Sallama

"Idan har kana son tsira da Rayuwar ka, to ka tafi ka bar gurin nan a yanzu, in ba haka ba ko kai ko UwarWakin naka Waya ze iya rasa ransa"



SHARE PLEASE =?O?=?O?=?O?

Ayshercool
07063065680

_*A?IDA TA*_







PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*A?IDA TA *

I dedicated this book to my Mum???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

_Ha??in Mallaka ?& : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ?unsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani Sangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
_
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends



? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?? PART1
? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? Page 7




Da sauri Yusuf ya koma gurin partyn ba tare da fargabar komai ba ya shiga kutsawa yana neman Widad, amma babu ita babu alamar ta a gurin, can ya hango Nurat tana ?o?arin fita, seda ya bari ta fito daga gurin party, sannan yabi bayan ta a guje ya sha gaban ta, seda ta tsorata da ganin sa ta Wan tsaya ta kalle shi tace "Are you ok?"

"Ina Widad?" ya jefo mata tambayar

"ban sani ba na barta akan stage tana rawa" tai maganar cikin wata irin gurSatacciyar hausa.

Subhanallah shine abunda Yusuf ya furta, yai gaba yana sake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login