Showing 33001 words to 36000 words out of 190707 words
sosai ga idanun sun jike da hawaye sosai sakejin wani abu yayi namai tafiya aciki dasauri ya dauke kai yay baya da kujeran dayake kai zai tashi hakan yasa Yasmeen tai maza cikin kuka ta yunkuro daura kanta tayi akirjinshi in so much agony cikin wani kalan kuka tace “wlh wlh nima saika kasheni, I can’t live anymore mai amfanin rayuwana kannena sun mutu? Wlh wlh saika kasheni baraka tafiba” tacigaba da bubbugamai kanta akirjinshi, baitaba ganin mutumin dabaya tsoronshi ko shakkan shi ba irin yarinyar nan, cikin kakkausan murya yace “dagani to nadauki bindiga na nakashe ki” cikin kuka ahankali ta yunkura zata tashi da jikinta daya mutu sosai karaf ta tsaya sabida yanda gashinta ya makale a boturin jikin riganshi ba karamin zafi abin yamata ba dasauri cikin kuka tace “washhhh” takai hannunta dasauri zata daura akan kirjinshi cikin dan tsawa yace “don’t touch me ke!” Tsayawa tayi cikeda gajiya da komi na duniya tace “to kacire mini” dan kallon kan nata dake saitin kirjinshi yayi da yanda gashin yay tangling akan boturin shi, tsaki yayi kadan tareda yatsine fuska yakai hannunshi ahankali kaman mai tsoron taba gashin nata yace “look at her dirty hair kazamiya” cikin kuka tace “eh naji amma dai inada imani kuma ban taba kashe kow…..” wani kalan kuka ne yaci karfinta mai bala’in kara this time tunawa da yakashe Nana da Farida yanzu, kasa taba gashin nata yayi ahankali yaduko da kanshi kasa yana kallon yanda take kuka ta runtse idanunta gam tana kuka mai taba rai har harshenta yake hangowa jajajir sabida yanda take kukan, wani abu yaji ya tsayamai arai yanda take kukan nan tausayi ne shi baitabajin tausayin wata ba baima cika jin emotions ba to meke damunshi, jitayi kaman ana kallonta hakan yasa tabude rinannun idanunta cikin kuka karaf suka hada idanu saida gabanta yafadi shima haka dasauri yadauke kai tareda kai hannunshi da sauri yana cire gashinta daga jikin riganshi da sauri yakasara cirewa cikin fushi yace “now get up” tashi tayi dasauri tana kuka, shima yamike tsaye yahade rai tareda jawo drawer yaciro bindinga yadago kanshi yakalleta, kallon bindigan tayi yay pointing bindigan saitinta yace “kince na harbeki ko”? Gyadamai kai tayi cikin kuka tace “eh” ahankali yana kallon kwayan idanunta ya matso dab da ita tareda daura bindigan akan goshinta lumshe idanunta tayi da sauri tana wani kalan nishi hawaye na fitowa ta gefen idanunta ta sadakar kawai, pulling trigger yayi bindigan tai wani kalan kara har cikin scull nata taji karan batasan sanda ta kurma wani kalan uban ihu ba. “Wayyoo Ammi na mutu” jikinta ko’ina narawa, wani kalan murmushi ne ya kufce mai daga baki yana kallon yanda ta zare ya girgiza kai kawai yasauke bindigan kasa ahankali yace “ahaka ake mutuwa ko”? Chak ta tsaya tadan zaro idanu saikuma takalli kanta ita wlh tadauka ta mutu, hannunta takai tashafa saman goshinta inda yadaura bindigan ta lakato tadawo dashi gaban idanunta taga ko akwai jini taga bakomi hakan yasa tadago manyan idanunta ta kallai, wani kalan dan iskan kallo yamata sannan yawuce yafara tafiya zaiyi hanyar kofa kaman wanda akace dole yayi magana yace “your sisters are alive” wani kalan zaro idanunta tayi takalleshi dasauri tabi bayanshi tace “da gaske” kojuyowa baiyiba balle yakalleta but hakanan taji kawai ta yarda dashi they’re alive, ganin yakai kofa yasa dasauri tace “dan Allah ka maidani wajensu” chak ya tsaya hakan yasa itama ta tsaya dasauri batare daya juyowa cikeda gadara yace “this is your punishment” cikin wata kalan sanyin murya kaman marainiya tace “dan Allah kayakuri kayafemini” wani kalan juyowa yayi yazuba mata mayun idanunshi dasauri takoma baya tasauke kanta kasa dasauri, anatse yace “I don’t forgive mistakes” juyawa yayi zai bude kofa yafita hakan yasa dasauri Yasmeen tace “ni kuma I forgive you duka abinda kamini da kannina” haryasa kafa yafita ya tsaya chak juyoda fuskanshi yayi yakalli side nashi batare daya juyo yakalleta ba, ahankali yace “why”? Matsowa kusa dashi tayi kadan tace “sabida you are a good person dabai da kow……” wani kalan juyowa Maheer yayi kaman zaki dayasa maganan ya makale abakinta tazaro idanu adan firgice kafin abalain tsorace tace “kayakuri I guess I misspoke” wani kalan juyawa Maheer yayi yabar dakin azuciye tareda rufo kofa.
✨KK✨
✍🏻M SHAKUR
EPISODE 2️⃣0️⃣
ZAKI IYA SHIGA GROUP DIN DANAKE POSTING ✨KYALKYALIN KAUNA✨TA HANYAR DANNA LINK DIN NAN
https://chat.whatsapp.com/HyR79BijM7XFBaNPrFcBYn
***
Daga Baba dake wajen aiki harsu Ammi dake gida babu wanda ya runtsa ranan, dan saida dare yayi Ammi ta birkice sosai dan all this while bata yarda anyi kidnapping yaranta ba saida dare yayi, dare yayi taga yaranta duka basa tareda ita an daukesu kenan yanda take kuka sosai saida Baffa yafita yakira wani likitan anguwansu yazo yama Ammi alluran bacci sannan suka samu tai bacci.
Shima Baba dake station baiyi bacci ba saida ya sumar da direba daya cikin direbobin har saida su Aliyu suka fito dashi daga dakin amman direbobin nan sunki magana ganin yanda ya sumar da dayansu kuma yake fushi yasa suka gane Pablo yadauki wani abu nashi that means sun kusa fita hakan yasa suka kara dake ransu sukaki bada any information dan dasuyi betraying organization din dake basu mahaukacin kudin nan dabasu taba samun irinshi arayuwan su ba gwara su mutu a police station din dasu bada information akan Pablo.
Wuraren 7:15 na safe Baba na zaune kan dogon kujeranshi ya lumshe idanu hannunshi rikeda wayan da babu abinda yake sai fatan Allah yasa Pablo yakirashi Aliyu zaune gefenshi daya damu sosai wayan hannun nashi yayi kara hakan yasa dasauri yabude wayan hannunshi har rawa yake saiga video, Yasmeen ce tafara kokarin karatu saida Farida dasuke bayanta itada Nanah sun kankameta tafito takarba tafara karanta abinda ke paper da yanda tafashe da kuka akarshe, yaran sunyi zuru zuru kaman sunyi shekara dari hannun criminals, kasan sau goma Baba yakalli video sannan yakalli Aliyu yabashi wayan yace “sake kiramin number” dialing number Aliyu yayi kaman tsafi number yayi ringing dauka akayi dasauri Baba ya karbi wayan yace “Hello Pablo” Dan ne yayi magana yace “Oga is unavailable, yariga yamaka kiran dazai maka trust me har abada Oga bazai kara kiranka ba kuma” ijiyan zuciya Baba yasauke ahankali yace “hope my children are fine” dasauri Dan yace “absolutely” ahankali Baba yace “zan saki kayanku yanzun nan bada jimawa ba amman shipment din zan fara saki sainaga yarana zan saki direbobi ku” dan murmushi kawai Dan yayi kadan yace “deal namu is direba da kayanmu, nonetheless Oga always keep promise nashi, za’a kai shipment namu trailer park a ijiye we will take it from there” Dan na maganan ya katse wayan Baba yawani kalan fuzar da ijiyan zuciya abin namai kaman bashiba baitaba sanin wani abu zai iya faruwa dazaisa yayi compromising any case ba sai yau! Bude idanunshi yayi ahankali yakalli Aliyu yace “get the boys ku dauki motocin ku kai inda sukace” dasauri Aliyu yace “direbobin fa” lumshe idanu Baba yayi yace “sainaga yarana tukunna” ijiyan zuciya Aliyu yasauke yawuce kawai yafita wato Baba akwai taurin kai shi bazai iya magana ba Ogan shine he must obey abinda yace amman har cikin ranshi yaso Baba yasaki komi nashi, samin yaranshi yayi dasuka iyajan mota aka kwashi motocin aka tafi dasu har zuwa tipa garage din akai parking tsayawa sukayi suka shige cikin mutane trying to see wanda zaizo yadauka. Baba na zaune a office wayan yayi kara dasauri yadauka cikin kakkausan murya Dan yace “call your boys kace subar wajen nan kafin Oga ya chanza mind dinshi” dip ya katse wayan dasauri Baba yakira Aliyu yace subar wajen dan dole suka tare keke suka shiga sukabar wajen.
***
Fitowanshi daga wanka kenan yana daure da wani short towel a waist nashi da karami a hannunshi yana tsane kanshi, knocking akayi saida yakarasa kan couch dake dakin ya zauna sannan yace “shigo” shigowa Dan yayi cikeda girmamawa yace “Sir munyi securing shipment din komi lafiya lau saidai bai saki direbobin mu ba” dan gejeren murmushi Maheer yasaki sannan yay crossing kafa daya kan daya tareda ijiye karamin towel din a gefenshi sannan yadago kai yakalli Dan yace “kasa Wike to drop the 2 kids, abar babban anan” gyadamai kai Dan yayi yace “yes sir” yajuya yafita daga dakin.
Farida da Nanah nazaune adaki kaman marayu idanunsu sun kumbura kaman babu komi Wike ya shigo da yaranshi dasuka rufe fuskokinsu yana dariya yace “hip hip hurray, time to go home children” fashewa da kuka Nana tayi Wike yamata wani mugun kallo yace “dabakin ta kaman na kifi ke dauketa kafin na bugamata bindiga tasume, mutafi” dasauri Farida dake sanye da hijabin Yasmeen ta dauketa tana leken kofa ganin bataga Yasmeen ba saikuma tai tunani kila tana mota, wani bakin yadi Wike yasamata a fuska yasama Nana sannan aka kama hannunsu aka fita dasu faduwa kawai gaban Farida yake Nanah sai kuka take tanaji aka sasu a mota bata sake sanin ina sukeba sai tafiya suke hankalinta yaki kwanciya, ita batasan iya dadewan dasukai a mota ba but akalla sunkai awa daya sannan taji motan ya tsaya awani waje aka zare hulunan kansu aka bude kofa Wike yamata wani mugun kallo yace “ku sauka”dasauri Farida ta jujjuya takalli motan ganin bataga Yasmeen ba yasa tace “ina Anty Yasmeen”? Wani mahaukacin kallo da Wike yamata yasa tasauka daga motan da gudu tana daukan Nana a hannu yace “idan kinje gida ask your Daddy” sannan sukaja motan dawani kalan bala’in gudu, bin inda suke Farida tayi da kallo sai yanzu tagane ashe agaban school nasu take, goya Nana tayi abaya tashiga tafiya dasauri sauri gudu gudu dan gani take kaman zasu kara zuwa su daukesu kuma tai gida dan basu da nisa sosai da gida, daga Baffa, Baba, da Baba Karami da Aliyu police duk suna tsaye a kofar gida dan yanzun nan Baba yadawo tareda Aliyu baima iya ya shiga cikin gidan ba, kaman daga sama yaji ance. “Babaaaa” dasauri yajuya, hango Farida yayi goye da Nana tana gudu kaman mahaukaciya dawani kalan sauri dagashi harsu Baffa sukayi kanta yana zuwa Farida batai wata wata ba tafada jikinshi sai kuka Baffa kuma ya karbe Nana daga bayanta, dago Faridan yayi daga jikinshi bakinshi har rawa yake yace “i…….ina….ina Yasmeen?”.
✨KYALKYALIN KAUNA✨
✍🏻M SHAKUR
EPISODE 2️⃣1️⃣
KINASON MAGANA DANI M SHAKUR DIRECTLY click on this link
wa.me/+2347012181461
Sake rushewa Farida tayi da kuka jin tambayan da Baba yamata tace “nima bansani ba Baba” ganin yanda ake kallonsu yan layi dake wucewa yasa Baffa yace “muje gida tukunna” gida suka wuce Ammi na zaune a tsakar gida akan tabarma tabuga tagumi ga tuwo agabanta amman takasa tabawa babu abinda yashiga bakinta tun jiya, jin an bude kofa yasa ahankali ta dago kanta, Nanah dake hannun Baffa wani kalan dirkowa tayi kaman wacce tai shekaru bataga Maman ta ba tawani kwasa da gudu tace “Ammi Ammi Ammi na oyoyo” unbelievably Ammi ke kallon Nana batasan lokacin da itama ta taho dasauri ba tana zuwa wani kalan rungume Nana tayi tana kuka, itama Farida ta taho dasauri Ammi tahadasu ajikinta ya rungume kowa ya tsaya yana kallonsu abin gwanin taba rai, sakinsu Ammi tayi tadago kanta tana leka wuraren gate ganin bataga Yasmeen ba yasa tadawo da kanta takalli Farida tace “ina Yasmeen”? Shiru Farida tayi tana kallon fuskan Ammi takasa magana hakan yasa Ammi tadago kanta ahankali ta zubama Baba wasu kalan idanu sai kawai tasake fashewa da kuka ta kankame su Farida da Nanah ajikinta suma suka fashe da kuka, itama Yaya zuwa tayi tazauna gefensu tahau matsar kwalla tace “mudai muna ganin jifa’i kala kala Innalillahi wa innailaihi raji’un, Ya Allah, Ya Allah kabamu ikon cin jarabawan nan, Ya Allah ka tsare Yasmeen aduk inda take aduniyan nan” juyawa Baba yayi yace “zonan Farida” ahankali tasaki Ammi ta tashi tabi Baba da yashiga daki tambaya yamata tabashi tundaga farkon abinda yafaru har karshe tass, anatse Baba yace “kinga fuskan Ogan nasu da kyau?” Girgiza kai tayi tace “a’a ban gani ba mutane uku naga fuskansu, dawani baki mummuna dakuma yan sandan dasuka zo school namu” shiru Baba yayi kafin anatse yace “zaki iya kwatanta su”? Girgixamai kai tayi hakan yasa ya shafa kanta kawai anatse yace “sun muku wani abu”? Girgixamai kai tayi alamun a’a saikuma ahankali tace “Baba maisa basu saki harda Anty Yasmeen ba” shiru Baba yayi baice komi ba sai chan yace “itama zasu saketa, jeki wanka kici abinci kiyi salla” gydama Baba kai tayi Baba ma yabata tausayi duk kamanninshi ya chanza daga gani baiyi wanka ba, yana zaune anan Baffa yayi sallama yashigo wani kallo yama Baba anatse yace “Ibrahim daman duk nuna soyayyan dakake ma yaranka na karyane eh”? Baffa yamai maganan cikeda tsananin fada dayasa Baba ahankali yace “menayi Yaya”? Cikin fushi Baffa yanunashi da yatsa yace “kada ka kara kirana da Yayanka dan baka nuna mini na isa Yaya agareka ba, kabama Pablo abubuwan su kabasu rabi yanzu gashi sun rike Yasmeen so kake su bata rayuwan yarinyar nan? Did you even know the effect of abinda kayi Ibrahim” hannu Baba yasa yakama kanshi tareda sauke kanshi akasa dan kanshi kaman zai fashe ana neman 48hrs kenan baiyi bacci ba koya kulle idanuwanshi, sai yanzu yagane Aliyu ne yagayama Baffa komi, cikeda damuwa batare daya dago kanshi ba yace “Yaya kayakuri” cikin fada sosai Baffa yace “dukanku a family nan are my responsibility, hakki nane ku gabaki dayanku Ibrahim, nace maka kai abu bakayiba kabasu rabin abu, sun baka kaima rabi, Fatima nachan sun rike, what is your problem bari kaji nafada maka” Baffa yay maganan cikeda tsananin baccin rai yace “inhar aikin nan naka zai zama danger akan rayuwan iyalina ina nufin dukanku tatas yan gidan nan wlh wlh zakabar aikin nan I don’t care cewa kayi shekara da shekaru kana dan sanda zakabar aikin ne dukanmu muhadu mukoma kasuwa, and listen listen very well if anything happens to Fatima!” Baffa yanunashi da hannu cikeda mugun baccin rai yace “wlh wlh sainai fushin daban tabayi dakai ba tunda iyayenmu suka kawomu duniya” Baffa yajuya fuuuu yafita daga dakin, Baba yakai kusan minti ashirin zaune awajen yakama kanshi dake sarawa sannan yaciro wayanshi number su Pablo yay dialing amman bata shiga an kara cireta daga kan network ijiye wayan yayi agefenshi yasake kama kanshi daga bisani yamike yatashi yafita daga dakin ko kallon inda su Ammi suke baiyiba yawuce yafita Aliyu ne yama su Baffa sallama sannan yabi bayan Baba da sauri yana zuwa yashiga mota Baba yaja motan zuwa police station.
Yana shiga parking yayi wajen parking sannan yajuyo yakalli Aliyu dake kokarin bude kofa yafita hakan yasa Aliyu ya tsaya batare dayace komiba, anatse Baba yace “jeka sallame su sutafi” gyadamai kai Aliyu yayi dasauri yace “Alhamdulillah” yabude kofan yafita da sauri yamaida kofan yarufe, wani kalan dukan kujera Baba yayi zuciyanshi namai zafi sosai kafin yayi huci anatse yace “you won this time Pablo but trust me next time I will be the one that’s gonna win”.
*****
Taba kofan tayi da sauri tareda bugawa tace “dan Allah kubude ni ku komarda ni wajen Kannaina” bude kofan taji an shigayi hakan yasa takoma baya dasauri ta tsaya kirjinta na dukan uku uku tana kallon kofan, tura kofan akayi aka shigo, wata faran mata ce kaman ma shuwa ce matan tashigo dakin tana sanye dawani lafiyayyen lace purple mai shegen kyau yaji duwatsu da flowers anyi dinkin riga da skirt, batada wani kiba dan yanayin jikin matan kaman na Ammi, matan nada boobs sosai da katon ass, tana rikeda wani birkin bag wanda ake saidawa miliyan sha biyar sha uku din nan mai shegen kyau da jimmy choo heels da duwatsun saman are diamonds, dawani dan karamin mayafi data yana kanta dashi wanda babu dan kwali akai gashinta a gyare anyi parking an zubo dasu har tsakiyan bayanta, sai kamshi take sosai kana ganinta kaga kudi, kudi sun zauna ne Alhaji!, yanda Yasmeen ke kallonta haka itama ke kallon Yasmeen din tundaga kai har kafa ta hade rai kaman bata taba dariya ba arayuwanta, wani wulakantaccen kallo tama Yasmeen sannan tajuya batare datacema Yasmeen ci kanki ba zata koma waje dasauri Yasmeen tace “Anty Please ki kaini wajen kannaina” wani abune Hajiya kawai taji yatokare mata wuya sabida yanda taji muryan yarinyar dakeda bala’in dadi gashi da sanyi mai bala’in ratsa zuciya kaman tana shagwaba, Juyowa Hajiya tayi tamata mugun kallo kafin awulakance kaman taga kashi tace “namiki kama da wacce zaki aika?” Dasauri Yasmeen ta girgixa kanta ganin matan batada mutunci murya chan kasa tace “yakuri” wani kalan tsanan ta kawai Hajiya taji yashiga ranta shigowa tayi cikin study din takai hannunta gaban rigan Yasmeen cikeda wani kalan wulakanci ta fincikota tajawota waje tana tafiya da ita suka fito daga dakin dasauri Yasmeen tashiga binta bata wani damu ba da yanda take janta kaman baiwa danta dauka wajensu Farida zata kaita, cikin wani babban falo taga Hajiya ta bullo da ita ga su Nas zazzaune suna shan XTC, ta tsakiyansu tabi da ita zuwa wani babban kitchen tana shiga tawani kalan jefata tsakiyan kitchen din saida kanta ya bugu da bango takoma baya dasauri tareda kai hannunta kan goshi ahankali tace “wayyo kaina” azuciye Hajiya tace “arrange this kitchen tass sannan I don’t care ki dafa abinci for maza na 55, yau biyar bazaa kashe siyo abinci ba, daga yanzu kin dawo slave agidan nan harsai ubanki yagama bamu abinmu dake hannunshi, kinyi kadan kice zaki rayuwa in peace in our house” tajuyo azuciye takalli su Nas daduk sun mike tsaye tace “ku tsare gaban kitchen din nan kartai attempting guduwa” sannan tasake juyowa takalli Yasmeen dake liliya goshinta da hannu dahar ya kumbura tace “bazaki fara abinda nasaki ba” Gyadamata kai Yasmeen tayi dasauri dan hakanan taji Allah yasamata tsoron matan sama da kowa na gidan”.
✨SPARKLES OF AFFECTION ✨
✍🏻M SHAKUR
EPISODE 2️⃣2️⃣
For your original Egypt Abayas,home decor, Gold (new and used), shoes that are qualitative and unique at affordable price , siyen daya ko sari (wholesale and retail) contact wa.me/+201123302418
Instagram @Shopper_topia
WhatsApp group *Maryam’s Egypt abaya *
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj
Wucewa sama tayi duk su Nas suka bita da kallo,