Showing 57001 words to 60000 words out of 177131 words

Chapter 20 - Bororoji Compelet COMPLETE HAUSA NOVEL

01 Sep 2024

14835

ka ga yadda zan yi da Yaronka."

"Wallahi baka isa ba! Ni zan Barka a raye domin ganin yadda zamu yi dashi." Inji malam Ansar,
"Hhhh! Ni Mohammed Mamman Mohammed Nasir Aghali Mohan na kara gaya maka na maka alkawarin kana raye zaka gan mu da idanun ka, kai ba kai ba hatta shaidanin zuciyarka sai ya gan mu a tare balle kai banza irinka... 2k Words 😁
_😌😌😌 Anya zan cigaba kuwa wallahi Vote yayi kad'an ko na ajiye shi ne na fara Kishi a tsakanin zubda jini ne dan na ga kuna mutuntta labarin kuɗi sama da free book_
[7/22, 9:49 PM] RamlatArManga: 🐂🐂BOROROJI🫀🫀

~The Journey of Destiny💔~

Mai_Dambu

Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....

BABI NA ASHIRIN DA D'AYA.

Cikin ihu da masifa yake bin bayan Mohan tare da niman riko rigar shi, amma zaratan sojojin da suke bin bayan MG Mohan suka cafke shi, tare da shiru suna jiran Umarnin shi.

"Ku kyale shi ya rayu. Na barshi ya rayu domin idan kuka dake shi sai ya leka lahira ya dawo." Ya fada tare da cigaba da tafiyar shi,

     Ganin Almamoon baya motsi ya sashi karawa da sassarfa, yana kallon fuskar shi, hular kanshi ne ya zame, lallausar gashin sa da yake tufke baki wuluk wanda yake warware. Kallon shi yake yana kara mamakin yadda namiji dashi yake da uban gashi haka.

       Yana fitowa ya ajiye shi a cikin motar su, kallon Fahad yayi tare da kallon bike din shi, sara mishi yayi sannan ya koma, gurin bike din ya ja machine din da gudu, yayi da suma suka rufa mishi baya. Tab'a bluetooth din shi yayi tare da cewa.
"Malam turo min wani likita daga barikin sojan maradi."

   Tab'e abin yayi tare da sauke wani irin ajiyar zuciya.
"Yallabai an tura masu wani motar da zata kwaso su."

          "Hmm" ya faɗa, yana me kallon zoben hannun Almamoon,  a hankali yake me jin kamar ya rufe Ansar ku baki daya, amma bai san girman da yake dashi a duniyar Almamoon ba, sai ya farka.
Suna isa gidan ya sauke shi cak, har yana mamaki.
*Dube bakin shi da ya iya zungure min goshi, nan kuwa tsiwa ce zallah babu wani karfi dube shi kamar ba namiji ba*

Ya fada a kasan ranshi, yana jin wani dariya yana niman kwace mishi, yanzun ma idan ya farka zai koma kamar da yadda zai cigaba da rena mishi hankali, dan yana son haukar yaron baki daya ya kam manta da batun shi din wani ne yayi ta shirme.

  Shigowar wani likita tare da wasu mata biyu, suka fara aikin su a kan Almamoon, tashi yayi ya bar musu gurin. Can suka ci-gaba da aikin su, sai kallon juna suke musamman bayan da likitan ya gama nashi suka fara nasu. Abun mamaki ya basu. Me yasa haka?

       Dan gulma sai da suka yi ta duba shi har cikin, tsoro ne ya kama su lokacin da Mohan yayi gyaran murya, da sauri suka bar shi. Juyawa suka yi. Likitan ya fara magana.
"Yallabai mun debi jikin shi, zamu bincika muga abinda yake cikin shi. Nan da awa daya."

    "Amma Likita mara lafiyan yana"
"Na Fahimta muje Insha Allah zamu kara dawowa, sannan na sami sauran birbidin maganin da aka shaka mishi zamu yi bincike akai."

Suna barin gidan likitan ya balbale su da faɗa, yana gaya musu.
"Dan baku da hankali taya kuna gaban MG na soja zaku saka bakin ku a cikin maganar mu kusan waye shi?"

    Shiru suka yi dan sun san halin shi masifaffen ne, har suka isa asibitin, cikin abinda bai fi awa daya ba aka gama binciken. Yana karanta abinda ya kusan da sauri ya kira Dan Ba'are ya gaya mishi.
"Don Allah ku tawo da majiyancin nan rayuwar shi tana cikin hatsari"

        Zunzurutun tashin hankalin da  dan Ba'are ya shiga kamar zai dira a maradi, dan haka ya kira Mohan a hanzarce.
"Yaron nan yana cikin hatsari a kai shi asibiti gani nan zuwa."

    Kashe wayar Mohan yayi mishi.
"Hello Hello! Kai kai katsaya mana" babu shiri ya dauki kayan shi bai tsaya wata wata ba. Ya kira wata wayar da take cikin Office din shi, ya faɗa musu abin da yake bukata, cikin kankanin lokaci suka hada mishi kome, yana fita ya daga Office gidan shi ya nufa, ya haɗa abinda zai hada, 

....

A dakile ya watsar da wayar tare da shimfid'a dogayen kafaffun shi a samar table, yana kallon Almamoon da fuskar shi yayi wani irin fayau kamar wanda aka kwashe mishi jinin jikin shi. Bakin shi kuwa fari yayi fayau.

     Idan ya cigaba da rike yaron mutuwa zai yi, dan haka a zuciye ya dauke shi, yana fitowa dauke da Almamoon, sojojin da suke gidan suka mike, tare da nufar inda motar aikin su yake, suka yadda saka shi yayi tare da shiga ya zauna ya daura kanshi a kan cinyar shi.

       Lumshe idanun shi yayi yana tuno yadda ya birkice yau ganin halin da ya shiga, duk yabi Cameras na cikin gidan yaga  yadda yaron yayi ƙoƙarin kula da lafiyar shi. Da yadda aka yi ta had'a mishi mugun abu a cikin gidan a saka Hajiya Safiya tayi ta dukar shi. Ya rasa inda zai saka zalincin Hajiya Safiya baki daya.

         Sai dai wani abu daya da ya lura dashi. Bude fararren idanun shi yayi akan kofar asibitin. Ga Nurse da suka tsaya suka jiran fitowar su, a hankali ya fita tare da bude inda Mamoon yake kwance. Ya fitar dashi,

   Tunda aka shige dashi wani daki bai kuma ganin wani ya fito ba.  Tun yana kirga lokacin da aka shiga har ya kai ya daina duba agogon lokacin sallah nayi suke fita da Malik.

   Bayan awa biyu sai ga Dan Ba'are, kallo daya Mohan yayi mishi ya dauke kai Kamar bai tab'a ganin shi ba. Asalima haushin yadda yake bashi umarni yake sai kace irin shine a kasar shi. Wani b'ata rai yayi yana shan kamshi kamar bashi ba.

    Shi kuwa bawan Allah bai fahimci halin abokin shi ba, abu daya zuwa biyu ya tambaye shi.
"Ya jikin ka? Ya jikin Almamoon?"
Wani basarwa yayi tare da mai da smart watch din shi hannun shi yana wani cin magani, dakyar bakin shi ya motsa da cewa.
"Da sauki"
Ka sake Dan Ba'are yayi yana kallon shi. Kafin jikin shi yayi wani iri, komawa gefe yayi ya zauna tare da ɗaukar wayar shi yana latsawa,shi kuwa Mohan sai wani tsare gida yake irin ba zai yiwu ba.

     Fitowar likita ya sa dan Ba'are mik'ewa ya mikawa Dr Faruq hannun suka gaisa.
"Faruq meye a ke ciki?"

     "Yallabai rayuwar shi ta fita daga matakin tsari, sai dai bamu da kayan aikin da zai tacce jikin shi."

"Dama kunsan baku da kayan aikin uban waye ya ce kuce a kawo ta?" Ya fada tare da watsar da su baki daya gefe yayi wucewar shi cikin dakin.
"Mohan ka tsaya ayi magana kaji yace idan da za a fita dashi kasar waje ko Saudi za a dace."

"I fuck nonsense words, taya zaka gaya min maganar banza kaniyar kasar waje hell You da kasar wajen" ya faɗa a tsawa ce. Yana bankawa dan Ba'are hararar.

           Dan ya tsani duk wanda zai mishi iyayi akan Mamoon.
"Amma dai meye na zagi? Kamar wanda aka mishi wani abu? Yaron nan dai ni na kawo shi dan lura da lafiyar ka, so it's my responsibility na tsayawa rayuwar shi if not me kake tsammani za a dauke ni, don Allah kayi hakuri a dauki matakin da ya dace."

      Kura musu ido yayi cikin nutsuwa ya juya zai fita daga asibitin, zuciya kawai yake dawainiya da shi, yana fita ranshi ya kuma b'aci dan haka bai tsaya a asibitin ba ya nufi gidan shi, dakin motsa jikin shi ya cire kayan shi ya rage daga shi sai farin wando. Daukar karfe yayi yana nazarin yadda dan Ba'are ya nuna mishi fin karfi akan Almamoon ne. Ba zai kuma shiga damuwar su ba.

Dan haka abinda yake gaban shi zai yi ya cigaba da boye matsalar shi,.kiran Malik yayi tare da zubawa kofar idanun shi. Wanda suke cike da masifar rikici.

Yana zuwa ya zuba mishi wasu files a gaban shi, tare da kamewa ya sara mishi tare da yin alamun yana da magana.
"Humm" yace a hankali,
"Yallabai! Na gama tattara bayanan baki daya, sai dai yaron bai da matsalar kome, kuma ba shi da alaka da Ansar Yusuf. Wancan kuma akan case din su.."
D'aga mishi hannu yayi tare da kafe kofar shiga da idanu.

Sara mishi ya kuma sannan ya juya tare da barin d'akin, yadda kan shi ya dauko zafin nan idan ya cigaba daukar magana ji yaƙe kamar zata fashe shi yasa ya bar asibitin dan ranshi ya fara b'aci.

A hanyar fita suka haɗu da Dan Ba'are.
"Ina mara mutuncin yake."
"Yana dakin motsa jiki"
A fusace ya shiga tare da banke kofar, ya d'aga ruwa yana sha.
"Kai wani irin mutumin banza ne haka? Akan wannan maganar sai kayi zuciya da Yaron?"

" Kasan kanin Ubana ne da zan zauna muku" ya faɗa bayan ya ajiye goran ruwan,
"Banza kawai waye ya kawo batun Iyaye?"

Bai kula shi ba, zama yayi tare da sassauta murya yana faɗin.
"Mohan yaron yana bukatar kulawa"
"And so what?" Ya tambaye shi yana zare mishi ido,

"Jinin shi bai da karfi, kwayoyin sinadirin kulorin da kuma Cocin aka hada ya shaka, Kuma shi sinadarin yana lalata huhu da makogaro, don Allah kayi wani abu a fitar dashi kar ya rasa rayuwar shi, gashi ban san inda Iyayen shi suke ba Ansar Yusuf ne kawai ya san inda yaron ya fito"

A matukar tsoro yake amma kuma a yadda ya nuna rashin mutunci akan fuskar shi sai ka rantse zuciyar shi bata rawa akan abinda aka gaya mishi.
"Wani hali yake ynzn?" Ya tambaya fuska a daure,
Gyara zama ɗan Ba'are yayi Y
Tare da cewa.
"Yana nan dai sai a hankali, ina tsoron kar wani abu ya same shi ne wallahi"

Mik'ewa yayi ya fita tare da nufar dakin shi ya shiga ban daki, wanka yayi sannan ya fito ya bude wardrob din shi ya dauki kayan shi wani riga da wando, rigar ja ce sai wandon baki. Sakawa yayi tare da rufe closet din shi,bai cika amfani dashi ba, kasancewar akwai Abubuwan sirrin shi.

Lumshe idanun shi yayi lokacin da ya gama shiryawa ya fito, yana saukowa tare da nufar inda Dan Ba'are yaƙe. Ya dauke kai Kamar bai ganshi ba. Haka yasa dan Ba'are jan tsaki me ƙarfi. Bai kula shi ba dan yasan ya shaka ne yasa yayi tsaki.

Ko a motar babu wanda ya kula wani asalima dauke kai suka yi dan kowa da jin haushin dan uwan shi, suna isa asibitin Office din likitan suka shiga, suka samu yana duba wasu sojoji.fita suka yi tare da zama.

"Ko zamu je kaga yadda yake?"
Kamar ba dashi ake ba, shiru yayi yana latsa agogon hannun shi.
"Amma kai kan anyi dan iska idan ba zaka ba kayi min bayani mana ka tashi ka share ni kamar wani abu mara daraja" kallon shi Mohan yayi tare da tab'e baki yace mishi.
"Idan kai ne da kafana dauke ni ka kaini"
"Ok ince kai maganar bakin ka kashi yafi shi daraja"

Sanin bai son magana yasa shi dauke kai yana kallon yadda Asibitin yake. Mik'ewa yayi tare da nufar hanyar da zai kai shi cikin asibitin Dan Ba'are yana gaya mishi bi nan can zamu shiga har suka shiga inda Mamoon yake, Ya kai hannu zai bude kofar Dan Ba'are shima ya kai nashi hannun, a lokaci guda suna kalli juna. Tsuke fuska Mohan yayi dole Dan Ba'are ya cire hannun shi, koda ya shiga cikin dakin, rufe kofar yayi yana me jan tsaki.

Jingina yayi da kofar tare da kura mishi ido, tausayin yaron yake ji. Haka kawai ƙaddara ta kawo shi inda bai da muhalli, inda yana da gata babu me tozarta shi, amma yau gashi ana watangaririya da rayuwar shi.

A sanyayye ya mike daga jikin kofar, ya nufi inda yake a Mamoon yake kwance, ya dafa kujeran da yake gaban gadon, tare da juya shi a hankali sannan ya zauna yana fuskarta shi.
Riko hannun shi yayi tare shafa, shi a hankali yana me jin tausayin shi a ranshi, kara rike hannun yayi yana kallon shi zara zara, kafin ya kai hannun fuskar shi. Yana tuno abinda ya faru kafin wannan lamari d'azun da safe. Musamman yadda yake zaro mishi ido, murmushi yayi tare da cewa.,
"Allah ya baka lafiya" ya faɗa a can ƙasar makoshin sa......
*Har na bude data sai naga Yan Baroriji fans 😂 suna nimana ido a rufe kamar ka sace Mamoon na b'oye🙄😠😏 ku gode yau bana jin rashin daraja da ban muku typing ba🙄 Insha Allah na kusan fara muku rashin darajar nan.... Ban sani ba ko zan sami damar typing gobe, idan nayi zakù gani idan bai yi ba toh na tafi leka Gyatuma ce kusan abinka da mai kaka sai anayi ana leka su thank You so much 💓💞*
[7/23, 8:24 PM] Hafsatu Hafs: 🐂🐂BOROROJI🫀🫀

~The Journey of Destiny💔~

Mai_Dambu

Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....

BABI NA ASHIRIN DA BIYU.

Karar bude kofar yasa shi maza ya mike tare da mai da hannun Almamoon, daidai shigowar Dan Ba'are. Wani irin b'ata rai yayi kamar wanda aka zo amsar wani abu a gurin shi.sai wani hura hanci yaƙe. Dariya yaso bawa dan Ba'are amma ya share shi dan bai da lokacin sa. Gashi ya wani tsare inda Almamoon yake sai wani b'ata b'ata rai yaƙe irin me kazo yi?

    Ƙoƙarin leka Almamoon yake ya wani tare shi.
"Meye kake nufi?" Ya wani fada yana hararan dan Ba'are,
"Kai bana son Iskanci ka bari na ga halin da dan mutane yake ciki indai na so kake a fara sintiri munyi kisar kai"

Matsa mishi yayi tare da zama yana kallon su,.kai hannu Dan Ba'are yayi zai tab'a Almamoon yayi maza ya dauke kan shi saboda har cikin zuciyar shi yaji haka amma bai wani nuna a fuska ba. Kamar ance ya kalli inda Mohan yake yaga bai wani damu da abin da yake ba, dan haka ya sha jinin jikin shi bai kai hannun ba ya fasa tare da kallon Abokin nashi da yayi mishi mugun sani.

    Idan ya fahimtar kamar dai kodayaushe baya son mu'amalar wani da abinda yake tare da shi yanzun sai ya iya cire abin a ranshi yayi mamaki da bai yi haka akan Mamoon dan yasan sun tab'a yin haka akan wata budurwan shi, yarinyar ta makalewa Mohan ba laifi ya fara kula ta, ba wai dan yana son ta ba, kwatsam sai Dan Ba'are ya fara kula yarinyar irin wasan abokin saurayin nan. Har su zauna su sha hira. Tunda aka yi haka a kan idanun shi ya b'ata rai bai ce kome ba. Aka kuma ba biyu bai yi magana ba. Yana tare da su.

        Wata talata ya dawo daga tafiya yana shiga gidan su yaga yarinyar me suna Sayyidah tare da dan Ba'are suna jiran shi,  yana sauka a motar Mohan ya tattara kashin su ya watsar suna mishi Barka da dawowa, amma fir yaki kallon inda suke asalima kamar bai gansu ba.

    Allah Sarki kallon Dan Ba'are tayi sannan tace mishi.
"Ko na mishi laifi ne?" Ta tambaye shi a dame, tab'e baki yayi sannan yace mata.
"Babu abin da kika yiwa ɗan iska" ya faɗa tare da mik'ewa zai bar gurin,
"Ko zaka raka ni na tambaye shi?" Cikin takaici yace mata.
"Dalla can sai kace ba mace ba dan banza ya dawo dan bai kula ki ba sai ki damu karki sake ki fara nuna miki zakalewarki tun ynazun dan wallahi zaki wahala da Mohan."

      "Toh uban munafukai zaku fitar min a gida ko sai na watsa ku a waje?" Ya fada yana daure fuskar shi alamar babu wasa da sassauci.
"Mohan yarinyar nan tun safe take jiranka kuma ka dawo ka watsar da ita, ai ko babu kome zaka girmama soyayyar da take maka"

Kallon mamaki yayi mishi kafin ya gyara tsayuwar shi bayan ya zuba hannun shi dukka biyu a cikin aljuhun wando shi domin wandon unifoam ne a jikin shi sai wata shimi ta soja. Kallon yarinyar yayi daga sama har kasa  kafin ya mai da idanun shi kan Dan Ba'are.
"Kanin Ubana ka gama?" Ya tambaye shi tare da mishi kallon kurilla.
"Ayya Ayya Mohan wallahi ina kaunarka da dukka zuciyata karka wulakantani"

"Ka dauki wannan abin ku bar min gidana idan kuka sake na fito sai na saka bindiga na harbe yan iska mara sa mutunci irin ku masu cin amanar Abota."

     Ya juya a fusace kamar zai wuce dakin, yarinyar kamar zata yi hauka, amma Mohan bai saka shi jin ya hakura ba, Dan Ba'are yayi mishi bayani amma fir yaki kula zancen kuma ba iya ita ba yan mata dayawa sun sha wulakancin shi.

    Ajiyar zuciya Dan Ba'are ya sauke lokacin da ya koma bayan shi ya tsaya tare da cewa.
"Kayi duk abinda ya dace, Ni zan tafi dashi kai ka koma bakin aikin ka" ya faɗa tare da mik'ewa yana gyarawa Mamoon fuskar shi da take kara tsutsewa.

     Cike da mamaki yake kallon Mohan,
"Amma kuma"
"Na baka umarni a matsayin shugaban ka."  Ya fada tare da barin d'akin baki daya domin idan akwai abinda ya tsana ya zauna daki daya da wani, bayan wanda yake tare dashi, shi yasa ya bar dakin domin zuciyar shi ba zai dauka ba.

    Kuma baya son ya kaftawa Dan Ba'are tijara, sannan shi wani irin mutum ne da baya son raba kome da wasu,idan zai yi abu akan shi yake tsayawa shi yasa yake jin haushin Dan Ba'are da ya zake akan Mamoon.

        Yana fita aka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login