Showing 153001 words to 156000 words out of 177131 words

Chapter 52 - Bororoji Compelet COMPLETE HAUSA NOVEL

01 Sep 2024

14804

   Sai mutane na hudu suna shigowa rayuwarka ce dan su amfana da baiwar ka, ko wani abin ka, sannan babu wani abinda zai saka su kaunaceka domin ba kaunar ce ta kawo su ba, dama sun zo ne domin ribantuwa da kai. Kuma suna gamawa zasu tattara ka su watsa gefe, ba iya a rubutu ba, ba iya a zamantakewar mu ba, ba iya a gurin ayyukan mu ba, a ko ina akwai irin su.

Kinga mutane na biyu da na hudu kiji tsoron Allah akansu, domin zasu iya kaika lahira da sawun ka kuma babu wanda ya isa ya dakatar dasu. Muna tare da su yau da kullum. Allah yasa mu dace...
👇🏻
Wannan labarin yana faruwa damu kuma muna tare da irin su ban saka dan kome ba, sai dai idan kana cikin masu irin wannan halin don Allah ka daina.
*🤭 bari nayi wani Karambani, wata yar makotar kasar mu, ta tab'a niman Number na, sai aka ce mata wai mai_Dambun kike niman layinta? Matar da bata da mutunci a Media 🤣😂 Wallahi kusan shekara biyu kenan, lokacin ina rubutu masarautan Jordan, kawai sai tace musu eh ita nike nima, sai aka samu wata tace mata kinga ni babu ruwana da ita bana shiga harkan ta, kuma ina ganinta amma saboda ance bata da mutunci yasa bana kulata! Sai tace a bata Number na, maybe zata ji ni indai har yau tana tare dani, sai ta min sallama ba amsa, tace ga abinda take so nace mata to na tura mata MJ na cigaba da uzurina, Alhamdulillahi sai gashi ta kirani tace na ce ki bani book kin bani kuma baki tambaye ne kome ba, wallahi saboda yawan Jama'a yasa na manta ban tambaye ta ba, kuma wani abu anan sai da na kwana biyu ta kuma min magana don Allah taya zan ce mata bani kuɗin, sai nayi dariya nace mata ok bar kudin idan nayi wani book ki saya... Labarin na da tsawo, amma shi alkhairi jifa ce! Dan haka a ranar ban yi mamaki ba da ta gaya min haka. Kuma nayi godiya sai dai wani hukuncin Ubangiji na gama magana da ita, wata baiwar Allah ta min wani Alkhairin da bazan manta da shi ba. nagode sosai domin rayuwa ciken yake da jarabawa da kalubale  sai an maka haka zaka san WHO Are You? Allah ka hada mu da masoyan Manzon Allah (S.A.W) domin sune babu tsatsa da lamba a zukartar su*
Taku har kullum
Ramlat abdulrahman manga
#Mai_Dambu...
[8/14, 10:44 AM] Joindah: https://www.wattpad.com/1115273030?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=%2FGBnJnXNijQUPspekfVSCvdwVvA67jfZnwBxxbrgfB3mZ707r2j51R%2BtHtXGLFFQhRnwEzTOFYN6wtlFDeefWMBEls9vr15DqQCkIJyDScb3H2il28oON918W3al4mnK
🐂🐂BOROROJI🫀🫀

~The Journey of Destiny💔~

Mai_Dambu

Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....

Ana harin account ɗina fa, musamman wannan account ɗin... Wallahi 😓

BABI NA SITTIN DA BIYU.

Dan haka dole ki koyi mu'amalar irin mutanen wani lokaci ma sa masoyanka kake fada, sai ta kwab'e maka zaka Fahimci haka, sannan da gaske ne dole ki koyi hakuri, domin duk inda zaki zauna dole ki koyi hakurin nan shi yasa Allah madaukakin sarki yace masu hakuri yana tare dasu, dole ki koyi kawar da kai.(🌚🤣wallahi sai ina jin kunya idan na rubuta maganar hakurin nan 🙄domin ban da ita da rashin daraja ce zan iya fada akwai ta buhu buhu 🤨😒😏🌝🤸) mahaifiyar Mohan tana da zafi da fada, kuma irin su dole ka zama ruwan sanyi, sai a zauna lafiya. Bari na gaya miki wani abu, duk yadda aka kai da zaman aure dole ki samu positive and negative, dole cikin biyu ayi daya imma dangin miji su kauna ce ki bawa, umma miji yaki ki. idan aka yi dace kuma kika hada soyayyar dangin miji da namiji kin dace, idan kuma aka yi rashin dace uwar miji taki ki.
(Kuyi hakuri bawai babu Yaren Novel bane a labarin amma ina son ku fahimci wani abu ku mata ne! Kuma dole a gaya muku rayuwar wasu dangin mijin baka san da wanda Allah zai had'a ka dasu ba, amma yana da kyau mu fahimci kan rayuwa ba wai nace babu Sex bane a'a kawai labarin na gina shine akan wannan yanayin 🙄🤨 yan buta roro, idan aka barku da shugaban karamar hukumar wandon cinye shi zaku yi. Wallahi ba sex story bane labari ka fahimci sakon labarin shine damuwar, idan naso sai nayi labarin kamar Kwarkwarah 😂🤣 lami kenan a gaban Uban kowa ma za a karanta labarin babu jin kunya ko rufe fuska 👏🏼)

    Ba wai na gaya miki mugun hali ne ko muguntatta ba, a'a tana da fada amma tana da kirki, kowani dan adam yana da kirki yana da banzan hali, idan Allah yaso halin kirkin ya danne banzan halin ka huta idan kuma halin banzan ya danne na kirki ka banu, domin duk wanda zai fadi wani magana akan ka toh halin banzan zai fada akanka. Ba zai tab'a duba tarin alkhairirronka ba, burin shi ya fadi wancan mugun halin."

Rike hannuna tayi sosai, tare da kallona.
"Jinki Allah ba zai tab'a jarabtarki ba? Ko yayi dake ne ba zai tab'a jarabtar rayuwarki ba? Maimunari idan har namiji zai dauke ni ranar aurena bayan an daura min aure da wani yaje yayi rayuwa dani meye yafi wannan muni da jarabta? Maimunari idan har zai tafi dani bai tab'a mu'amalata ta cikin nutsuwa ba meye yafi haka cin rai?" Damke hannunta nai hawaye na wasan tsare a fuskana,  "kinsan me ya faru? Hatta rayuwar ki nice na lalata miki, domin ba zan manta ba bayan na gama tsine mishi, sai da nayi furucin da nasan shi yake dawainiya dake." Riƙe hannun juna muka yi, kwalla na zuba mana.

    " Nice na jefa ki a ƙaddara, da a lokacin ban ce wani abu nakanki ba da yau rayuwarki bata cikin matsala. Kiyi hakuri da dangin shi da kuma Mahaifiyarshi."
"Mommy ba zan koma gare shi ba, shi daya yayi aure uku bayan Bana nan? Mommy wallahi ina son Mohan, Mommy kinji zuciya tab'a kiji yadda take bugawa, Mommy Mohan wani shashine na rayuwata, amma haka yayi watsi da ni, wallahi ina son shi. Mommy ban san yadda zan gaya miki yadda nake kishin sa ba, shi din mijina ne, Mommy ki min addu'a ko zan sami sauki a zuciyata. Mommy Mohan kamar zinari ne a cikin tsakiyar taku.

   Shi din Kamar ruwa ce min a zafin sahara, kyauta ne da na samu bayan na rasa kome na, Taya ba zanyi kuka ba, amma nagode zan koyi hakuri zan kuma koyi dauke kai, amma Tabbas ba zan iya hakuri a min irin abinda aka miki ba, ba zan iya dauke kai a cutar dani ba, wallahi zan yi magana, kuma idan ka takani zan rama, sai dai idan ba zan iya ba."

Dariya yayi tare da isowa gurin mu.
"Yar Baba gaya mata dai ke ba irinta bace, zaki iya yaki dan kwatar kanki. Karki yarda wani ya taka ki, kina da Uban da zai tsaya miki, ko ita uwar Mohan kyaleta nayi sabida Mohan amma da na mata abinda zata nime ki da kanta, amma bana son haka domin xan fi son ki sami soyayyarta da zuciyar ta, shi kuma Mohan ba yadda kike tunani bane, Yaron yana sonki"
Mikewa nayi ina kunkuni.
"Haka kawai ai da ya damu da Ni, ba zai zauna ba sai ya nimo ni amma bai zo ba yana can ina soyayyar shi da yan mata dama ai nasan nice na takura mishi toh na fita a rayuwar shi. Allah ya bashi hakuri ya cigaba da zama da Kanwa dan Ba'are, Allah zai saka min"
Na fada ina kuka.

    Su kansu dariya na basu domin ba dage sai faɗa nake, zaunar da Ni Abie yayi ya mika min ruwan addu'o'in da kullum yake bani, nasha sannan na sauke ajiyar zuciya.
"Kiyi hakuri" kallon shi nayi kafin, nayi kwafa.
"Wallahi da zan ganshi sai na sashi ya dauki cikin shi nima na gaji, tunda bai da."
"Ai ke kika da hankali tunda gashi zaki sauke mishi cikin ya dauka, rigimammiya kawai" Mommy ta zungure min goshi.

Cikin sabon bakin ciki na kuma fashewa da kuka.
"Abie ka ganta ko? Ni aka yiwa laifi amma ita haushina take ji, wallahi sai na rama akan Mohan duk abinda aka min tunda ya cuce ni"

       "Kyale ta, Uwata haka take bata da kirki, kinji babu wanda zai kuma sa min ke kuka kina da Jarumin Uba irina, ko na miki kiranye Mohan din ne duk inda yake ya sussuce ya fito niman ki"

"A'a!" Na fada,
"Yawwa Yar albarka Ubangiji yayi miki albarka Insha Allah zaki yi kyakkyawan karshe da kyakyawan sakamakon hakurin ki."

   Gyada mishi kai nayi, tare da mik'ewa a hankali. Wato lallabani da Abie yake kamar wata kwai, amma ba zai hana idan nayi rashin hankali ya taka min birki ba. Ashe Benazir ta haukacewa Khalil. Allah Sarki baki daya ta nuna ba zata aure shi ba. Babu wanda ya sani.

***
Niger.

Baki daya ya Surkukurce idan ka ganshi ba zaka dauka Khalil din da ka sani ba zaka yarda shine ba.

"Mohan yarinyar taki fahimtar ba da gayya aka hada auren ba, wallahi duk yadda naso na mata bayani taki, yanzun haka ta yi ta rufe Ni a WhatsApp ɗinta. Mohan ban san inda take ba balle na je."

   Wallahi duk sai ya bashi tausayi, ya rasa yadda zai yi dashi.
"Khalil ban san me zance maka ba, domin kuwa nima ina cikin yanayin da kake ciki, kuma nasan maganar baki ba zata wadatar ba, dole sai da rarrashi. Kayi hakuri Insha Allah zaku dai-dai ta."

     "Ba zata yarda ba, wallahi ba zata yarda ba, duk yadda na bata hakuri taki asalima cewa tayi ba zata aure ni ba, ni da zasu amince da sun duba alamarina "

"Zasu amince mana." Inji Mohan,
"A'a na hakura da ita, sabida itama Umma Umarnin Nahnah take bi, sabida soyayyata ba zan hana Mahaifiyata yiwa nata Mahaifiyarta biyayya ba, Allah ya zab'a min wacce ta fita, akan dangina ba zan zab'e ta, dukda ina kaunar ta, amma na zabi Mahaifiyata na barta"

Wani irin sanyi jikin Mohan tare da kallon Khalil, wani irin Tausayin Khalil yayi wani irin mutum ne shi da yake cike da sonka kowa ya zauna dashi sai tayi rashi mai girma, duk wanda ya rab'a sai ya rasa wani na jikin shi yanzun Khalil ya rasa yarinyar da yake matukar kauna. A hankali ya mike tare da barin gidan su, tunda ya shiga cikin gidan su. Ya sami mahaifiyar shi tana fada da Radiyah, zama yayi tare da daura kanshi a zaman gwiwar Hajiyar shi.
"Ammyn na amince zan auri Jalilah!"
"Haba? Lallai ka kyauta min, Nagode kuma kaga ta samu tarbiyya na gari"

"Ammyn don Allah ki so Maimunari mana! Don Allah ki kaunace ta, wallahi zan miki biyayya"
"Koda zaka dawo da ita, sai naga yadda ka zauna da ita ta kuma samu kwanciyar hankali a rayuwar ku zan duba yadda zaku zauna."

   Lumshe idanun shi yayi tare da sauke ajiyar zuciya, a kai akai yana kuma kara jin kamar ya gama rasata kenan, tabbas ba ji bane ya rasata baki daya, domin yasan ya rasa ta baki daya. Kwallar da yake danne shi, a hankali yake jan numfashi, sabida yadda yake jin kirjin shi tayi nauyi, Yana ji yana gani ya rasa yarinyar da ya kaunata.
"Ammyn me kike so nayi domin ki Huce!"
"Ka hakura da Ita" ta faɗa tana shafa kanshi, d'ago kai yayi yana kallonta.
"Ka hakura da ita bata dace da kai ba! Bata damu da kai ba, asalima matar da ta kai iyayen ta kotu meye zata haifa maka tsiya da bala'i, ba matar zama bane."

"Amma da baki tozarta ta ba, ai ba zata kai iyayen ta kotu ba, me yasa kike manta laifinki hmm Ammyn Kenan,  wallahi abinda aikata shi yake kore min manema na, zan koma gurin Haddir, domin idan na cigaba da zama bakin cikin ki ne zai kashe ni, gashi nan ana zaman lafiya yarinyar da Hammah Khalil zai aura tace ta fasa sabida rashin adalci irin naki, sai ki Cigaba Ni sai ba zan cigaba da zama da wannan abin ba."

      Ta fada tana kuka, sabida tausayin Yan uwan ta, tana kallon abinda mahaifiyar su, amma babu halin magana, babu wanda ya isa ya dakatar da ita..

  Haka ta tasha kuka sosai domin  tana son Safwan amma mahaiyarta,, tayi mata sanadin rashin sa, har abada domin ta samu labarin ya kusan aure, shi kan shi ma ya turo mata hotunan amaryan shi, kuma ya gaya mata yana sonta har kwanan gobe, kawai Mahaifiyarshi yake son yayi mata Biyayya, yana son ta rabu da Mahaifiyar shi lafiya, yana son idan zata sauko karta sauko...
Wannan Pagen yana magana ne fa akan biyayya ga Uwa.... Alhamdulillahi Ubangiji ya jikan Iyayen da suka rigamu gidan gaskiya, wallahi biyayya ga Iyaye shine babban kalubalen wannan zaman kuyi kokarin rabuwa dasu lafiya! Don Allah Karki yarda karka yarda rayuwar ta tashi babu ka tashi zero! Iyaye ba abin wasa bane, iyaye ba abin yarwa bane, karka yarda aci kasuwa a watse iyayen ka basu ribanci kasuwancinka ba, Karfin nasarata Addu'o'in iyayena, karfin Cigaba na Fatan Iyayena, bani da shekaru masu yawa. Amma Alhamdulillahi na rabu da mahaifana lafiya Yar uwa, ki gwada rabuwa da iyaye lafiya sai ki wayi gari ki rasa me kika yi Allah yake rufa miki asiri..... Addu'ar Iyaye ce.... Alhamdulillahi.....
_Kuyi hakuri babu lokaci yau din nan ne, yau addu'ar arba'in makociyata. So dakyar na samu damar typing ɗin su, kuma idan nace sai dare wallahi zan manta daki domin aiki zan shiga_
#Mai_Dambu
[8/15, 4:59 PM] Joindah:  https://www.wattpad.com/1115798063?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=H4PLUmmQMtRivq0LpRHlS38%2Fr1hLcjzt2XEZ3yHCmyzI3xoWStQC02%2FROcdRbxcPubxgSNp7F%2BbsI7AVD0kyhHL5jlei18XLmYIFmbPXjnlRmUgtZXxtCYJkkmcIRyXT
#sun-Aug-2021
HAKKIN MALLAKATA
BOROROJI

~The Journey of Destiny💔~

Mai_Dambu

Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....

BABI NA HAMSIN DA UKU.

Yana son duk abinda zai yi da amincewar mahaifiyar shi, yana son ita da kanta tace mishi ya je ya auro Radiyah, yana bin duk wani sharadin ta, dan a zauna lafiya.

    Shi yasa baki daya yaƙi d'aga hanaklin shi, shi yasa yaki damuwa da irin hukuncin da ya yanke, baki daya ya ki mai da hankali kan Radiyah. Burin shi Mahaifiyar shi, ta ji dadin biyayyar da yayi mata, wannan dalilin da yanayin ya saka shi dauke kai akan Radiyah, kuma ita kanta tana mamakin yadda tunda tace bata son ganin su, har yau bai kuma mata magana ba, bai kuma kallon ta da batun ba.

Dan koda tace ya nime auren Yar kawarta amincewa yayi jikin shi har da rawa, haka da yayi ne yasa ta jin lallai zata barshi ya auri Radiyah, amma sai ta nunawa mahaukaciyar uwar su basu da hankali zata amince mishi.
*
Gefe Mohan ya motsa sosai kuma ya maida hankali, duk da yaki zuwa gurin Jalilah da sunan zance haka bai hana a fasa kome ba, Maimunari ce dai yasan ya rasata kenan. Shi yasa ya rungume auren Jalilah bawai dan yana da bukatar haka ba, kuma yau da gobe yana bukatar kulawar mace, idan ya dubi shekarun shi kara hawa suke, matar da yake so baya tare da ita.

    Dan haka ya watsar da damuwar shi, domin yayi imani da Allah. Tunda mahaifiyar shi taki Maimunari ba zata tab'a kaunarta ba, ya kan zauna yayi dogon nazari akan me yasa kome yazo mishi a jagule! Me yasa kome yake bukata sai ya rasa? Shin ko dan bai kyautatawa mahaifiyar shi ce? Ya rasa gane abinda yake faruwa da al'amarin shi.

             Da sallama ya shigo falon mahaifin shi, sanan ya nemi guri ya zauna, kafin yace mishi.
"Abbu kana jin labarin Maimunari kuwa?" Yayi tambayar a sanyayye.

"Baka tambaye ni, me yasa naki auren Yar Sarkin maradi ba?" Sunkuyar da kai yayi yana wasa da capter din falon.

"Abbu kayi hakuri, nasan tun wata biyu da suka wuce ya dace a ce anyi bikin kuma Allah bai nufa ba, ban san me ya faru ba. Kuma bana son na tambaye ka kar na shiga abinda bai dame ni ba. Ba wai damuwarka bata dame Ni bane sai dai bana son na cika bincike ne!" Ya fada mishi.

"Eh toh da farko yarinyar ta amince amma daga baya taki, wai na mata tsofa, na zata ko wani abu nayi ashe iya kawai girman da nayi ne, shine nace mata toh babu damuwa, kuma Allah yasa haka shine mafi alkhairi." Ya fada yana kallon Mohan da ya sunkuyar da kanshi.
"Mohan Maimunari ta kusan haihuwa, domin cikin ta ya girma. Sai dai kuma tana cikin damuwa ne, domin ko kwana biyu da suka wuce naji labarin bata da lafiya jininta ya haura." Da sauri ya D'ago kan shi yana kallon mahaifin shi.
"Abbu don Allah, ka hada ni dasu, dan girman Allah ka taimaka min, ina son sanin halin da Mata ta, take ciki ne idan ma cire abin cikin za ayi a cire. Ta huta wahalar tayi yawa"

"A'a yanzun take da wata takwas, idan aka cire karfi da yaji, abin cikin ba zai rayu ba..Insha Allah sunce nan da sati Uku zasu mata aikin shi." Kamar Ya fashe da kuka,yana faɗin.
"Abbu don Allah" ya zube gwiwar shi a kasa, idanun shi jajjur.
"Kayi hakuri! Insha Allah akwai lokuta da zaka ganta."

"Abbu kafin nan na kuma rasata kenan, na rasa ta har abada, ina kara hango nisan da take min, Abbu kayi wani abu, sabida ni Khalil ya hakura da Benazir, an tace ba zata aure shi ba dan zan auri Jalilah, don Allah Abbu kayi wani abu, don Allah ka taimaka min kar ya rasa yarinyar da take so, na yarda zan dauki kome amma ban da na zama sanadin rasa masoyin shi."

"Insha Allah ba zai rasa ta ba, ba zai rasa ta ba."

        Sam iyayen su basu san abinda yake faruwa ba, sai da Mohan yayi bayani, kuma koda Hajiya Nuratu taji labarin bata ji zafin Benazir ba, sai ma burge ta da tayi tana son taga mutum na kishin dan uwan shi, uwa uba son kai ƙarara da aka nuna musu,idan wasu ne zasu ga kamar dama haka shiryayyen al'amari ne.
Dan haka ita da kanta ta sami Abban Khalil tayi mishi magana shima ya gaya mata ai ya samu labarin, dan haka suka kira Abie tare da tuntubar shi. Dariya yayi musu sannan yace musu.
"Ai shi ya biye mata ne har da d'aga hankalin shi? A'a kar ya damu tana taya yar uwarta kishi ne, shi yasa take ganin idan tayi haka shima zai ji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login