Showing 33001 words to 36000 words out of 177131 words

Chapter 12 - Bororoji Compelet COMPLETE HAUSA NOVEL

01 Sep 2024

14790

dashi a makaranta?"
"Sunan Baba nane" inji Malam, sabida ya dauke hankalin Almamoon daga batun, ita kuwa Innar had'iye kukan tayi lokaci guda, haka kawai Almamoon yaji a ranshi, akwai abinda suke boye mishi, amma koma meye wata rana zai fito. Daukar kudin tayi tare da yafa mayafinta ta fita, sayo sabulu, kafin ta karasa ta tsaya a wani lungu. Ta fashe da kuka, sai da ta durkusa a kasa tana wani irin kuka. Me yasa malam yayi mata haka?  Me yasa ya zab'i cilla rayuwar Almamoon wata duniya, me yasa ya aikata haka? Komawa tayi tare da zama.

   Tayi kuka kamar ranta zai fita, kafin ta goge idanunta, sannan ta nufi shagon, ta sayi abinda zata saya. Sannan ta juya tare da komawa gida.

        Ita da kanta ta ware kayan Almamoon ta wanke mishi aka kiran magarib tana shanya kayan, sannan ta zauna bayan ta ga Almamoon yana alola.
"Gama ka bani butar na taimakawa malam"
"Toh ina"
Haka ya gama ya mika mata bayan ya cika ruwa a cikin butar, ya shiga dakin sallah.
"Malam gashi" ta faɗa tare da dauke kanta daga gare shi. Riko hannunta yayi cikin nashi yana faɗin.
"Nasan nayi laifi, amma haka ba yana nufin b'ata miki rai bane, idan har sabida kin yi fushi yace ba shi komawa makaranta waye zai gaya mishi yaji? Rayuwar shi zaki duba? Waye shi ba shi bane me muhimmanci ba, rayuwar shi na gobe shine mai muhimmanci.

     Idan da ace sabida ke ce wallahi ba zan saka baki ba, amma dake saboda yaron ne dole na saka baki, yana miki wata irin kauna ce ba iya ke ba hatta ni, kaunata yaƙe, sabida mu ya sadaukar da karatun shi ashe ba zamu tsayawa rayuwar shi dan wata dama ta same shi ba? Kinsan mutanen da suke niman dama irin da ya samu yau? Wallahi ba kwadayin abin duniya ya sani amsar wannan batun ba, sai dan rayuwar shi, ai ko babu kome zaki duba ki ga waye shi?

     Ina zai shiga? Meye Allah ya ƙaddara mishi, shin zai iya jure ƙaddaran shi? Shin meye mizanin ƙaddaran shi? Wannan shine abinda nake son ki Fahimta, amma idan kin fahimta idan baki fahimta ba, ki barshi yayi ya zama. Allah yayi mishi baiwa amma zai kare ta a matsayin dan dako, nasan waye na ke zaune dashi. Tunda nake da yaron nan bai tab'a ɗaukar abin wani ba, amma lokaci guda an daura mishi laifin da bana shi.

    Idan muka ce kullum gudun ƙaddarar shi zamu yi wata rana ba zamu iya gudu ba, kyale shi ya fita yayi rayuwar shi kamar kowa, ya fahimci muhimmancin rayuwa, ya san yadda Goben shi zai kaya, idan muka cigaba da boye shi wata rana zai iya tambayar mu me yasa? Ina jin kunyar na gaya Mishi waye shi.

Don Allah Karki Cigaba da abinda kike aikatawa, don Allah na hadaki da shi karki kuma abinda ya sani magana."

Share kwalla tayi tare da SUNKUYAR da kanta.
"Malam don Allah karka kuma haka"
"Insha Allah ba zan kuma ba, leka karki kuma ki barni nayi iko da shi." Ya faɗa,
"Inna yau ba zaki mana abinci bane?" Ya fada tare da tura baki,
Tashi tayi tare da cewa.
"Ga tsakin can dambu ne" zama yayi tare da kallonta,
"Innah dambun kuma?"
"Ina da zogale da busheshen lawashi"
"Inna da magarib zaki mana dambun?"
Ya fada kamar zai fashe da kuka, haka ya mike.
"Toh zoka sayo maka makaroni." Da sauri ya mike, tayi mishi lissafin, bayan ya mike ya dauki kudin ya nufi shagon unguwar.

Tun daga nesa ya hango yan daban, sunan shi Shege. Cikin shi ne ya cika da ruwa, haka ya isa shagon ya gama sayayyan shi, sannan ya juya zai tafi, yaji an matse mazaunin shi. Maganar gaskiya Almamoon yana da halittar mazaunai, duwawun suna nan masu dan tudu, ba laifi abinda yake jan hankalin matasan yan daban suke bibiyar shi.

Shege dan iska, yana bin mata da maza. Tun shekara daya da ya wuce yaga Almamoon yake Masifar son ya kusanci bayan shi. Amma haka bai samu ba, sai da magarib nan yake ganin kamar zai iya shigar shi da karfin tsiya.

Kwace jikin shi yayi tare da kallon shi.
"Malam Meye haka?" Wani nishi ya sauke tare da takowa gabansa.
"Kamshin mace naji a jikinka"
"Malam bana son damuwa" ya faɗa da sauri yana ja da baya, ganin Almamoon zai subuce mishi ya kara kai mishi cafka Allah ya bashi sa'a, ya arta a guje.

Shi da yaran sa, suka mara mishi baya Allah bai basu Sa'a ba, har ya shiga cikin gidan, tare da rufe kofar gidan yana haki, kamar Mahaukaci haka ya shiga gidan yana haki.
"Lafiya?"
Nan ya basu labarin biyo shi da shege yayi, shiru Malam sanda yayi sannan yace mishi.
"Insha Allah gobe zaka bar garin nan"
Innah da cikinta ya duri ruwa kamar zata fashe da kuka.
"Eh gwara ka tafi, zaman ka a nan masifa ce gwara can"

Shima munafikin da yaji haka, ai amincewa yayi babu shiri a daren suka tafasa taliyar suka ci, wajen asuba. Ya shirya kayan shi. Sannan suka mishi addu'a, kafin suka sanya shi yayi Sallah tare da niman dacewa.

Karfe bakwai na safe ya bar gidan, cike da zulumin rayuwa,
Haka ya nufi tasha, yana zaune har motar su, ta tashi. Anan ya sauke ajiyar zuciya.

**
Karfe hudu na yamma ya same shi a quarts din malaman jami'ar, a hankali ya shiga buga kofar get din, dake yasan Almamoon zai zo shi yasa ya bude da kwarin gwiwar shi, yana buɗewa, ya shigo. Bai san lokacin da ya fisgo shi tare da rungume shi ba, yana wani irin jin dadi da nutsuwa yana saukar mishi.

(Labarin zai koma bakin Mata maza🙄🤣 Salon da na saba 🙆🏾‍♂️😜)

Cikin wani irin takaici na kalli Malam Ansar.
"Toh meye haka? Idan Baba Mari ta ganmu ta zarge mu da wani abu ko?"

Kamar zai sake min kuka yace min.
"Kayi hakuri nasan babu dad'i amma kuma nayi kewar ka ne sosai."

Ƙaramin tsaki kayi a raina sanan nace mishi.
"Toh Ni gaskiya bana son haka." Na ture shi tare da juyawa zan fita.
"Don Allah kayi hakuri"
Banza nayi dashi. Kamar dani yake ba,
"Toh shi kenan, ba zan kuma ba." Ya fada a sanyayye, shiga cikin gidan nayi ina wani hura hanci irin ganin nan an min laifi.

"A'a ba nan ba, BQ" na wuce da jakata ina shiga na kalli Baba Mari. Cikin wani irin murna ta taso tare da amsar kayana.
"Dan mutum kai ne a gari"

Kaunar tsohuwar ya taso min tun daga cikin raina har jinin jikina, ba zan iya cewa ga yadda nake ji akan ta ba, kwalla ne ya cika min idanuna.
"Wallahi matar gani nan". Na zauna ina kallonta, kura min ido tayi, sannan tace min.
"Idan na kalle ka sai na tuna da Abuh, yanayinku, kayi hakuri na tsare ka da surutu.."

Tashi tayi ta fara hada min abinci, tare da duk wani abun da take dashi a dakin. Cikin kauna da gata, take min.
"Maza zauna kaci" haka ta hada min na fara ciki ina janta da hira, har ma gama na kwashe kwanikan na wanke, na dawo dakin nayi sallah,haka na tattara kome na koma dakin da aka bani, na gyara shi tsaf.

Sannan na dawo dakin ta muka shiga hira, har malam Ansar ya kuma zuwa, wani shegen kallon yake min, dan haka na dauke kai na tare da b'ata rai. Haka muka sha hiran mu tare da basu labarin halin rayuwar da muka sha, wanda ma na bar su.
"Yanzun ma ai bawai na dawo bane saboda kaje, wani gantalallen mutum ne ya dame ni shine Inna da Baba suka yarda na zo."
Ya fada tare da tsume fuska, dan bakin nan ya cuno shi gaba, alamar wannan Almamoon da mace ce (🙄😜🤣) tabbas zata yi tsiwar bala'i, ina dalili dauke idanun shi yayi daga kanshi, domin kowani seconds na bugawar agogo jin bugun zuciyar shi yake yana fita kamar da sunan Almamoon, tsabar kaunar da yake mishi (Dalla can mata mazan🙄😠😏) kasa sakewa yayi dan gani yake kamar Baba tasan abinda yake yi akan Almamoon, ya tashi ya bar gurin tare da cewa.
"Baba bari na fita na dawo"
"Allah ya tsare"
Ta faɗa mishi.
***
Abinka da mara lafiya, ganin yadda agwagwan ke wanka haka shima ya tawo da mugun gudu ta dirka a cikin ruwan ji kake famjammm, ya fashe da wata irin dariya yana gurnani kamar Mahaukacin kare, bakin shi yana zubda yawu, sai buge fuskar shi yaƙe alamar kuda na binshi.
"Hrmrmrmnnnnnrrr" masu kula da lafiyar shi, ne suka taru a gurin da hodar da suke shaka mishi.
"Ku nutsu a hankali"
Inji Hurayyah, sadaddewa suka yi tare da shaka mishi hodar ta bayan shi, anan suka yi a rangama daukar shi, kai ciwo makiyin mutum.
"Amma Hurayyah idan Dan Ba'are yazo da?"
"Toh kai da mu bari ya dake mu ai gwara mu shaka mishi tunda naga ai ba laifi bane, kuma idan ba haka muka mishi ba kana ganin zamu sha lafiya ne, gwara mu shaka mishi."

Haka suka dauke shi zuwa dakin shi, aka kwantar dashi, suna kokarin cire mishi kayan Dan Ba'are ya shigo. Ganin halin da suke ciki ya shi musu wani irin banzan kallo, babu shiri suka bar d'akin, tare da nufar waje, suka shi ya kintsa shi sannan ya zauna yana kallon shi.

"Mohammed Insha Allah zaka samu lafiya ina jin haka a jikina, sai dai ta inda lafiyar zata samu ne ban sani ba" ya faɗa tare da rungume hannunsu guri guda. Tausayin shi yake, yasan idan ya samu lafiya bai zama dole ya koma bakin aikin shi ba, tunda ga halin da yake ciki. Koda ya ji sauki sai dai ya nemi wani aikin kawai. Kiran wayar shugaban jami'ar yayi suka yi magana, shafa kan shi yayi yana murmushin jin dadi.
"Nagode"
Ya fada cikin wani irin abu yaji ya tsaya mishi a raina,

Dan haka ya mike tare da nufar waje, ya kalle su dakyau.
"Insha Allah jibi za a kawo wanda zai na kula da lafiyar shi, ku sai ku tsaya akan aikinku,."

"Toh" suka fada lokaci guda, sannan ya juya tare da barin gurin su.

Ko minti biyar ba ayi ba aka kira shi, daukar wayar yayi tare da mannawa a kunnen shi.
"Akan me zaka ce su tsaya akan aiki su? Karka yarda ka kawo min wani mutum da zai kula da lafiyar Mohan domin kome na shi yana hannuna."

Murmushi yayi sannan yace mata.
"Ko Ammi bata da ikon hana ni abinda ya dace akan Mohan balle ke, dan haka ki fita idona na rufe idan na rufe dake mmm" ya kashe wayar yana tsaki, fitowa yayi tare da tara su,

"Wallahi sai na kore ku kuma na kwana lafiya, kunyi na farko kunyi na karshe kar na kuma kama wani dan iska da min tsurku, idan kuma na sami haka"

Nad'e hannun rigar shi yayi tare da kallon su, yana lashe lashe bakin shi, cikin zunzurutun masifa da bala'i. Ya tsani renin hankali. Shi yasa ake ganin kamar baya son mu'amala da mutane kananun magana ne ce ya tsaya, yan iska kawai sai ya hana Hajiya Safiya shigowa gidan da shi take zancen fita yayi tare da danna wani kararrawa, kafin kace kwabo.

Kafatan jami'an tsaron sun halara a filin gidan, haurawa saman wani dakalin yayi yana kallon su.

Kafin yace musu.
"Jibi Insha Allah zan bar garin nan zan koma gurin aikina, kuma jibin zan kawo me Kula da lafiyar Mohan, idan yazo ina bukatar a kula da lafiyar shi! A kula da duk wani abun da zai zo dashi sannan ina kyautatta zaton zai zauna anan ne zai na tafiya makaranta a bashi driven da zai kai shi ya dawo dashi. Ina son kuma a saka ido akan masu zuwa daga Fadar firaminista da sunan duba lafiyar Mohan, kowaye matukar Ba Hajiya Latifah bace ko Daya daga cikin Yaranta ko Mai Girma Shugaban kasa ban yarda a bude kofar gidan ba, idan kuka ga mutum ya matsa zai shigo ku bude mishi wuta. Sannan ku kara saka ido akan masu aikin kicin da sauran bangarorin akwai munafukai. Da fatan zaku bawa Major General Mohan Mamman Nasir Aghali Kariya da Yardan Allah"

Duk suka hada baki da cewa sun amince, zasu yi aiki tsakanin su da Allah tare da bawa shugaban su kariya da yardan Ubangiji. Sanan ya gaya musu duk wanda ya karya dokan shi tabbas shima zai karya kafaffun shi. Dan haka su bi doka da oda. Suka kuma yarda tare da amincewa.

Kafin ya sallame su, ya shiga cikin gidan, yana shiga ya kira su baki ɗaya.
Kallon shi suka yi dan sun fara razana da al'amarin shi. Duk da sun zai bai da dad'i amma kuma basa tsammanin har ya kai yadda suke tsammanin.
" Idan mai aikin yazo zan tambaye shi matukar ya iya girki ba zaku kuma dafa mishi abinci ba" a rude suka d'ago kai suna kallon shi, a ransu kuwa ba karamin kwashe mishi albarka suke ba, ayi mutum da zunzurutun masifar tsiya, kome sai ya sauya musu tsarin su yake, Ashari'a kuwa yasha babu iyaka da Tsinuwar su akan ya sauya musu alkibla....
Please if you read hope me sharing to family and friends😭😭😭 karku manta da komens da bote, ko muje hutun kwana uku 😛😁😜🙄😩
#Mai_Dambu...
[7/14, 1:06 PM] RamlatArManga: *🐂🐂BOROROJI🫀🫀*
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
BOOK ONE
https://www.instagram.com/batool_spices
Fatima Batool enterprise
Yaji
Ginger and garlic
Onion powder
Pepper soup
Curry
Biryani spices
Mixed spices
Indian spices
Arab spices
Chai masala
Baharat blend
Tandoori blend
Thai masala
Garam masala
Provence
Tea spice
Zobo powder
    Gu garzaya Domin samun kayan kamshi na fatima Batool Enterprise. Domin samun yajin suyar na naman layya 😋

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azi_zat

*Gaisuwar ce wannan shafin Aunty Safiya Jos, Ummi Ilham Gombe, Mom Sayeed Kano, Mrs Faruq matar kakana Nagode sosai*

Sai da rai....
BABI NA SHA BIYU.
Da'go kai yayi tare da kallon su, cikin nutsuwa da yanayin shi na cin Uban kowa ya kwana lafiya, yace musu.
"Matukar wanda zai kula da ya iya kome dukkan ku barin gidan nan zaku yi domin ban yarda da fuskar ku ba. Ku b'ace min da gani marasa mutunci"

      Rabil da Hurayyah suka wuce kitchen, Bilal da Moussa suka wuce gurin wanki, Sarah da Nouhu suka wuce bayan dakin da ake ajuye kayan aikin cikin gidan.

Hurayyah da Rabil girki suke, Bilal da Moussa, wankin da guga suke. Sarah da Nouhu sharan gidan suke da goge goge. Kusan idan ya cire Hurayyah itace Mohan ya kawo ta da kanshi sauran kuwa. Daga can fadar gwamnati aka kawo su. Kuma yana kyautatta zaton Hajiya Safiya ce. Ya tsani matar nan kamar me.
      ***
Niamey.

Shige take da fice, tana hango yadda Hajiya Latifah ta harde ana mika mata wasu takardu, zata saka hannu. Murmushi tayi sannan tace.
"Da Sannun zan ruguza ki, tunda nai babban nasara kawar da wanda ya tsaya muku"

       Fitowa tayi cikin shigar Alfarmar ta nufi gurin da Hajiya Latifah take.
"Barka da hutawa ranki shi dade"
Sai da ta b'ata lokaci kamar ba zata amsa ba kafin tace mata.
"Hmm"
Ta cigaba da aikin ta, kamar bata san da tsayuwarta a gurin ba.
"Hmm, dama ranki shi dade akan batun matsalar Mohan"

     Ta faɗa tana kallon yanayin da Hajiya Latifah ta shiga, ganin yadda Jikinta yake rawa yasata sake murmushin mugunta, sannan ta cigaba da cewa.
"Dama naga"
"Kije bana son jin sunan shi tashi ki bar min nan"
Ta daka mata wani irin tsawa, wanda yasata mikewar dole, domin babu karya ta razana. Bayan tabar gurin kan Hajiya Latifah ya shiga sara mata kamar zai rabe biyu.

        Tsaki tayi tare da mik'ewa, ta nufi cikin gidan, koda ta shiga har ta manta kome akan shi. Itama Hajiya Safiyar dadi ya sata bata kuma bin wani abu akan Mohan din, sai dai tana da kudirin jibi Insha Allah zata dira a Maradi ta cirewa dan Ba'are rashin mutuncin da yake kan shi.

       Kuma wallahi ta isa sai ta ganawa Mohan azaba, dan duk cikin Yaran Hajiya Latifah ta tsani Mohan sama da kowannen su,, shi yasa bata yi kasa a gwiwar gurin tsayawa sai da kome ya faru dashi kafin hankalinta ya kwanta. Shima dan Ba'are sabida ba haka kawai yake ba da ta jijjiga shi da karfin ta. Ta kuma nuna mishi Allah daya ne.

***
Washi gari
Kamar ba zan shirya ba, amma sabida irin yadda Malam Ansar yake bina da idanun yasa ni hada kayana, na raba biyu. Na saka rabi a cikin wata jaka, rabi kuma na barshi a dakin Baba Mari, sanan na tsaya tare da cewa.
"Baba idan aikin da sauki zan na zuwa duba ki, Insha Allah."

      "Allah yayi miki albarka, ya kuma kare ki daga sharrin shaidanun mutane da shaidanun Aljanu, karka yi wasa da ambaton Allah a duk inda kike, gurin da zaka shiga haka kawai nake ji a jikina akwai babban Al'amari a gurin. Dan haka a rike Allah babu wasa sallah nafilla, walaha da duk wani sallah bayan sallah farillah, ba ayi da La'asar da magarib, amma ana yin shafa'i da wutiri, karka manta Alhamis da Litinin kayi azumi ka nemi dacewar Ubangiji.."

     Rike hannu na tayi tana kallon fuskana tace min.
"Wallahi nayi mafarkin inda zaka  cike yake da ƙaya masu matukar hatsari, shi yasa na mike da nima maka kariya, Insha Allah zaka yi nasara amma karka manta gaskiya tafi kome tasiri kar manta da karatun Alqur'ani domin itama haske ce s duk inda mutum yaƙe."
Wato matar nan jinta nake kamar ita ta haifi Innata, zunzurutun kulawa. Sannan ta bani addu'o'in.
"Baba zamu tafi makara muke"

"Allah yayi muku albarka" ta faɗa tare da juya mana baya, mu kuma muka fita, ina lura da take taken shi magana yake son min, amma na wani b'ata rai, sai da muka fita daga gidan ya rufe Kofar gidan sannan ya tako har zuwa inda nake, ya bude motar ya shiga. Shiru ne ya gifta tsakanin mu. Kamar ba zai yi magana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login