Showing 36001 words to 39000 words out of 93691 words
dan ɗa gyar muta ne suka yadda na ukun yarasu sa ka makon harbinsa da akayi dan sun ce muta ne uku ne. Jita yi jiri na ɗibanta a haka ta suma, dan kanta ta farka bayan wani lokaci, a firgice ta yunƙura tsaye badan an kulle ta ba da sai fa fi ce daga gidan, kuka ta sha sosai sai can ta samu natsuwa tana kallon agogo wanda ke nuni da ƙarfe 5pm na yamma, toilet ta shiga ta sakar ma kanta shower ta na mai tunanin abin da ya janyo kusu wannan mugun ƘADDARA.
END.
𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶
[6/28, 09:05] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪
ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️
𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈
ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ
✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿
Typing
Page 27.
Flash back
Ita marainiya ce kahu ne ya tsinci ta tin tana jaririya, sai ya kaita rigarsu can ƙasan ƙauye malam auta, ko da ya kai yarinyar sai da suka samu saɓani da matarsa Adda wacce yaronta ɗaya mai suna Mus'ab, to da yake Adda na ta tausayi yasa ta yadda ta amsa jaririyan wacce ke ta tsala ihu, da madarar shanu suka raini yarinyan wacce suka raɗa mata Sakeenat, kahu mutum ne mai son karatu dan haka yasa rayansa makaranta, a haka kullum suke wahala gurin fitowa daga ƙauye zuwa makaranta dan sai an shiga cikin gari ake samun makarantar ma su kyau, a haka suke lallaɓawa har suka gama secondary sai ya sanya su makarantan koyan na'ura, da ya ke ita Sakeenat Allah ya bata fasaha sosai sai ake ta ma ta jumping daga low level har high harma ta wuce tabar yayan na ta, sannan a lokacin suka bar rigan suka dawo cikin gari suna rayuwa, ɗan Sakeenat ba makaranta kaɗai ba hatta wasu da ga wani guri sukan kawo mata aiki, kaman in ayi ma mutum hacking account ɗin sa, ko bank ta samu matsala ɓarayi to akan ne me ta ɗan warware cases ha ka, A wata ranan Jumma'a ranan da ita ce silan rugucewan komai na rayuwan su, mota ce me ɗauke da tambarin EVANT INTERNATIONAL SCHOOL a jiki bayan motan ta zo wucewa da matuƙar gudu, Adda wacce ta je byuɗe account a bank sai ta yi mantuwa passport dan hakan yasa ta miƙo hanya cikin sauri sauri, ta zo tsallake titin kenan wannan mota ta taho da mugun gudu, take suka yi ciki da ita, ganin ya kaɗe mutum yasa motan ta tsaya, gaba ɗaya student din suka fito, ganin mace kwace cikin jini, da yake safiya ce ba yalwan muta ne sosai, Driver din ne yasata cikin napep tare da bawa me napep din kuɗi daya kai ta asibiti, sanann ya koma motan tare da cika umarnin ƴan matan daya ɗauko, yaso ya kaita asibiti amma sun ishe wai yabarta gudun ƙar susa a koreshi a aiki yasa ya ta da motan, Me napep ya jaita wani asibitin gomnati sukuwa suka ce dole sai an fara biya kuɗin komai tare da ɗauko police saboda accident ne. Me napep anfani yayi da wayar majinyanciyan ya ƙira number ɗaya gani a farko an sa My SK. bugu biyu Sakeenat ta ɗauka, basu yi wani gausuwa ba ya faɗa mata komai a matuƙar rikice taje asibin tana isa suka hadu dashi me napep din, labarin komai ya bata yana sannan ya wuce, gurin Adda tanufa wacce ke kwance cikin jinin dan harsun bubbushe, haka Sakeenat ta dinga zage asibiti da Adda tana rogon wanda ze ceci ranta amma kowani Doctor ta samu sai su zulle, haka ta samu ta zauna tana kallon Adda, sai a lokacin ta kira Kahu da Mus'ab, cikin minti 30 sai gasu, su kansu yadda su ka ga Adda sun san babu rai ajinta, basu ɓata lokaci ba suka nufa gida da ita aka mata sutura sannan aka kaita zuwa ga makwancinta, Sakeenat ta sha kuka kaman ranta ze fita, ana kwana uku da rasuwan sai Sakeenat ta nufi makarantan, da ta je da ƙyar suka bari ta shiga ciki, head office ta fara zuwa, tana nan ta yi mai complain akan abin da ya kawato buɗan bakinsa sai yace "Ranta kike so mu dawo da shi ko mene? Malama nan kasuwanci muke yi za ki iya tafiya." Ba ta yi mamakin jin haka dan tafahimci tin shigorta irin kallon da yake mata. A daidai nan ƙararrawan makarantan ta kaaɗa in da ɗalubai mata suka dinga fitowa daga classis, dan mata ne zalla, musulmai da Chirstans ne amma dukkansu babu wanda ya sanya Hijab ɗaiɗai ne masu hula. tafiya ta farayi tana mai kallon makarantan dan ya matuƙar burgeta, ko da takusa fita sai ta hangi school bus guda 5 a parking lot, sai ta nufi gurin tana zuwa tayi ma ɗan tsohon da ta gani magan bayan ta gaida shi ya amsa
"Sir pls ƙasan drivers din motocin nan?"
" Eh Madam nima ɗaya daga ciki ne, lafiya?."
" Eh lafiya, akwai wanda ya kaɗe wata mata 3dys back, shi na ke ne ma." take jikinsa ya yi sanyi tare da dabur ce wa
" Ni....ne me yafaru." kalman 'nine' sai da ta ji wani irin a hukunta take ta kulle idanuwan ta sannan ta buɗe duk sun sauya launi, zama ta yi gyefansa da taga wani kujera.
" Kai ne ka kashe min Mama, sannan katafi kabarta a gurin, naje asibiti na dinga yawo da ita sunƙi amsa ta harta mutu, ba wai kuɗi ne ban da ba amma sunƙi ma amsan ta gaba ɗaya." ta kai magana tana share kwalla, shima kuka ya fara yi yana tsugunnawa har ƙasa yana mai ce wa
" Wlh ba da sona ba ne, ki ya femin ina cikin motan yaran ciki sun sani gudu, ga complain da suke tamun banyi au ne ba na kaɗeta, na so na kaita Asibiti amma yaran suka ce abakin aikina shine na ba da kuɗi don a kaita."
" Bangane ba? suwaye yaran ?" Ta jero mai tambayan bayan ta ɗaga shi daga tsugun nan.
" Eh student's ne amma wani ban zan tsari ake dashi ba'a tankwarasu, harda teacher's ni kai na badan banda wani sana'ar ba ta tuni na bar makarantan."
" Hmmmmmm yara ne su?"
" A'a sun ta sa teenagers ne."
" Zan kai ƙara koto dan haka sai ku jira sammaci" ta miƙe tsaye daidai nan P.C ya iso gurin yana mai ce wa
" Kotu, kotu kika ce, to Allah ya kaiki lafiya, masu gadi ku min waje da ita" haka yasa masu gadi suka koreta da cewa kar su kara bari ta shigo. Samun guri ta yi ta zauna tana kuka sai bayan da ta gama sannan ta wuce, a hanya ta ga station ba dan ta shirya ba ta shiga ciki, gaishe da wani ta yi sannan ya ta zauna gurin wani ta wanda ta faɗa mai komai, amma dajin sunan makarantan ya ce ta yi haƙuru makarantan na Babban Barrister ne, kuma makarantar masu kuɗi ne faɗa da su babu riba, duk hanyar da tabi sai tozarci da hulaƙanci, haka ta koma gida jikinta babu ƙwari, zama tayi kusa da Mus'ab tana mai ce wa
" Yanzu shike nan wa'inda suka aikata sun sha, dukda yara ne amma ai sun san rai dai."
" Ki ya ƙuri kinji mubar maganan." hawaye ne yaci gaba da sauka akan fuskanta, jin abin da ya ke faɗa, take hankalinsu ya koma kan TV dan jin Rash ne yauma ya sheƙe wasu, take brain ɗin ta ta hasko mata abu a ciki, sai tasaki murmushi tana kallon Mus'ab, shima da mamaki ya ke kallon na ta sai tace
" Na sa mu Idea akan abin da zan aikata akan wancan makarantar."
" Me ke nan SK?." take ta faɗa mai yadda brain dinta ya mata huɗuba, sai yaƙi yadda saboda tsoro amma sai da ta samu ta shanyo kansa, haka Kahu shima, aikuwa washe gari ta koma makaranta, sun hata shiga amma sai da ta haɗu da tsohon nan, bayan sun gaisa ya ce da ita
" Ƴata ni yanzu na ma fara azumin kaffara, ki ya ƙuri banda kuɗin da zan biya diyya."
" Ni ba dhi ya kawo ni ba, na kai case din kotu kuma sun amsa sai dai na yi wani tinani kawai abu ɗaya nake so in kamin shike nan komai ya wuce." har jikinsa ya fara rawa, cikin karkarwan murya ya ce
" Ina...jin..ki." sai da ta yi murmushi sannan ta ce
" Sunayen yaran dake cikin motan kawai nake so tare da numbers dinsu, zan bi gida gida gurin iyayensu."
"Ranan su 30 ne kawai sai dai Madam yaran ba suda tarbiyya, a ganina iyayen ma basu dashi."
"Karka damu." daga haka ya koma makarantan, cikin minti 20mnt ya dawo tare da ba ta takadda,
" Da ya ke akai file dinsu shine na kwafa miki, Nagode Nagode."
" Ni ce da godiya, dukkan su suna da wayoyi koh?."
" Eh Madam manya manya ma kuwa." sallama suka yi ta koma gida abinta. Bayan isha'i ta zauna da system dinta tare da bincike akan ko wani number anane tafahimci gaba ɗayansu yaran masu kuɗi ne sosai, ko da taje gidan wasu daga cikin sai hulaƙanci da cewa ai Driver din za tabi ba yaran su ba, hakan yasa ta shirya babban plan akansu, wanda cikin fasaha da kwarewa ta yi shi.
A yau Laraba shine ranan da ta zaɓa. Zaune ta ke a cikin wani hole in da ya ƙawatu dan ta kashe kuɗi sosai, ƙarfe 11:30pm dai dai, yara students suka fara shigowa ciki, nan danan suka haɗu a cikin gurin in da ya ƙawatu ga kuma abubuwan sha iri iri aikam suka sha dan wanda ke bakin get din gurin ya ce har Zee ta zo amma ta je ta dawo, can sai ga Zee Ita ma ta zo aikuwa gurin ya hau shagali kaman me, suna rawa jiri-jiri na ɗiban su a haka duk suka zuɓe agurin, fitowa SK ta yi tare da Mus'ab sai Kahu, nan take suka kwashe dukka yaran suka sanya su cikin babban mota, sai wani ɓoyayen gida wanda ba'a gama ginawa ba, anan suka yi komai harda video akan Garkuwa da Rash ya yi sannan suka watsa a duniya, suku ma yaran da suka farka kowa ya bada number babansu, a take sa ƙo ya shiga akan gobe ake da ɓugata tw Million akan kowa, sun san kuɗin be yi yawa ba duba da iyayensu na su masu kuɗi ne sosai. Ko da washegari ta yi duk SK ce ta haɗa komai, tare da ɓoye sunan account din da suke sa kuɗin, tayi wasa da hankalin muta ne sosai, dan in dai na'urace dole a sara mata. sannan kuɗin ko da suka shiga direct gidan marayu suke zuwa da wasu ma ta sa ƙarfi, na ƙauyuka, da gidan talawaka sai dai su yi ta ganin ɓoyayyen alart na maƙudan kuɗaɗen. Sai gashi anyi ram da su, amma ta san akwai wani, wani can wanda ke bibiyan na ta, wani mayen na'ura, shine ya yi mata tarko kuma ta faɗa dan ƴan sanda ta wuce hasashen su da tinanin su.
END.
𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊
[6/28, 20:59] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪
ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️
𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈
ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ
✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿
typing....
Page 28.
Continuous
Wankan ta gama sannan ta fito daga bayin gurin kayansa ta buɗe, wando da riga ta ɗauka ta za ɓa wanda zai yi mata ta sanya sannan ta koma Parlour tana mai bin ɗakin da Idanuwa, sai ta koma gurin window tana hangen compound din gidan iya in da take iya hange, mamaki ne ya kamata amma sai ta share ta koma Parlour ta yi zamanta tana mai ƙurama wani guri ido ko ƙaftawa bata yi, sai misalin 7pm na yamma ta jiyo jiniya na motoci, sai ta koma tana leƙe, a ranta tana cewa 'wai dama nan gidan Governor Aliyu Haidar abdulqadir ƙanƙara ne, wow'. Jami'ai ne ta gani sun kewaye gidan, shi kuma shugaban gayyan ya shige ciki tare da matarsa wacce ta sanya kayan police, jita yi an cire key ɗin ƙofan, ta ma san wane ne, me dakin ne ya iso, aikam yana shigowa ya kulle ƙanshin tirarensa taji ya doke ta kaman ba tin a station ya shirya ba, karaf idanuwan su suka haɗu guri guda, take zuciyarsa ya tsinke, a hankali ya furta
" Na same ki lafiya?." Kai kawai ta ɗaga mai, sai ya shige bedroom, yana shiga ta fito ta dawo ta zauna a kan kujera ta na ta tunani kan taya zata samu na'urori dan na ta duk yana wajen ASP wanda ba ta san sunan sa ba, sai bayan ya yi wanka ya fito, shima zama ya yi, sai ta zame zuwa ƙasa tana ce wa
"ASP wani aiki zan ma ka sallame ni da wuri dare ya nayi."
"Babu in sa za kije ai." ya faɗa da kakkausar muryansa mai daɗin gaske. jitai kaman ba ta ba ta fahimci abin da yace ba, sai taji ya ci gaba da ce wa
"Ina da wani surprise da zan minki yau." haɗe fuska ta yi sosai, ranta in ya yi dubu ya ɓaci ace ƴan uwanta an kamasu amma yana ce mata akwai surprise da ze mata, gani take komai na duniyan sun isheta dan ma ta na da karfi hali, ya dai taimaketa dan haka ta ayyana ba ra dai ta ga iya gudun ruwa shi dai, Nan take yaji an fara Knowcking kafin ya ce komai aka buɗo aka shigo dan ne sa key ba, da idanunta ta bi su cikin mamakin da ya cinyeta, sai da ta iso tsakiyar Parlourn ta buɗa baki ta na ce wa
"Yaya Umar, me wannan matsiyaciyar take yi anan? harda sanya kawayanka? Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un."
Be ba ya amsa ba, domin be ma san me ze ce mata ba, yasan be kyauta ba daya barta a cikin ɗakinsa kuma su biyu amma be ka mata Fatima ta furta haka ba, be ka mata tayi mai mugun zargi ba, Idanuwan sa ya lumshe sai ya buɗe da sauri dan jin ƙaran mari Tas, ya za ci Fatima ce ta mari Sakeenat sai ya ga saɓanin abin da yake tinani, Sakeenat ce ta dallama Fancy mari, idanuwanta ta ƙara waresu, sannan ya ga tana naɗe hannun rigarta tana ce wa
" Maimaita naji, wace ce matsiyaciyar? Ki kiyaye harshen ki ko na murɗe muki wiya, ba'a zagina a kwana lafiya." Takai maganan tana tsayawa gabanta wanda sun haɗe, sun haɗa kafaɗa, sai dai Sakeenat doguwar ce dan ta bi Fancy tsayi, itako Fancy marin ya shige ta sosai, ga hawaye da suka cika idon na ta, ta so Zaki ya yi magana amma ya yi tsit hakan yasa ta yi ƙwafa da ƙarfi ta fice da cikin gudu-gudu...
*************** *********************
Tin bayan wayan da suka yi cikin daren jiya, ta ƙudurta washegari za taje don ganin ƙawarta don ta ce mata tana son ta zo suyi wani sirri, bayan ta kammala aiki har abincin rana sannan ta shirya ta yima Maman Rabi sallama ta ɗauko hanyan milinium city, ba ita ta isa ba sai ƙarfe 1:12pm, tana shiga sai data yi sallah sannan suka hau hiran yaushe gamo, kaman ba kullum suna tare a waya ba, jin yau za'a tsai da ranan auranta ta re ta biyan sadaki yasa ta yanke ce wa anan za ta kwana kawai sannan taje ta nemi mara kunyan da ta faɗa mata ɓakan magana a waya jiya. tare suka ci abinci a daining area, hira suka sha sosai a yinin ranan, Ramlat tayi-tayi takwarar ta faɗa mata maganan da za suyi na sirri sai tace ta bari washegari kawai. tin jiya rabon da suyi waya da Zaki, sai misalin 6pm ya kira bayan sun gaisa ya ce ma ta
" Yanzu Pazars sun ƙira ni akan an tsaida 3 mounth, har sa da ki sun biya naji daɗin yadda suka ce an karramasu na gode Babyna" sai da ta yi murmushi sannan ta ce
"Allah sarki ba damuwa, Allah ya nuna mana, Ni ma ai nice da godiya."
" Hmmm na so zuwa yau amma gobe zan zo, tare da surprise da zan miki."
" In ka so kagan ni yau za ka ganni dan a gidan ku zan kwana, in ka samu time ka leƙo kawai Part ɗin Babban yaya."
" Wow ma sha Allah, ki ce kin zo gurin matar Boss kenan."
" Uhmmm " Daga haka suka ra bu, amma bayan minti 30 sai ya kuma ya kiranta tare da ca mata, dan Allah an jima ze kira ta sai suzo da matar Boss ya nuna mata surprise ɗin, da harta mu sa amma sai ta amince tinda su biyu ya ce suzo kuma ya ce baze iya zuwa da surprise din ba ne. suna idar da Isha'i suka sha hijabai sannan suka fita bayan Ramlat (Kifaty) ta sanar ma Babban yaya ta waya kuma ya yadda. sannan suka fita ta ainiyin ƙofa fyuta suka fara tafiya suna hira, guards sai gaishe su suke yi, compound din abin sha'awa duk da dare ne amma gurin aikwai watan haske sosai ga muta ne ba laifi, sai dai suka sha za gaye da ƙafafun su, suna hira abinsu gwanin sha'awa dan ƙawance su ya koma ƴan uwan ta ka.
End
ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ
✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿.
[6/29, 19:26] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪
ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️
𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍
𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈
ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ
✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿
Page 29
****************** *****************
Ta na fita sai Sakeenat ta juyo ta na ce wa " Wace ce wannan yarinyar? shi ya sa nake ta ce mata ka sallame ni ina son na tafi, akwai abubuwan da nake so na yi gaskiya." Be tanka ta ba ya ci gaba da kallon TV abinsa sai da ta kuma magana shine ya jiyo ya kalleta kallo irin na ƙurulla
" Ko ka bar ni na fita ko kuwa na fice da kaina, na iya gudu,