Showing 21001 words to 24000 words out of 145203 words

Chapter 8 - SAKATARIYA TA COMPLETE

Azizat   

13 Jul 2024

25678

daga office ɗin...


Sana'ar zoɓo da kunun aya kam Farida ba ta fasa ba sai dai ta chanja salo. Duk mai so zai yi booking ne tana zuwa tun kafin ta shiga office za ta bi ta rarraba ta ƙarɓi kuɗinta wani lokaci kuma sai an kusa tashi ta biya ta karɓi kuɗi. Anas na ɗaya daga cikin ma su son zoɓonta kullum sai ya sha gora biyu. Najeeb bai sake ma ta maganar sana'ar da ta ke ba duk da ya san bata dena ba.

Yau wani ƙaton kula ta fito da shi daga keke saboda sana'ar zoɓo da ya ƙarɓe ta. Dan ko gora hamsin ta yi sai ya ƙare.
Tana faman ɗauka sauke da kular Najeeb ya zo wucewa, a lokacin ta sauke ta na ƙoƙarin murza hannunta saboda zafi, ya tsaya yana kallonta. Haka kawai ya ji ta bashi tausayi. Yarinyar nan da garaje ta ke ina ita ina wannan ƙaton abu. Ya wuceta ba tareda ta ganshi ba, yana zuwa bakin ƙofa ya ce da security da ke wajen ya je ya ɗauka ma ta kayan...


Yau ɗan wake ta zo da shi dan haka da su ka je Cafeteria ita da Sister Munibat ta wuce wajen su Anas.

"Yayana ban san ko kanacin ɗanwake ba?"

Anas ya ce " ci kai. Ai duk lokacin da mu ka je gidan Hajiya Mama sai ta sa an yi min"

"To barin zubo ma ka"
Ta je ta zubo ma sa a plate harda dafaffiyar ƙwai akai da ɗan ganyen lettuce da albasa sai ƙamshi ya ke yi.

"Gaskiya na gode sweet sister. Allah ya miki albarka"

Ta yi murmushi ta tafi. Ko kallon inda Najeeb ya ke ba ta yi ba.
Anas ya fara haɗa ɗanwake da shinkafa yana ci yana santi.

"Are you flirting with her?"

Anas ya ɗago da mamaki ya kalli Najeeb.

"Wannan shine dalilin da ya sa yarinyar nan ta ke abinda ta ga dama a office. Because of you"

"Dude are you....are you jealous?"

" im serious Anas stop flirting with her"

Tashi yai ya bar wajen ya bar Anas da baki buɗe.

Idan dai idon sa ya ga dai-dai to tabbas kishi ya gani a idon Najeeb. But why?.... ko dai.....
Ya juya ya kalli Farida da ke ta zuba uwa surutu cikin zuciyar sa ya ce " indai abinda na ke tunani ne to, Farida kin ciri tuta. I wish ke za ki maye gurbin Sabreen a zuciyarsa"...

.....................


Tana ɗaki tana cin abinci taji alert na kuɗi ya shigo ma ta daga wajen aiki. Sai dai tashi ta yi cikin sauri saboda abinda ta gani. Ba abinda aka ce za'a biyata ba kenan, kusan kaso sittin kawai aka biyata cikin albashinta.
Cikin tashin hankali ta fara kiran numbar Najeeb sai dai bai ɗauka ba.

Ta kira numbar Anas shima bai ɗauka ba.
"Lallai ma! Kan Uba. Wallahi ba zai yiwuba na yi uwa ayyukan nan ba dare ba rana ace wannan kuɗin za'a turomin. Ta tashi ta fara shiryawa.

Maijiddah da ta shigo ɗaki ta ce " Anty ina zuwa haka"

"Wajen aiki zan je. Yau Sir Najeeb ya taɓo ni"

"Anty ba yanzu ki ka dawo ba"

"Ke dai bari zamu yi maganar idan na dawo"

A hanya Anas ya kirata akan ta yi haƙuri ɗazu suna meeting ne shiyasa bai ɗau kiran ba.

"Yayana kuna tareda Sir Najeeb ne?"

"Eh tare mu ka yi meeting ɗin amma ni na fito na barshi a office yana ƙarasa wasu ayyuka. Lafiya dai ko?"

"Ba lafiya ba Ya Anas 60% na albashina kawai na gani"

"60% kuma?"

"Eh. Na san Sir Najeeb ne yamin haka, dan haka yau ni da shi, sai ya bani cikaton kuɗina ko yaga bala'i" ta kashe wayar tana huci.

Kamfanin yai tsit saboda an riga an tashi. ID card ta nuna aka bari ta shiga duk da kuwa ma su gadin sun santa. Ba ta wuce ko'ina ba sai office ɗin Sir Najeeb. Ba ya main office ɗin sa dan haka ta je wani ɗaki da ya ke yin ayyukan sa na zane acikin office ɗin. Ta ƙwanƙwasa ƙofar.
Yana tsaka da zane ya ji ana ƙwanƙwasa ƙofa. Who could it be? Dan ya san Anas ya tafi tuntuni.

Na'urar computer da ke gabansa ya danna nan da nan Farida ta bayyana. Yadda ya ganta ya san maganar albashi ne ya kawota. Wajen da ya ke waje ne da bayan shi sai Anas babu wanda ya ke da access na shiga, work place na shi kenan. Anan ya ke duk wani zane-zanen sa. Wajen zagaye ya ke da glass. Glass ɗin daga ciki za ka ga mutum amma daga waje mutum ba zai ga na ciki ba. Kana shigowa ɗakin idan ba ka da katin buɗe ƙofar glass ɗin to ba tayadda zai buɗu...

Tana tsaye ya buɗe ƙofar ya fito.
"Sir Najeeb ban gane manufarka ba. Me na yi aka cire 40% na albashina?"

Yadda ta ke maganar kamar za ta doke shi.

Bai kulata ba ya je ya zauna a kujerar sa.

"Sir Najeeb i demand an explanation"

"Ofcourse Miss Salihu. Ni na cire 40% na albashinki as a compensation for all your irrational behaviours in this company"

"Sir Najeeb idan ma yaren China ka ke gara ka dena dan ni banjin wannan yare. Ka tura min cikaton kuɗina kawai, abinda na sani kenan"

Murmushin yaƙe yai sannan ya ce " next month ma ki dinga take dokokin kamfani and i'll keep on cutting your salary"

"Cabɗi! Wallahi ba ka isa ba"

Tasowa yai ya nufi kanta ta fara ja da baya.
"Mi za ki yi idan na cire? Yau ma hugging ɗina za ki yi? Go ahead and i'll make sure you get what you are looking for"

Ganin ta kai jikin bango ya sa ta haɗiyi miyau.

"Come on hug me. Na san abinda ki ke so kenan, well yau ba Anas ba yayanki, nobody is here just me and you"

"Idan ma giyan wake ka sha. Wallahi na fika hauka. Kkkka matsa min"

Kallonta ya ke yi yadda take fitar da numfashi da sauri-sauri har yanajin bugun kirjinta.

"Scary bitch..."

Buɗe ƙofar da akayi ya sa yai saurin juyawa to his dismay sai ga Joseph biye dashi kuma wasu zaratan maza guda uku.

"What the hell are you doing here Joseph?"


Bindiga su ka fito da shi Farida ta ƙwalla ƙara ta ɓoye a bayan Najeeb jikinta na rawa tana salati.

"If you comply, nobody gets hurt" a cewar Joseph

Najeeb ya ce "Let the girl go"

"Shut up" ɗaya daga cikin guys ɗin ya daka ma sa tsawa

"Tie them both"

Farida na jin haka ta ƙwalla ƙara ta ƙara ƙanƙame Najeeb....



..........................

A yadda ya tsara sai ƙarshen wata idan Aneesa ta zo Lagos zai ma ta bayanin komai sai dai ko a ina Aneesar ta ji labari?.

Yana zaune a office su na waya da gimbiyarsa, Aneesa ta shigo fuuuu.

"You liar, sai yaushe ka ke son sanar da ni? Bayan an ɗaura aure?. You evil son of a bitch"

"Anny minene haka kuma"

"Munafuki, asirinka ya tonu ai. Wato har sadaki ka kai. To barin gaya maka Abdul wannan auren ba zai taɓa yiwuwaba"

"Aneesa kenan. Dama abinda ya taso da ke daga Abujan kenan. To ki sani aure babu fasawa tunda dama na gaya miki ai"

"Abdul Wallahi ba zai yiwuba. Idan ma wasa ka ke gara ka janye, i will never share you with anyone"

"Ina son ki Aneesa amma duk abinda ya faru ke ki ka jawo. Ba ni da ra'ayin mata biyu sai da ki ka zaɓi aikin ki fiye da ni"

"Wallahi sai dai ka zaɓa ko ni ko ita dan ba zan zauna da kishiya ba"

"Its too late Aneesa. Wata biyar da su ka wuce da na gaya miki saƙon Hajiyata what did you say?"

"Haka za ka ce ko. To mu zuba mu gani and i'm taking my kids with me"

"Tunda daga gidan ku ki ka zo da su ba"

Ficewa ta yi daga office ɗin kamar wata zararriya...


............................

Har ƙarfe tara na dare ba Farida ba dalilinta ga numbarta ba ya shiga. Maijiddah ta je ɗakin su Yakubu lokacin shima ya dawo daga hira kenan zai ci abinci.

"Amarya Amarya, ya akayi?"

"Yaya Yakubu Anty Farida ta kira ka ne?"

" Farida kuma. Ai ni tun da mu ka dawo daga wajen aiki rabona da ita"

"Yaya numbarta ba ya shiga kuma ta ce za ta je Kamfani wajen Oganta"

"Sir Najeeb"

"Eh"

"To barin kira Anas na ji"
Sai da ya sake gwada numbar Farida still baya shiga kafin ya kira Anas.
Anas ya sanar ma sa yadda su ka yi da Farida sannan ya ƙara da cewa shima ya yi ta gwada numbar Najeeb amma ba ta shiga.

Yakubu ya ajiye waya ya kalli Maijiddah ya ce " barin je Kamfani in dubata. Ko tana chan dan numbar Sir Najeeb ma ba ta shiga"...


Anas ne ya riga shi isa Kamfanin, lokacin da Yakubu ya iso a wajen motar Najeeb ya tarar da Anas da wasu securities su na magana.

"An ganta kuwa?" Yakubu ya faɗa a kiɗime

Anas ya girgiza kai ya ce " Yaks i think they have been kidnapped"

"What!"....



*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*



*Free page*

0️⃣0️⃣9️⃣


"Wayyo Allah Ummi na. Wayyo Ummi naaaaa" abinda ta farka da shi kenan lokacin da ɗaya daga cikin mutanen da su ka sato su ya watsa musu ruwa.

"Shut up" ya daka ma ta tsawa. Nan kuma ta fashe da kuka tana cewa " dan Allah kar ku kashe ni, ni ɗaya ce a wajen Mahaifina kuma ko jika ban haifa ma sa ba"

Tare aka ɗauresu da Najeeb bayansu na gogan na juna sai dai tun da ya farfaɗo baice ƙala ba.

"Sir Najeeb ka ce su bar ni na tafi. Iyayena talakawa ne, ba su da kuɗin da za su basu, yanzu ma Baffa na cikin bashi yake saboda hidimar biki da yai..." saukar mari taji a fiskarta wanda ba shiri ta fashe da wani matsananci kuka.

"Chachachacha, you talk too much abeg"

Buɗe ƙofar ɗakin aka yi Joseph da sauran su ka shigo.

"Well well well. The Almighty Sir Najeeb, the perfect man. Mr get out of my office" ya sa hannu ya murɗe kunnen Najeeb da ƙarfi.

"I will make sure you suffer before this is over"

"Untie him" ya faɗi yana yiwa Najeeb kallon tsana.

Kunce shi su ka yi ya ce su ma sa tsirara ai Farida na jin haka ta fara bada haƙuri.

Ɗaya daga cikin su wanda ya ke kamar shine Oga ya zuƙa wiwi da ya ke sha ya ce ma sa ɗan uwa ba haka akeyi ba, idan kana so su biya kuɗi to dole 'yan uwan sa su tabbatar yana cikin ƙoshin lafiya.
"Emeka why now?" Joseph ya faɗi cike da takaici

"Bros let me handle it" wanda aka kira da Emeka ya faɗi. Zuwa yai ya cirewa Najeeb takalmansa da agogo yace " so na designer you wear" naushin cikin Najeeb yai wanda sai da Najeeb ya wantsila.
Shi kuwa Joseph zuwa yai ya taka kafar Najeeb. Ba ƙaramin zafi ya ji ba amma haka ya shanye bai nuna ba.
Lokacin da za su tafi Joseph ya tofa wa Najeeb miyau a fiska. Har su ka fita daga ɗakin bai buɗe ido ba saboda tsananin ƙyanƙyamin abinda Joseph ya ma sa.
Ɗankwalin atamfar ta ta ɗan yaga ta zo ta goge ma sa miyau ɗin.
"Wai mi ka yiwa wannan guntun ne? Joseph ko me su ke kiran sa"

Bai buɗe ido ba kuma bai yi magana ba.

"Dalla buɗe idon. Ba na riga na goge miyau ɗin ba"

A hankali ya buɗe rinannun idanunsa ya ɗaura akan na ta. Itama ɗin shi ta ke kallo for some weird reasons sai ta ji ya ba ta tausayi. Wannan fa ɗan gata ne gaba da baya, CEO na babban kamfani amma Joseph ya ma sa wannan walaƙanci.

"Wannan bayan kuɗi da su ke so akwai bita da ƙulli tsakanin ku. Allah ya sa dai kar su kashe mu"

Ta kalli ƙafar da Joseph ya taka yatsun wajen sun yi jaa sun kumbura. Ta kai hannu za ta taɓa ya janye ƙafarsa da sauri.
" kaa! Dan ma zan taimaka ɗin, to ka ci kan ka"
Ta koma chan gefe ta zauna. Yanzu da aka kuncesu ta ɗan ji saƙayau.

"Ni wallahi yunwa na ke ji, ba dan kai ba da yanzu ina gida ina cin abinci. Ni daga mun kai gida lafiya ma ajiye ma ka aiki zan yi. Irin wannan aiki da kasada ba dani ba"

Tana cikin surutu aka buɗe ƙofa, abinci aka kawo mu su, take away guda biyu na shinkafa da satchet water guda biyu. Ko kallon inda abincin ya ke Najeeb bai yi ba. Farida kam jawo abincin ta yi ta fara ci dan Allah na gani ba ta iya juran yunwa. Abincin ba wani yawane da shi ba hakanan nan taste ɗin dai ba laifi da alama daga restaurant su ka ƙarɓo.

"Sir Najeeb ka ci abinci fa, da zafin sa kar yai sanyi"

Tashi yai ya ɗau ruwa ya shiga wani ƙofa da ke cikin ɗakin wanda ya ke tunanin banɗaki ne. Banɗakin ne sai dai gaba ɗaya a ƙazance ya ke da ƙyar ya kama ruwa yai alwala ya fito dan ba ruwa a wajen, famfom baya aiki.

Sai da ta ga ya je gefe ya tada sallah itama ta ankara ba ta yi sallar maghrib da Isha ba, gashi ta shanye ruwanta.
Dole sai taimama ta yi bayan ta leƙa banɗakin ta ga ba ruwa.

Tana zaune ta jingina da bango ta fara gyangyaɗi ƙarshe baccin wahala ya saceta....


..........................

Kafin ƙarfe goma na dare iyalen Alhaji Adam Jibo sun samu mummunan labarin rashin Najeeb da Sakatariyar sa. Abinda ya ɗaure mu su kai har lokacin ba a kira su gameda ransom ba. Bacci kam ƙauracewa iyalen yai bama kamar baby da ta dinga kuka wiwi da ƙyar Mom ta shawo kan ta ta yi shiru.


Gidan Baffa Musa ma dai hankulansu a tashe ya ke. Ba ma kamar Baffa Musa wanda ya ke gani kamar sakacin sa ne ya sa Farida ta faɗa wannan hali. Yadda Baffa ya hana a sanar da Ummi amma hakan bai yiwuba dan kafin yai maganar ma tuni Anty Hanne ta kirata ta sanar ma ta an sace Farida. Hankalin mutanen Jos ya tashi a wannan dare, a daren Ummi ta so ta zo amma Baba da Nanna su ka hanata, su ka ce ba abinda za ta yiwa Farida sai addu'a ta bari idan gari ya washe sai ta je.

Haka aka wayi gari gidajen biyu ba kwanciyar hankali. Ƙarfe tara na safe aka kira Alhaji Adam Jibo bayan an tura ma sa hoton Najeeb da Farida ɗaure. Miliyan hamsin su ke buƙata cikin awa ashirin da huɗu ko kuma su rasa su gaba ɗaya.

Anas ya sanar da Yakubu cewa kidnappers ɗin sun nemi ransom na 50million. Ya kuma kwantar ma su da hankali akan za a kuɓutar da su.

Baffa Musa da Yakubu su ka nufi gidan su Najeeb. Sun samu su Alhaji Adam su na meeting da wasu special police kan al'amarin sai da su ka gama sannan Dad ya saurare su.

"Alhaji dama maganan kuɗin nan ne. Ni dai a wajena idan na shiga na fita za a samu miliyan uku sai dai kaga ko rabin abinda su ke buƙata ba a kai ba"

"Alhaji Musa ka kwantar da hankalinka Insha Allahu komai zai zo da sauƙi. Maganar kuɗi kuma Alhamdulillah an fara arranging na su. Kar ka damu"


.......................


Da safe Emeka ya shigo ɗakin ya fara faɗa harda marin Najeeb wai 'yan uwansa ba sa son shi suna buƙatar 48hrs su haɗa 50million.

"I thought your parents are super rich. They better not play games with me"...

Emeka cousin ɗin Joseph ne, ya jima yana fashi da makami kafin daga baya ya koma harkan kidnapping. A Kaduna ya ke operation ɗinsa sai dai wata ɗaya da ya wuce Joseph ya kira shi akan yanaso ya kidnapping Najeeb saboda ya ɗau fansar abinda ya ma sa. Wannan ya sa ya zo Kano su ka fara tsare-tsaren yadda komai zai tafi. Da ke Joseph yai aiki a Najeeb constructions hakan ya bashi daman sanin hanyoyin da za su aiwatar da ƙudirin su.

Da safe ba a basu abinci ba haka da rana, gaba ɗaya Farida ta galabaita. Tana chan ta cure gefe guda ta yi kukan ta yi surutun har ta gaji. Najeeb kam ko ehem bai ce ma ta ba.

Buɗe ƙofar ɗakin aka yi, ɗaya daga cikin ma su tsaresu ya shigo ɗauke da bindiga. Zuwa yai ya jawo Farida da ƙarfi, Najeeb ya tashi zai yi kan sa. Ya nuna ma sa bindiga tareda cewa "sit"

Farida ganin anyi hanyar waje da ita ta fara cewa Najeeb ya taimaketa.

"Dont hurt her" Najeeb ya faɗi da kakkausar murya

Wani ɗakin ya shiga da Farida bayan ya kulle Najeeb a ɗakin da su ke da farko.

Ganin ya yo kanta ya sa ta ƙwalla ƙara tana kiran Sir Najeeb da Umminta.
Guje-guje su ka fara yi a ɗakin wanda ya ke cike da tarkacen kayan maye. Cak ta tsaya lokacin da ƙafarta ya taka wata fashashshiyar kwalba. Hakan ya bawa mutumin damar kamata ya kwantar da ita da ƙarfi, sai ihu ta ke ta na ƙoƙarin tureshi amma ta kasa. Ya kama hannayenta da hannunsa ɗaya, ɗaya hannun kuma yana ƙoƙarin zuge zip ɗin wandonsa.
Wani razannannen ƙara ta ƙwala wanda gaba ɗaya gidan sai da ya ɗauka.

Emeka da wasu biyu su ka yo ɗakin da su ka ji ƙaran da gudu. Ganin Larry na shirin afkawa Farida ya sa Emeka ya ture Larry tareda kwaɗa ma sa mari.

"Are you crazy?"

Larry ya ce" the girl too hot Oga. I feel...."

"Will you shut up. You want to ruin my business abi"

Ce wa ɗayan yai ya maida Farida ɗakin da Najeeb ya ke.
Da ɗingishi ta shigo ɗakin saboda har lokacin kwalbar da ta caketa na ƙafar.

Tunda aka fita da Farida hankalinsa ya tashi yasan ba kasheta za'ayiba amma ba makawa sai sun yi raping ɗinta. Lokacin da ya ji ƙaran da ta yi sandarewa yai a wajen jikinsa ya fara ƙyarma yana ayyana abinda zai yiwa Joseph da crew ɗin sa idan sun fita anan. Ganin yadda aka shigo da ita ya sa yai kan ta da sauri. For the first time tun jiya da aka kawo su ya ma ta magana.
"Miss Salihu are you Ok. Mi su ka miki?"

Shiga jikinsa ta yi tana kuka jikinta na rawa. Ta gama tsorata dan ta sadakar Larry

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login