Showing 135001 words to 138000 words out of 177131 words
daren, zan hada maka kome kuma zan sayo jarunta a wannan daren sabida kar na hanaka sukunin aiwatar da muradinka, Hammah Mohan daga wannan daren karka tausaya min ka fanshe duk wani soyayyar ka, a cikin shi ka nuna min sakamakon kaunar da kake min Ni kuma zan boye kuka na da kome zan baka kyautar daren, zan tsara maka daren ya zama mafi girma da darajar, zan Kawata maka shi. Zanyi kome domin ka, hmmm sannan zanyi kuka da!"
Murmushi yayi tare da zungure goshina yana dariya.
"Idan kika yi kukan zan rarrashe ki, zan baki kyauta na musamman, nan dan mallaka miki zan baki dukkan shi zuciyar taki ce, zan zame miki farin dare zan raya miki daren da so da kauna, zan shirya miki shagalin da ba zaki tab'a Mantawa, ranar zan baki kyautar kaina baki daya, zaki ganin iya ganin idanunki, zan tsaya a gaban ki na juya ki ga irin mijin da kika aura. Ubangiji ya bamu yawan rai yadda zan share miki kukan ki, Ubangiji ya nuna min yadda zan sanyaki farincikin a wannan daren ya rabbil alamina ya nuna min yadda zan kayata miki daren ki! Ina addu'ar ki same ni a yadda kika sannin kika yi fatan haka, akwai shagali yarinya babu tausayi babu ruwana da Yarantarki! Zaku hadu da katon tuzuru ne!" Rufe mishi baki nayi ina zare ido....
#Mai_Dambu...
[8/14, 8:18 AM] +234 815 778 5691: https://www.wattpad.com/1113398663?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=%2BxTW4N%2Fi3%2B1dAQX5gbjmfTxgxiRMRb8Nl%2F50OD4pV94UP35Ih%2FrlfzEmYSOqSePFjk4F6wQI4BmDexcUn1v%2B6q7S5wMuA0Uc%2FC5OPGYtcFd9ON0zvTrtgtJg8WkJ5LAn
🐂🐂BOROROJI🫀🫀
~The Journey of Destiny💔~
Mai_Dambu
Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....
BABI NA HAMSIN DA HUƊU.
*Ana ta zare idanu 🙄🤡🙋🏾♂️*
Ni a karan kaina nasan ina son Mohan, kuma shima ya san da haka,shi yasa na b'ata lokaci ina hira dashi tare da bashi labari. Kafin na kalli agogon dakin na zare hannuna cikin nashi.
"Zan tafi!" Na fada mishi,
"Bana son kiyi nisa dani, amma babu yadda na iya, Allah ya kiyayye hanya, ki kula min da kanki" murmushi nayi mishi sannan nace.
"Insha Allah! Amma ka godewa Allah da Abbu da Abba da Wallahi sai dai ka nime wacce take." Rufe min baƙi yayi da nashi.
"Don Allah a bar zancen kawai, wallahi ina son mata ta haka." Cizon hannunsa nayi tare da kura mishi ido.
"Ahhh!" Sannan ya sumbaci gurin, yana murmushi.
"Ina sonki"
Girgiza kai nayi, tare da ɗaukar jakata na fito. Na same su har wasu sun zo.
"Don Allah, ki tuna yana da kane irin wannan sakawa a lungu, baki daya. Toh Allah yasa kar muzo cin shinkafar amarya a hana mu ganin ango."
Kasa magana nayi domin Salman yana da raha kamar dan Film.
"Toh zan tafi, na gama abinda ya kawo ni Niamey."
"Ke dai kice zaki gudu an kusan amarcewa"
"Sai anjimar ku" na musu sallama na tafi, sannan suka shiga dakin sun same shi kamar mai barci.
"Munafuki idan zaka bude ido ka bude domin yarinyar ka ta nuna mana ka farka." Inji Dan Ba'are Ya fada tare da kallon shi. Gyara kwanciyar shi yayi tare da cewa.
"Dan Ubanka idan ban tashi ba sai ka d'aga ni"
Nan suka shiga fadar su ta gado, dan zance ta gado. Kafin suka shiga taimaka mishi yayi wanka da alola, yazo ya gabatar da sallah da yake kanshi Allah Sarki. Yana yi yana huta. Haka ya sauke sallah da yake kanshi, ana hira da shi Ammyn ta. Shigo ita da Maman Hanan ko inda suke bai kalla ba, sai b'ata rai yaƙe,
A hankali sauki yake samuwa, tare da sanin kulawa daga yan uwan shi, da mahaifin su amma fir yaki amincewa Hajiya Lateefah, sosai yaki sake jiki da ita, idan ya fara waya da Maimunari kuwa kowa sai ya tashi inda yake, domin kasa kasa yake maganar kamar ba zai yi ba, baka tab'a jin abinda yake faɗa.
Satin shi daya aka sallame shi saura sati biyu bikin su. Ba karamin shiri ake ba,duk ta inda kake tsammanin abin ya wuce haka, bikin saura kwana tara aka kai kayan lefe, akwati ashirin da hudu (😏😒☹️ saura kuce zuki tamalle🤣😂) tare da kyautar motar sabuwa jaguar, kukan da Innah keyi Allah kadai ya sani, domin babu wani da zata ce danginta ne sai Al'ummar Annabi, sune suka mata kara, dama tun kafin a kawo kayan Radiyah ta turo min, da ranar da za a kawo, tuni na dawo gida na shiga Niman inda za ayi mana abincin alfarma. Tare da kayan ciye ciye dake ban san yadda ake abin ba, sai da ta gaya min.
Na kawo kayan drinks aka ajiye, sai da na gama kome tare da bawa Innah kudi me yawa ta basu tukwaici. Aikuwa haka ce ta faru. Amma Innah taki amsar motar da gwala-gwalan cikin kayan.
Atamfoffin kuwa kamar shagon sayar da kaya za a bude, haka akayi ta kirga su har suka gaji suka bari, tunda na ga kayan gabana ya tsinke, ban kuma samun kwanciyar hankali ba, ga mugayen mafarkai da suka sani a gaba, a tsakanin kwanakin har saukar Alqur'ani sai da nayi, ana saura sati za a saka ni a lalle na koma gida bani da kawa bani kowa sai su Salihu Muhmuda, sune abokaina dan haka da su muka yi ta zirga-zirga.
"Malam ina jin tsoron Allah ina jin tsoron kar wani abu ya faru, ina tausayin yarinyar nan wallahi ba zan iya daukar tashin hankalin da zata ji ko zata gani ba." Inji Innah,
"Babu abinda zai faru, sai Alkhairi." Baba ya gaya mata.
Shiru tayi tana kallon kasa, kafin ta sauke ajiyar zuciya, tana wasa da abincin da yake gabanta.
"Naji tace zai tace zata Niamey, ban san me zata je yi ba."
"Eh wannan alkalin zata kaiwa katin gayyata na bikin, kuma Insha Allah zata dawo ana saura kwana kwana uku."
"Toh Allah ya nufa, ina tsoron abinda ya faru"
"Don Allah idan ba zaki fadi Alkhairi ba kiyi shiru."
***
Washi gari da asussuba nayi sammako sai tasha. Ina zuwa motar farko zata tashi Allah ya soni na samu guri.
Ina biyar kudin tana d'agawa bakina dauke da addu'a, haka muka dauki hanya.
..
Diffa.
Juya mishi baya Uban yayi, tare da kin sauraron shi, yana jin yana magiya.
"Don Allah ka ajiye kudirinka na cutar da ita, karka manta wallahi ba dan kudirinka nake aikin nan ba, ina sonta don Allah karka cutar da ita don Allah" a fusace ya juya da sandar Azurfan shi ta tsafin ya buga mishi a goshi.
"Kai ka isa ka hanani farin cikina! Ka dauko min ita ka kasa, kayi min abinda ya dace ka gaza anya ni na haife ka kuwa? Wallahi da kai jini na ne ba zaka tab'a ɗaukar mace da daraja, macen da rigar sawarka tafita daraja itace kake rokon kar na mata kome!"
"Ita nake so ka dauko min ita, so nake ka daukota ka kawo ta nan! Idan ma soyayyar ta kake ji a ranka toh ka daina, domin ita din da ni, gumin mu ake son ya hadu guri guda, daga nan kuma ina zaune mulki zai zo min har inda nake" cike da mamaki yake kallon Mahaifin shi wato abar kaunar shi ce zai kwanta da ita.
"Tab wallahi babu wanda ya isa yayi min wannan gangancin na dauka, yarinyar da na gama cin bakar azaba da duka sabida ita, toh ai gwara ka tsine min albarka da na kawo maka ita, kai dai ka kare a gurgunta amma ita wancan kayar tawa ce.
Kuma na rantse idan kayi gangancin aikata wani abu, hmm toh wallahi sai na zame maka alakakai, kana ji kana gani zan kashe ka, kaiii Dattijo ban damu ba dan baka dauke ni a d'anka ba. Amma ita ka tab'a inuwarta wallahi sai na binne ka da ranka. Ita din guguwar sauyin ƙaddara ta ce, dama daya tak nake jira kuma Insha Allah na kusan samu idan ka gadama ciwon daji ya kashe ka ko ta zuciya"
Daga haka ya juya zai fita ya tsaya tare da cewa.
"Daga yau zan zame mata inuwarta duk inda ta shiga ina biye da ita, kai kuma zan zame maka tankar tafiyar Ajali domin duk lokacin da ka ganni tabbas mutuwarka ce tazo maka. Ba zan d'aga maka kafa kana Ubana ba, zan maka kisar munmuke da sai kayi danasanin haifata da kayi. Kaiii Wa'adi Ansar wallahi idan har jininka na mugunta da keta be bin kowa lungu da sako na jikina wallahi na rantse da wanda ya mallaki alrshi sai na maka kisar da ko gawarka sai ta bawa kowa tsoro. Karka tab'a Maimunari domin ita ruhina ce. Idan kuma kana ganin haka da sauki.... Ma gwaji ya gwada"
Yasa kai ya fita tare da dukar kofar fita daga gidan, rintsa idanun shi yayi da mugun karfi, yana jin yadda Hisham Waadi ANSAR yake mishi barna duk wani abu me daraja sai da ya lalata a gidan, sai da ya fasa kome har da motocin gidan, sannan ya kwashe kayan shi ya nufi gidan shi da yake wajen gari ya kwanta.
Bayan an mintinan wayar shi tayi kara. Kamar ba zai duba ba ya dauka.
*_Saura kwana biyar bikin Maimunari da Mohan!_*
A zabure ya mike tare da danna wayar jikin shi yana rawa.. ya kira ta.
"Maimunari! Meye nayi miki da kika tsane ni? Haba ashe soyayya zata zama k'iyayya? Ina sonki sannan ina miki fatan Alkhairi, naji zaki yi aure. Allah ya cika miki burinki."
"Malam Ansar ba wai naki ka bane, sai dai tun farko na gaya maka kai dan uwana ne, Hammah Mohan kuma Masoyina ne, shi na fara so. Kai kuma na shaku da kaine, ka fahimta mana so daban shakuwa daban. Wallahi ban tab'a jin soyayyar ka ba, amma kayi hakuri ba cin fuska bane! Wallahi kasan hali!a bana boye abinda yake raina, kayi hakuri kaji"
"Na hakura kanwata, karki manta ki dauke ni abokin shawaranki Insha Allah zan zo daurin auren da duk wani shagali da Ni za ayi."
"Kai Hammah na, nagode sosai da ka fahimce ni, kuma naji dadin haka don Allah ka gafarce ni, yanzun haka ina hanyar Niamey ne zan kai katin auren amma ina ganin gobe Insha Allah zan dawo zan bi jirgin sama."
"Ai girmanki ce, Surukar shugaban kasa, idan baki biyo jirgi ba ai nayi musu ba'a, karki manta Insha Allah duk abinda kike bukata ki gaya min Insha Allah ni kuma zan cika miki burinki, karki manta da haka ina kaunarki har kwanan gobe, amma yanzun ya koma ba yan uwana"
"Gaskiya Nagode da samun babban masoyi irinka, Ubangiji ya baka wacce ta fini don Allah kashe kiran surukinka ya kirani"
"Toh!" Ya fada da sauri bayan ya kashe kiran, very sad ya kalli wayar, sannan ya sake murmushin farin ciki, kafin ya mike ya nufi ban daki, yayi wanka sosai cikin nishadi da jin dadin.
**
Yana kashe wayar, na dauki wayar Hammah.
"Ranka ya dade! Mazaje."
"Hmm! Sarauniyar kyan zuciyar Hammah Mohan! Dawa kike waya?"
"Kai Hammah! Da abokin karatuna ne fa!"
"Ok na zata wani saurayi ne ya kira min mata nasa sojojin kasar Nijar su dira a kofar gidan su, a dauko min shi a kai!"
""Kai Hammah Mohan! Lafiya? Akan me? "
Cikin murmushin kasaita yace min.
"Sabida ya kula matar Babban sojan" dariya na saka ina kara gyara zamana, ina faɗin.
"Toh gani a hanyar garin ku, Niamey"
"Don Allah? Toh a ina zaki sauka?"
"Toh ai kaji irinta, wallahi sai gidan Abie domin na gaya mishi tun a tasha. Kuma yace min idan zan koma a jirgi zan koma!"
"Toh ni dai Allah ya gani na fara kishin wancan tsohon ina dalili ya zake dayawa da!"
"Allah Sarki,wallahi kamar mahaifina nake jin shi, idan kace na daina kula shi sai na daina." Na faɗa.
"A'a ban isa ba"
"Ka isa mana."
"Hmm! Har yanzun ban warke ba"
"Ayya dama kaji ciwo ne?" Na fada mishi ina dariya.
"Gaskiya kin jiwa zuciyata ciwo? Kuma zan rama duk ranar da zan rike ki a hannuna sai kin gane" katse wayar nayi ina dariya, kafin na share zancen shi.
Har muka isa Niamey ina jin nutsuwa a raina, Driven baba yazo daukana. Ina isa gidan na sami motar Hammah MOHAN.
"Sannun da zuwa Uwata, Sannun Uwata an kusan girma."
"Ooh Abien Moonah sonkai tsirara, ina laifin ka min kara ka maidani kamar Bature tunda nazo ruwa kawai ka bani, amma tunda Moonah tayi sallama ake jera wancan table din Abie dan ban gaya maka zan zo bane?"
"Abie Hammah Mohan kishina yake, dan yaga kafi sona" na fada ina murguda baki, kwafa yayi irin zamu hadu dake.
"Abie kaga tana murguda min baƙi!"
"A'a Abie shi yake harara na"
"Toh Mohan ya daina Harara. Maimunari ta daina murguda baki."
"Abie"
"Muje muci abinci sai kiyi wanka ki huta,"
Haka kuwa ta kasance bayan na gama cin abinci nayi wanka da alola na.gabatar da sallah da ake bina da kuma na magarib da isha.
Sannan ya tara mu, yayi mana nasiha akan rayuwar mu da kuma wanda zamu fuskanta, sannan ya kara mana da kyautar da ya bani, tare da wani katon gida a Zurich ƙatuwar gida ce, wanda har kwanan gobe ana tayawa yaki sayarwa.
"Ga waɗannan sune wanda na baki su, bansan me zan baki ba, amma ina jinki har cikin jini na, Allah ya albarkaci rayuwar ku."
Mun yi hira sai da Abie ya kore Hammah Mohan, amma sai ya tafi zai kuma dawowa, yace yayi mantuwa haka dai karshe Abie ya turo ni, tunda na shiga motar shi na bige da barci. Fitowa yayi daga daya gefen sannan ya bude inda nake, ya dauke ni.
Cikin gidan ya wuce dani, Abie yana zaune. Ya shigo dni.
"Ina zan kaita?"
Nuna mishi dakin yayi tare da shiga da sallama, dakin ta yara ce aka ware shi, domin akwai kayan wasa kala kala. Sannan ya kwantar dani bayan yayi min addu'o'in, Kafin ya ja min kofa ya fita.
**
Washi gari.
Da wuri na farka, na kuma shiryawa sannan na karya kafin Abie da kanshi ya kai ni. Airport,
"Uwata gashi kin kawo katin bikin ni kuma zan tafi Nijeriya taron bita na Alkalai, ban sani ba ko zan sami daurin auren amma duk yadda za ayi zan zo ayi dani."
Idanuna ne ya cika da kwalla.
"Toh shikenan!"
"Kiyi hakuri Insha Allah zan zo"
"Toh" nace ina share kwalla, haka kawai nake ji idan da Ubana ne babu abinda zai hana shi zama a daura aurena amma yau sai gashi ina niman ina ma zan ga Ubana su ko tausayina basu ji ne da suka tafi suka bar ni. Ba zan taba barin dana haka ba, har na shiga jirgin yana d'aga min hannu.
Bayan tashin shi yake kara jin babu dad'i, idan da yar shi ce babu inda za shi dole ya zauna ayi kome akan idanun shi, Allah sarki. Haka ya fada.
Yana komawa gida Mohan na zuwa sosa kai kai yayi sannan yace.
"Abie mun ina kwana?"
"Toh ta tafi lafiya lau!"
"Haba?"
" Zan maka wasa ne?"
"A'a ya faɗa tare da sunkuyar da kai yana kara jin girman Abie yau sosai.
"Toh, Allah ya sauke ta lafiya. Zan tafi"
"Ka gaida gida"
**
Karfe goma da rabi na isa gida na samu ana ta hidima.
... Biki ake sosai a gidan duk har. Ana gobe daurin aure aka sani a lalle, haka kawai zan zauna nayi ta kuka, sun zata kawai dan zan rabu da Innah ce a'a kawai kukan tausayin kaina nake ji.
Ranar sha biyu ga watan Maris aka daura aurena Ni da Hammah Mohan, da misalin karfe sha daya na rana, a babban Masallacin Damagaram, ana daura auren babu b'ata lokaci aka dauke ni a jikin Innata, ina kuka tana kuka. Haka muka nufi Niamey.
Ba zan manta da wannan al'amarin ba.
Niamey.
Tunda muka isa da yamma aka fara wani irin biki na fitan hankali..
**
"Boka kayi wani abu, bana son yarinyar ta shiga cikin gidan."
"Ai kin makara, shiga kuwa tuni ta shiga. Ni dai ku tafi bani da abinda xan muku idan kuka nace min kayana konewa zasu yi kutashi kafin masifar da kuka lakato ta same ni"
Koran kare yayi musu cikin kunar rai suka fito, kamar mahaukaciya Hanan take kuka tana ihu, garin haukarta ta taka wutsiyar maciji,a fusace ya zabga mata sara, tana ganin shi ta fasa ihu, tare da faduwa uwarta ma ihu ta fasa, haka Bokan ya fito ya same su. Ganin sarar maciji ne ya koma cikin Bukar shi ta dauko magani ya shafa mata, shine ta farka. Ya bata wani tasha. Tayi amai sannan yace musu.
"Maza ku tashi, gaba da gaban ta, yarinyar Allah yana tare da ita, idan kuka nace zaku mutu maza ku b'ace min da gani"
Jikin su yana rawa ta dauki Hanan suka bar gurin.
**
Ana ta shagalin na bikin babu wanda ya damu da kowa, sabida harkan arziki da ake.
"Hajiya kinyi bako!"
" A wannan lokacin! Kana ganin z a kai amarya d'akinta ne don Allah yayi hakuri Kuma kaga yanzun aka gama liyafa."
"Wai abin yana da muhimmanci ne don Allah ki zo"
Haka tafita ba dan taso ba, bayan ta haɗu da bakon, ta dawo jikinta yana rawa, tasan ba zasu bata goyan baya ba.dan haka ta ajiye abin a ranta.
***
Daga Ni sai radiya da Auta tare muka zauna har angwaye suka zo, akayi abinda ya zame na al'ada, kafin suka mana nasiha,. Radiyah ta riko hannun Auta suna gudu daga bari muyi rakiya. Suna fita kuwa Hammah Mohan yana shigowa cikin ɗakin.
Zama yayi a bakin gadon, yana kallona.
"Alhamdulillahi gani ga Maimunari, Maimoon, Almamoon! Mamoon! Mata maza"
A hankali ya yaye mayafin fuskana, sanan ya matso tare da janyo ni jikin shi.
"Tashi muyi sallah"
"Toh"
Na shiga nayi alola sannan nazo muka gabatar da nafilla kamar yadda Manzon Allah ya umarta ya dage goshina yayi min addu'o'in da aka wajabta, kafin ya ya tashi ya kawo min kayan kwalamar da ake kawowa daren,
Alhamdulillahi munci mun sha, sannan muka kwanta, bayan na sauya kayana.
"Moonah dawo kusa dani"
"Hmm! Barci nake ji"
Na fada mishi.
"Toh"
Ya fada kamar Maraya,matsawa nayi jikinshi na kwanta, a hankali rayuwar da ya tsara mana tare da shirya mana wani irin rayuwa na musamman,. Wannan daren na yarda Mohan namiji ne na gaban kwantaccen, Mohan, Mohan ya kai ni duniyar da ban zata ba, ashe duk abinda nake fada duk cika baki ne, domin kuwa daga yan tab'e tab'e lashe lashe, tsutsa tsotse, sai da Mugun ya fara gangarawa madaidaiciyar hanyar na Fahimci Allah daya ne, yanzun na Fahimci