Showing 39001 words to 42000 words out of 177131 words
rai din na rasa, yana tsaye a jikin window. Ya zuba hannun shi dukka biyu cikin aljuhun wando shi, yana kallon movement na tsuntsaye, sanye yake da riga da wando masu bala'in kyau grey color, sai hadaddiyar gashin kanshi da ya sauka a dokin wuyar shi,he look gorgeous, gashi yayi wata irin tsayuwar da ba zaka tab'a dauka bayi da lafiya ba. Motsin da yaji ne ya sashi juyawa, kafin ya koma kan abinda yaƙe.
Daukar ruwan addu'o'in da yake sha nayi na mika mishi.
Sau daya ya kalle ni sannan ya kuma dauke kanshi yana kallon yadda tsuntsaye suke shawagi.
"Karb'a Hamma Mohan"
Dake babu lafiyan bai ko motsa ba, haka ya cigaba da tsayuwa har zuwa lokacin da na isa gabansa, sai na ganni kamar irin a saka dan tsako a gaban giwa, duk sai na kasa tabuka kome, ina me mika mishi magani, ina kuma fatan ya sha, amsar maganin yayi sannan ya kalle ni, irin kallon nan na marasa lafiya.
Kai hannuna nayi tare da tura mishi maganin bakin shi, gumtsa yayi sannan ya furza min a fuskana, sannan ya kwashe da kakkarfa dariya, yana kallona. Kamar na fashe da kuka, haka nake kallon shi.
"Zaka gani ba zan kuma wasa da kai ba" na fada mishi ina jin kwalla na taruwa a idanuna,
Hankad'a ni yayi na fadi can sai da bayana ya amsa,kallonshi nake kamar zanyi kuka. Wato shi ko a jikin shi sai dariya yaƙe kamar zai shiɗe, haka na bar mishi gurin na fita na koma dakina, sauya kayana nayi tare da kallon kayan da ya zuba min maganin. Duk abinda zai min bai tab'a min ciwo ba, duk abinda zai min baya min zafi, asalima Uzuri na zab'i na mishi a rayuwar shi, domin kuwa ai bai da lafiya. Murmushi nayi tare da kallon kofar.
--- A fusace ya bar gidan, zuciyar shi tana zafi, a bakin kofar fita Malik yayi mishi magana.
"Tsaya malam" cak ya tsaya,
"Meye matsalar ka da Yaron nan ne?"
"Tambaya kake nima sani?" Cikin isa da sanin waye shi yace mishi.
"Gidan nan cike yake da sojoji, tabbas akwai matsala idan ka kuskura kayi wani shirme mara fa'ida, tambaya na da kai na karshe meye matsalar ka da yaron ?"
Cikin karfin hali ya kalli idanun Malik yace mishi.
"Ka je ka tambaye shi" ya juya tare da barin gidan, sam Malik bai wani damu can ba, amma kuma kalmar Almamoon ya tsaya mishi a rai.
_Na sani na sani na sani, Ni ruwa biyu ne?_ shafa kanshi yayi yana jan iska a bakin shi tabbas akwai abinda yake faruwa a tsakanin su.
***
Aiki yake bayan ya cire hular shi, duk da ya maida hankali akan abinda yake haka bai hana shi kara hango gizon Mamoon ba, ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon abin da yake a Laptop din shi, amma ba fahimta yake ba tura na'urar yayi tare da dafe kanshi.
Idan ya fahimci yanayin da yake ciki, lumshe idanun shi yayi na wasu few seconds, kafin ya bude akan na'urar wanda yake ganin kamar hoton Almamoon ne shimfid'e a kai. Murmushin sa yanayin Yaron kamar ba namiji ba, dafe kanshi yayi tare da mik'ewa yana me bude firjin din kusa dashi ya dauki goran ruwa, ya bude bakin ya kafa kan shi sai da ya sha rabin goran, kafin ya d'ago kai yana me bude window Office din shi da yake inda ake koyawa sabin sojoji training. Ltn Khalil Ibrahim Dan Ba'are, yana kallon yadda wani matashi yake ta ƙoƙarin, sai ya tuna mishi ranar da suka bar Almamoon a asibitin.
Abinda ya tsaya a ranshi yadda yaron yake zubda kwalla, tare da nuna cewa yana son zama da Mohan. Shafa kanshi yayi tare da kurawa hoton Mohan idanun. Yasan Mohan sanin gaske koda ua dawo hankalin shi bai zama dole ya kula da Almamoon ba.
D'aga wayar shi yayi tare da kiran Malik bayan Malik ya dauka sai da ya Lumshe idanun dhi kafin ya sauke ajiyar zuciya.
"Ya Mohan da jikin?"
"Yallabai da sauki sosai"
"What about Mamoon?"
"Gashi can"
"Ok bashi"
"Toh"
Yana jin lokacin da Malik yake kiran shi, "Hamma Malik waye ne?"
Ya tambaye shi yana me daura wayar a kunnen shi.
"Mamoon!" Ya kira sunan shi sound tone. Kamar ba zai iya kiran shi ba.
"Hamma Na? Ya aiki? Baka zo mana ba"
Cikin wani irin farin ciki, Dan Ba'are ya shafa kanshi yana faɗin.
"Cuter Brother zan dawo, Insha Allah ya jikin Mohan?"
"Jikin Hamma Mohan da sauki sosai, kuma dai ya daina firgita. Sai dai toh Allah ya kyauta"
"Gaya min meye?" Ya tambaye shi yana murmushin jin dadi, shima Almamoon murmushin yayi sai da Dan Ba'are ya cire wayar a kunnen shi, yana jan ajiyar zuciya, sannan ya saka wayar a record, ya maida kunnen shi.
"Almamoon! Gaya min meye yake faruwa?" Ya tambaye shi a daukence,
"Hamma ai babu kome,"
Ware idanun yayi kamar yana gaban Almamoon.
"A'a gaya min dai"
Ya fada da wata irin murya yana murmushi,
"A'a fa Hamma na, kawai Hamma Mohan bai jin magana, idan ka zo sai yayi tsallen kwado sau goma, kuma dama d'azun na rike mishi kunne, sai na mishi bulala da tsintsiyar kwakwa."
Zaro idanu yayi tare da cewa.
"Mohan Mamman Nasir Aghali din zaka zane?" Ya tambaye shi yana dariya, kamar wanda yake gaban dan Ba'are ya shiga kunkuni.
"Toh ka san meye yake min?"
"Gaya min ina jinka?"
"Yawwa wancan ranar zuba min magani yayi a jikina, jiya kuma ture keyata yayi na faɗi, yau kuma ina tsaye kawai sai naji ya dauke ni sama, gaskiya yaci na mishi duka."
Wani irin abu yaji yana dukar kirjin shi.
"Amma bai maka kome ba ko?" Ya tambaye shi kirjin shi yana bugawa very faster. Shi Almamoon bai fahimci ma'anar tambayar ba dan haka ya kwashe da dariya yana faɗin.
"Ai yayi min kome, shi yasa nake son kazo muyi mishi bulala domin ya daina min haka"
Kasa magana yayi jikin shi har wani rawa yake.
"Hammah na kayi shiru baka ce kome ba?" Yadda yayi mishi tambayar yayi mugun kashe mishi jiki, kuma dama ga muryan Almamoon ba irinta maza bace.
"Hmm" yace mishi, shima Almamoon ya sake murmushi yana faɗin.
"Hammah na zan tafi na kula da abincin" ganin zai kashe wayar yayi saurin mishi magana.
"Almamoon! Don Allah ka kula da kanka."
Shafa kanshi yayi sannan kuma cigaba da cewa.
"Karka yarda wani kazamin wasa ya shiga tsakanin ku, ka tsaya a mai kula da lafiyar shi, please"
"Toh shi kenan" ya fada a sanyayye,
"A'a ban ce karka kula da shi ba fa kawai ka kula da yadda kuke mu'amala ce, bawai ban yarda da kai bane na yarda da kai, dan haka ka kula da kanka"
"Toh babu damuwa" suka yi sallama, Malik yana amsar wayar ya shiga masifance shi.
"Tsabar shashancin taya zaka bar yaro nan shi daya yana kula da lafiyar Mohan? Baka san nauyin zai mishi yawa ba? Karka kuma bana son haka, ka saka ido akan su, Allah ya bashi lafiya"
"Am sorry Yallabai" ya faɗa kamar yana gaban shi,
"Ya Wuce" sannan ya kashe wayar shi, yana kuma hasashen yadda Mohan yake kokuwa da Almamoon, dukar tabirin gaban shi yayi yana me jin babu wani dad'i.
"Toh me yasa nake jin babu dad'i? Me yasa nake jin kamar ana cutar da yaron?" Dafe kirjin shi yayi da yake bugawa kamar me,
Kafin ya dauki sauran ruwan shi ya sha, yana jin kamar zuciyar shi zata kama da wuta. Shafa kanshi yayi ta yi, yana kuma sauke ajiyar zuciya. Wannan wacce irin jarabbtace haka? Zama yayi tare da kallon sama, yana nazarin meye yake shirin Faruwa da shi, a iya sanin shi dai Almamoon namiji ne irin shi? Kuma bayan haka babu wani abin da zai alakanta shi da mace, dafe goshin sa yayi da yatsu biyu na hannun shi.
"Ina ruwan mahaukaci, kowa yaji labarin nan sai an nemi saka ni a turu, dariya ne kuma ya kama shi yana yi yana shafa kanshi, Tabbas ya cika babban mahaukaci, duk me hankali yaji abinda yayi sai yayi dariya balle kuma kuma mahaukata yan uwan shi.
***
Wasu manyan mutane ne su uku, suka shiga wani sunkurun daji, bayan sun yi tafiya me nisa, kafin suka fara nufar wata tsohuwar hanya. Sai da suka yi tafiya me nisa, suna jin kukan wasu irin dabbobi masu matukar ban tsoro, wata siririyar hanya ce da zata kai su wani gada, haurawa suka yi, kowa yana nad'e babban rigar shi.
Suna isa bakin kofar wanda yake sakale da Kwarangwal din mutum, suka shiga cire kayan su, tare da kwab'e kome na jikin su. Haka suka shiga cikin gidan, inda wasu yan mata suka taso musu da kwarya a hannun su, suka yi ta zuba musu wani irin ruwa, a saman kansu, kafin suka zuba gwiwar su a kasa, aka kuma basu wani irin ruwa suka shanye tass, rike hannun su yan matan suka yi har zuwa kofar dakin da bokon yaƙe.
"Ina la'annnu suke? Ina marasa rabon suke? Ina tsinannun la'annnu suke? Ina marasa rahama suke, Ku zo ga la'anannen arnen nan a gaban ku."
Dariya suka saka tare da shi, sannan suka shiga d'akin, tare da zuɓewa a gaban shi kamar masu sujada, kallon shi suka yi ganin wata budurwa kyakyawa akan cinyar shi, yana having sex da ita, duk da ya tsufa bai hana shi jin kanshi kamar wani matashi ba.
Kallon juna suka yi, kafin yan matan dazun suka shigo dama suna sanye da wata fatar bauna na ya rufe musu gaban su, sai ganye da suka rufe kirjin su dashi. Suna shigowa suka wuce gaban su, tare da kallon su.
Kowacce ta zauna akan cinyar mutanen a hankali sukayi ta kazamar mu'amalar su a gurin, kafin suka fara kokarin zubda ruwan kazamtar su, dan shi ya riga su gamawa, yana tashi ruwan shi da na yarinyar zubawa yayi a wata tasa,.mai fadi na zinariya, suma haka suka juye nasu a tasar, kafin Yan matan suka dauki wani irin abu kamar ludayi suka saka a gaban su, ruwan ya fito, suka juye a tasar, kana suka fita a d'akin. Tura tasar yayi can lungu, suna kallon gurin wani katon guza ya fito a hankali ya saka kanshi yana lasar kazamin maniyyin su.
Yana gyada kanshi. Irin dadin da yake ji. Kara watsa wani abu yayi akan guzar,ya cigaba da lasar maniyyin su, har ya shanye tass. Ya koma lungun da yake, kallon su yayi. Tare da gyada kanshi. Jinjina kai yake yana kara jin wani irin gamsuwa, kafin ya kalli manyan mutanen.
"Har ni za a lalatawa darajojina?"
Watsa izgar yayi tare da kura mishi ido. Wata uban kara ya kwala tare da mik'ewa jikin shi yana rawa.
"Waye haka?"
Hoton Mohan da Almamoon, suka kokuwar zai bashi magani, bayan ya sha, ya fadi aka cilla Almamoon gefe, dakin ya dauki duhu, can sai ga Mamoon ya saka karatun Alkur'ani a wani radio, ihu da aljanun da suke tare da Mohan suke tare da yagar kamar jikin su, suna watsarwa.
A tare bokan ya kuma tura wasu aljanu, basu kai da shiga cikin gidan ba, suka dawo a guje. Karshe da ya nace sai ya tura wannan guzar ce ta kuma fitowa tare da sake wata irin kara kamar karan Aradu. Cikin fusata da b'acin rai ya shiga aikin babu kama hannun yaro, yanayi yana watsa wata irin mai me kama da jini, yana karanta ɗalasuman tsafi..watsa manyan yaƙe,
Zunzurutun taurin kai da bala'in zafin rai yake aikin domin gani yake idan ya kasa tankar ya gaza ne, taya za a cigaba da zuwa gare shi? Taya zai iya fuskantar mutane da cewa anyi galaba akan shi.
Ina karya ne! Watsa man yayi wata irin koriyar wuta tayi sama sai da yaja da baya, take ya kuma dawowa cikin ƙwayar tsafin ya zauna. Yana yi yana juyawa.
"Karya ne! Ba haife su ba, basu isa ba, da Ni zasu ja? Har sun kai matsayin da zasu buga dani?"
Ya nuna kanshi s fusace yana aikin,.yaki ya saduda dan haka wutar tayi kanshi da karfi, dole ya juya tare da matsawa da baya. Cikin mugun tsoro sannan wutar ya kuma komawa cikin ƙwaryan.
Ranshi ne ya b'aci, ya shiga aikatawa su Almamoon da wasu abubuwa da ban tsoro, yana kuma diban ruwan jini a wata kwarya ya bude wata kwarya ya saka hannun shi, kwari da tsutsa ya kwaso, ya zuba a cikin jinin nan yana karanta wasu mugayen ɗalasuman tsafi, munana ya d'aga ƙwaryan sama. Wadanan kalaman har da wasu kalmomin Arabia, tare da sunan Allah, kafin ya sake ƙwaryan a tsakanin sama da kasa, yana ambaton sunan Allah.(Look da gaske akwai kitabul sihir, na niman mallakar manyan ifiritai. Dan haka a sani akwai kalmomin sihiri wanda yake basu damar mallakar djinn)
Su kansu masu nima a gurin shi hankalin su ya tashi, balle shi da yake aikin ba karamin bala'in wahala yake ci ba, kuma yaki ya nuna yana cikin damuwa, sai da ya sauke wannan shaidanin aljanin me kai kamar na maciji ta tura shi, sannan ya mishi magana akan lallai ya tafi ya shiga jikin Mohan, ajiyar zuciya ya sauke bayan aljanin ya shiga cikin ƙwaryan, ya cigaba da had'a wanda zai hana yana kallon ƙwaryan.
Bayan kamar mintinan ƙalilan, sai ga dakin da suke yana girgiza, kamar za a fasa dakin, duhu ne ya mamaye d'akin, kafin wani abu ya fado dakin kamar wani katon dutse dif.... Ya dira a gaban su.
Huuuhuuuuhuuuuu!!!!" Ya fashe da kuka, yana ihu yake yana burgima.
"Karkuzu ka aike ni gurin da aka lalata min jikina wayyo ni, wayyo ni rayuwata." Burgima yake.
"Tashi munkiri tashi mara kunya, har akwai mutanen da zasu ja dani?"
Da sauri ya b'ace rashin a b'ace. Ya kalli Mutanen cike da bakin cikin yana me jin wani matsanancin kunya da faduwar darajar shi. Ya nuna musu hanya tare da dauke kai yace.
"Ku dauki ƙwaryan jinin da zaku gani a waje ku had'a tare da jaririn mage da kuma jinjirin jaki ku binne su da ransu."
Haka suka mike tare da mishi sujada, sannan suka fita da bayan sun.
Suna fita yan matan suka wanke su da ruwan bayan sun basu wasu kananun kwarya me dauke da jini.
Kafa kansu, suka yi sai da suka shanye tass, sannan suka yi gatsa. suka fadi bukatar su tare da yarda akan shi zai iya musu, tare da barin gurin, suna isowa suka kwashi kayan su, suka bar gurin.
***
Yau kam yafi ko yaushe bani wahala, domin kuwa ban tab'a jin ko ganin tashin hankali ba tunda na bashi maganin, nake tsaye a bakin kofar. Cak naga ya mike kafin kuma ya fara amai, yana yi yana jijjiga, shigowar Malik ya sashi kura mishi ido shima, yana mamakin wannan al'amarin.
Can ya fasa ihu, wanda ya sa dakin ya amsa. Kwanciya yayi yana burgima. Kafin ya fara karkarwa can kuwa sai ga dakin ya kama jijjiga, karatun Alqur'ani muka kunna, haka muka yi tashan wahala kafin can ya lafa, bayan ya gama gwara kan shi a bango.
"Alhamdulillahi" inji Hammah Malik, ajiyar zuciya na sauke ina kallon shi, kafin nace mishi.
"Da saura fa, dan har yanzun bai dawo hayacin shi ba. Ina jin sai mun had'a da limamin masallacin Makarantar mu ne Insha Allah"
"Eh toh Allah yasa a dace."
"Amin Ya Allah," muka bar dakin bayan mun gama gyara mishi kwanciyar hankali.
* Wannan karon kudina ma gida na kai, sabida ban tafi hutu ba ne zauna a jikin Hammah Mohan, koda naje gidan Innah ta kasa ta tsare. Sai dai itama kamar Malam Ansar ce domin kuwa ce min tayi.
"Karka ganka cikin gidan kudi kayi tsammanin Allah baya ganin ka ne, kasan waye kai ka kuma san yadda halittar ka yaƙe, karka sake naji wani abu ya fito, ka kame kanka domin masu kudin nan ba kirki ce ta wadacce su ba.
Domin na lura da kwaɗayi na damun ka, nan Malam Ansar ya kawo min korafin rashin mutuncin da kake mishi Almamoon!" Ta kira sunana. Cike da tsoronta nace mata.
"Inna shima me yasa baya jan girman shi. Sai ya"
Kai mun duka tayi abinda bata tab'a yi ba, sabida Malam Ansar tayi min.
"Kai min shiru butulu kawai, kasan kanka ai, kuma da yake kwadayi ya rufe maka idanun."
Idan na fahimta malam Ansar yazo ya had'ani dasu Innah ne, lallai ka bar mutum a inda yake, ban yarda nayi wani abinda zai saka tayi fushi ba, na kwantar da kaina nayi ta bata hakuri, har ta sauko.
Muna cikin ji Baba ya kawo min maganin da zan cigaba da bashi.
"Assalamu alaikum! Sannun ku, Mamoon kana ta jirana ko?"
"A'a kawai dai zan isa da wuri yasa na kagu."
"Toh Toh,,, gasu nan dai sai dai ban sani ba ko zai amince ya ci, wannan garin maganin Insha Allah idan ka karanta suratul Yasin, zaka tofa ko ka rubuta mishi, sai wannan zaka had'a zuba a wani mazubi me kyau kayi ta bashi yana sha, wancan me suratul Yasin, duk wanda yayo mishi sharri zai koma kanshi kaikayi kenan, wannan kuma suratul Rahama zaki karanta mishi, duk inda aka nufi shi da sharri zai kasance yana kaucewa ba tare da ya sani ba.
Wannan kuma Insha Allah zai kasance mishi kamar a saka wani abu ne s jikin shi, babu karfe ko itaccen da zai yi tasiri a jikin shi.
Wannan kuma Insha Allah zai taimaka mishi gurin, gano duk me shirin cutar dashi, Allah yasa mu dace"
Haka bayan mun gama na ce mishi.
"Baba dama maganar gidan fa?"
"Eh Almamoon mun gama kome sai dai muje ka gani, ko kuma."
"A'a muje dai" na fada mishi, haka muka tafi gidan, muka duba yayi kyau kuwa, ba laifi daga nan muka sami me gidan muka zanta dashi tare da cewa.
"Kayi hakuri Insha Allah nan da kwana ashirin zan kawo maka kudin ka, Nagode"
"Karka damu, Allah ya kai mu lokacin." Haka ya faɗa tare da rufe gidan, Ni da Baba muka nufi tasha. Bayan na sami motar Maradi muka yi sallama da Baba na Danka mishi