Showing 54001 words to 57000 words out of 99653 words
din daga baya se musan yanda zamu bullo musu....in su da adiri suka dogara to mu da Allah muka dogara
Nan Mahmud ya bada shawarar ayi ta saukar qur'ani tare da zuwa makarantu su taya su da addu'a...ya kuma cewa muma kuma zamu rage bacci mu zanki rayashi da nafilfili da addu'a ..
Sosai sukayi na'am da shawarar nan .....
Maysam tace Allah ya bamu nasara akansu..nima na samu Mijina ya dawo kusa dani..muyi....
Tsit tayi ganin irin kallon da suke mata ..
Se lokaci ta tuna ashe fa a gaban Surikarta fulani take ..ai da gudu da shige kuryar daki tana dariya ga kunya kamar kasa ta nutse ta shige ..
Dariya Mahmud ya shiga yi mata ...
Fulani na fadin yaki dawo y'a ta ai bama yar haka dake...
Amma ina Maysam ta ware ..
.nan Mahmud yayi mata sallama tare da jaddada mata gobe2n nan zesaka a fara saukar alqur'ani..sanna ya fice.
Fulani tabishi shi ma da addu’a dan a gaskiya samun aboki kamar Mahmud a yanzu se an tona..
A ranar su duka ukku baccin da sukayi kadan ne dan kwana sukayi suna rayashi da nafilfili da addu'a Allah ya basu nasara akan su Murza ya kubutar da Murad da ga sharrin su ...
Love you all
Yawan comment dinku shi ze bani kwarin guiwar yin typing me yawa
Fasma ce
Story&Written
by
*FASMA*
*I miss you my Arfat and my in law Xaynabqueen ..wai ina kuka shige ne kwana biyu ...Allah de yasa you are fine*
Dedicated to all my fans
79__80
```Manzon Allah(SAW) ya ce''wanda duk yayi imani da Allah da ranar lahira to ,ya fadi alheri ko kuma yayi shiru.
Bukhari da Muslim suka rawaito shi..```
[29/07/18 à 18:40] Washe gari Maysam ta fito cikin shirin ta dan jirgin 10 na safe zasu bi . zuwa Niamey daga can kuma su daga zuwa England
Da ka ganta kasan tana cikin damuwa .,,duk ma se take ji kamar ta fasa tafiyar nan duk jikinta yayi sanyi ...gashi wanda take zumundin son zuwa England dan shi ,din ma Murza sun mishi Asiri .
Haka tayi break sokoko da ita duk Fulani na lura da ita ..dan haka seta ja ta jikin ta da nufin lallashi
Ai kuwa kamar jira take ta kuwa fashe mata da kuka.
Itama Fulani se zuciyar ta karaya duk se taji ba dadi .....
Haka tayi ta lallabata tare dayi mata nasiha me ratsa zuciya .. ..
Da kyar tayi shiru har fulani na tsokanar ta da fadin ko se ta goyaki ta ne zatayi shiru....
Nan ta kyalkayale da dariya..
Fulani tayi mata jagora fardar sarki tayi mishi bankwana ..sosai ya yi mata nasiha shima ..
Suna fitowa fulani ta. bata wata tsaleliyar waya ,,koda na leka na ga iphone,7,..zo kaga Murna wajen Maysam yau tayi waya ..dan dama Murad ne ya hana a bata ,to amma yanzu halin tafiya yayi sanadin an bata..
Fulani tace duk number kowa tana ciki na samiki..
Maysam ta kauda kai tare da fadin har ta yaya na ...
Fulani tayi kamar bata gane ba tace ai ..na samiki har ta yayanki Mahmud...
Tayi kicin2 ta fuska tace Momy ta mijina fa nake nufi ...
Fulani tayi dariya tace tofa an zo wurin masu miji manyan to har ita na saka miki...kai har da photunan shi na tura miki dan daman sun cike mun waya..
Maysam tace kai Momy kin ceci zuciyana fa da yanzu zance a turo min dan ko bacci zanyi sena saka ka photon a .. ...se kuma tayi shiru da sauri tasa tafin hannuta tana kare fuskarta dan Seda tayi maganar taji kunya amman ta mazge dayi mata godiya...ita kanta bata san dan mi yasa ba bata iya controling din kanta wani lokacin..
A gurguje ta shiga bangaren Abbata tayi mushi sallama haka ta daure ta shiga Dakin Murza tayi mata sallamar.
Kamar gaske tana wani dariyar yake wai ita dole yanzu son Maysam take ,,a zuciyarta kuwa fadi take ina nan kwanan nan zaki dawo gida kici Ubanki shegiya kullum se kara kyau take kamar yar sarkin aljanu..
Itama Maysam sakin jikinta tayi kamar ba'ta ji komi ba ..amma addu'a ce fal ranta ....
Haka suka rabu da fulani duk kwalla ta cika mata ido inda Mahmud zeyi mata rakiya har AEROPORT DIORI HAMANI na birnin NIAMEY......acan suka hadu da sauran kawayenta Su Mufeedah suma sun iso duk da yan uwansu nan suka gaigaisa ....suna na zaune aka fara kiran passengers ..haka suma su Mufeeda suka rabu da familly ,
,,Mahmud yana nan har jirgin ya daga ..
Wata yar dantijuwa. na gani ita da mijinta wacce tun lokacin da ake kiran passegers naga ta tsurawa su Maysam ido bata ko kiftawa. mijinta na mata magana aman bata ma san yana yi ba . hankalinta rankatakwab yana. Wurin su Maysam din.....Mijin ta na mata korafin su huce tun dazu amman hankalinta baya ma wajenshi shima ya meda kallonshi ya ga miyene ya dauke mata hankali haka amma lokacin su Maysam tuni sun shige jirgin ....
Suna nan har se da jirgi ya tashi naga ta sauke wata nauyayar ajiyar zuciyar...
Da sauri mijin ya kalleta yace ya akayi ne ?ko jikin ne...?
Girgiza mishi kai tayi kamar karamar yarinya tace a'a naga wata yarinya ne me kama da Baby na...
Shima ajiyar zuciyar yayi ya ce ya kamata yanzu yaci ace kin sakawa zuciyar ki hakurin rashinya ta ....shekara nawa kuma kusan kullum se kinga me kama da ita ....
Da sauri tace a'a wannan ta banbata da sauran wanda nake gani kullum..
Dan murmishi takaici yayi yace kamar kullum kenan haka kike cewa ...kiyi hakuri ki rumgumi kaddara ..idan har tana raye Allah ya bayyana mana ita ..
Ameen ta amsa amma kam ta kwallafa rai a kan yarinyar dan ta so tayi mata magana kamar yanda take yi duk wacce taga tayi kama da Babyn ta..
Sun juya da niyar tafiya ..naji Mahmud ya ce Mom,da,Dad... parent din SWEETBABY ne.ashe..
Juyo wa sukayi suka ga Mahmud ne ..
Nan ya gaishe su cike da.ladabi ..
Suka amsa suna fara'a ..
Mom tace que est ce que te venu faire ici. ?
dan sosa kanshi yayi yace matar Murad ne na kawo zata fice England.....
Dad yace a'aa Masha Allah..
Mom tace kash yau ma babu rabon zanga ta ashe ko dayake fulani taso ta turota kafin ta fice to se akayi rashin sa'a muna Paris.hakama lokacin da akayi aure bama kasar..da nasan yau ne tafiyar ma ai da tun jiya zamu dawo dan naga matar d'ana..
Su Dad sukayi yar dariya sukace ai gaba da yawa zaki ganta. Wata rana
Itama dan murmushi tayi tace hakane to Allah ya nuna muna ya kuma sauke ta lfy .
Suka ce ameen...
Nan Mahmud ya yi musu sallama tare ya fice dan yana son a fara yi mishi saukar tun yau dan karfe da zafi2 ake dukanshi.
Suma driver ya huce su gidan su.
A raina na ce kenan de su anan Niamey suke. .
Ko sarki fulani bata sarna mishi ba halin da Murad yake dan bata da wata sheda .....
To daman gata da temakon talakawa dan kowani wata biyu ko ukku se an kai tamako kauyika ko Mutuwar SWEETBABY ma suna hanyar kai temako wani kauyen ne sukayi shi.
Wanna abu ba kamramin faranta ran sarki yake ba shiya sa ma kullum sonta yake kara shiga zuciyar shi sabanin Madina da ko yan Uwanta bata son temakawa bare wani ..
Shiyasa ma yanzu da sarki yaga kusan kullum se an kai wa makarantu taimakon se beyi wani mamaki ba dan shi ya aza ta sauya takun ta ne na temakon....
Har ranar suna fada da dare su ukku yake tsokanar ta da fadin wai kode dan taji labarin zeyi ta ukku ne yasa take shiga da ficen nan dan addu'ar ta amsu ya fasa auren. ..
Madina da bata san irin wannan wasan ba ta kuwa dafe kirji tace na shiga ukku . aure fa kace ka tsufan nan mi zakayi da wata macen.kuma shine ni ba'a gaya mun ba se yanzu tana wani kumbure2...
Share zancenta sukayi sema
Fulani da ta son tsokanarta kawai yake ta amshe karaf da fadin muna maraba da ita ...fatan zaman lafiya nake maka tanayi tana wani kashe me ido ..tace kuma ai har yanzu dan saurayi shatak yake ,,ni kam bana ganin tsufanshi.....
Takaici ya kusan kashe Madina daga zaunen banda zabgawa fulani harara babu abunda take ..
Sarki yace wannan haka yake nima kullum kamar yar sha bakwai nake ganin ki ...wai ma miye sirrin nan ne .um yan matana...
Fulani tayi wani far da ido ta ce to kawo kunnenka kaji..
Babu gadama ya kuwa dan karkato kunnen shi yana dariya ..
Cike da shaukin so da kaunar junan su ta kuso da bakinta zatayi me rada dan fa su sun manta da wata Madina na wurin...(kuji wani salon soyyayar tsofi ko )
Se ji sukayi Madina tayi tsaye tana fadin tsofe2 daku amman kuna wani abun kamar kananun yara ...wannan ai ko Murad baze yi abunda kukeyi ba tanayi tana dokawa fulani harara....
Fulani a ranta fadi take ...ke kike ganin mun tsufa amman ai ita soyyaya bata tsufa..( to fa kunji tsofafin ko?)....
Fulani mikewa tayi tana fadin seda safen ku dan Madina keda girki yau..
Sarki yace zo ki fada mun mana kafin ki hucen ...
Fulani na dariya kasa2 ta ce to ai ya fice sede wani jikon..kuma
Kallon zamu hade naga yana jifanta dashi...
Wanda ya kara harzuka zuciyar Madina ..ta shige kuryar daki fuuuu ..tana fadin jarabbabiya kawai.macce se jarabar iya kissa mtssss.
( Madina kina sha'anin ki fa )
..
Su Maysam sun isa England lafiya ..daya ke gwamnati ce ta tura su kafin ma su isa har an turo musu bus din dazu dauke su dan ba su kade bane suka samu promotion din ba....
Direct babbar university England aka akaisu ..nan aka rarraba musu dakuna su anan cikin hostel din makarantar...
Amman cikin rashi sa'a se ba a hadasu daki daya ba ...Mariam da Mufeedah da wata dakin su guda se kuma Maysam da wasu yan mata suma dakin su guda..
To fa nan ake yinta Maysam ganin an ware ta da su..da kyar da siddi suka shawo kan yan matar sukayi changé da Maysam.ta koma daki daya da su Mariam.dadi kamar ya kashe su ...
Tun washe gari suka fara zuwa lecture dan har an fara da sati suka zo ..dan haka babu zancen hutu ma ...
Class dinsu guda wato medecine dan sunce mutuwa ce kawai zata raba su ..komi nasu iri daya ne kai har dressing dinsu ma iri daya suke yi .kuma kullum zaka gansu da hidjab din su basa yarda su fito hakanan duk da suna garin turawa....., .suna taka tsantsan da rayuwar su ...sun meda hankalin su ga abunda ya kawo su..
Ba kadan ba suke birge ba mutane da basu sha'awa dan duk gani suke trijumelles ne(yan ukku)......
Yanzu har sun cinye 1 mois da zuwa ..suna ta karatun su cikin kwanciyar hankali banda Maysam data tsanan ta tunanin ta oga Murad ...shi yasa ma basa barinta ta zauna ita daya koda da second daya ne dan yanzu zata saka photon Murad a gaba tana ta tunanin shi..tun abun baya damunsu har yazo kuma yana yi dan sunsa miyasa Murad din be nema ta ba suma kullum cikin taya ta da addu'a suke...
Yau ma kamar kullum su Mufeedah sun dan fita suka bar Maysam a daki tana dan exercice..
Amma mi ko minti daya basuyi ba da futa ta ture komi gefe ta fara sa'arta wato kallon photon..
Shigowar su kenan ...suka ji Maysam na fadin ita kade wly duk ranar da muka hade da kai ko to sena tsotse bakin nan tas ..dan gaskiya Allah yayi hallita a wurin nan ..dan lips din nan shine ake kira Kiss me babyn nan ..ita duk jitake a ranta tayi maganar
Tana kallon photon tana doka murmushi.
Mi su Mariam zasuyi in ba dariya ba suka kuwa tun tsire da ita har tasaki baki tana kallonsu dan bata san mi suke yiwa dariya ba
Mufeedah ta matso tace inda muga irin lips din nan da ake ta wani yabawa haka...
Wani waro ido tayi tace wai kuna nufin dama a fili nayi maganar nan ne..
Mariam tace a'aa a Mafarki ne..
Gaba dayan su suka saka dariya ...haka suka ci gaba da rayuwar su .cikin jin dadi.
.
A can gida kuwa sauka yi ake ba kakkau tawa ..
Haka kawai ranar wata juma'a Murad tun safe ya tashi da wani matsene cin ciwon kai ..lokacin yana likita ne dan haka ya tattara ya dawo gida amma ciwon kamar karashi ake ...
Ba bu zato yaji bakin shi yana abaton addu'a wanda rabon daya ce yayi addu'a kai koda bayan salla ne to ya manta...
Kan kace mi bacci ya sure shi ..bashi ya farka ba se wajejen sha biyu da rabi na rana duk wani iri yake jinshi kamar wanda iska zata dauke shi yake ji fayau2 kawai....ganin lokacin sallar Juma'a yayi dan haka wanka yayi ya fice Masalaci duk da akwai yar tazara dashi da masallacin. Amman har yanzu kan be bar mishi ciwon ba...
Tunda sheik din ya fara huduba jikin shi yayi sanyi duk se yake jinshi imcomplete kamar wanda ya rasa wani abu a rayuwar ya ke ji dan akan yin biyyaya ne ga uwaye...ake hudubar..
Haka jiki ban kwari har akayi sallar ..suna gamawa mutane suka fara tafiya dan ba wani yawa ne da su ba daman...
Amma shi Murad nan ya tsinci kanshi da ya zauna ...yana yiwa fiyyenyen Halitta SALATI ..
Mark dake share guda yana kallon shi duk mamaki ya cika shi ...duda yasan wannan al'adar shi da Murad ce in akayi Sallar juma'a nan zasu zauna suyita istigifari tare da salatin Nabiyi ..to aman fa shi Murad ya dade da fasata ..dan ana gama sallar yake tafiyar shi...
Be gama tsinkewa ba seda yaga an tada sallar la'asar anyi shi da Murad din dan ba kullum ba yake ziwa masallacin ma agida yakeyin sallar shi...
Shi kam Murad tun da ya fara yin Salatin ya ji zuiiyar shi ta nutsu ..wani rin nishadi yake ji yana bin duk illahari jikinshi
Kasa hakuri Mark yayi ..bayan sun gama sallar ya matsa kusa da Murad din yayi mishi sallama nan suka gaisa ciki da fara 'a Murad din yake amsawa ..
Mark de ya boye mamakin shi dan ba kamar kwanakin baya ba da sama2 suke gaisuwar ma..
Nan Mark cikin dakewa yace yau fa duk kawani sauya mun ...
Murad yace mi ka gani ne.....
Mark daman kamar jira yake nan ya kwashe komi ya fada mishi har da zuwan Mahmud din da yanda sukayi dashi ...
Inna lillahi wa inna.ileyhi raji'un ... A bunda bakin Murad ke memetawa kenan .....
Be gama tsinkewa ba seda yaga babu numb familyn shi ko daya a wayar shi ...
Mark yayi karfin halin fadin ai ka canza layi tun da dade wa....
Hawaye kawai ya shiga zarya a idon shi yama rasa abunyi ya kuma rasa miya sa shi yin haka gaba daya baya iya tuna komi......
Mark daya fara dan zargin wani abu se yaji tausayin shi ya kama shi dan shi dama yasan da walakin goro cikin miya ...Murad dayake tsananin son familyn shi aman farat daya ya yanke duk wani contact dinshi da su ...
Nan Mark ya shiga yi mishi Nasiha tare da jan hankali kan ya rike addu'a don ita ce takobin mumuni....
Daga haka Mark ya bashi shawara ya kirayi su fulani yanzu ..
Kallon agogon hannushi yayi ya ga hudu na yama kenan yanzu goma na dare ne a can ..
Amma duk da haka ya danna number fulani dan ya haddace ta a zuciyar shi tun da dadewa...
Lokacin fulani tana shirin fita zuwa wajen sarki..kiran ya shigo..
Ringing a na biyu ta daga duk cike da zumudi dan taga number england ta aza Maysam ce ta ari wayar kawayen ta kira...dan haka tana dagawa ta fara da fadin asallama yar gidan Momyn ta .....
Murad daga can a ranshi ya shiga dan tunani nan da nan zuciyar shi ta fara aikin zut2 dan tuno mata da Maysam...katse shi fulani tayi da fadin hello..
Cikin da sanyi jiki zuciya na mishi fat2 ya amsa sallamar tare da fadin Momy nine...
Wani farin ciki marar misultuwa ya ratsa zuciyar fulani ...tace son kai ne...
Cike da kwarin guiwa jin bata dau abun da zafi ba ya ce nine Momy ..dan Allah ku yafe mun wly basan miya sa man ba yana fadin yan kuka..
Godiya ta shiga yiwa Allah (SWT)daya kubutar mata da son dinta ....dama ai addu'a bata faduwa kasa . kuma ```Manzon Allah (SAW) ya ce'' idan zakayi roko ,to ka roki Allah ,kuma idan zaka nemi temako ,to kanemi temako a wurin Allah.(Tirmizi)
```
sanin bayin kanshi bane yasa tace na yafe muka daman can ban rike ka ba ...nan ta shiga yi mishi nasiha da ya rike addu'oi dayin sallar nafila..dan ```Manzon Allah (SAW) ya ce''Addu'a itace ibadah (Tirmizi``` )
Sosai zuciyarshi tayi wasai ...sun jima suna wayar sanna ya kashe tare da fadin se zuwa safe ze kirayi Sarki dan har sha daya tayi...seda safe sukayi wa juna tare da gaya mata gashi nan cikin satin nan in Allah ya yarda.....cike da murna kamar karsu kashe wayar ..har ze kashe se kuma ya sake fadin Momy ina Yarinyar nan take ..
Ganin dare yayi Fulanin kar sarki ya jita shiru dan ita keda duty yasa tace tana nan she is fine tana can tana wurin karatun ta...
Bakinshi yayi nauyi tambayar a 'ina se kawai ya kashe kiran ..
Fulani dan murmushi tayi tare da fadin ni kam ido ne nawa...
Yana kashewa ya dannawa Mahmud kira ...
Ringing biyu shima ya daga duk jiyake su Mufeedah ne shima...
Amman mi se yaji muryar Abokinshi wanda ko cikin dubunan jama'a ze iya sheda ta..
Cike da zumudi yace M2 kai ne ko kuma kunuwana ne suke mini gizo...
Murad yace nine aboki pls kayi hakuri da abunda....
Be gama ba Mahmud ya katse shi da fadin ai komi ya fice a kiyayi gaba de...shima de nasihar rike addu'oin tsari na safe da yamma yace ya rike kamar yanda fiyyenyen Hallita ya umarce mu da yin su...(suna nan cikin HUSNUL-MUSLIM)..
Murad yace hakika ka cika aboki na kwarai Allah ya bar kauna da zumunci masu dorewa...
Ameen ya amsa ..
Se kuma Murad ya ce kenan de yar gidan Momy bata ci jarabawa ba ko kuma fasa yi musu tsallaken class din akayi ne dan na tambayi Momy tace tana can wurin karatun...
Mahmud yace ita kuwa suka samu dan har da mention excellent SANADIN haka har gwanati ta tura su karatu England itada kawayen ta ...
Yan zu haka suna can. enland...
Tunda Mahmud ya fara bashi