Showing 174001 words to 177000 words out of 177131 words
ba, ana gama aikin aka fito da ita, likitan ya mikawa Mohan hannu.
"Anyi nasara! Amma zaka yi hakuri kwanciyar da tayi zai saka ta yi ta abubuwa irin na yara, kafin ta gama shan magani zata warware da Yardan Allah ku,"
Cikin gamsuwa Mohan ya mika mishi hannu, babban burin shi ya ga Maimunari a tsaye tana mishi murmushin jin dadi.
Yana tsaye aka kai ta dakin ta,sannan ya bisu.
Sai da ta share kwana biyar tana barci, kafin Allah ya nufa zata farka, tunda ta bude take kallon dakin. Ganin haka likitocin suna shigo aka shiga mata abinda ya dace. Sai da suka kai awa daya akan ta, kafin suka fita. Kallon Mohan take kamar wacce ta farka cutar makanta, takowa yayi a sanyayye ya zauna a gefen ta. Ya mika mata hannu.
Dauke kai tayi kamar bata tab'a ganin shi ba.
"Maimoon" banza tayi mishi. Duk abinda ya dace yayi mata yayi, karshe ma kara mishi ciwon kai take, musamman da suka cire mata na'urar kanta domin tayi wanka, ai kuwa sai da ya kai zuciya nesa, domin wallahi yayi hakuri wata kusan takwas, yana jinyarta, babu abinda ya fisge shi kamar kirjinta, had'iye yawun yayi makwat, tare da kallon yadda take mishi bori.
Matseta yayi da bango hannun shi yana bisa duwas ɗinta, yana matsawa yace mata.
"Ya isa haka, Hammah Mohan dinki ne"
Kallon shi tai a sanyayye kamar tasan meye ya gaya mata kafin ta tura mishi bakinta, aikuwa ya kame bakin ya shiga cinye shi, hannun shi yana yawo a jikinta, kai Mohan dan jaraba ne.(🙄 A jinyar ma ba za kyale ta ba)
Dakyar ya iya rike kanshi ya kawo ta waje, ya shirya ta cikin kayan asibitin, sannan likitocin suka kuma kwantar mishi da hankali zata dawo daidai, yayi hakuri, kafin su koma gida da lafiyarta zasu koma.
Aikuwa Yar nima tasaka shi a gaba da rikicin banza kukan banza, kuka mara tushe balle makama, amma da zai tab'a yar banza shiru take tana zare idanun kamar tsohuwar mayya, tunda ya gano ta, Malam Mohan kakar shi ta yanke saka, domin tana fara mishi hauka zai kai hannun shi mazauninta. Ko ya riko dukiyar fulaninta,,. Sai dai kuga yar banza tayi luf. Tun tana da lafiya ma Mohan yasan sirrin rigimar ta balle yanzun da take pagal.
*
Sake shi hukumar gidan yarin suka yi, daga can nesa ya hango Khalil da wasu lauyoyi, cikin isgilanci ya isa gare su..
"Ina labarin Maimunari!" Murmushi Khalil yayi mishi sannan ya shiga motar ya zauna lauyoyi ma haka.
"Mohan ya baka damar ka rayu domin kaga yadda za a buga soyayya. Ka rayu domin ka ga yadda Maimoon zata kasance da Mohan, wannan alfarma yayi maka domin yasan zaka so ka ga yadda zasu rayu"
"Karya ne wallahi sai ka kashe su dukkan su biyu."ya fada a fusace,
"Kuwa zaka mutu"
Barin shi suka yi a gurin, Khalil ya kira Mohan ya gaya mishi sun gama kome.
"Toh nagode sai dai har yau bata dawo daidai ba domin tunanin ta ya birkice wallahi ina cikin damuwa!"
"Karka damu Moha, Allah yana tare da kai, ana kam muku addu'o'in kuma nasan Allah zai amsa."
"Nagode sosai, Khalil da tsaya min da kayi da babu kai wallahi da ba zan tab'a tsayawa da kafana ba. Nagode sosai da Aminta mu"
"Karka damu nagode sosai nima"
Sannan suka yi sallama, cikin nutsuwa Khalil ya koma Niger.
***
Bayan wata ɗaya.
Alhamdulillahi domin lafiya ta samu, kuma duk wanda ya ga Maimunari ta samu lafiya, domin tunaninta ya dawo, yanzun haka suka kasar Moscow.
Inda Mohan ya tafi domin kasuwancin shi.
Ina gyara jikina ya shigo d'akin juyawa nayi tare da amsa mishi sallamar shi. Sake towel din nayi ina murmushi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da takowa gabana.
"Zaki kashe ni da shagali Matar Mohan"
"Burina kenan na raya mijina da shagalina."
Karban kayan nayi na watsa a kujeran dakin, sannan na ja hannun shi muka shiga ban daki, tare muka sake wanka, bayan na cinye shi da salona musamman, sannan muka fito daga ban ɗakin, kai Hammah Mohan.
Tunda muka fito muke manne da juna, abu daya muke tare da cinye junar mu, sai da ya shiga babban birnin lintsin kafin muka sake ihu lokaci guda, wani irin dad'i da yanayi na musamman, yasa muka haukata kan mu.
Bayan awa daya.
Ina sanye da doguwar riga, na yane kaina da farin mayafi muka fito cin abinci. Ban san wani irin yanayi na riski kaina ba, amma Tabbas ina cikin farin ciki samun mutum irin Mohan a matsayin abokin rayuwata.
Haka muka gama yawo sannan ya kai ni har dubai, wannan dakin dai shi ya kai ni, inda na rasa wani irin dad'i nake ji. Sati biyu muka yi a can.
"Wallahi ba mu koma ba, mutane su hnnai sakewa da mata na!" Ya fada yana hararan gefe da gefe,
"Hammah na ina kuma zan iya maka Ni fa babu ruwana,idan kace kar na kula su shikenan."
"Ni zaki haɗawa aiki? Na manta ban gaya miki ba, wata biyu da suka wuce Beenah ta haihu an sami mace, kuma Kinsan me? Sunanki aka saka. Suna kiranta Jewanah, wato (God gift in Urdu language) dan haka sai ki buɗe bakin aljuhun ki, domin samun takwara da wahala"
"Kai Hammah Mohan, me nake dashi sai dai kai, zaka a ra min na yi musu idan yaso na biyaka" na d'aga mishi gira.
"Gaskiya kan zaki biya dan ban koshi ba, kuma gaskiya ki biya yanzun sai a wuce gurin"
Aikuwa makale mata ya makale min sai da ya samu kanshi muka shiga wanka tare, sannan muka shirya tare da nufar kasuwa, minti sayayya sosai, sannan muka dawo masaukin mu, washi gari.
Muka dira a kasar mu ta gado, aikuwa kamar yadda ya fada, sai da muka yi sati biyu bamu ganin juna, saboda jama'a ga Mommy da tsohon ciki, dan ma ina jin wai zasu mata aiki ne, na tausaya mata domin ya hadu da girma da shekaru, kullum cin fada take. Gashi abinda na lura ta tsani ta bude ido taga Abie a kusa da ita, tayi ta kuka tana masifa duk shi ya janyo mata wannan fitinar, tass take mishi, rabonta da haihuwa shekara goma sha biyu,. Amma bawan Allah nan ya cuce ta.
Allah Sarki sai yayi ta bata hakuri, kamar zugata yake, haka zata kawo min karar shi, ni kuwa sai nayi ta kuka. Lokacin Yar Jewanah tana da wata biyar, haka muke zama muna rarrashina Mommy, idan muka matsa muyi gulmarta ni da Beenah.
"Addah Munah, Mommy gata yayi mata yawa kiga yadda Abie yake rarrashinta amma ba zai hana an jima ta saka shi a gaba da kuka ba, wallahi wancan satin da fushi na bar gidan, haba ta saka mana Uba a gaba da rigima dan bata shiga kauye ne, da ta ga abinda bata tab'a gani ba, matan da suka fita manyanta da ciki."
"Toh Magulmaciya Beenah gulmata kike da yar Uwarki?"
"A'a Mommy ba gulmarki ba muke ba."
Aikuwa ta shiga fada kamar zata dake mu, Abie na zuwa ta fashe da kuka.
"Kana jin Yaranka zagina suke wai na samu gata sai abinda na gadama nake"
"Uwata ya haka? Beenah zaki daina zuwa gidan nan da"sannan ya lallabata suka bar mu, aikuwa muka sake Dariya.
**
Na koma gidan su Hammah Mohan, nan ma sai da muka tafi har Agadaz, lokacin Widad tayi girman ban mamaki,. Daga can muka wuce Damagaram, inda na nimo abokaina Salihu Muhmuda da Amadu Bukar. Sunyi aure har da iyalin su, nasaka Hammah Mohan yayi musu alkhairi bayan ya dauke su aiki, sannan muka dawo.
Kwanan mu ashirin da biyar da dawowa aka yiwa Mommy tiyata, tare da ciro mata yaranta Biyu mace da namiji. Tun dare aka yi aikin Hammah Mohan bai gaya min ba, sai da asuba. Kuka na saka tare da kai mishi duka, yana dariya.
"Saura ke!"
Daukar matashi nayi na rufe shi da duka.
Haka muka kasance har bayan mun karya muka nufi Asibitin kamar ba a cire mata Babyn ba, sabida mun samu tana hira tas.
Zuwa nayi kan yaran ina kallon su.
"Hammah na kalli nafi yaran kyau"
"Ina za a gwada! Pure love!" Inji Mohan,
"Gaskiya kin fisu kyau, First Love." Inji Mommy
Daka tsalle nayi na rungume Hammah Mohan, abinda Mommy ta faɗa.
"Ai dukkan su munanan ne, kace karshen kyau!" Inji Abie.
Kuka na fashe da shi, ina kara rungumar Hammah Mohan, murna nake ji yadda iyayena suke nuna min. Kamar zan shige jikin Mommy
Sai dare muka koma domin an kawo abinci daga gida, na gaji sosai.
"Yan mata ya kama ta kiyi wani abu dan wallahi ina son ganin ki da ciki."
Dariya nayi na gyara kwanciya ta a jikin shi.
"Kayi wani abu"
"Ai ina kan yi ko kin sha maganin hana haihuwa ne?" Da sauri na tashi zaune tare da cewa.
"Wallahi ban sha kome ba, hutu ne kawai."
"Gaskiya bana son hutun nan ya isa haka."
Gyada mishi kai nayi sannan na ce mishi.
"Toh Hammah na, Allah ya kawo mai Albarka."
** Sai da Mommy tayi sati biyu sannan aka yi suna Bayan sunan inda aka sanyawa yaran Mariya da Mustapha,
Inda muke kiran Mustapha da Aneen Mafiya kuma muna kiranta da Anam.
Bayan sunan nima na fara nawa. Laulayin kamar yadda Hammah Mohan yaso.
Bayan wata tara Allah ya nufa ba sauke katon Yarona namiji, wanda tare muka yi nakudan da Hammah Mohan.
Aka saka mishi sunan Abbu muna kiran shi Abul Khair,
***
Bayan wasu shekaru.
Mun fito makarantar su Yumnah, anyi bikin yaye su, Aneen da Anam suna fada, gefen su Widad ne, tana kallon su. Bata musu magana ba, na shigo motar.
"Ummin Abul Khair, Kinga Aneen tana ce min dan lukuti" ya fada idanun shi na cika da kwalla.
"Ummi wannan kawu Aneen din bai da kirki zaginta yayi wai munafuka." Inji Widad da take kallon su.
"Toh ya isa haka ko na hada mu da Appa yayi min maganin ku"
Bubbuga glass din motar aka yi na kalli wanda yake wajen motar tare gabana ya fadi na kuma saka key tare da kiran Mohan, yayi ta buga motar yana ihu, can sai ga Hammah Mohan.
Kwallon da Hisham wanda ya dawo Mahaukaci karfi da yaji, sannan aka janye Hammah Mohan, yazo ya fito dani, ya rike hannun.
"Mata ta! Maimunari Isma'il Wodaadabe, tana dauke da cikina na hudu a jikinta, inuwarta ka kuma rab'a sai na kashe ka." Sannan ya juya muka bar gurin.
*
Koda muka dawo gida na razana ba iya ni ba hatta yaran tsoron Baban su, suke sai da na shiga ban daki jini ya tsinke min dole muka nufi asibitin, sai da aka bani hutun wata biyu, yaran suka koma gidan Beenah, dake Su Aneen da Anam sun koma gidan mu gurin Mommy, Allah sarki Abie da kanshi ya haɗa min maganin da na sha cikin ya koma ya zauna, sati na ɗaya aka sallame ni.
Mohan ya dauke min kome, haka na cigaba da kula da cikina..
Anyi bikin Radiyah dan sai yanzun Uwar Safwan ta amince sakamakon rashin dadin da matar da ta aura mishi take fuskanta a gurin shi, ita da kanta ta roki Umman shi ta aura mishi Radiyah.
Jalilah itama tayi aure a can Saudiya kanin mijin Muslimah ya aure ta, beenah ma Yaranta uku.
Mace mai suna na, sai Mai sunan Umman su, sai Mai sunan Baban su da baban shi, ana kiran shi Hanif, mai sunan Umma kuwa ana kiranta Walidah. Sai Jewanah.
Nairah itama anyi bikinta ta auri dan Sarkin Kano, an sha biki sosai mune manyan yayyu.
***
Cikina yana wata bakwai, Allah yayiwa Matar Salman rasuwa, gurin haihuwa, mugun tsoro ya kamani, babu shiri na shiga nakudar wata bakwai, haka na haifi yarinyar yar karama da ita, aka saka ta a kwalba. Khausar ce a kan mu.
Sai da muka yi wata biyu asibitin aka sallame mu, itama ta koma gidan mijinta sai dai Ammyn ce da Allah ya daura mata jinya sosai, kullum ta ganni sai tayi kuka da niman gafarana. Ga Small Mom itama yaranta biyu, Armaya'u da Areeshah.
Bayan shekara daya, idan ka ga yarinya na ba zaka dauka yar wata bakwai bane, wacce muka saka mata sunan Ammyn muna kiran ta, Khairat.
Zirga zirga muke domin bikin Yumnah da Abie ya bawa Salman ita, bata son shi amma sabida biyayya yarinyar nan ta amshe shi hannu bibbiyu..
Haka muka sha bikin su, dake ya dawo gida da aiki, aka kai ta gidan shi da yake Maradi. Muma haka kawai Mohan ya saka mu muka koma Maradi.
Bayan bikin da wata uku aka mai da mata yaran Salman ɗin.
Rayuwa cike da kaddarorrin masu kyau da marasa kyau mun amshe su, na cigaba da shiga daji ina wayar da kan al'umma Fulani musamman Bororoji babban burin Baba Mari, ya'yanta da suka b'ace. Su dawo amma babu labarin su. Alhamdulillahi domin duk inda muka samu labarin su muka kai musu kayan tallafi da kulawa. Har da musu burtsaitsai sai makaranta ya'yan makiyaya.
Wannan gudunmawar da nake badawa yasa Hukumar Majalisar Dinkin Duniya, suka bani lambar yabo, tare da bani matsayin na musamman inda ake biya na da dallar Amurka, shi wannan kawai ya ishe ni nayi hidimar al'umma.
Ganin yadda nake son dakatar da muguwar dabi'ar Hammah Mohan da kanshi ya tafi asibiti da ni, aka dakatar da haihuwar mu, yace min.
"Ki bautawa Allah, sannan ki tuna da Al'ummar Annabi, karki manta da igiyar aurena akanki na yarda dake ki shiga ki wayar da kan al'ummar Bororoji."
Nayi kuka nayi farin ciki, sannan na cigaba da abinda ya sani. Kuma na yarda da Allah, yana tare da mu.
Gefe guda kuwa Hisham yana ganin Cigaban bakin cikin yadda yake ma ya ishe shi, uban shi ya mutu mutuwar wulakancin, sai a anan aka samo gawar mahaifiyar Hisham din da ya tsafeta yana aikin sabo da ita, shi yasa ake son ka gina Alkhairi zaka same shi a gaba.
**
Shafa wuyana yayi tare da cewa.
"Radiyah ta haihu, baki samu zuwa ba, Nairah kan tace na.miki godiya sako ya isa."
"Radiyah Beenah ta je mana amma Insha Allah zamu je da Yaran."
"Toh Allah ya kai mu"
***
Washi gari
Muka je gidan tare da Alkhairi, dan muna hira wata rana, ta tab'a ganin wata mota tace tana so, dan haka ya saya mata motar, na sami yan uwan mijin suna mata dariya, dan Uwar mijin ta mata bawa Uwargidan ta kyauta kujeran Umra, da muka shiga gidan suna mata wannan tsiyar gani na yasa kowa ya shiga hankalin shi, haka tayi ta gaya min abinda suke mata.
Mika mata key motar ta nayi, ta fito da guda tana ihu, ai babu shiri suka fito, kowa ganin motar ta sai da jikin shi yayi sanyi, dan haka na nuna mata karta damu, bayan mun koma gida na gaya mishi yayi mata Alkhairi akai mata domin haka zai saka dangin mijin su d'aga mata kafa,. Har sauran yan uwan ta, suna kokarin share mata kuka. Sai gashi hatta mijin shima binta yake yi.
......
Mommy tun daga Yan biyu tace ta yafe a kai kasuwa, sai dai mu yaranta, Yumnah ma da ta haihu ba laifi aka yi hidima. Ta samu ya mace aka saka sunan Mommy.
Bayan wani lokaci mai tsawo na ajiye aikin inda na tubure zan kuma haihuwa bai Musa min ba, muka je aka cire min abinda aka saka min a hannu na.
Wata na zuwa kuwa Sai ga cikin nayi ta addu'a Allah yasa na samu takwaran Innnah.
Ai kuwa Allah cikin ikon shi, na samu cikin, aka nuna mana namiji ne, haka ya kashe min jiki, bayan watanni da na dauka Allah ya sauke Ni lafiya, na samu da namiji ne, aka saka sunan Abie, muka kiran shi Adeel.
Watan shi tara na samu ciki. Na sha bakar wahala kamar zan mutu, kafin na haifi yarana biyu mata, Aka saka musu Ummul Khairi sunan kakan Mohan, sai fatar sunan Innah ana kiranta da Meenat.
Naga gata da soyayyar mijina, kuma har yau ina alfahari da mijina, domin ya d'aga darajata daga cikin mutane masu yawa,
***
Bayan shekara goma sha biyar.
Arziki yaci Uban da, na kara kankaro daraja ta, Ammyn kuwa bata moruwa, a cikin shekarun nan muka ji labarin mutuwar Hajiya Karime.
Addu'ar barci na tofa musu, sannan na rufe dakin na nufi namu dakin.
Karfi da yaji ana niman lalata min miji wai ta fito ta karar siyasa, abinda had'a mu kenan. muke rigima, ina shigowa ya riko hannuna.
"Na janye kudirina na bawarwa dan Uwansa Ahmad Bala Raees, daga karamin mataki har zuwa shugaban kasa zan mara mishi baya."
"Shima ce maka akayi Halimah Ishrat zata yarda mijinta yayi ta yawo da Gantali irin na yan siyasa? Salon yaje ya hadu da wasu manta su lalata mishi rayuwa?"
" A'a karki ce min kema zaki fara kishi a tsakanin zubda jini?"
Cikin fushi na ture shi zan wuce.
"Mohan mijin mace daya ce kuma ke ce matar shi a duniya da lahira. Kuma nasan shima Ahmad!"
"Wai ina ka bar Sheikh Zunnur Bin Jonah(Alhubbuh Fihi Mararatun) da kanin shi Yunus Zunnun bin Jonah? Ko ka manta da Arshan ne(Ruwa a jallo) toh idan ka manta su ka bude idanun ka kaga Malam barci nake ji"
Bakin shi a sake yace min.
"Nasan Ashraf,.nasan Mehran, nasan Aliyu Asadullah, nasan Malik da Maheer, nasan Dr Yohanna Chibok! Nasan Ahmad Halwani! Toh na kuma san Aalim da Aamil sai wane?"
"Yunus mai Nasara tare da Ahmad Roma da Amaan Mandara idan ka manta bari na tuna maka su! Da alamu ka manta Jikar Innah wuro, Sadeeq da Aminin shi Imran"
Daukata yayi cak yana faɗin.
"Gaya min sirrin Labarin Addah Ramlat!"
"Eh toh da zaka ce Dambujebuje da zan fi tuna maka kome, cikin nutsuwa."
*Alhamdulillahi Ubangiji Nagode maka sosai da ka bani damar kammala labarin nan akan lokaci kuyi hakuri wallahi bani da lokacin kaina kuma yau ina da zuwa ganin likita amma na tsaya na karasa labarin nan,kuyi hakuri da yadda na kawo shi karshe wallahi ina da uzurirruka masu yawa! Kuyi hakuri! Koda hidimar Muwaddah da Walid aka