Showing 90001 words to 93000 words out of 99653 words

Chapter 31 - SANADIN ACCIDENT COMPLETE BY FASMA

FASMA   

05 Jul 2024

14099

dauko ta saka a hannunta tace ashe nan na boyeka muka sha wuyar dubaka..cuwat ta mike tana fadin bari na kira babyna na sanar mishi...

Wayarta a palo ta fito ta dauka ..kira na daya na biyu ya daga cikime da jin dadi suka shiga hirar su ta masoya Maysam tace wai kana ina ne kaga wani abu ?

Yace gamu dawo wa daga tarben su Mom. ...to miye za'a gwada min ..

Maysam tace devine quoi?

Seda yayi yar dariya yace to waya cemiki ana fadin gift din dazakayi bawa mutum ai seki bari har zuwa gobe tukon ko..

Dariyar tayi tace to waya fada maka gift dinka ne zan fadama ..

To in bashi bane minene?

Tace yanzun nan ina duba wani abu na ga Zoben nan dana taba baka labari gashi nan ma a hannuna in fadama maka ....

Wata irin faduwar gaba yaji yace gani nan zuwa yanzu in gani kada ki fidashi daga yatsarki ...

Zatayi magana taga shigiwar Murza palon fuskar nan ba annuri kamar kullum ..

Murza tace shigen ciki me taurin kan tsiya irin na ubanka da uwarka ..ashe kananan baka zube duk irin maganin dana baka ...to ai yau gani nan da kai na yau me rabani da kai se Allah..
Itade Maysam cike da tsoro take kallonta kuma tana jin irin maganganun da Murza keyi suka dada tada mata hankali ..Murad de yana jin magana kasa2 aman bayajin abunda ake cewa ...yana ta kira Maysam3 aman ba amsa ..

Ita kuwa Maysam ganin Murza ta tunkarota ta wata wuka tana fadin yau sena kaiki lahira dake da shegen cikin nan yasa ta kwalla wani uban ihu kan kace mi tuni ta zube nan kasa sumamiya (nasande baku matan da yanda Maysam ke tsoron Murza ba)gashi kuma babu bayi duk Murad ya koresu

Jin irin ihun da tayi yasa hankalinshi ya dada tashi gashi kuma da dan tazara kafin su iso ...ya sake kira yaji sweet off

Dan haka ya kira Mahmud ya sanar mishi daya je bangarenshi ya duba mishi Maysam yayi sauri ...

Dayake yana cikin masarautar dan haka da sasarfa ya fice part din..
Yana shigowa lokaci Murza ta kaiwa cinkin Maysam Halbi da kafa ta daga zata kara Mahmud yayi kukan kura ya damki kafar ya cillar da ita can....kafar me lafiya ta bugu da wani karfe kuma kanta ma ya bugu da da wani da center table a take ta sume...


Tana sumewa nima nace bari nayi nan .....

Se mun hanu a next page wanda nake sa ran last page ne.......ina sonku irin dayawan nan kuma ina kara baku hakuri ...❤❤❤❤❤❤😍😍😍😍😘😘😘😘

Nice de taku har kullum


Fassouma ce🖊(yar mutan Zinder)
[9/14, 9:14 AM] A A Dboy: *_POST BY GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100_ 📚📚_*
[9/14, 9:24 AM] A A Dboy: 🌟 *STAR WRITER'S ASS* 🌟✨🖊
( _Home of spécial 🏡&extraordinary writers_ )


🌹🌹 *SANADIN ACCIDENT* 💥🚑🌹🌹

S.W.A✍

🇳🇪Story&Written
by
*FASMA* 🇳🇪

*Sakon gaisuwa dubun godiya da kuma ban girma zuwa ga yan groups din*
ZURI'ARMU FANS2
MEERAH FANS GROUP
UWAR RIKO FANS
KALAR TAWA UWAR FANS
SALMA FANS
NOVEL CAT BY YA-YUSUF
SURBAJO FANS
HAUSA NOVELS
RAYUWATA FANS NOVEL
PLM TRUE LOVLY FANS
GENTLE LADIES HAUSA NOVEL
FATIMA (AS)HAUSA NOVEL
NISA'UL KHAIR
DON AMARIYAR SATIN NAN
BRILLANT NOVEL FANS
NOVELS LIBRARY
ANSHOLLY NOVEL
M.HAUSA NOVEL
AYSH NOVEL
HAUSA NOVEL AYAU
004HAUSA NOVEL BOOK
FANS NOVELS ..
🤣🤣 *kai walahi kuna da yawa fa kuyi hakuri wanda ban ambata ba kusan kuna raina kuma ina yin ku irin more completly totaly din dan ❤😍😘😘* 😘😘




Dedicated to all my fans😍❤😍😍❤❤



🅿111__112
( _First of last page_ )



```Manzon Allah (SAW) yace''marowaci ba zai shiga Aljannah ba ,haka ma mai mako.''
Al-Khatib ya rawaito shi``` .



'' _Dayawa suna korafin sunan Sweetbaby to sunanta MUNIRA ....kuma Maysam yana nufin SWEET,Murad ma yanada nashi ma'anar ..zaku gane komi a last page'''..and kuma ai in kun lura kaf tunda littafi ya fara sunan mutanen_ _cikin yana farawa da 'M'' ne yake kamar su Ma'u,Murtala ,Murza,Musa etc..so ku bini zaku gane don mi na zabi sunan MUNIRA .. Thankx da tambayoyin ku_ .. _dan wanan yana mun nuni da kuna bibiyar book din_ 😍❤❤😘😘


[09/09/18 à 23:31] Mahmud kam gashi likita aman ya rasa irin temakon da ze bata ..kira yayi aka turo nurse din cikin asibitin masarautar..haka de da kyar kafin su iso ya dedeta nutsuwarshi ya shiga neman ceto ta ..ya jima kafin numfashinta ya dawo ..cikin ikon Allah kuwa tana farfadowa nurse din suna shigowa sede mi jini ya ballewa Maysam kamar mi..da sauri akayi emergency da ita kusan kaf doctororin masu fanin haihuwa wato gyneco da kuma sage femme dake asibitin suka shiga dan ceto rayuwarta...

Abunka da gidan sarauta kafin ma Mahmud ya sanar da su fulani tuni labari ya isar musu
Kan kace mi tuni fulani ta iso asibitin ganin Mahmud na kai komo yasa hankalinta kara tashi ..ta iso tana tambayarshi abunda ya faru..nan ya sanar mata tundaga kiran Murad har bugon da Murza tayiwa cikin. Nan ta shiga fadin inna lillahi wa inna ileyhi raji'un tare dayin salati ....se kuma ta bada oder da atafi a kama Murza a kai a kulleta kafin ta kudu ...


A bangaren Murad kam hankalin shi ba karamin tashi yayi ba jin faduwar wayar Mom da suke tare itake tausarshi tana bashi baki kan babu abunda ze sameta ...gudu yasa aka kara dan duk iya hakurinshi ya kasa gashi in ya kira Mahmud din ma baya daga wa ......

Lokacin daya iso direct bangarenshi ya nufa dan yana da yakinin nan ze tarar da ita huyangi nayi mishi bayanin aman be masan abunda suke fada ba shide fatanshi ya saka wifyn shi a ido ..

Ai kuwa abunda ya gani ne ya qara daga mishi hankali dan jini ne kamar wanda aka yanka kaza a tsakar falon ...ga kuma wasu kuyangi suna aikin gyaran gurin ..

Nan suka zube suna gaishe shi aman ko takan gaisuwar bebi ba ya shiga tambayar su ina Maysam ...kasa magana sukayi dan suna tsoron hukuncin daze musu inyaji wanan abun ta bakin su..

Wata tsawa ya daka musu ai ba shiri daya daga cikin su ta shiga yi mishi bayani kan sude sunga an fice da ita asibitin nan kuma tana zubar da jini ..

Be ma bari sun karasa ba ya fice se asibitin su Mom dake bayan shi suma suka mara mishi baya duk da ita ba wani dadin jikinta take ji .....

Tun daga nesa ya tsinkayi su Mahmud harda gudu2 ya hada dan shi yama manta da shi yarima ne bare ya tuna da wata sarauta har ya kai ga tuna da bayi a gurin ....

Ganin yanayin su fulani yasa jikinshi yin sanyi ko ba 'a fada ba yasan wifyn shi ce ba lafiya..da kyar ya hada miyan bakin shi yace Momy ina Wify ta ?miya sameta ?

Fulani kam ta rasa ta inda zata fara mishi bayani..se Mahmud ne yayi karfin halin rumgumeshi yana mishi nasiha kasa2 kan yayi hakuri da komi na rayuwa sanan ya sanar mishi yanda abun ya kasance ..beyi aune ba yaji lema a kumatunshi koda ya shafa yaga ashe hawayene yake Mahmud ya kalleshi yace pls kayi hakuri ai ba ancemaka ta mutu bane addu'ar ka take bukata kuka baze anfane da komi ba...

Kara rumgume Mahmud yayi yace baka ji yanda zuciyana ke mun bane jinake kamar zata faso kirjini idan na rasata nima na tabbatar da binta zanyi ...

Mahmud yana dan bunbuga bayanshi alamun lallashi yace ka rumgumi kaddara kamar ba musulmi ba ...haka kayi lokacin sweetbaby har ka kusa halaka kanka ..pls ka meka lamuran ka wurin Allah komi se ya zo maka cikin sauki. . ...fulani da Mom ma suka matso suna bashi baki tare da nasiha har yaji zuciyarshi ta fara dan saki bisa kulewar da tayi ...

Nan kuma ya tada rigimar seya shiga ..babu muso suka barshi ya shiga ..ai kam seda yayi dana sani dan ganin irin bakar wahalar da Maysam ke sha ....

Duk wuyar data ke sha tana ganinshi ta mika mishi hannu alamun yazo ..ai da gudu ya isa yasa guiyoyin shi kasa tare da rike mata hannu ...idon nan nashi yayi jajur alamun yasha kuka kenan ....ita ma ido duk su firfito se zufa take...tana jujuya kai kukan ma yaki zoma ta ....

Likitoci kam kallon ikon Allah suke ..shi yazo ya hanasu aiki kuma shima bayi yake ba da kyar suka lallabashi ya fita a cewarshi ze doko rigarshi ta likitoci dan baze iya barin wify shi itakade ba...

Yana fitowa ya shige office ya doko rigar..ze koma Mahmud da fulani na bashi hakuri kan yabari sauran docto suyi aikin su aman fafur yaki suna haka se kuwa ga Sarki ,M.Musa da kuma Dad suna shigowa asibitin suma .. Nan yaje ya rumgume sarki har da yar kallarshi kan wai su fulani sun hanashi shiga.... kallo daya sarkin yayi mishi ya ga baya cikin nutsuwarshi ..ko ya shiga ma ba wani abun ze iya ba dan duk ya wani gigice .....
sarki ya shiga bashi baki se suma su dad suka shiga zancen da kyar ya hakura de ya zauna zaman jira ..aman bini2 se ya lekata ...



Kaf dinsu babu wanda ya samu ya rumtsa kusan dukansu bisa sallaya suka raya daren suna me rokon Allah ya Tashi kafadarta .bama kamar Murad da M.Musa .ba Kai abu kamar wasa har gabbanin asuba Maysam nacin bakar wuya ..kuma likitocin sun tabatar da nakuda take dukda EDD inta saura two week.......

Wajejen hudu na asuba Murad ya saka farar rigarshi ya shiga dayake duk mata ne gyneco din yasa ya fara rena aikin su acewar shi basu san kan aikin su ba ... ....duk ta gala baita idon wanan shine. Shi kam ba karamar firgita yayi ba duk wata nutsuwarshi ya tattaro da sauri ya shiga dubata ..yaga da dan sauranta kafin ta haihun ..yanzuma..kawai yanke shawara yayi da 'a amata cs dan kada a rasasu su duka biyun dan daga ita har babyn su galabaita .......nan ya bada umarnin a kawo mishi form ya saka hannu kuma shida kanshi zeyi mata dan bayason a samu matsala..(ni kuwa nace dama kai da faninka ne ka tsaya sanya seda ta wahala haka🙄)

Maysam ta dan ji ysoro aman jin shine zeyi mata yasa taji sanyi a ranta.....

Su fulani ma sun tsorata bare da sukaji za'a iya rasa su duka biyun dan bata kai haihuwa ba tsokanota ne akayi kuma gashi Murad ne zeyi ba dan suna shanku be iya ba a'a sede ganin yanda ya bi ya damu ya susuce lokaci guda...

Ba' a dau lokaci ba aka shiryata aka shiga dakin operation din ..shi kadene namiji a ciki duk sauran mata ne ..ko Mahmud hanashi shigowa yayi dan tsabar kishin tsiya(kai Murad a rashin lfyr ma seka nuna kishin🙄).......

Ai kam cikin ikon Allah kamar wanda take jira a shiga har an doko alurar kashe zafi ..nakudar ta taso mata kadan2 ..nan Murad ya dakatar dasu . yana dubawa yaga contractions ne Dama shine kusa da ita ai kuwa wata damka tayi mishi tare da yin nishi akai2 cikin yarda Allah sega kan baby nan har yayi rabi aman mi ita kuma a lokaci ta fara lumshe ido karfinta ya qare.........

Cikin ikon Allah Cike da kwarewa Murad ya zaro shi ya doramata bisa cikin ya durkusa yayi sujudu shukur ..dede kuma lokacin aka fara asalatu dan asuba tayi..zagayo wa yayi yabata light kiss...ai kam yana dubawa yaga da namiji ne . ya so ace mace ce da yayi wa sweetbaby takwara to Amman wa ya isa yaja da ikon Allah haka namijin yayi niyyar bashi ..dan haka yashiga yin tasbihi da godiya ga Allah da sauke Maysam lafiya..lokaci guda wata mahaukaciyar kaunar yaron ta shige shi barema daya ga kamarshi daya da sweetbaby lokacin da'aka haifeta ..kaishi walahi seyace ma itace dan in ya leka ma kara lekawa yake wai kode mace ne dan shi gani yake bama kama ba ce ..a'a sweetbabyn ce ma gaba daya..nan ya shiga sakin murmushi tare da dariya kya3..bini2 se ya bata kiss itada baby ..ita abun ma kunya yake bata.. lokitocin ma sakin baki sukayi suna kallonshi ..

Duk wani gyara shiyayi kayanshi daga nurse za suyi se yace ya gode su bari..doctororin kam ikon Allah suke kallon dan su kansu ba wani barin suba yayi ba sukayi aikin su ...abin mamaki baby bashida komi ma'ana yana cikin koshin lafiya duk wani test yayi mishi aman she is very fine dan ..haka ya saka aka kai Maysam dakin hutu tare dayi mata Allurai ciki harda ta bacci shi kuma ya fito da jaririn a hannunshi direct wurin su fulani ya zo yana doka murmushi suma suna ganin shi suka taryoshi ...hum irin rashin ta idon Murad ko fulani yaki ya baiwashi ...wai acewarshi sweetbabyn shi ta dawo kuma babu me amsarta bare ya rabashi da ita ....

Mom tayi murmushi tace hala macece...

Yana kallon yaron yace a'a namiji ne aman walahi kamar shi daya sak da sweetbaby na ..duba ki gani ..se lokacin ya bude misu shi . .ai kam a tare suka dau kabbara da tasbihi ga ubangiji dan gaskiya kamar har ta bace

Murad yace walahi da macece da sweetbaby zanyiwa takwara kuma ma wani ikon Allah kinga rana guda lokaci guda aka haifosu ..dan shima wanan a kiran asalatu ya fado duniya kamar sweetbabyta itama .....gaban .Mom ne ya fadi nan zuciyarta ta kara tsanan ta bugawa har ta kasa hakura tace ka tabbata na mijine kuwa..
Yana murmushi ya bude musu suka gani ..kowa na wurin se barka suke mishi ..fulani ta tambaye ya Maysam din nan ya sanar musu tana dakin hutu..Mufeeda da Mariam baki har kunne se dadi suke ji suma sun zama uwaye wau...ai nan kowa ya fara rigay2 san amsarshi ..

Hum oga kam shafawa idonshi toka yayi keme2 ya ki bawa kowa .
Fulani cikin fada tace kasan baza mu shirya da kai ba inde har haka zakayi ko . haka lokacin da'aka haifi MUNIRA ka hana kowa ganinta bare daukanta ...to wannan karon kam bazan samaka ido ba..

Turo baki yake kamar karamin yaro shi adole anyi mishi fada aman still yaki basu shi...

Mahmud ya lallabashi da kyar dan har an fara kiran sallah asuba ...badan yaso ba ya bawa Fulani shi se waywayen yake ....

Suna dawowa direct ya nufi amsar danshi su fulani kam se kallon ikon Allah suke shi irin kunyar nan ma ta yan fari baya nuna wa....har sha biyu na safe ba'a fito da Maysam ba tana dakin hutu ya hana kowace nose shiga inba shiba ...fulani ganin har sha biyu yasa tace ni Murad ina dauther nane ko zamu iya ganin ta ..

Babu kunya yace Momy ta gaji dayawa fa shiyasa na mata allurar bacci ...kawai inta tashi zan muku magana se ku ganta .

Ai kuwa fulani ta shiga fada ai so ba hauka bane dazaka hanumu shiga ganinta ...

A memakon ya barsu sema yayi kasa da murya yana fadin Momy kiyi a hankali kada ta farka da yake kusa da dakin suke........

Su fulani kam koma gida sukayi dan kimtsa tunda de yaki bari su ganta..

Mahmud ya ce wai ni ya zancen birtday ne ko an fasa ne..

Wata dariya Murad yayi yace wani birtday ai ni yau wife ta cike mun birtday dina tunda ta haifo mun sankacecen yaro ai kuwa kaga birtday ya qare...sede ko na dagashi har ranar sunan yaron ..tunda shima kaga ranar haihuwar mu daya dashi.. Se a hada

Mahmud yace to ya kake ganin za'ayi da waccar azulumar ne...

Dan danan fuskarshi ta sauya ya dena dan murmushi ma dayake yace walahi badan Dady yace na bari ze dau mataki ba da ni kade basan irin hukunci dazanyi mata. .ai ita so tayi ta kashemun mata da babyna to kuwa walahi ina me tabbatar maka dana rasa daya daga cikin su ita ma da ta bisu ...dan hukuci sak na addinin misulinci za'ayi mata. ..yanda ta kashe da gangan to itama jininta ya halasta..

Nan suka ci gaba da hirar su wanda kusan duk akan Maysam ne da babyn

Dad da Mom kuwa tunda suka koma gidan hankalinsu ya kasa kwanciya gaba daya son yaron ya shige su bare da suka ga tsananin kamar shi da sweetbabyn su...dan ita Mom taso ma taga matar Murad din nan data haifi me kama da diyarta ...


Bayan sallar azahar Murad ya shiga dakin da Maysam take da babyn a hannu...aka koyi sa'a ta tashi sede da gani bacin be ishe ta ba...ganin shi yasa ta sakar mishi da murmushi ...

Matsowa yayi ya kwatar mata da babyn kusa da ita .ta kurawa yaron ido .. doko mata brush yayi bayan ta gama ya hado mata tea me kauri tasha dan dama ya tanadi kayanshi a dakin jiran farkawarta kawai yake .wani irin farin ciki su ji su duka sunma kasa furta komi kawai sun zurawa babyn ido .....
Can Murad ya rankafo ya sumbaceta a goshi yace na gode my lovely Maysam kin gama min komi kin haifamin yaro me kama da sweetbaby ..sede ince Allah ya saka miki da mafifici alheri. Allah ya biyaki da aljannarsa ma daukakiya ....

Ita kanta maysam din wani sanyi dadi take ji yana shigarta bare inta ga baby wai fa itama yanzu uwa ce...se kuma hawaye shar2 ya fara zarya a kumatun ta . .

Hankalin Murad ya tashi ya shiga tambayar menene ?ina yake miki ciwo.?duk yabi ya rude .
Shafa fuskarshi tayi da hannuta tace ina kukan rashin mahaifa nane ,?ina tunanin wani irin laifi nayi masu da ta barni ne?a yanda naji wahar haihuwa yanda take bana tsammani ko shege ka haifa zaka iya jefar dashi........

To fa gaba daya kan Murad ya kulle ya shiga duniyar tunani tomi Maysam tke nufi ne.....

Ganin hka yasa Maysam fadin am sorry babyna yau birtday dinka kaga ko happy birtday banyi maka ba...

Kara rankofowa yayi yace wani happy birtday bayan baban happy da kika mun har da gift din dakika

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login