Showing 69001 words to 72000 words out of 124287 words

Chapter 24 - MAJANUN HAUSA NOVEL

18 Nov 2024

16697

me nake shiryawa.

Na samu na had'a kudi dubu dari da saba'in wanda zan sayi kayan aikin da zan had'a mata gado da kujeru, da yake duk na iya komai, tunda sana'ar gidanmu ce, bisa tsautsayi na shiga da kudin gida, ashe Fatima taga lokacin dana d'aga kasan gado na ajiye kud'in! wallahi a daran na shiga wanka ta kwashe kudin, kwabo bata bari ba, tana zaune a falo na fito daga wanka na same ta, na ce" Ke kuma zaman me ki ke baki kwanta ba"

A sanyaye ta ce" Yanzu Ummana ta kira ni a waya bata da lafiya sun tafi ma asibiti! kasan tana da ciwon suga to shine ya tashi a daran nan.

Cikin alhini na ce" Allah sarki! addua za kiyi mata Allah ya bata lafiya."

Ta amsa da ameen kafin ta ce"Don Allah ka bari na je tunda dare beyi ba kaji kuma babu nisa a tsakaninmu"

Ganin yanda take had'ani da Allah da annabi yasa jikina ya mutu! na ce ta tashi taje Allah ya sawwak'e! aikuwa da saurin gaske tasa hijabi ta kama hanya fita.


Har 'karfe goma sha biyu da rabi bata dawo ba, hakan yasa na rufe gidan, domin zuciyata ta aiyyana min cewa a can zata kwana.


Har ga Allah ban kawo komai a raina ba, domin sai sauri nake na shirya na fita don gabatar da uzurirrikan dake gabana, ciki kuwa harda zuwa gidansu Fatima domin duba jikin mahaifiyarta


Sai dai me ina d'aga kasan gado da niyyar d'aukar kud'i na ga wayam! hankali ya tashi ainun! na sauke katifar gabad'aya tare da karagar gadon wai ko sun fad'a 'kasa! sai dai duk iyakar dubawar da nayi ban ga komai ba sai tarkace da 'kura!

Na zube kasan d'akin kaina na wani irin juyawa! tabbas ba kowane ya d'auki kudin nan ba sai Fatima domin na riga na san halinta ciki da waje, amma ya akayi ta san na ajiye kudi a k'asan gadonta, tunda lokacin tana kicin tana aiki.

Da 'kyar na rarrafa na fita zuciyata cike da damuwa da tunanin faruwar al'amarin.


Sai da na samu saukin aiki tukkuna na kira wayarta nake tambayarta, duk da ina da tabbacin ita ta dauki kudin, amma sai na tsinci kaina da tambayarya, kawai sai ta fashe da kuka da fad'in" Kullum idan na nemi abu na rasa a gidan sai na dinga zarginta, ina d'ora mata sata, alhalin ita bata kwana a gidan ba, gaskiya ita ta gaji da wannan abu.

Kashe wayar kawai nayi na rabu da ita, domin dai gabad'aya kaina ya k'ulle na rasa irin tunanin da zanyi.


Ko da na shedawa mahaifiyata halin da ake ciki, ta ce nayi hakuri kada na sake maganar, abunda ya samu ayi haka.

Na ce"Mama yanzu haka za a kai yarinyar nan gidanta babu gado? hakan kamar bai da ce ba, kuma kin ga daga b'angaran mu ake samun matsala! a kowane lokaci bai kamata a sake d'aga bikin nan ba"

Ta ce" Ba za a d'aga ba insha Allahu. za a yi abinda ya sawwa'ka idan ya so da kud'in sadakinta sai a saya mata katifa, ni kuma da 'yan uwana za mu had'u mu saya mata labulaye da kayan kicin, zanin gado da sauran abubuwan bukata"

Na ce" Amma Mama ba haka naso ba wallahi, kuma ina da tabbacin cewa Fatima ce ta d'auki kudin nan.

Ta ce" Tunda na ce ka bar maganar to kada ka sake tayar da ita.

Ajiyar zuciya na sauke da fad'in" Shikkenan Umma Allah yasa mu dace." Ta amsa da "Ameen ya Allah.


To a takaice dai haka aka aurar da Sadiya babu gado ballanatana kujeru, hakan yayi wa zuciyata ciwo sosai da sosai, amma na kudire a raina cewa; duk sanda na samu faraga zan sharewa yarinyar hawaye.


Sosai na shiga takatsantsan! da Fatima bana yarda na shigo da kudi gidan, ballanatana ta gani ta d'auka, amma ban d'auki matakin komai a kanta ba, kawai na zuba mata idona, cikin zuciyata nake mata adduar shirya a gurin Allah.


Cikin watannin da suka gabata, gabad'aya ta sauya hallita lokaci guda tayi wata irin 'kiba da haske na d'aukar magana, fatar jikinta tayi luwai! bayan manya-manyan sutturun da take sanyawa, haka zan dawo gidan na samu tayi abinci mai rai da lafiya, bayan kayan d'aki da ta sanja sabbi irin na company, abin ya dame ni sosai! na zaunar da ita ina tuhumar ta, ta ce" Business suke da Jamila.

Na ce "Wane irin business ne wannan da yake kawo muku wannan mahaukatan kudi haka? kuma bana raba ki da Jamila ba?"

Ta ce" Order kayan kicin mu kayi daga india, kuma babu yanda za a yi na rabu da Jamila domin abokiyar rufin asiri na ce."


Na ce" To naji a ina ki ka samu kud'i? har ki ka fara kasuwanci?"


Shuru tayi. Na ce" Yanzu kin tabbatar da zargin da nake miki ko?"

Ta'be baki tayi ta ce" To meye ai gashi nan, ni da kai muna cikin jin dad'i! lokaci guda rayuwarmu ta sauya, amma da ka tattare kud'i zakaje kayi gwaninta"

Takaice ya rufe lullubeni, na ce" Saboda na rufawa 'kanwata asiri shine gwaninta, Fatima anya kuwa kina da hankali?"


D'auke kanta tayi tana surutai! zuciyata tayi zafi sosai! amma sai na daure ban yi mata komai ba na tashi na bata gurin, zuwa nayi na kwanta domin samun nutsuwa, kwana biyu sam bana jin dadin jikina, ciwon kai mai tsanani da jiri, dole dai ko ina so ko bana so naje asibiti likita ya duba ni.


Likita ya tabbatar min da cewa jinina ya hau sosai! dole ne kuma na kiyaye shiga damuwa da gujewa duk abinda zai janyo min 'bacin rai! kuma na dinga samun isashen bacci!

Banyi mamaki ba, domin na san halin da nake ciki zan iya kasancewa a jerin masu 'karancin lafiya, na tabbatar da cewa; hakan baya rasa nasaba da tashin hankalin da Fatima take jefe rayuwata a ciki.

Akan magani aka d'ora ni, na dawo gida ina bin ka'ida, amma na san hakan bashi ne maslaha ba, samun lafiyata yana da ala'ka da Fatima.

*MAJANUNI*
75&76
To ko da taga ina shan magani, bata tambaye ni dalili ba, sai rama nake a tsaitsaye, babu abinda ya dameta, sai narka 'kiba take tana gogewa tare da tu'ammali da sutturu na alfarma, babu wanda zai ga Fatima a lokacin ya ce ita d'in matata ce domin tafi kama da matan hamshakan masu kudi sosai abin yake damuna tare da cin rai! don haka sai na samu iyayenta da maganar, kan cewa su binkici a ina take samun kud'i, domin abinda take yayi yawa.

Bud'ar mahaifita wato Baba Auta sai ya ce" Halak take nema domin shi yana da labarin komai, saboda haka kada na sanya mata ido ko nayi mata ba'kin ciki, tunda dai ni bani 'kwakw'kwarar sana'a to babu lefi don ta nema duk rufin asirinmu ne.''

Wannan shine abinda Hajiya ta maimaita domin itama tayi goyi da bayan Fatiman.

Sai kawai na tattara na rabu dasu, amma duk sanda na dawo gida ta kawo min abinci, wanda nasan bani nayi cefenan ba, to bana ci haka zai wayi gari ta d'auka ta bawa almajirai tana surutai irin na rashin kunya.


Duk da shan 'kwayar da take hakan bai hana Allah Zartar da ikonsa ba, ciki ta samu, kuma bai tashi bayyana kansa ba sai da yayi wata hud'u a jikinta sannan ta gane cewa tana da ciki lokacin da taje asibiti likita ya tabbatar mata da watanninsa.


Halin damuwa ta shiga mai tsanani! ta daina walwala a gidan, kullum idan na dawo daga gurin aiki cikin damuwa nake samunta, har dai na gaji na tambayeta, kawai sai ta fara min rashin kunya tana k'okarin zagi na, wai ba zata sake amincewa da bu'katata ba.

Na ce" Duk me ya janyo hakan?" tana kuka ta ce" Ciki ne dani watansa hud'u harda kwanaki."

Na ce" Na gode Allah! yanzu kin tabbatar da cewa; ba a yiwa Allah wayo ko?"

Tayi shuru tana kallona, na ce" Duk abinda ki ke a gidan nan ina sane, nasan cewa kina amfani da k'wayoyin hana daukar ciki, amma na zuba miki ido kawai, saboda kin fi k'arfina Fatima, amma yanzu Ubangiji ya nuna miki cewa baki da dubara."


"Wallahi sai na zubar dashi" tafad'a tana gurshe'ken kuka! na ce" To babu lefi sai ki d'aura d'amara" tashi nayi na bata guri, domin ina kallonta zuciyata zata iya tarwatsewa saboda b'akin ciki!


Bayan kwanaki shida da faruwar al'amarin, na fita gurin aiki da kamar minti talatin, sai kawai na gilmawar mota ta wuce ta gabana. babu shakka Fatima ce a ciki domin ita d'in ba sabuwar hallita bace a gurina, sai dai wacce take tuka motar ce ban gane ba.

Hankalina ya kasa kwanciya domin ba muyi da ita cewa zata fita ba, aiki nake amma gabad'aya hankalina can wani guri.


Daf da mariba na tashi daga aiki na nufi gida domin hankalina ya kasa kwanciya, a bud'e naga gidan, sai naji nutsuwa a raina, domin na tsani yawon dare, amma duk da haka sai na tuhumeta wane guri taje d'azu!

Ina sanya 'kafa ta a d'akin na ci karo da wata leda viva! a bakin k'ofa, ban kawo komai a cikin raina ba, na shiga dakin na sameta a kwance duk tayi zuru-zuru!

Na ce" Fatima ina ki kaje d'azu?"

Shuru tayi min, sai da na sake maimaita tambayata tukkuna ta ce" Wani guri na je" na ce" Kin gaya min zaki fita ne?"

Ta girgiza kai. na ce" Ina ne wani guri? ko bashi da suna"

Zum'bura baki tayi ta ce" Ni fa bana son damuwa don Allah ka rabu dani na ji da ciwon da yake damuna"

Na ce" Billahil-lazi la'ilahaillahuwa sai kin fad'a min gurin da ki kaje, idan ba haka ba sai na ji miki ciwo a gidan nan"

Zaune ta tashi tana kallona kafin ta ce" Sai dai kuwa ka kashe ni wallahi domin zuwa nayi na zubar da wannan jarabar daka 'kunsa min, ga d'anka can a leda a bakin k'ofa!

Da saurin gaske na juya ina kallon bakin kofar, ashe abinda na ci karo dashi gudan jinina ne, jikina na rawa na kalleta da fadin" Yanzu sai da ki ka zubar da cikin nan Fatima?"

"To meye amfaninsa, ni wallahi ba zai katse min hanzari ba, domin saudia za mu tafi tare da Jamila zaman shahada"

"Innalillahi-wa'inna-ilahi rajiun! wannan adduar nayi ta nanatawa kafin na samu nutsuwa!

Na kalleta tana zaune turmin danya babu abinda ya dameta, na ce" Da izinin wa zaki tafi zaman shahada?"

"Kai nifa dama na gaji da zama da kai wallahi! dube ka, kullum jiya i yau, babu wani cigaba a tare da kai, ka dube ni da kyau kai kanka, kasan yanzu nafi 'karfinka don haka wallahi dole ka sake ni na gaji"

Na ce"Shine hujjarki na zubar min da ciki?"

"Kwarai kuwa domin ba zan tafi da nauyinka a kaina ba"

Wallahi a lokacin rasa bakin magana nayi domin duk wasu dabaru na sun 'kare, jiki a mace babu kuzari na shiga daki na dafe kaina, hawaye masu tsananin zafi suka shiga kwaranya a saman fuskata.

Koda ta shigo d'akin ta sameni ina zubar da hawaye, ko a jikinta, ina kallonta ta shirya ta kama hanya ta fita tana 'kananun maganganu, cewa ita ta gaji da zama cikin talauci, bayan ban gaza mata da komai ba.


Ashe kukan da nake shafar mai ne, domin ledar gudanan jinin da aka fara yiwa hallita ta d'auka ta nufi can gidanmu, har d'aki ta samu Mamana a kwance tana fama da kanta ta ajiye mata ledar, tare da fad'in" Gashinan an fara yi masa hallita saboda haka sai ayi masa suttura a aje a binne, ita bata shiryawa haihuwa yanzu ba, bayan haka kuma ta gaji da zama cikin talauci lallai ita a sawwa'ke mata, domin ta je ta auri daidai da ita"

Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! ai tana fita daga dakin da 'yan mintina Mamana ta had'iyi zuciya ta mutu, sai gawa muka tarar! likita kuma ya tabbatar min da cewa zuciyarta ce ta buga sakamakon 'bacin ran da ta jima a ciki.


Wallahi na shiga tashin hankali da damuwa a lokacin, domin kamar zautacce haka na dawo, babu ci babu sha! na rasa ina zan tsoma rayuwata na ji sanyi, gashi a lokacin kowa ya san Fatima ce sanadin mutuwar mahaifiyata amma saboda rashin adalci suka ce a lullub'e maganar kada wasu a waje su ji abinda yake faruwa.
Amma Hajiya jikinta yayi sanyi sosai! domin kuka sosai ta dinga yi lokacin da aka fito da Mamana za a kai ta, gidanta na gaskiya sai neman afuwarta take.

Har aka share makoki Fatima bata tako k'afarta gidan ba, daga karshe ma sai samun labari nayi cewa; sun tafi saudia ita Jamila 'kawarta.

A lokacin Hajiya tayi tur! da Allah wadai da halinta, ta kuma kira Baba Auta ta rufe shi da fad'a sosai! da yake 'yar tasa ta toshe masa baki da kud'i ko gezau! bai nuna damuwarsa ba, sai ma ya ce" Shi ya gaji idan auran nan, ba zai yiwu ba to a rabu kawai domin ya gaji da sasanci." Hajiya ranta ya 'baci sosai! a take gurin ta umarce ni dana sake ta, ban jira komai ba na furta cewa na sake ta, na kuma rubuta a rubuce, na bashi sheda! bai damu ba, ya kar'ba tare da buge rigarsa ya ta tashi ya tafi ya bar mu a zaune a gurin cikin tsananin mamaki.

A tsakankanin lokacin sai da na kwanta a asibiti domin tsananin ciwon kai da ya addabe ni, jina ne ya hau sosai! sai da likitoci suka rufu a kaina da kuma taimakon Allah na samu lafiya, na dawo gida da tarin magunguna tare da kokarin cire damuwa daga cikin raina, kamar yanda likitana ya bu'kata.

Wata uku da rasuwar Mamana wani abokina da mu kayi karatu tare dashi a kano, ya kira ni a waya ce maza na zo ya samar min aiki a wani kamfani, amma nazo da takarduna.

Banyi 'kasa a gwiwa ba, na shedawa Hajiya halin da ake ciki, tayi min addu'a sosai kafin na kama hanya na tafi.

Faruk ya dafa kafad'a ta da fadin Abokina insha Allah wahalarmu ta 'kare domin
"Babban kamfanin sarrafa shinkafa ne dake unguwar harad'a suke neman injiniyoyi irinmu, wannan dalilin yasa na kira ka nace maza kazo ko Allah zai sa a dace, domin ni har na fara zuwa aiki cikin satin da ya gabata"

Na ce" Na gode sosai Faruk Allah ya 'kara zumunci" ya ce."Babu komai abokina duk yiwa kai ne.


To shi dama lamarin ubangiji ne yana faruwa ne a lokacin da ba kayi tsammani ba, kuma wani lokacin baka samun farin ciki kai tsaye sai an jarabce ka.

Kasancewar takarduna sunyi kyau sosai! yasa aka daukeni aiki, akan matsayi mai girma! da albashi mai tsoka, kuma da yake shugaban company yana da tarihin rayuwata, wallahi gida ya dauka ya bani tare da abun hawa mota sabuwa mai kyau da 'kwari!

Nayi masa addua sosai da sosai! kuma na d'auki alkawarin yin aiki cikin gaskiya da amana.

Wannan shine mafarin dawowata garin Kano da zama, tare da Hajiya na tare a sabon gidana domin tun bayan rasuwar mahaifiyata take tausaya min, wannan dalilin yasa ta ce " Duk inda nake tana gurin" Baba Auta ya dinga kishi! ya kuma kasa 'boye hassadarsa akan abun alherin dana samu.
'Bangaran Baba Audu kuwa addua yayi min sosai, wannan yasa na dauki kudi masu yawa na bashi. Sadiya ma har gidanta na je na kwantar mata da hankali, na ce duk abinda take bukata ta kira ni, a waya insha Allah zan share mata hawaye! cikin damuwa muka rabu da juna.


***
Bayan shekara biyu da fara aiki na, rayuwa ta sauya min sosai! hankalina ya kwanta domin bani da wata matsala gagarima, kullum cikin nasara nake fita aiki na kuma dawo cikin fatahi!

Rana tsaka Fatima ta kira ni a waya, nayi mamaki sosai! na d'aga wayar muka gaisa, na ce "Ina fatan lafiya?

Sai cewa tayi " Kayi hakuri da abinda ya faru"

Na ce"Shine dalilin kiran?"

Ta ce"A'a" na ce" To ina sauraranki"

Ta ce" Na samu labarin abun alherin da ya sameka Allah ya sanya alheri ya kara d'aukaka"

Na amsa da "ameen ya Allah"

Ta ce"Ka bani address din gidanka zan zo maka da wani albishir wanda zai sanya ka farin ciki."

Tsaki na ja da fadin" Baki da hankali har yanzu Fatima" sai kawai na kashe waya ta na rabu da ita, tayi ta kira ban daga ba har ta gaji ta hakura


Ina tsammanin number wayata ta bibiya har ta samu gidana.karfe takwas na dare sai ganinta mu kayi tare da wata 'karamar yarinya da bata fi shekara daya da rabi ba.


Duka muka zuba mata ido da kallon mamaki a fuskokinmu, kawai sai ta zube kasan kafet tana kuka! tare da rungume yarinyar a jikinta!

Hajiya ta je ta kama yarinyar tana duddubata, sai ta kalleni bakinta na rawa, nima yarinyar kawai na zubawa ido ganin fuskarta irin tawa sak! sai dai bata da haske sosai! gabana ya dinga fad'uwa ina kiran sunan Allah a zuciyata cikin raina naji cewa wannan yarinyar 'yata ce domin kama take da Sadiya 'kanwata.


Hajiya ta ce"Fatima wannan kukan da ki ke bashi da wani amfani, kiyi mana bayanin matsayin wannan yarinyar."


Ta share hawaye murya a dashe ta ce" 'Yarsa ce" gabad'aya muka zuba mata ido.

Ta cigaba da cewa" Bayan naje likita yayi min allurar zubar da ciki, ashe tagwaye ne (twins) kuma d'aya ne ya fita. shima likitan be gane ba, saboda Allah ya 'boye al'amarinsa, sai bayan na je saudia domin fara gudanar da harkokina, kawai ciki ya bayyana, koda na je asibiti domin a zubar, likitan ya tabbatar min da cewa ba zai fita ba, domin kuwa ya riga ya girma, idan kuma na tsananta to zan iya rasa rayuwata, wannan dalilin yasa na hak'ura har na haifeta, amma na shiga damuwa sosai, saboda ina fargaba

29, August 2025
Mohamed Amina Nyam

Pls I want to download

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login